GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️ COMPLETE - (2024)

GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️ COMPLETE
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
_______
*DANDANO🥰*
*1*
Cikin tsananin gajiya da ishirwa nake tafiya burina kawai na isa gida na samu na watsa ruwa a jikina na kwanta na hutawa rayuwata. gabana ne ya fad’i! lokacin dana tuna d’an iskan yaron nan yana gari nasan da wuya ya barni na sha ruwa a gidan Khalid mugun fitinan nan yaro ne wallahi……..Daf da zan shiga layin namu motar Alhaji Nura take kokarin fitowa d’auke kaina nayi na bashi hanya domin ya wuce! girgiza kaina nayi ganin yayi parking din motar ya tsaya cikin raina nace”Ai dama na san sai ya tsaya, galashin motar ya sauke muka had’a ido fuskata na saki nace”Alhaji barka da rana.” Cikin kulawa yace.”Barka dai Sa’ida ya aiki.”? Nace” Aiki Alhamdullihi.” kokarin wuce wa nake ya dakatar dani da fad’in “Sa’ida ina al’kawarinmu.”? Gefan hijab d’ina nasa na goge gumin fuskata nace” Alhaji al’kawari yana nan inaso na ware ranakun da zan fara gudanar da aikin naka.”

Yace.”Me zai hana ki ware ranaku biyu a cikin sati wato alhamis da juma’a tunda a ranakun yaran basa zuwa isilamiyya in yaso idan sun dawo daga boko misalin biyu ko uku sai ki dinga shiga kina musu lesson d’in.”

Shuru nai ina nazarin maganarsa nace”Shikkenan Alhaji zan duba maganarka insha Allahu.” Yace.”To godiya nake gimbiya duk shawarar da kika yanke sai ki kira waya ta ki sanar dani.”

Nace”To shikkenan babu damuwa.” Har nayi yunkurin barin gurin ya dakatar dani! cikin k’osawa na tsaya amma ban nuna masa ba, kudi ya miko min kusan dubu biyar…..murmushi nai nace”Kasan ba zan kar’ba Alhaji nagode.” da sauri na bar gurin ina mamakin yawan kyautar da yake min duk had’uwar da zamuyi sai ya dauki kudi ya bani bayan uwar hidimar da yake mana a gida……..Tun kafin na karasa na hangoshi dogare a bakin kofar gidan namu yana sanye da k’ananun kaya 3qutar da singlet wacce ta matse shi gabad’aya suffarsa ta mazantaka ta bayyana Gabana ya yanke ya fad’i! duk sanda zan ganshi a haka hankalina yakan tashi ni kaina ina mamakin halin da nake shiga wannan dalilin yasa idan yana gida bana sakewa sosai mutukar zai dinga shige da fice a gidan babu sutturar arziki a jikinsa.

Fuska a murtuke na ‘karaso….”Malami Bani hanya na wuce.” babu wasa nayi maganar.

Hanyar ya sake tarewa yana kallona da ‘batacciyar fuska yace.”Aunty Sa’ida me ya tsayar dake a gurin wancan mutumin.”? wani irin kallo na watsa masa nace”Ina ruwanka da shiga sabgar da bata shafeka ba, dan Allah ni bani guri na wuce na gaji.”

Hanya ya matsa min naja tsaki had’e da kokarin ra’bashi na wuce kawai naji ya matseni a jikin kofar fuskokinmu suka hade numfashin mu na had’uwa.

Cikin fad’uwar gaba na tureshi! nayi saurin fad’awa soron ina addua akan Allah yasa wani bai ganmu ba! hannuna ya rike yana marairaice fuska yace.”Kina so zuciyata ta buga ko na hanaki kula wancan Alhaji kin raina magana ta ko.” Cikin takaici nake kallonsa a fusace! nace”Wallahi Khalid ranka zai ‘baci! mutukar baka fita harkata ba shin wai ni sa’arka ce da zaka dinga yi min iskanci.”

Zuba min idonsa yayi fuskarsa a had’e yace.”Ni ina sonki Aunty Sa’ida kuma kin san Allah baki da miji sai ni da kika raina zaki gane baki da wayo.”
Yana gama maganarsa ya fita, na dinga kallon bakin kofar ina mamakin maganarsa, bani da miji sai shi! Lallai Khalid baida hankali da tunani. tsaki naja na shiga gidan raina duk babu dadi.

“Ummatu sannu da aiki.” ciki-ciki ta amsa min ban damu da yanda ta amsa maganata ba kawai na shige ciki gidan, Gwaggo kakarmu na samu tana kad’in lagwani! hijab na cire na nemi guri na kwanta ina mayar da numfashi.

Kallona tayi tana cigaba da kad’in ta tace” Yau kin dad’e baki dawo ba Sa’ida anya baki fara yawace yawace ba ni wallahi wannan aikin naki ban yardar dashi ba.”

Cikin mamaki na kalleta, tace”Ai da gaskiyata wane irin aiki ne wannan da za’a fita tun karfe takwas ba za’a dawo ba sai karfe uku ko biyu haba jama’a.”

Murya na rawa Nace”Gwaggo mai kike nufi dani.”? ba tare da wata damuwa ba tace”Abinda nake nufi ai kin san shi.”

“Kina nufin ina yawon karuwanci kenan.”? da sauri tace.” Ooh! ni kada ki daura min jakar tsaba ba haka nake nufi ba.” hawaye na zuba nace”To meye na cewa baki yarda da aikina ba wato kema kin fara daukar magana aikaina ko.”

Shuru tayi tana cigaba da kad’in ta, komawa nayi na kwanta hawaye wani nabin wani! nace”Wato saboda ‘kasa ta rufe fuskar mahaifina shiyasa kike nema ki d’ora min kazafin na zina kamar bake kika haifi ubana ba.”

“Kinga Sa’ida kada kisa hawan jinina ya tashi da wannan magana taki ta isheni haka aiki kije kiyi tayi tunda ba zakiyi aure ba sharrin zina da bin maza dole jama’ar gari suyi miki.”

Da sauri na mike Nace”Gwaggo na gaji zan tattara kayana na koma gurin mahaifiyata tunda keda kika haifi ubana kin kasa yi min uziri a rayuwa ta ni ba ni zan dauki kaina nakai gidan aure ba sai ranar da Allah ya nufa to tunda kun kasa fahimta zan bar muku gidanku.” Saukowa nayi na fara hada kayana,

Kayan kad’in ta ajiye a gefe tace”Ke Sa’ida bana son shashanci da rashin tunani babu inda zakije kinji na fada miki maganar aure kuma ba zan fasa yi miki ba har sai kin tsayar da miji zanja bakina nai shuru to kaji.”

Jakar kayana na dauka na kama hanyar fita, sai ta fashe da kuka da fad’in” Au! takani zakiyi ki wuce to bari Babanku Iro ya shigo zan fada masa rashin mutuncin da kike min.” Saboda nasan banyi abinda take zargina dashi ba yasa ko sauraranta banyi ba na fita daga dakin da kayana a hannu, haba jamaa na gaji da masifar Gwaggo.

Turus! nayi ganin Baba Iro a tsaye suna magana da matarsa! ya kalleni yana kokarin yayi magana! Gwaggo ta fito daga daki tana kuka da fyatar majina da sauri ya karaso gurin yana fadin”Gwaggo lafiya kukan me kike.”? Ta ‘kara rurucewa da kuka da fadin”Gatanan saboda nai mata maganar aure shine ta hada kayanta wai gurin uwarta zata koma shine har tana sa kafarta tana taka ni ta wuce.”
Da sauri na kalleta ina mamakin sharrin ta gwaggo tsohuwa mai sharrin tsiya.

Baba Iro murmushi yayi inda sabo ya saba raba fad’a tsakanin mahaifiyar tasa da ‘Yar d’an uwansa Yace.”Haba Sa’ida in da sabo ai yaci ace kin saba da halin Gwaggo me yasa ba zakiyi hakuri ba yanzu da kika had’a kayanki ina kike nufin zuwa.” Gwaggo da sauri tace” Zataje can gurin Uwarta ne.” Cikin k’unci nace” Baba Iro wai kamar gwaggo itace take min k’azafi to meye amfanin zamana da ita.”

“Aa ni kada kiyi min sharri Sa’ida daka fada miki gaskiya sai kice nayi miki sharri.” Baba Iro yace.”Gwaggo maganar ta ‘kare haka.” Tace.”To kace mata kada ta tafi dan taurin kaine da ita.”

Baba Iro yasa hannu yana kokarin kar’bar jakar hannuna, nace”Baba dan Allah ka kyaleni na tafi wallahi na gaji da rashin hakurin gwaggo ka gafarce ni idan maganata ta ‘bata maka rai.”

Yana ‘kokarin magana ya shigo gidan hannunsa ri’ke da leda indomee yaje ya siyo, babu walwala a fuskarsa yace.”Me yake faruwa ne naga duk kunyi cirko-cirko a tsaye.”

Da sauri gwaggo tace”Yawwa d’a nagari ka ganta nan wai barin gida zatayi saboda nai mata maganar aure.” wani irin kallo yayi min kafin ya kalli jakar kayana dake hannun mahaifinsa, cikin yanayin takunsa ya karaso inda muke jakar kayan ya kar’ba hannun mahaifin nasa ba tare da yace wani abu ba ya shige dakin Gwaggo da jakar gwaggo bayansa tabi tana surutai!

Baba Iro ya kalleni a nutse yace.”Sa’ida kiyi hakuri kinji ko gwaggo tun kafin ta tsufa take da rikici ki fahimci halinta sai ki zauna lafiya kada wani sa’bani ya sake shiga tsakaninki da ita kice zaki bar gida nan shine tushenki, sannan kuma inaso ki bawa Alhaji Nura dama ya turo da maganar aure kamar yanda ya nuna alama.

Nace”Kawu babu wata maganar aure data ta’ba shiga tsakanina da Alhaji Nura kawai muna gaisawar mutunci dashi ne.” Cike da mamaki yace.”Sa’ida babu maganar aure data ta’ba shiga tsakanin ki da Alhaji Nura amma yake mana hidima a gida.” murmushin takaici nayi nace.”Wallahi Kawu babu maganar aure a tsakanina dashi.” girgiza kansa ya shigayi yana mamakin maganar, yace.”Shikkenan to tunda kince haka dukkaninmu zamu cigaba dayi miki addua akan Allah ya baki miji nagari.” a cikin zuciyata na amsa da ameen. gurin ya bari nima a sanyaye na d’aga labulan dakin Gwaggo na shiga, abinda naji suna tattaunawa yasa gabana fad’uwa….

*Masoya ayi min sharing A gruops👏🏻*

*IDAN KINA BUKATA KARANTA LITTAFIN NAN #400 NE NORMAL VIP GRUOP #600 ZA’A TURA KUDIN TA WANNAN ACCOUNT DIN…..0542382124….BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATIN WAYA ZAKI TURO SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
*2*
“Haba ‘Da nagari ai idan da gaske kake wallahi ni zan baka goyon baya kaga sai ayi towo na maina dama hausawa na cewa gida bai koshi ba ai ba za’a kaiwa dawa ba insha Allahu Sa’ida matarka c…..Shigowa ta dakin ya hanata k’arasa maganar gabad’aya ita dashi suka bini da kallo, ni kam jiri ne naji yana nema ya kayar dani a gurin dan tsaf na fahimci akan abinda suke tattaunawa Khalid yayi masifar raina ni da har yake iya bud’ar baki ya furta min kalmar so ina a matsayin yayarsa wacce ta girme masa nesa ba kusa ba na rasa wane irin tsaurin ido ne da yaron a matsayina da tsayin shekaruna sai nake ganin bai cancanta ya iya kallon tsabar idona yazo min da wata banzar maganarsa ba, Khalid da wayo na da shekaruna yayi girman jikin da yake tunk’aho dashi kuruciyarsa kaf a gaban idona yayi ta amma yau wai an wayi gari ni yake tare wa hanya yana cewa yana sona.

Kwanciya nayi ba tare dana cire hijabin jikina ba kawai na dinga binsu da kallo ina jin tsantsar takaici a cikin zuciyata ni kam ko zan rasa miji a gidan duniya banga abin aure a jikin wannan mara mutuncin yaron ba……..Tun sanda na kwanta a gadon yake min wani d’an iskan kallo irin na manufarci a hasale! nace”Wallahi idan baka daina yi min wannan d’an iskan kallon ba sai ranka ya ‘baci shashashan yaro mara kunyar banza da wofi.”

‘Bata fuskarsa yayi dan har sai da fatar saman goshinsa ta tattare haka yake tun yana yaro idan ransa ya ‘baci sai goshinsa ya tattare ya watsa min kallon banza had’e da girgiza kansa…….Yana kokarin yin magana ta rigashi da fadin” Ke Sa’ida meye kuma na kiransa shashasha ina laifin wanda zai tallafe ki ni wallahi naji dadin maganar da yazo min da ita duk girmanki da shekarunki ba zaki gagareshi ba dan mace komai girmanta bata fin karfin namiji.”

Tsaki! naja ba tare da nace komai ba na juya musu baya….’Kawataccen sajan fuskarsa ya shafa idonsa ‘kur! a mazaunanta da yake bala’in ‘kwa-‘kwa! duk da da hijabi a jikinta hakan bai hanashi ganin tudunsu ba, ya dinga jin wata lafiyayyar sha’awa na taso masa, a sanyaye ya kalli Kakar tasu yace.”Gwaggo ga indomee na nan ki dafa min zanje na dawo.” da sauri tace”To d’a nagari bari na kunna risho ai ina da kalanzir a ciki.” Fita yayi daga dakin yana shafa sumar kansa.

Sama-sama nake jin surutan ta kafin bacci mai nauyi yayi gaba dani……Can cikin baccin naji maganarsa sama-sama! “Haba gwaggo kefe ba’a abin arziki dake yanzu dan Allah haka ake dafa Indomee duba kin zabga mata ruwa sai iyo take a ciki kawai kinsa nai asarar kudina.” Zaune na mike nai saurin cire hijabin jikina jin yanda ya jike da gumi! ina kallonsa yasa hannu yana sosa kansa idonsa kur! a kirjina. girgiza kaina kawai nayi na fara yunk’urin mikewa……Tace.”Sa’ida duba dan Allah wai duk wannan gwanintar da nayi masa ban birgeshi ba cewa yake banyi daidai ba.”

Tukunyar indomee din na kalla da sauri na dauke kaina jin dariya na nema ta sub’ce min indomee guda uku amma ta cika tukunya da ruwa indomeen tayi tsululu duk ta narke a ciki………Yace.” gwaggo bafa zanyi asarar kudina ba ki cinye wannan indomee ki bani dari ukuna ba.” da sauri tace .” Wallahi baka isa ba ba zanci kayan atini ba hakan nan zaka daure kaci idan kuma ba hakaba Sa’ida ta baka wata indomee tunda tana da ita in yaso sai ka kaiwa babarka ta dafa maka tunda ni ban iya ba.”

Ta’be bakinsa yayi yace.”Sai dai na kwana da yunwa akan na kar’bi abunta ni ba shashashan namiji bane kamar yanda take kira na nafi karfin ta ciyar dani sai dai ni na ciyar da ita.”

Gwaggo sakin baki tai tana kallonsa sai kuma tayi dariya da Fadin”Khalid jarumi a gida da wajan ya’ki ka burgeni kwarai da gaske yanzu dai kayi hakuri akan ‘barnar da nayi maka.” Girgiza kansa yayi yace.”Bafa zan hakura ba bari ma ki gani.” da sauri ya fara lalaben inda take ajiye Pose d’inta….
Da sauri ta ri’ke gefan rigarsa “Aa Khalid kada ka daukar min kudi wallahi zanyi maka rashin mutunci idan ka daukar kwabo a cikin jakata…..Fita nai daga dakin na barsu suna bugawa dama inda sabo sun saba idan ‘yan abin arzikin na kusa suyi ta mutunci idan kuma ‘yan tsiyar na kusa suyi ta bugawa, Gwaggo san kudin tsiya ne da ita duk neman da take ba zata ci a cikinta ba sai tai ta tara kudin tana ‘boyewa a cewarta sai auran Sa’ida ya tashi sai tayi mata kayan daki da kudin……Pose din ya bude yaga kudi dan’kam ‘yan dubu dubu duk sunfi yawa, yace.” Lallai tsohuwar nan kudi ne dake duba dan Allah Jakarki kamar ta matar alhaji.”

Tana kokarin fizge jakar tace”Khalid wannan kudin da kagani ba nawa bane kada ka dauki ko kwabo a ciki.” Murmushi yayi yace.”Haba gwaggo ina ganin kudi ki hanani kin san Allah sai na dauka.” dubu daya ya zara yasa a aljihunsa ya mika mata jakarta, aikuwa ta dinga yi masa mita tana surutai dariya yayi ya kama hanyar fita daga dakin da fadin”Ki cinye indomee da kika dafa ni kuma anjima zanje tevur din mai shayi.” Tace.”Kaji dai dashi saboda kai zan sanjawa jakata guri haka kawai ba zaka zo kana daukar min kudi ba.”

Ni dai Ina alwala ina dariya a cikin raina gwaggo san kudi Khalid son kudi koda yake dole Khalid yaso kudi tunda dan makaranta ne yanzu haka yana daf da kammala karatunsa a jami’ar Bayero dake jahar kano yana zuwa gida duk bayan wata guda yayi hutu na kwana biyu ya koma makarana..

‘Dakin na shiga na sameta tana ta surutai uffan bance mata ba dan har yanxu haushinta nake ji akan irin abubuwan da take min, na gyara dadduma a nutse na fara kokarin tayar da sallah, tace”Sa’ida dan Allah ungo wannan jakar tawa ki ‘boye min Khalid ya gane inda nake ajiyeta nasan kuma shikkenan kafin ya tafi sai ya tatike ni.”

Ba tare dana kalleta ba nace”Ki ajiyeta nan na idar da sallah.” tace”To ‘yar albarka, tukunyar indomeen da sauke daga kan risho tana fad’in “Waye zai ci wannan ai ko almajiri ba zan bawa ba zubar dashi zanyi dan ni banga abinso a wannan abincin ba…..har na idar da sallah gwaggo bata fasa surutai ba nace” Yau me aka girka a gidan.”

Ta’be bakinta tayi ‘kasa-‘kasa tace”Kin san halin matar gidan da jarabar son d’anwake shi tayi masifaffiyar mata kawai na haifi d’ana amma tafi ni iko dashi dama nasan Rabi tana bin malamai akan Ibrahim.”

Cikin mamaki na kalleta halin gwaggo sai ita surukar ta ma bata kyale ba kullum cikin zaginta take amma ba tayi a gaban idonta sai a bayan idonta dan itama Ummatu bata daukar raini mara mutuncin kanta ce nace”Gwaggo dan Allah ki daina wannan halin ki zauna lafiya da kowa yanzu meye amfanin zagin Ummatu har kina cewa tana asiri.”

Baki ta rike tana kallon hanya tace.”Ke! Sa’ida maganar ta isa haka kada ki d’aga murya taji amma ni tuntuni Uwale ta tabbatar min da cewa Ummatu ba’a zaune take ba tana yawace-yawacan malamai wai shin bakya ganin ko kara ta ajiye babanku baya iya tsallakawa gashi muma ta daure mana baki dik abinda tayi a gidan shine daidai sannan kice nai mata sharri.”

Nace”Gwaggo ki rabu da Uwale munaf*cka ce wallahi tana so ta had’a ki rigima da surukar ki ita kuma ta zauna lafiya da tata idan ba hakaba meye na cewa Ummatu na bin malam……bakina ta rufe tana zazzare ido irin na rashin gaskiya tace.”Haba Sa’ida nace dake ki daina kiran sunanta kada taji haba jama’a yarinya ba’a sirri da ita mtssw maganar a barta haka.”

Murmushi kawai nayi na mike tsaye ina ninke dadduma, ta mika min pose din nata da fad’in “Kar’bi ki adana min kada ya shigo ya sake daukar min kudi.” karba nayi na bude gurin da nake ajiye tufafina nasa key na kulle……….Da yake idan mun dauki albashi duk abinda nake bukata naci da sha dana d’aurawa ina siyan abina na ajiye duk ranar da akayi abinda bana ra’ayi sai nayi girkina naci na koshi, fita nayi tsakar gida na dauko doya a kicin na zauna tsakar gidan ina feraye wa.

Fitowa tayi daga dakin da buta a hannunta Gwaggo duk rintsi bata bari yara suyi mata wasa da butar alwalarta kullum butar ta cike take da ruwa Macace mai tsafta da kula da ibadah dama dan adam tara yake bai cika goma ba, ganin ina feraye doya yasa ta washe baki da fad’in “A lallai kice yau dadi zamu ci a gidan.” Murmushi nai ina kallonta gwaggo akwai kwadayi amma bata yarda ta fitar da kudinta ta siyi abinda take so ba.

Nace”Eh lallai doya da kwai zan soya nayi miyar alayyahu saboda haka ke zaki bayar da kudin ‘kwai dan banda kudi.” shuru tayi tana kallona dariya ta kusa ta su’bce min.

Tace.” Inji dai guda biyu zai isa.” Nace”Haba gwaggo a wannan uwar doyar za’a sa ‘kwai biyu guda biyar zaki siya.” tace”Haba Sa’ida ‘kwai biyar nawa kenan.”? kai tsaye nace”Dari uku da hamsin.” shuru tayi tana nazari kafin ta girgiza kanta tace”Bari dai nai sallah muyi maganar haba Jama’a yanda rayuwa nan tayi wahala kice ‘kwai biyar ina laifi biyu ko uku.”

Bin ta nayi da kallo ina k’unshe dariya gwaggo kenan mai kwad’ayin tsiya…….Hayaniyarsu naji yo daga waje kafin nayi wani yun’kuri sun shigo gidan su uku, babu walwala na daga kaina ina kallonsu su biyu suna sanye da kayan ‘kwallo (ball) mayar da kaina kasa nayi na cigaba da abinda nake naji yace.”Salim ku jira ni nasa kayana na fito.” Suka ce okey kayi sauri dan Allah.” cikin zuciyata nace “Aikin kenan.” ” Aunty Sa’ida barka da Yamma.” a nutse nace” Barka Salim ya kuke.” ya d’an sosa kansa yana mirmushi yace “Lafiya aunty muna fatan kina lafiya.” ” Lafiya Kalau nake.” shuru gurin yay na minti biyu na dago kaina kawai sai naga sun zuba min ido! cikin ‘bacin rai nace”Salim kaima ka fara zama mara kunya ko.”? da sauri yace.”Aunty mai ya faru.”? girgiza kaina nayi nace”Kuje waje gashinan fitowa daga yau kada ku sake shigowa gidan nan tunda duk kun zama baligai.”

Wannan magana da tayi a kunnasa ya karaso gurin yana mata kallon daya saba “Akan me zaki hanasu shigowa gida abokaina ne na ‘kuruciya kin sansu kin san iyayensu kuma iyakacinsu nan bakin ‘kofa ko wani yayi miki abinda bai kamata ba.”

Nace”Khalid na hanasu shigowa gidan nan saboda bai kamata ba su tsaya a waje ka fito ka samesu.” Girgiza kansa yayi yace.” Keda Gwaggo babu nauyin auran kowa a kanku meye dan abokaina sun shigo kike fita kina yawo a titi gardawa na kallonki a ofis d’inku na malaman makaranta akwai baligan da suka ci uwar abokaina a kuyanci kike mu’amula dasu baki damu ba sai dan kawai abokaina sun shigo gida kice su daina shigowa ba zai yiwu ba.”

“Khalid ni kakewa rashin kunya.”? ba tare daya kulani ba yace.” Salim ku muje dan Allah.” gaba yayi suka rufa masa baya, girgiza kaina nayi aikuwa zan samu Baba Iro da maganar dole ya tsawatar musu akan su daina shigowa mutane gida kai tsaye………….
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*3*
Motsin fitowarta daga band’aki yasa nai saurin kallon gurin, asuwakin ta dake kan taga (window) ta dauka tana gyarawa tace”Surutun me nake ji ne ina bandaki naji kamar muryar Khalid kuna sa’insa.” shuru nayi mata saboda nasan ko na fada mata dalili bai zama lallai ta bani gaskiya ba, zama tayi kan kujera ‘yar tsuguno tana kokarin sanya asuwakin a bakinta tace.”Sa’ida in dai akace wannan namiji ne to komai ‘kan’kantarsa jagora ne idan kina hantarar Khalid wani sa’in haushi kike bani dan duk ‘kan’kantarsa da kika raina watarana shine zai jagorance ki.” Kallonta nayi ina mamakin maganarta “A’ina Khalid din zai jagorance ni gwaggo dan Allah idan zaki fad’i magana ki dinga tsayawa kina tunani kafin ki fad’a yaro ‘kan’kani kina maganar zai jagorance ni Khalid mai ya sani a rayuwa.”?

Tana goge bakinta da asuwakin tace”Oho! ni dai na fad’a miki gaskiya ki daina raina Khalid da ‘kan’kantar shekarunsa komai girmanki ba gagararsa zakiyi ba.” Cike da bacin rai nake kallonta, ta d’auraye asuwakin ta ajiyeshi a gefe cikin nutsuwa ta fara d’aura alwala.

Kaina na girgiza ina jin tamkar zuciyata ta tsage saboda ‘bacin rai gwaggo ta iya kuntukawa mutum abin haushi tayi kamar ba tayi ba, tabbas da wata ko wani ne yayi min wannan banzar magana wallahi sai nayi masa rashin mutumci amma da yake itace babu yanda na iya da ita dole nayi hakuri dan idan nace zanyi magana zata iya yanko wata maganar da zata tarwatsa min zuciya amma idan ba haka ba me zanyi da Khalid bayan manyan mazan dake sona a waje.

Sai da na daidaici cewa ta idar da sallahr na shiga dakin, tana zaune kan dadduma cikin hijabi da carbi a hannunta tana ja, ka’ida ne dama idan ta idar da sallar la’asar sai tayi zaman lazimi nace” Zan dauki kudin ‘kwan a Pose d’inki.”

Kanta kawai ta d’aga min na bude sif din na dauko pose din nata na zuge! gudar dari biyar na dauka na mayar da sif din na rufe…… fita nayi domin na samu yaron aike cikin ikon Allah na hango almajirin gidan Alhaji Nura ni’ki-ni’ki da kayan miya a hannunsa, da sauri nace”Sule dan Allah siyo min ‘kwai kantin Dauda.” da sauri yace.”To aunty Sa’ida.” kudin ya kar’ba ya tafi na juya da sauri na koma cikin gidan, Ummatu na samu ta fito daga gurinta tana d’auraye kwanuka. sannu nayi mata ta amsa ciki-ciki. wucewa nayi ciki ina girgiza kaina na rasa abinda na tsarewa Matar kwata-kwata bata kaunata duk abinda takeyi min a gidan na ganin ido ne.

Har yanzu Lazimin take sai kawai na shiga kwashe kayan wanke-wanken dake dakin na kaisu bakin rijiya na ajiye,

Wani irin kallo naga tana bina dashi kafin ta shiga bin kayan wanke-wanken da kallo tace”Sa’ida dan wulakanta abinci shine kika fito da abinci kika zuba masa ruwa idan bakwaci ai sai ku bawa almajirai shima wanda yake kawowa yana shan wahala kafin ya samo ya kawo amma na lura daka ke har Gwaggon bakwa tausaya masa.”

Jikina a sanyaye nace”Wallahi na manta ban duba ba na zuba ruwa akai kin san ni bana cin d’anwake shiyasa to ban san abinda ya hana Gwaggo cin nata ba.”

Da sauri tace”To yaya kuwa za’ayi taci bayan taga kina feraye doya ai ba zataci ba ni banta’ba ganin kwad’ayayyiyar mata irin wannan ba.”

Kallonta nayi ina mamakin maganarta tsaki taja ta cigaba da aikinta, Gwaggo ta bankad’a labulen d’akinta ta fito tana fad’in” Surutan me nakeji ne nifa bana san husuma a gida.” Ummatu aikinta ta cigaba dayi bata tanka mata ba nace.”Gwaggo babu wata husuma da zata faru ki koma d’aki.

Tace.”Ummatu naji kamar kina maganar d’anwake ko.”? Tace.”Eh hakane Gwaggo Sa’ida ta fito dashi naga ko d’aya baku ci ba shine nake mamakin hakan ai da kun san ba zakuci ba sai kuyi min magana na rage garin.”

Tace.”Au!! Sai na fada miki ? Rabi tuntuni fa kin san ni D’anwake bai dame ni ba me zai sanya ki dimanci yi mana shi a gida.” Da sauri tace.”To gwaggo shi aka bani akace na sarrafa shi Maigidan daya kawo shi zakiyi wa wannan maganar.” Gwaggo bakinta ta ri’ke tana jijjiga kanta

Ganin al’amarin na nema ya girmama yasa na shiga basu hakuri….Ummatu kwanukan ta ta dauka ta shige gurinta, Gwaggo ta zungura mata bakinta tanai mata yen-yen! da hannu. Dariya ce ta kusa ta su’bce min ta ri’ke hannuna ‘kasa-‘kasa tace”Rabu da ita Sa’ida ‘bakin ciki takeyi ganin kin yanka doya zaki soya tunda ta fito da hassadarta a fili ko d’and’ane kada ki bata mu cinye kayanmu.” Tsabar dariyar dake cina ta hanani bude baki nai mata magana da sauri na tsuguna domin wanke kwanukan. ta cigaba da magana ‘kasa-‘kasa! nace “Dan girman Allah gwaggo ki tafi ki zauna a daki kada taji wata magana ranta ya ‘baci matar nan iya ‘kokari tanayi dake duk wata rashin kunya da takeyi miki kece kike janyowa kanki.”

Tsaki! taja tace”Kinga na bar maganar yanzu ina canji na na ‘kwai ina lazimi naga kin dauki dari biyar.”

Ina kokarin bata amsa Sule ya shigo! sai ta hau washe bakinta tana kallon ledojin hannunsa dan ta dauka Alhaji Nura ne yayo aiken daya saba…….Yace.”Aunty Sa’ida gashi.” Kar’ba nayi nace.”Nagode Sule.” ya juya ya fita daga gidan bayan ya gaisheta…ta kalleni da fadin” Ganin ledoji a hannunsa Wallahi na dauka aike ne Alhaji yayo mana.” shuru nai mata na cigaba da wanke-wanke na sai ta bar gurin tana surutai irin wanda ta saba.

Ina daf da kammala soya doyar ya shigo gidan jikinsa bud’u-bud’u! d’auke kaina nayi ciki-ciki na amsa sallamarsa, bece min komai ba ya nufi bakin rijiya ya cika bokiti da ruwa yana wanke jikinsa, kamar wacce akace d’ago kanki ki kalleshi naga jikinsa jagab! yana kokarin cire rigar jessi d’in jikinsa cikin gaggawa na kauda kaina daga kansa gabana ya dinga faduwa ganin yanda gajeran wandon jikinsa ya ji’ke jagab dik ya manne masa a jiki girmansa ya fito sosai…… zama yayi bakin rijiyar ya cigaba da wanke jikinsa sam babu wata damuwa a tare dashi.

Har ya gama abinda yake a gurin ban sake kallonsa ba ta gefan idona naga tashinsa daga gurin, ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata nace”Khalid Allah ya shiryar da kai hanya mai kyau.

Bayan na gama sai na d’ora ruwan wanka na d’auki fulas din doyar na nufi daki dashi ,karo muka buga da ita tace.”Yawwa gwanda da da kikayi kika gama magariba tayi nima yanzu alwala zan d’aura.”
Ajiyar zuciya kawai na sauke na bata hanya ta wuce na shiga dakin fulas din hannuna na ajiye na fito domin nima na daura alwalar.

Sai da nayi wanka tukkuna na samu sukunin zama naci soyayyar doyar. lokacin ita Gwaggo har taci ta koshi ta kishingida tana saurarar redio, zaune ta mike tana gyara daurin dankwalinta tace”Sa’ida badan hali Rabi ba kisa mata biyu a plate a miqa mata ta mayar da yawu.”

Nace.”Aiko baki fad’a ba dama sai an bata hakkinta.” komawa tayi ta kwanta tana sake gyara ma daidaicin fulas din dake gabanta.

Nace”Wannan fulas din na gabanki meye a ciki.”? Tace.”Doya ce na ajiyewa Khalid saboda nasan yana san doya da kwai shima.”

Karamin tsaki naja nace”A maimakon ki ajiyewa Kawu sai ki ajiyewa wani Khalid Baba Iro shi yafi cancanta ki ajiyewa doya ba wannan yaron ba.”

Tana gyara redion ta tace.”Khalid nayi niyyar ajiyewa doya saboda haka sai ki shafa min lafiya.” Ta’be bakina nayi a nutse na fara cin doyar dake gabana ina had’awa da lemo.

Labulan d’akin ya d’aga yana magana, tayi saurin mi’kewa zaune da fad’in “Yawwa yaro nagari shigo kaci doya da kwai da zafin ta.”

Baiyi niyyar shiga dakin ba amma ganin mutuniyarsa cikin ‘karamar shart irin ta shan iska yasa ya shiga dakin ya zauna suna fuskantar juna….fulas din ta tura gabanshi da fadin” Gashinan da zafin ta dan bata jima da gama soyawa ba.”

Girgiza kansa yayi yace.”Bana bukata.” da sauri na kalleshi ina mamaki! nasan halinsa da kwadayi dole shima zaiyi sha’awar doyar amma kai tsaye yace baya so.”

Gwaggo jikinta ne yayi sanyi tace”Saboda me ba zaka ci ba.” Babu walwala a tare dashi yace.”Gwaggo daga ranar dana cigaba da cin abincin Aunty Sa’ida zata cigaba da raina ni daga yanzu mutukar abu nata ne a gidan nan to kada ki ajiye min idan ina bukata zan siyo da kudina.”

Tace.”Aa wannan ai doyar ce kawai tata amma ‘kwai ni na siya da kudina dan Allah ka daure kaci.” Girgixa kansa yayi yana duba wayarsa. Yace.”Gwaggo bafa zanci ba wallahi koda zan kwana da yunwa kuwa.”

Ba tare dana kalleshi ba nace”Kanka ka cuta yaro.” Uffan bece min ba ya cigaba da dube-dube a wayarsa.

Nace”Gwaggo ai sai ki ajiyewa Kawu dama shi yafi cancanta da ki kyautatawa ganin irin dawainiyar da yake.” cikin jin haushi tace.”Ke! banyi niyyar bashi ba haba jama’a kin dameni da wani Kawu to bazan bashi ba ga wanda nayi niyyar bawa tunda yace baya bukata gobe da safe naci kayata.”

Shuru nai mata na cigaba da abinda nake, dakin yayi shuru na tsayin minti uku, kaina na d’ago kawai muka had’a ido dashi gabad’aya hankalinsa na kaina ya zuba min shegun idanunsa na fitina.

Nace.”Naci maka bashi ne da zaka sani a gaba kana kallona.” shuru yayi bai ce komai ba kuma bai daina kallona ba. Girgiza kaina nayi na mi’ke na fita daga dakin na barsu.

Kan tabarma na zauna ina duba waya ta ya fito daga dakin yana sanya takalmansa na kauda kaina…..”Aunty Sa’ida.” naji ya kira sunana cikin sanyi murya. a nutse na kalleshi, ya lumshe idonsa tare da shafa sumarsa yace.”Wallahi kin had’u auntyna duk inda ake neman cikakkiyar mace kin kai duk sanda nazo gida hutu da tsananin sha’awarki nake komawa skull.”

Gabad’aya ji nayi yawun bakina ya bushe! na dinga kallonsa ina mamakin tsagerancin sa Murmushi yayi ya had’e yatsun hannunsa yayi heart 💘 Ilov u auntyna muuuuhhhh!.” ya hura min iskar bakinsa. kafin nayi aune har ya fice daga gidan, kaina na sunkuyar ‘kasa gabana ya dinga bugawa sosai al’amarin ya firgitani anya kuwa yaron nan bai fara shaye-shaye ba! ? ni kam ina zan kai kaina da wannan abin kunyar dole sai na tasar masa a tsaye zai daina yi min wannan iskancin, jikina a mutukar mace na mike na shiga dakin na kwanta ina tunanin matakin da zan dauka a kansa..

*Masoya ayi min sharing a groups👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR KARANTA LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE…..VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300 ACCOUNT… 0542382124…BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*_Ya Allah kayi mana katangar ‘karfe tsakaninmu da ma’kiya! Ya Allah ma’kiyi wanda na sani da wanda ban sani ba Allah ka katange ni dashi👏🏼 Ubangiji Allah ka tsare gabanmu da bayanmu Allah dukkanin mai nufin mu da sharri ko wane iri ne Allah ka mayar masa kansa, Allah a gida da waje ka kare mu damu da zuriarmu Ameen ya hayyu ya ‘kayyumu👏🏼_*

*6*
“A’a Sa’ida bana san sharri! A ina kuka had’u da Khalid d’in da har zakiyi masa wannan gundumeman sharrin yaron da tun d’azu ya fita dan babu yanda banyi dashi ba ma ya zauna yaci abinci yace baya ci sannan kawai kizo kice yana k’okarin lalata dake a soro.”

Ina ‘kokarin magana Ummatu ta bankad’a labule ta shigo dakin da fad’in”Wace magana naji kunayi kuna kuma kiran sunan Khalid.” Gwaggo tace.”Ke! Rabi abinda ba’a sa da kai ba dad’in kallo gareshi a’ina kikaji mun kira sunan Khalid da har zaki bankad’a labule kishigo a fusace.”

Murmushi tayi tace.”Gwaggo kenan duk fa maganar da kuke a kunne na ke Sa’ida ki shiga hankalinki dani wallahi wato Khalid din zakiyi wa sharri sabida baki da kirki to tun wuri kije ki nemi d’an iskan da yake lalubeki a soro amma ba Khalid ba.”

Ido na zuba mata har ta ‘kare maganarta ban tanka mata ba, Gwaggo tace.”To tunda dai kin fad’i abinda ya kawo ki tafi kuma wallahi kada naji maganar nan a bakin kowa mutukar maganar nan ta fita dukkaninku sai ranku ya ‘baci.”!

Ummatu ta’be bakinta tayi ba tare da tace uffan ba ta kad’a kanta ta fita daga d’akin.

Duk yanda naso na daure kasawa nayi hawaye na zuba nace.”Gwaggo wato nice ‘yar iska lalatacciya ko? dukkaninku baku yarda Khalid zai iya aikata abinda na fad’a ba kun goya masa baya ya cigaba da bibiyata ko okey to shikkenan Gwaggo yanzu na gane matsayina a gurinki dan gashinan a zahiri kin nuna min cewa kinfi kaunar Khalid a kaina alhalin duk kece kika haifi iyayenmu to babu komai Gwaggo kinji na rantse da Allah duk ranar da Khalid yayi kuskuran sake ri’ke min hannu sai na d’auki tsatstsauran mataki a kansa.”Cikin zafin zuciya nake maganar.

Tace.”To me zakiyi masa idan ya ri’ke miki hannu naga dai shine zai aureki to meye abin tayar da hankali kuma.” Da sauri nace.”Dake dashi zan kai ku gurin alkali sai kiyi masa bayanin da kikayi min yanzu.”

Ha’barta ta ri’ke tana girgiza kanta tace.”Lallai Sa’ida ni zaki kai gurin alkali.”? “Kwarai kuwa mutukar baki daina daurewa Khalid gindi ba wallahi sai na dauki wannan matakin.” shuru tayi tana kallona, nasan mamakina take, dan na ‘kara tsoratata nace” Yanzu ma bari na kira wani abokin aikina wanda d’an uwansa yake aiki a kotun musulunci ta kasuwa na fad’a masa dukkanin abinda yake faruwa.” Da sauri ta rike hannuna tana kokarin kar’be wayar tace.”Sa’ida ashe baki da hankali kina so ki tona mana asirin gida.”

Nace.” Wane irin zan tona asiri ai gaskiya ce idan munje gaban alkali sai kuyi bayani dake dashi wanda kike daurewa gindin.”

Hannunta na rawa tace”Yi hakuri dan Allah abar kaza cikin gashinta domin hakan yafi mutunci zan samu Khalid din naja masa kunne ya daina ta’baki tunda dai ba’a d’aura aure ba.”

Nace.”Shin yanzu kin yarda da maganata akan Khalid din ko kuwa baki yarda ba.”? Da sauri tace.”Haba na yarda mana dama sabida kada maganar tayi tsayi ne yasa kikaji nace ban yarda ba amma nasan Khalid zai aikata kuma zanja masa kunne kiyi hakuri kinji ko.”

Ajiyar zuciya na sauke nace”To wannan karon dai na hakura idan ya ‘kara kwatantawa to zaiga abinda zai biyo baya.” Tace.”Bama zai ‘kara ba insha Allahu.”

Mi’kewa nayi na fita daga dakin ina jin tana fad’in”Kizo ka abincin naki ai tuntuni na shigo miki dashi daki.” Nace.”Wanka zanyi tukkuna.” Da sauri tace.”To shikkenan sai kin fito.” Bakin rijiya na nufa na cika bokiti da ruwa na dauka na kai bandakin, dakin na koma domin cire kayan jikina.

Bayan sallahr isha’i kasancewar ana zafi a gari gashi babu wuta sai mukayi shimfid’a a tsakar gida muna hira, Ya shigo gidan cikin rashin ‘kwarin jiki ya zauna kusa da ita da fad’in “Wash Allah Gwaggo na gaji wallahi nayi mutukar galabaita.”

Zaune ta mi’ke tana gyara daurin dankwalinta tace.”Yaron kirki ina kaje ne kuma me kayi ka gaji kana yawo cikin ka babu komai ina fata dai ka samu wani abu kaci.”?

Ajiyar zuciya ya sauke ‘kasa-‘kasa ya d’an kalli mutuniyar tasa kafin yace.” Wallahi Gwaggo har yanzu banci abinci ba Yau Salim ne ya jani yawo cikin adaidaita sahunsa.” Tace.”Allah sarki to ina fata ka samo d’an kwabo da d’ari.” Goshinsa ya murza yace.” Na samu me kike bukata.”?

Baki ta washe tace.”Ina bukatar Gashashshiyar kazar Malo mai nama.” Dariya yasa yana kallonta yace.”Gwaggo kina san dad’i a rayuwarki duba dan Allah kin iya fad’ar Malo mai nama.” itama dariya tasa harda tafa hannu tace.”To yaron kirki waye baya san dad’i ai mutukar ban takura maka ba to ka siyo min kazar malo mai nama.” Khalid ya dinga dariya yana kallonta.

Takaicin abinda suke ya isheni sai kawai na dauki wayata ina dubawa, naji yace.”Gwaggo ko kudin kenan yau sai kinci kazar Malo.” Yun’kurawa yayi ya mi’ke tsaye yana kokarin sa takalmansa yace.”Auntyna ke me kike so.”? Banza nai masa, Tace.”Sa’ida kina ji ya nayi miki magana ko babu dai kyau gaba.”

Ba tare dana kallesu ba nace.”Bana bukatar komai.” Tayi sauri tace.”Kaji wai bata bukata.” Yace.”Okey to babu damuwa ai ” hanyar fita ya nufa tace”To ina jira dan Allah kada ka fita abokai su ri’ke ka har nayi bacci.” Yace.”Yanzu zan dawo nima yunwa nakeji ai.” tace.”To kafin ka dawo bari na fito maka da abincinka.” Ba tare da yace wani abuba ya fita daga gidan

Mi’kewa tayi ta shiga daki ta dauko masa fulas din abincinsa kana ta dauko kofin silba ta ciko masa da ruwan randarta tazo ta ajiye a kusa da ita.

Kallonta nayi rai a ‘bace nace”Gwaggo keda zaki sanja masa fuska saboda laifin da yayi shine harda dauko masa abinci ko da yake ai nasan kin manta tunda kinga ya samo kudin siya miki kaza idonki ya rufe to har yanzu ina nan akan bakana.”

“Aa Sa’ida ban manta ba ina sane inaso yaci abinci ya huta sai nai masa maganar.” “Umm! nace naja bakina nai shuru! jin maganarsa shida abokansa a soro yasa na mi’ke na shiga daki, yana shigowa kai tsaye ‘kofar Ummatu ya nufa da fad’in ” Gwaggo ina zuwa.”

Da sauri tace.”Aa zo ka bani leda ta kafin ka shiga bana so ta za’be abinda ka shigo dashi.”! Dariya nasa ina mamakin ‘karfin halin Gwaggo mata ta haifi d’anta amma ta fita iko dashi…..Dawowa yayi da baya ya mi’ka mata leda guda tace.”To yawwa yanzu naji magana ka fito ga abincin naka.” Yana ‘yar dariya yace.”To Gwaggo.” Gurin mahaifiyar tasa ya nufa domin itama ya bata tata ledar.
kwance a d’an tsakar gidanta ya sameta da Mafici a hannu tana firfita shigowarsa yasa ta mike zauna tana kallon ladar hannunsa…..Zama yayi gefan tabarmar da take zaune yace.”Ummatu me zai sanya ki takura kanki bakya fita babban tsakar gida kisha iska sosai.”

Girgixa kanta tayi tace.”Khalid ‘kyaleni anan yafi min kwanciyar hankali akan na fita Gwaggo ta fad’a min ba’kar magana.”

Yace.”Ummatu idan da sabo yaci ace ki saba da halin Gwaggo wata irin macace mai wani irin hali bayan haka kuma akwai rikicin tsufa a tare da ita.” Girgiza kanta tayi tace.”Khalid dama ai kai baka ganin laifin Gwaggo duk abinda tayi daidai ne a gurinka.”

Girgiza kansa yayi yace.”Ba haka bane wallahi Ummatu yanzu a matsayin na shekarun Gwaggo dole ayi mata uziri shiyasa kikaga duk abinda tayi nake biye mata saboda samun nutsuwarta ba wai bana san laifinta bane.”

Tsaki taja tace.”Duk da da akwai tsufa to da akwai iskanci wannan tsohuwar guda ce Khalid ni kad’ai nasan irin takaicin da take kuntuka min a gidan nan.”

Yace.”To kiyi hakuri dan Allah komai mai wuce wa ne gashi kema na siyo miki nama.” Kar’ba tayi tana duba ledar tace.”Sai da ka kai musu suka za’ba tukkuna ni aka kawo min saura ko.”

Girgiza kansa yayi yace.”Aa Ummatu duk d’aya ne wallahi dake da Gwaggon.” Tace.”Ai kamata yayi ka daina daidaita ni da ita tunda ni na haifeka idan kana neman albarka sai kayi min biyayya.”

Yace.”Ummatu dan Allah ki daina irin wannan maganar wallahi dake da Gwaggo duk daya kuke a gurina ke kika haifeni dole kina da martaba ta mussaman a gurina Gwaggo kuma itace ta raine ni har na girma Gwaggo bata san ‘bacin raina komai ta samu nawa ne abinci wannan Gwaggo bata ci sai tare dani sai dana na tafi makaranta tukkuna muka raba kwano da ita Gwaggo takan iya hana cikinta abu ta ajiye min Ummatu kada ki manta Gwaggo itace tayi rabin dawainiyar Karatuna idan tayi sana’arta haka zata tattara kudin ta bani nayi hidimar makaranta dasu duk lokacin da nazo hutu sai ta bani kudi wata bukatar zata taso Gwaggo tayi Baba yayi a haka fa akayi ta tafiya har Allah ya kawo ni wannan lokacin da nake daf da kammala makaranta kinga kuwa dole na kyautata mata domin ta taka muhimiyyar rawa a rayuwata.”

“Khalid wato ka sani a gaba kanayi min gori ko? to ko banyi maka hidima ba ai ba zaka iya biyana irin dawainiyar cikin ka da haihuwar ka ba, saboda haka kada ka sake sani a gabana kana kawo min wata banzar magana.”

Shuru yayi yana jinta sai fad’a take masa yace.”To Ummatu kiyi hakuri dan Allah insha Allahu ba zan kara ba.” Shuru tayi masa ta mike ta nufi kicin plate ta dauko tazo ta zauna tana kokarin sa naman a ciki…..mikewa yayi ya fita daga gurin, nan ya samu Gwaggo a kashingid’e har taci ta gyatse tana gyangyad’i! zamansa a kusa da ita yasa da sauri ta tashi zaune tana fad.”Khalid ka fito.”
“Umm.” kawai yace ya zauna ya dafe kansa, cikin kulawa tace.”Menene yake damunka.”? Shuru yayi yana girgiza kansa, ‘kasa-‘kasa tace.”Kada ka damu da barazanar Sa’ida akan abinda kayi mata d’azu nan ta tit*iye ni tanayi min jaraba wai sai ta kaimu kotu ni dakai.”

Cike da mamaki! yace.”Akan wane dalili zata kaimu kotu kuma me nayi mata da har take wannan furucin.”? Da sauri tace.”Yi magana a hankali Dan bana tsammanin tayi bacci.”

Tsaki yaja ‘kasa-‘kasa yace.”Me tazo tace anyi mata.”? Gwaggo murya a ‘kasa tace.”Wai cewa tayi kana tare ta a soro kana lalubeta.”

Yanda Gwaggo ta fadi maganar yasa dariya ta ‘kwace masa yace.”Ni sharri kawai tayi min abinda ma yau ban yini a gida ba.” Gwaggo tace.”To nima haka nagani ta shigo fuska a murtuke ta dinga jaraba dan har mahaifiyarka taso ta biye mata na shiga tsakaninsu, jin tana maganar kaimu gaban alkali yasa na bata hakuri nace zan ja maka kunne.”

Yace.”Gwaggo da kin sani ma baki wahalar da kanki gurin bata hakuri ba ni ba d’an iska bane da zatayi min irin wannan sharrin nima zan dauki mataki a kanta dan kafin ta kaini ‘kara kotu ni zan kaita tunda tayi min sharri.”! Sosai ya fitittuke yake kare kansa Al’amarin ya dinga bani mamaki! dan duk maganar da suke ina jinsu raina kuma ya ‘baci sosai da naji Gwaggon na rarrashinsa har tana cewa ai dama tasan Sharrin nai masa ba zai aikata ba, naji tamkar na fita naci masa mutunci sai dai kawai na taushi zuciyata na hakura na kyaleshi ina tunanin irin matakin da zan dauka a duk ranar da ya sake kuskuran ta’ba jikina..

*Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE…..VIP #600 NORMAL#300 ACCOUNT…. 0542382124…..BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*4*
Sa’ida cewa nayi fa ki sawa Rabi doyar nan kada mu wayi gari ta dinga yar mana da habaici kin san dai halinta bata da hakuri.” Gwaggo ce ke wannan maganar a lokacin da take kokarin shigowa dakin da buta a hannunta da alama bandaki taje.

Zaune na mi’ke ba tare da nace mata komai ba na fara kokarin bud’e fulas din dake kan tabarmar ta. ido ta tsira min a lokacin da nake zuba doyar tace.” Bafa cewa nayi ki kwashe mata ba guda biyu kika sa mata ta isa tunda itama idan tayi soye-soyen ta ba bamu take ba.”

Nace.”Gwaggo dan Allah abin duniya ya daina rufe miki ido mecece doya da ‘kwai tun d’azu duk kin damu kanki.”

“Sa’ida kada ki fad’a min magana akan Rabi na lura kema asirin nata ya fara tasiri a kanki ai sai kije ki ‘karata ke da ita.” shuru kawai nayi mata na fita daga dakin.

Ummatu na zaune a gurinta tana saurarar redio na shiga da sallama a bakina, kallon mamaki ta shiga bina dashi, nace.”Ummatu doya ce na kawo miki.” Babu yabo babu fallasa tace”To nagode.” Kar’ba tayi ta ajiye kusa da ita nace”To sai da safe.” kamar bata so tace.”Allah ya tashe mu lafiya.”

Koda na koma dakin gwaggo samunta nayi har ta kwanta bacci kan gadonta redion ta a kusa da kanta tana saurara Gwaggo bata kashe redio kullum a kunne take kwana shiyasa kullum cikin siyan batir take da daddare idan ta isheni da shuuuuu! zan tashi na kashe amma idan ta farka sai ta kunna alhalin ko wace tasha sun rufe, al’amarin Gwaggo nada wuyar sha’ani.

Da wuri na tashi nayi duk abinda na saba karfe bakwai da rabi na shirya tsaf a gurguje na karya kummalo nayi mata sallama domin tafiya gurin aiki…..Shuru tayi min ba tace komai ba nace.”Gwaggo kina ji ina magana ko.”? kallona tayi da fadin.”Me kika ce.”? cike da mamaki nake kallonta nasan sarai taji abinda na fada amma wai tambayata take, ajiyar zuciya na sauke nace.”Na tafi sai na dawo.” a maimakon tayi min irin adduar data saba sai kawai naji tace.”Umm!! juyowa nai ina kallonta nace”Gwaggo ba zakiyi min addua ba.”‘

“Sa’ida kyaleni dan Allah kije kawai ni da wannan aikin naki gwara babu kullum kina yawo a kan titi zagade-zagade babu mijin aure duk wannan kyawun naki da kyawun surar zai tashi a banza a wofi wannan al’amari yana damuna.”

Jim! nayi ina kallonta kafin nace.”Gwaggo Al’amarina ya daina damunki komai da kika gani yana da lokaci ki cigaba dayi min addua.”
“Umm.”! ta sake fada tana ta’be bakinta, kaina na girgiza kawai na kama hanyar fita daga dakin, karo mukaci dashi a lokacin da yake ‘kokarin shiga, yana sanye da singlet fara kal da 3qutar fuskarsa ta nuna alamun bai jima da tashi a bacci ba.

Cikin kulawa yace.” Aunty Sa’ida ki bari yanzu zamu fita cikin a daidaita sahun Salim sai mu kai ki makarantar taku.”

Ba tare dana kalleshi ba nace.”Bana bukata.” da sauri na ratse shi na wuce! Ina jin sautin muryar Gwaggo tana surutai wanda suke nuni da jin haushin abinda nai masa.

Sai da nayi dana sani akan k’in kar’bar tayin da Khalid yayi min domin nafi karfin minti goma sha biyar a tsaye a bakin titi wani abun hawa na haya bai gilma ta gabana ba motocin gida ne kawai suke wuce wa, dama wani sa’in ina fama da irin wannan matsalar ta rashin abin hawa, wani lokacin kuma ina fitowa titi nake samu yau dai al’amarin sai addua dan tamkar anyi musu gori ko kuma wa’inda suka tafi yajin aiki, agogon dake daure a hannuna na duba takwas saura minti biyar gashi karfe takwas da minti goma nake da Period ajiyar zuciya na sauke ganin adaidaita sahun nasu na kokarin fitowa daga layin duk abuna dole nayi hakuri na shiga mutukar baso nake na makara ba, Motar Alhaji Nura na sake hangowa tana bin bayan babur d’in nasu, saurin dauke kaina nayi ina kallon hanya tabbas nasan sai ya tsaya yayi min magana gashi gabad’aya ban yanke hukunci akan maganarsa ba gabad’aya ma na manta munyi magana dashi jiya.

Aikuwa gabana yayi parking ya sauke gilashin motar fuskarsa dauke da k’ayataccen murmushi yace.”Ranki ya dad’i an fito kenan.”? sakin fuskata nayi nace”Eh wallahi Alhaji barka da asuba ya kwanan iyali.” ? cikin kulawa yace.”Lafiya kalau sun tafi skull yanzu me zai hana ki shigo na rage miki hanya.” Yafada yana kallon kwayar idona, ina kokarin magana adaidaita sahun nasu ta tsaya kusa dani. da sauri nayi ‘yar dariya da fad’in”To nagode Alhaji dama na jima a tsaye babu abun hawa.” cike da jin dadin kar’bar tayinsa yasa hannu ya bude mota kofar had’e da fad’in ”bisimillah.” ba tare da na tsaya na saurari maganar da Khalid yake min ba na shiga motar da murmushi na mussaman a fuskata duk dan na cuzgunawa zuciyar yaron……Motar ya kunna muka bar gurin ko da wasa banyi kuskuran kallonsa ba so nake na ‘kuntata masa dan saboda nasan ya tsani ya gan ni tare da mutumin bayan haka kuma inaso na nuna masa bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane ni ba matar ‘kananun yara bace.

Khalid iskar dake gurin ya kaiwa naushi! rai a ‘bace ya shiga kai kawo a gurin zuciyarsa kamar zata tsaga kirjinsa ta fito saboda tsananin kishi! Salim yace.”Khalid dan Allah shigo mu tafi ka rabu da ita.” Yana huci! ya shiga motar, Salim ya mika masa pure water da fadin”Kar’bi kasa zuciyarsa tai sanyi kar’ba yayi kamar gaske sai kawai yayi wurgi dashi kan titi lips d’insa ya ciza da fad’in “Allah Salim wannan Alhajin idan baiyi wasa ba sai nayi masa rashin mutunci babu ruwana da wani kud’insa da shekarunsa wallahi mutukar bai fita daga harkarta ba sai na bashi mamaki.”!

Salim girgiza kansa yayi yace.” Khalid idan da zan baka shawara ka d’auka sai nace maka ka rabu da Aunty Sa’ida saboda nasan kai kanka kasan ba tsaranka bace aunty Sa’ida matar manya ce ganin idonka babu wani gajarabul d’in mutum da yake tunkararta duk masu nemanta manyan mutane ne kana dai kallo da idonka duk kudi da muqami irin na Alhaji Nura idan ya ganta rawar jiki yake mata.”

Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yana kallon abokin nasa yace.”Salim duk abinda ka fad’a akan auntyna gaskiya ne wallahi ni kaina ina mamakin tsaurin idona a kanta Salim na rasa yanda zanyi wallahi aunty Sa’ida ta shiga zuciyata tayi kakagida! a cikinta, Salim bari na fad’a maka wani sirrina da ba kowane yasan dashi ba, tun inada shekara goma sha takwas a duniya na fara mafarki da ita haka zan wayi gari jikina a ‘bace! to tun daga sannan na gane cewa na balaga na zama cikakken namiji wallahi Salim babu ranar da zan kwanta bacci banyi mafarkinta ba kuma kai idan kaga irin rayuwar da muke da ita a mafarkin sai kayi mamaki wallahi sosai nake sex da ita ina jiyar da ita dadi tana jiyar dani! na rasa yanda zanyi da wannan masifar Salim ko a skull haka nake fama da wannan jarabar dan dai kawai adduar iyaye na tasiri a kaina amma da badan haka ba da tuni na nemi hanyar da zan biyawa kaina bukata.”

Girgiza kai Salim yayi yace.”Gaskiya Abokina na tausaya maka domin ni tuntuni na gane son maso wani kake yi domin jikina na bani aunty Sa’ida bata sonka duba da irin halin ko’in kulan da take nuna maka me zai hana kayi ya’ki da zuciyarka akan abinda kasan ba zaka samu ba.”

Ranshi a ‘bace! yace.”Salim idan kaga na daina bibiyar Aunty Sa’ida to aure tayi kai wallahi ko aure tayi ba zan hakura da ita ba saboda bata da wani miji sai ni wannan dalilin ne ma yasa na samu gwaggo na fad’a mata maganar ina ganin ko kowa ya’ki amincewa ita zata goya min baya.”

Salim yace.” Khalid ina jiye maka wahala wallahi na fada maka Aunty Sa’ida tafi karfinka ka hakura kawai.” a fusace! yace.” Salim wai wannan wace irin magana ce kake? a’ina ka ta’ba ganin mace tafi ‘karfin namiji! Auntyna nada 28year ni ina da 23year sai ka fad’a min ina tazarar take kai ni a yanda nake jin jarumta idan an had’a min iri-irin ta goma zan iya dasu ballantana ita da tun a mafarkina na gama da ita na fad’a maka a mafarkina fa tuntuni na gama mata aiki.” Salim ya fashe da dariya yana dukan sitiyari yace.”Kai Khalid wallahi baka da mutunci wato dai yanzu kana nufin fanko kake kallonta.”

Murmushi yayi ya d’an sosa tarin sumarsa yace.”Aa mafarki daban Zahiri daban yanda nake sarrafa ta a mafarkina to inaso na sarrafata a zahiri wallahi sai na ‘kure duk wata fitinar ta.” Salim ya dinga dariya yana fad’in Khalid baka da dama wallahi Allah ya baka aunty Sa’ida ka more ‘kuruciyarka dan wallahi nima ina son mace mai kyau da tsarin jiki irin nata kullum kamar ‘kara mata ‘kuruciya ake.”

Murmushi yayi yace.”Nagode da addua abokina.” Wasu mata ne suka tsayar dasu, Salim yace.”Hajiya ina zakuje.”?
“Gidan Murtala.” matar ta fada tana kallonsa, yace.”To ku shigo muje.” da sauri suka shiga, shi kuma yaja babur din suka bar gurin.

****
Cikin murya mai taushi yace.”Ranki ya dad’e har yanzu banji daga gareki ba inaso ki sha’ku da iyalina kafin Allah ya kawo ki cikinsu shine babban dalilin da yasa nace kina shiga gidan a cikin ranaku biyu kinayi musu lesson itama matar gidan tuntuni nayi mata bayani kuma ta amince da manufata.”
Alhaji Nura ne ke wannan maganar a yayin da suke tafiya a motarsa.

Ajiyar zuciya na sauke na d’an kalleshi da gefan ido mamaki sosai nake da maganarsa yana sona da aure amma kuma yana kawo wata gurguwar magana mara ma’ana Ta yaya zan dinga shiga gidansa da sunan yiwa yara lesson bayan da maganar aure a tsakaninmu hakan sam bai dace ba, ita kanta matar gidan da ta amince da hakan nayi mamaki amma dai nafi zargin gatse tayi masa tunda mafi akasari maza basu sanshi ba.

A nutse nace”Alhaji ni ina ganin ba lallai sai na shiga gidanka nayi wa yara lesson zamu sha’ku dasu ba, hakan kamar bai dace ba tunda har magana aure ta shiga tsakanina da kai a yanzu sai mu bari muga abinda Allah zaiyi idan har Allah ya kaddara aure a tsakanina da kai yara basu da matsala insha Allah zan tsaya na kula da harkar karatunsu amma maganar na dinga zuwa nai musu lesson ka ajiyeta.”

D’an murmushi yayi yace.”Sa’ida kenan ai da amincewar matar gidan nake miki wannan maganar ina ganin hakan duk ba wani abu bane tunda duk an riga an zama d’aya.”

“Alhaji kenan na yarda da amincewar matarka amma ni a ganina hakan ba kamata ba dan Allah kayi hakuri da wannan maganar domin ina ganin hakan shi yafi alkairi.” Yace.”To shikkenan tunda kince haka yanzu a’ina maganarmu ta kwana? inaso wannan karon ki bani dama na turo da magabata na akan maganar auranki.” Jim! nayi ina nazarin maganarsa “Insha Allahu zan kira wayarka idan na koma gida.” Cike da farin ciki yace.”To masha Allah Nagode ‘kwarai Sa’ida sai na jiki.” Murmushi kawai nayi ban sake magaba ina dai jinshi yana ta bani labarin yaransa sai da dariya yake gaskiya yanda na fuskance shi yana da son yara sosai……..cikin wannan halin ya sauke ni bakin gate din makarantar da nake koyarwa a nutse nace”Alhaji nagode kwarai.” kokarin bud’e mota nake yace.”Idan kun tashi ina iya turo direba ya dauke ki.” Da sauri nace”Aa Alhaji bani da matsalar abin hawa idan zan koma gida domin ‘kawata Hauwwa tana da mota tana rage min hanya.” Yace.”To shikkenan ranki ya dade a fito lafiya.” Nace.”Insha Allah nagode.” motar na bude na fita da sauri na daga masa hannu hade da fad’in “A sauka lafiya.” cikin sauri na nufi cikin makaranta kafin na shiga sai da muka gaisa da masu gadi cikin mutunci sannan da sauri na shige ciki…….

*Masoya ayi min sharing a groups👏🏼🥰*

*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE……VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300 ACCOUNT.. 0542382124…BINTA UMAR GTBANK…..IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*DUNIYAR HAUSA NOVEL*

_*Cannal ne na mussaman da zaku samu littafan hausa ko wane iri ne maza ku tafi YouTube kuyi sarcing d’in Cannal din zaku samu ‘kyatattun littafai masu dadi! kada ku manta da sunan channal din *DUNIYAR HAUSA NOVELS*_

*5*
“Sa’ida tun kafin mu fito daga ofis nake miki wani irin kallo sai nake ganin kamar kina da damuwa a ganina bancanci ki ‘boye min abinda ke damunki ba tunda nima duk wani abu da yake damuna bana ‘boye miki.”
Hauwwa ce kenan wannan maganar a lokacin da suke cikin motarta domin komawa gida.

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Wallahi Hauwwa ba ‘karya kikayi ba ina damuwa na kuma rasa yanda zanyi na warware ta al’amarin dai sai godiyar Allah.

Murmushi tayi tace.”Haba ‘kawata abokin kuka shi ake fad’awa mutuwa ki fad’a min damuwarki ko akwai shawarar da zan iya baki.”

Murmushi nayi nace”Dama ina tunanin fad’a miki kikayi magana Hauwwa kin san wannan yaron na gidanmu ko.”?

Tace.”Khalid ko bashi kike nufi ba.”? Nace.”Shi nake nufi Hauwwa Khalid ya takura min a gida wallahi wai saboda tsabar rashin mutunci da raini kamar ni zai duba yace yana so.”

Hauwwa dariya tasa tana kallona da mamaki a tare da ita, tace.”So.”? Ta’be bakina nayi nace.”Kwarai kuwa Hauwwa Khalid sona yake dan duk wasu alamu ya nuna harda fad’awa Gwaggo wai zai aure ni yaron da a gabana ya girma meye nasa ban sani ba amma da yake yanzu yaga ya fini tsayi da girman jiki shine yake furta min wannan kalma.”

Hauwwa draving take tana girgiza kanta tace.”Sa’ida Khalid yayi tsaurin ido amma kuma idan an duba tarihi za’a ga baiyi tsaurin ido ba tunda hakan kamar sinna ce mai zai hana ki aureshi tunda hakan ba haram bane.”

Wani irin kallo na watsa mata “Hauwwa wannan wace irin magana kikeyi me zan aura a tare da Khalid bana tsammanin zan iya auran ‘karamin yaro a yanda nake a haka nafi bukatar cikakken namijin mai kima wanda yasan rayuwa amma auran yaro mai ‘karanci shekeru akwai kalubale a ciki.”

Murmushi tayi tace.”Sa’ida wane ‘kalubale kike hangowa a tattare da auran Khalid? Yaro kyakykyawa da siffar mazantaka Khalid bai da makusa matsalar kawai kice bashi da kudi sannan kuma bashi da aikinyi in banda haka menene abin’ki a tare dashi.”?

Girgiza kaina nayi nace.”Hauwwa Ra’ayi na ne kawai haka bana sha’awar auran k’ananun yara dan sai nake ganin kamar basu san meye aure ba wannan dalilin yasa gabadaya bana kulasu nafi tsayawa na saurari magidanta masu iyali da suka dad’e a cikin harkar.”

Hauwwa ta’be bakinta tayi tace”Sa’ida mazan fa suna suka tara kamar yanda matan ma suka tara duk kallon kitse kike musu ni zan fad’a miki wannan kinga dai ni bazawara ce ko to wallahi ba zan auri namiji ba sai na tsaya na duba tukkuna saboda ni kad’ai nasan bala’in dana shiga a gidan aurena kafin na fito.”

“Hauwwa kenan kin san kowa da tunaninsa amma gaskiya bana yi miki sha’awar auran ‘karamin yaro domin kinfi ‘karfinsu ki auri namiji daidai dake dan Allah kada kibi son zuciyarki daga baya kizo kina nadama.”

“Sa’ida kin san Allah ko d’an 20years ne yazo da niyyar aurena na gamsu da shi sai na aureshi domin hakan ai ba haramun bane akan naje na auri babba nazo na sake shiga wata matsalar gwara na auri yaron na cigaba da rainonsa har yayi ‘kwari.”

Cikin wani irin yanayi na mamaki nake kallonta…..tasa dariya da fadin”Kina mamaki ne.”? Girgiza kaina nayi nace.”Sosai kuwa idan kin auri dan 20years kin auri d’an cikin ki ko ba haka bane.”

Still tana dai dariyar tace.”Aa Sa’ida bana san sharri a ina na haifi dan shekara ashirin Walid yarona na farko duka shekaransa tara Safna kuma shekararta bakwai.”

Nace”Kin gani ai tunda kika haifi dan shekara tara kin zama uwa me zai baki sha’awa a gurin auran karamin yaro dan shekara ashirin.

Hauwwa baki ta ta’be tace.”Ke Sa’ida bari dai na fito miki a mutum! ni Hauwwa ina da tsananin bukata wannan dalilin ne ya janyo mutuwar aurena domin babansu Walid bashi da maida hankali a wannan gurin yafi mayar da hankalinsa gurin neman kudinsa nasha wahala a hannunsa Sa’ida ina fada miki Walid da Safna tsanani rabo ne yasa aka haife su saboda babansu sai ya shafe wata biyu ko uku bai had’a shimfida dani ba, kullum yana yawo a jirgi sai kace tsunsu shi dai ya samu kud’i ni kuma ya barni cikin wahala da bukata wannan dalilin yasa na yankewa kaina shawarar yanke zama dashi dan ba zan iya da halinsa ba.”

Na jima ina mamakin maganarta kafin nace.”To Hauwwa shi ‘karamin yaron da kike ‘kulafuci a kansa kina da tabbacin zaki samu abinda kike bukata mazan fa duk kusan haka suke tunda dai ba ‘kwan’kwasawa zakiyi ki gane daidai dake ba .”

Murmushi tayi tace.”Sa’ida ana ganewa wallahi shiyasa ai nace miki kafin nayi auran sai na tantance tukkuna kuma ina rokon Allah ya bani daidai dani.”

Nace.”Ta ina zaki gane jarumin namiji Hauwwa.” murmushi tayi tace.”Sa’ida kenan.” draving d’inta ta cigaba dayi ta barni cikin tunani nima irinta ce mai yawan sha’awa da son soyayya shiyasa gabad’aya na shiga tunanin ta inda zan gane jarumin namijin da zai iya daukar lalurata……Alhaji Nura ne ya fad’o min a rai na dinga tunanin siffofinsa dogo ne mai ma daidaicin jiki kwayoyin idanunsa jajaye ba irin na Khalid ba da kullum suke da haske, nace”Hauwwa tunda kin’ki fad’a min ai na gane.”

Tace.”Yawwa ai dama so nake ki gane sai kiyi min bayani.” Dariya nayi nace.”Kamar dai Alhajina ina nufin Alhaji Nura ya cancanta da wannan sunan.

Shuru tayi tana nazari tace.”Eh gaskiya kam kwayoyin idanunsa ma sheda ne ina miki sha’awar auransa gashi yana bala’in sonki to amma ai matarsa ce matsala Sa’ida a rayuwata bana san kishiya wallahi.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Hauwwa ni wallahi kishiya bata firgita ni za’bin Allah kawai nake nema idan Allah ya kaddara Alhaji Nura ne mijina babu ruwana da matarsa tunda ba itake aurena.”

“Hakane Sa’ida to ina rokon Ubangiji Allah ya za’ba mana abinda yafi alkairi.” na amsa da ameeeen ya rabbi……Da wannan hirar ta sauke ni a bakin layin mu ta juya kan motar hannu na daga mata da fadin”Nagode ‘Kawata sai gobe idan Allah ya kaimu.” ta amsa da “Ameen Allah ya kaimu lafiya.” sai da ta bar gurin sannan na nima na bar gurin……..

Tunda na hangoshi a zaune a kofar gidan naji gabana ya fadi! hakika Khalid ya zame min ‘karfen ‘kafa, kici-kici nayi da fuskata, kafin na karasa naga ya mi’ke ya shiga gidan, ajiyar zuciya na sauke naji dad’in hakan saboda na tsani kallon da yake min……Ina shiga soran naji an fizgo hannuna kafin nayi aune naji ya ru’kun’kume ni ta baya! numfashinsa naji yana fita da sauri da sauri ya d’ora kansa a kafad’ata sosai ya ri’ke ‘kuguna! gabana ya dinga fad’uwa! murya na rawa nace.”Khalid wane irin iskanci ne wannan? zaka sake ni ko sai nai maka rashin mutumci d’an iskan yaro kaw……Kafin na ‘karasa naji yayi cikin bayan k’yaure (‘kofa) dani, a zabure! na juyo fuskokinmu suka had’u guri guda!

Hawaye ne naji suna kokarin kufce min wane irin fitinan nan yaro ne wannan? matseni yayi a kirjinsa yana kiran sunana cikin wani irin sauti “Aunty Sa’ida kina so na mutu ko? ki taimakawa rayuwata kada ta salwance.” hawayen takaicin da nake kokarin dannewa sune suka kufce cikin rawar murya nace.”Khalid sake ni.”

“Um!um! Aunty naji dadin rungumeki ki bari na samu nutsuwa ina cikin tsananin damuwa.”
Yafad’a yana goga gefan fuskarsa a tawa.

Shuru nai jikina gabad’aya ya mutu ko yaya nayi motsi da niyyar kwace jikina zai sake matseni sai wani irin nishi yake!

“Khalid ni kake wa wannan iskancin ko? ni kake matsewa a soro saboda baka da mutunci Khalid.”! murya a sha’ke nake magana.

” Aunty Sa’ida har abada babu tozarci a tsakani na dake abinda kikayi min d’azu ya ‘bata min rai ko abinci na kasa ci Aunty me yasa zaki za’bi wancan Alhajin ki barni me nai miki ko ni ba namiji bane.”
Cikin sanyin murya yake maganar yana yawo da hannunsa a jikina.

“Khalid ka daina mafarkin abinda ba zai faru ba kasan Allah duk maitarka akaina sai ka hakura dan ni nafi karfin’ka kaje ka nemi daidai da kai.”

Fuskata ya d’ago yana kallona, naga idonsa yayi jajawur a take tsigar jikina ta tashi! fuskata na fizge! da sauri na daga hannu da niyyar kwad’a masa mari! yayi saurin ri’kewa.

Girgixa kansa yake Cikin ‘kunar zuciya yace.”Ni nafi karfin ki mare ni auntyna! na amince ni maye! ne amma akanki aunty Sa’ida ba zan fita a rayuwarki ba sai na tabbatar da cewa kin zama mallakata mu zuba ni dake.”!

Tsaki naja na tureshi da fadin”Shashasha mara hankali kawai.” gabana ya tare cikin ‘bacin ran da banta’ba ganinsa dashi ba yace.”Kada ki ‘kara kirana da shashasha zan baki mamaki.”

“Me zakayi min.”? nafada ina watsa masa harara……Murza yatsun hannunsa yayi yace.” Sai ranar da kika ‘kara kirana da kalmar sannan ne zakiga abinda zanyi.”

“Mtwwws! tsaki naja na ra’ba ta gefansa na shiga gidan…..Ajiyar zuciya ya sauke bayan shigewarta gidan ya shiga shafa kirjinsa yana lumshe ido har yanzu yana jin tudun nonowanta a kirjinsa, cikin mutuwar jiki ya fita daga gidan.

” To shikkenan Uwale zan duba maganarki wallahi dama nima sai da nayi wannan tunanin ace yarinya kwata-kwata bata so ayi mata maganar aure bayan tana da mane ma dole ne a nemi taimako.” Uwale na kokarin magana na shiga dakin, sai ta washe baki da fadin”Babban mace hakima kin dawo kenan sannu lallai kin dauko rana.”

Sama-sama na gaisheta na cire hijab din jikina na fita daga dakin na tsani alaqar Gwaggo da Uwale ko kad’an……Bayan fitarta Uwale tace.”To shikkenan Gwaggo sai kinzo ina sauraranki.” Gwaggo mi’kewa tayi domin yi mata rakiya tana fad’in “Insha Allahu gobe zanzo sai muje Allah dai ya rufa asiri.” kallo na bisu dashi ina tunanin inda zasuje….Gwaggo ta dawo gidan tana kallona a fakaice kafin ta shiga dakin, mikewa nai nabi bayanta domin na kafa mata hujjata akan irin iskancin da Khalid keyi min…

*Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼🥰*

*IDAN KINA SO KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE…..VIP GRUOP…600 NORMAL 300 ACCONT…0542382124…..BINTA UMAR GTBAK IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️*

*Pegen na yau naki ne*
_*Gwanata FATIMA SUNUSI RABI’U Matashiyar marubuciya mai fasaha da amfani da basirar ta a inda ta dace Ina kaunarki Takwara kamar yanda kike ‘kaunata💗😊*_

*7*
Cikin nutsuwa na kalleta tana ta shiryawa nace.”Wai Gwaggo ina zakije ne da sassafe haka.”? Tana shafa mai a kafafunta tace.”Wallahi ugunwa zamuje da Uwale amma ba zan dad’e ba zan dawo dan ina da aiki a gabana Salisu mai kanti yace nayi masa lagwani zai siya.”

Nace.”Gwaggo wannan wace irin unguwa ce da zakuje da safe karfe bakwai da rabi kifa duba lokaci ki gani ko karyawa bakiyi ba amma kina kokarin fita.”

“Kinga Sa’ida kada ki takurawa rayuwata ina ruwanki da inda zani zaki dameni da surutai.” Nace.” Babu ruwana amma bari naje na fad’awa Baba Iro cewa Uwale zata jaki yawo.”

Da sauri nayi yun’kurin fita ta ri’ke gefan rigata da fad’in “Dawo na fada miki inda zamuje.” komawa nayi na zauna ina kallonta, tace.”Jikar Uwale ce take aljanu shine zamuje mu kar’bo mata magani gurin wani malami.”

Cike da mamaki nace.”Gwaggo Uwale ta fara d’ora ki a turba mara kyau ko yanzu tsofai-tsofai daku ina ku ina zuwa gurin malami.”

“Sa’ida kada ki fassara mu da wata manufa bakiji abinda na fad’a ba jikar Uwale Nafisa itace take aljanu shine zan rakata ta kar’bo mata magani.”

Nace.”Dole sai kin rakata ita bata san hanya ba.”? A tausashe tace.”Tasan hanya mana nima ai inso malam d’in ya taimaka min.”

“Me yake damunki da zakije gurin malami ya taimaka miki ba zakiyi alwala ki roki Allah ba.”

shuru tayi bata bani amsa ba, nace.” Gwaggo ki kiyaye kada Uwale ta jaki gurin bokaye da girma da mutuncin ki me kike nema a duniya wanda ba zaki rok………”Sa’ida wai ni sa’arki ce ne da zaki zauna kina kokarin fad’a min maganar banza waye yace miki gorin bokaye zamuje.”?

Ganin yanda ta fusata yasa na sassauta murya “Gwaggo kiyi hakuri idan kinji shaushin maganata halin Uwale na sani na rashin tsoron Allah da san duniya.”

“To naji wuce kiyi tafiyarki nama fasa zuwa tunda zargin da kikeyi min kenan.” Murmushi nayi na cigaba da shirye-shiryen tafiya makaranta…….Ummatu ce ta daga labulan dakin ta shigo da sallama a bakinta, dukkaninmu muka amsa mata ta ajiye jug din kunun dake hannunta tace.”Gwaggo ina kwana.”? Ciki ciki ta amsa tana dauke kanta kamar itace tai mata laifin…..Ummatu ta juya zata fita a nutse nace.”Ummatu antashi lafiya.” ? ta amsa ba tare data juyo ba…..”Rabi yau kuma ina k’osan zaki zo kawai ki ajiye min ruwan kunu a gabana.”

Kai tsaye Ummatu tace.”Nima shi aka bani na kawo miki.” a fusace! tace.”Magana zaki fad’a min Rabi wallahi ki shiga hankali a gidan nan idan ba hakaba zanyi maganinki .”

Tace.”To Gwaggo magana kika fad’a na baki amsa daidai da maganarki Maigidan yau bashi da kud’i sai kowa yaci aljihunsa ” Gwaggo tsaki taja ta dauke kanta….Ummatu rai a ‘bace ta fita daga dakin.

Nace.”Gwaggo dan girman Allah ki dinga tauna magana kafin ki fad’a bai kamata ki dinga irin wannan zaman da surukar ki ba.”

Tsaki taja ta dauke kanta, nace”Na nawa ‘kosan zai isheki idan na fita sai na bawa yaro ya siyo miki.”

“Na hamsin ma ya isheni.” tafada tana bud’e jug din kunun……..Hijabina nasa nace”Ni zan tafi.” tace.”Ba zaki tsaya kisha kunun ba.”? Girgiza kaina nayi nace”Yau haka na tashi cikina a cunkushe idan naje ofis zan samu ruwan tea nasha da biscuit. ”

Shuru tayi tana kallona…..Nace.”Kada ki damu Gwaggo.” tace.”To sai kin dawo.” Nace.”Insha Allah.” Ina fita na ganshi a zaune a bakin rijiya yana brush dauke kaina nayi daga kansa nayi sauri na fita daga gidan.

Gwaggo na zaune tana sa’ke-sa’ke yaro ya shigo da sallama a bakinsa Labulan dakin ta d’aga tana amsa sallamar y….Yace.”Gwaggo wai gashi anty Sa’ida tace na siyo miki kosai.” Kar’ba tayi ta bude ladar ta bashi guda biyu tace.”To jeka nagode.” Yaron da sauri ya juya ya fita daga gidan da ‘kosan a hannunsa.

Gwaggo guda d’aya ta dauka tasa a bakinta ta ‘kulle ledar kunun tasha sosai tana jiran shigowar mutumin nata ta bashi……Baba Iro ne yayi sallama a dakin ya shiga ya zauna a nutse ya fara gaisheta ta amsa babu yabo babu fallasa a tare da ita.”

Yace.”Gwaggo sai hakuri da yanayin rayuwa yau na tashi babu kudi a hannuna shiyasa ba’a siyo miki kosai ba.” Tace.”Aa babu komai Ibarahim yau da gobe ai kayan Allah ne kana kokari damu sosai da sosai Allah ya cigaba da bud’a maka.”

Yace.”Ameeen ya Allah gwaggo ni zan tafi kasuwa.” Tace.”To ubangiji Allah ya bada sa’a .” ya amsa da ameeen ya rabbi.”

Bayan fitarsa da kamar minti goma Khalid ya shiga dakin cikin shirin fita, washe bakinta tayi tace”Sarkin ya’ki ina zuwa naga kayi kwalliya haka.”? zama yayi kusa da ita da fad’in “Gwaggo yau ake daurin auran wani abokinmu shine zamuje gurin daurin auran ni dasu Salim.”

Tace.”Allah sarki Allah ya sanya alkairi ya nuna mana lokacin naku.” babu kunya ya amsa da “ameeen Gwaggo.” Tace.”Ina fatan dai ka karya ko.”? girgiza kansa yayi yana yamutsa fuskarsa…..ta dauko jug din kunun da ‘kosan tace.”Khalid kada ka fita baka karya kummalo ba maza sha kunu ga kosai nan Sa’ida ce ta siya min.” Sai da ta fad’i maganar kuma tazo tana data sani dan tasan da ‘kyar idan zaici.

Girgiza kansa yayi yace.”Gwaggo ki bari kawai idan na fita zan tsaya gurin mai shayi nasa ya dafa min indomee.”

‘Bata rai tayi tace.”Khalid bana so ka saba da zuwa tevur din mai shayi kada kazo kuna rigima da iyalinka akan haka sabida wasu mazan haka zasu had’a matansu da koko su kuma su tafi tevur din mai shayi ayi musu hadin kauri susha.”.

Dariya yayi yace.”Gwaggo nima ba’a san raina nake zuwa ba lalura ce amma insha Allahu idan nayi aure na daina zuwa da yardar Allah.” tace.”To haka nake so naji kasan wani abu kuwa.”?

Girgiza kansa yayi yana kallonta tace.”Yanzu nake so na tafi gidan Uwale domin muje gurin wani malami ya taimaka mana akan Sa’ida Alamu sun nuna cewa ba’ka’ken aljanu ne suke damunta.”

Cike da mamaki yake kallonta kafin Yace.”Gwaggo aljanu kuma? A’ina Aunty Sa’idar ta had’u dasu dan Allah ki daina wannan maganar sannan kuma ki rabu da wannan Uwalen bata da kirki.”

Rike bakinta tayi da fadin”Kai jama’a wai shin me Uwale tayi muku ne kuke zaginta Sa’ida ma kafin ta fita sai da ta zageta tatas sannan ta futa haba Khalid Uwale bata cancanci hakaba.”

Yace.”To naji ni dai kada kije gurin malami aunty Sa’ida lafiyarta lau bata da wani aljanu zaki ‘bata kud’inki a banza ki wahalar da kanki a wofi.”

“Khalid da kake wannan maganar kai waye ya fada maka bata da iskokai sune fa suke shiga tsakaninku kuke saurin fad’a da juna ba kaga bakwa jituwa da juna ba nifa saboda kai zanje a taimaka mana a karkato da hankalinta kanka.”

Dariya yasa ya shiga sosa tarin sumar kanshi da tasha gyara sai kyalli take yace.”Ni dai idan saboda ni zakije gurin malami ki bari bana bukata da iskokai da babu aunty Sa’ida tawa ce babu wani aljani ko mutum daya isa ya shiga tsakaninmu soyayyata kuma da kaina zan dasa mata ita a cikin zuciyarta.”

“Umm!” tace alamun maganar bata gamsheta ba. Wayarsa ya dauko dake famar ringing yasa a kunne da fad’in “Salim ganin fitowa ina sallamar uwargidana ne.” Daga d’aya ‘bangaran Salim yace.”Wace uwargida bayan ban jima da ganinta ta tafi aiki ba.” ‘Yar dariya yayi yace.”Kai wannan ai amarya ce ina nufin uwargidana Gwaggo.” Salim yasa dariya da fadin”To yanzu na fahinta amma yana da kyau ka sallameta da wuri ka fito dan kai kadai muke jira mu tafi gurin daurin auran.” Yun’kurawa yayi ya mike tsaye da fadin” Gani nan ma fitowa na sallameta.” kashe wayar yayi ya kalleta babu cikakkiyar walwala a tare dashi yace.”Gwaggo dan Allah kada kije gurin nan.” Da sauri tace.”Haba ai na fasa zuwa kaga yanzu ma zan fara kad’in lagwani dan Salisu tun shekaran jiya ya kawo min da kudinsa.”

Yace.”Yawwa gwara ki tsaya ki nemi kud’inki shi yafi amfani ki dai cigaba da yi mana addua .” Tace.”To shikkenan Sarkin Ya’ki sai ka dawo.”
Fitowa yayi daga dakin yasa takalmansa masu gidan yatsa ya kama hanya ya fita daga gidan.

Sai da taji shuru ta daina jin motsin Ummatu sai ta yafa mayafinta ta futo da kwad’o (key) taja kofar dakin nata ta kulle sad’af-sad’af ta fita daga gidan, Gwaggo sai da ta ganta a gidan Uwale tukkuna hankalinta ya kwanta.

Uwale na dakin girki tana d’umame taji sallamar ‘kawar tata da sauri ta fito daga kicin din tana fad’in “Gwaggo ashe kina tafe.”? Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya da fad’in ” Wallahi tun safe naso nazo muje yaran nan Sa’ida da Khalid suka sani a gaba kamar munaf*cka haka na sid’ad’o na fito daga gida

Uwale tace.”Oh kiji ni da yara sai kace wa’inda suke auranki zasu hanaki fita.” Tace.”Kema dai kya fad’a Uwale.”

Dariya tayi tace”To shiga daki ki zauna na kawo mana d’umame muci sai mu tafi.” Gwaggo ta shiga dakin ta zauna Uwale ta shigo dakin hannunta dauke langa cike da d’umamen towon shinkafa da miyar kuka harda man shanu! nan suka ci suka koshi suka sha ruwa kana suka gyara lullu’bin mayafansu suka tafi gurin malamin zaure.

Kasancewar yau juma’a yasa sha biyu da rabi muka tashi, zaman da nayi da yunwa ya janyo min rawar jiki da zazza’bi a galabaice na shiga gidan na tarar dashi shuru ko’ina a bushe ‘Katon mukullin dana gani a kofar dakin Gwaggo yasa gabana ya fad’i wato dai Gwaggo sai da ta fita kenan…..Jakata na fara lalubawa ina addua Allah yasa na samu spire na key din dan dama rabawa mukayi ita ta dauki biyu ni kuma ta bani daya, cikin ikon Allah na lalubo key din dakin na bud’e na shiga Jin yanda ya dauki zafi yasa na d’age labulan na d’ora kan kofar hijabina kawai na cire na nemi guri na kwanta wai na d’an huta kafin na nemi abunda zanci…….Ba tare dana ankara ba bacci mai dadi ya dauke ni.

Koda ya shigo gidan kai tsaye dakin Gwaggon ya nufa yana fad’in “Gwaggo ina fata dai kin gamawa Salisu aikinsa dan yanzu ya tare ni a hanya yake min magan…….Kasa ‘karasawa yayi ganinta a kwance a dakin tana bacci! ajiyar zuciya ya sauke ya cire takalmansa a nutse ya shiga dakin .

Kai tsaye bakin gadon da take kwance ya zauna jikinsa na ta’ba nata, fuskarta ya tsirawa ido yana ayyana abubuwa da yawa a kanta, a hankali ya ra’ba ya kwanta a gadon ya nani’ka da jikinta sosai yasa hannunsa k’asan rigarta ya fara shafa cikinta da ‘kasan mararta ajiyar zuciya ya dinga saukewa yana sake nanuwa da jikinta yayin da yake sake cusa hannunsa cikin rigarta yana shashshafa cikinta da mararta sai yayi sama da hannunsa gabansa na fad’uwa ya d’ora kan breast d’inta guda breziyar ya d’an janye ya janyo brest d’in ya fito dashi cikin fitar hayyaci ya fara mulmulashi a hannunsa yana murza nipples d’in yana sakin wani irin nishi tare da cije lips d’insa…..

*Masoya a taimaka da sharing a gruops👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE……VIP GRUOP#600 NORMAL GRUOP#300….ACCOUNT.0542382124…..BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*8*
Kamar a mafarki nake jin al’amarin. motsi nayi da niyyar na gyara kwanciyata naji an matseni! lokaci guda gabana ya fad’i! da sauri na bud’e idona gabana na cigaba da bugawa ina kuma jin hucin numfashin mutun a wuyana! hannuna na karkarwa na d’ora a saman hannunsa dake matse da breast d’ina yana lugwigwitashi! hannun na ri’ke tamau! yawun bakinta ya bushe! innalillihi wa’ina ilaihi raji’un! waye wannan.”? cikin zuciyata nake wannan tambayar sabida rashin kunya hannuna na dam’ke da nasa amma a hakan yake ‘kokarin cigaba da ta’ba breast d’in. murya na rawa nace.”Khalid.”! Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke kafin naji muryarsa a shaqe ya amsa da “Na’am auntyna.”
Dama abinda nake so na tabbatar kenan! a sukwane! na mi’ke zaune juyowa nayi jikina na kyarma! na d’aga hannuna da niyyar kwad’a masa mari! yayi saurin ri’kewa yana girgiza min kai.

Yanayin yanda naga ‘kwayoyin idonsa sun sanja ne yasa nayi saurin sunkuyar da kaina k’asa wasu lafiyayyun hawaye suka shiga tsere a kan fuskata, Zuf d’in rigata a zuge breiziyata a ‘balle duk nonuwa na a waje yaron nan ya samu yana lugudarsu.

Jikina ya matso sosai har yanzu hannuna na ri’ke a hannunsa shima sai sai kyarmar jiki yake yace.”Auntyna kiyi hakuri kinji Allah kasa daurewa nayi.”

wani ‘katoton abu yazo ya tokare min a makogwaro! a sha’ke nace.”Khalid yaushe ka zama d’an iska? yanzu ni kake ‘kokarin haikewa wace irin mummunar rayuwa kake so ka jefa kanka a ciki.”?

Shuru yayi yana kallona nace.”Ka zuba min ido kana kallona ko Khalid ina kwance ina bacci kazo ka fito min da nono kana wasa dashi meye amfanin hakan.”?

Sumar kansa ya sosa a sanyaye yace.”Kiyi hakuri dan Allah na fad’a miki cewa kasa daurewa nayi dama kuma kullum sai nayi wasa dasu a mafarkina.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Khalid zama na a gidan nan ba zai yiwu ba tunda kana farautata zan tattara na bar muku gidan a yanzu nasan duk wanda zan tunkara da wannan maganar ba zai yarda ba saboda haka zan bar gidan shi yafi alkairi.”

Jikinsa na rawa yace.”Aa Aunty Sa’ida kada ki tafi ko’ina dan Allah ki zauna insha Allah ba zan ‘kara ba cikin satin nan ma zan koma skull sai ki zauna lafiya tunda bana nan .”

Hannuna na fizge daga nasa na gyara rigata sauka nake ‘kokarin yi daga gadon ya ru’kun’kume ni! jikinsa na rawa yace.” Dan Allah ki tsaya ki fahimce ni wallahi banyi miki hakan da wata manufa mara kyau ba aunt Sa’ida sha’awarki ce tayi min yawa shiyasa dana samu wannan damar na rage.” Yana maganar yana tatta’ba min kirji.”

Tunkud’eshi nayi a fusace! nace”Ba zaka shiga hankalinka ba ko.”? kamar wani zautacce ya sake kawo min raruma! da yake abin yazo min a bazata sai kawai muka fad’i a gadon a tare! kafafunsa yasa ya hard’e nawa! ya ri’ke ni tsam! yana shanshana jikina kamar tsohon karan da ya samu nama d’anye.

Hankalina ya tashi nace”Khalid sake ni na tashi.” “Um!um!.” yafad’a cikin sigar shagwa’ba, tsigar jikina ta tashi! “Khalid ba zaka sak……Kasa ‘karasawa nayi jin bakinsa a cikin kunnena yana tsosa!

Ihu! na kurma! da karfin gaske! na kai masa duka! ” Dan ubanka ba zaka sake ni ba.”! nafada ina haurinsa da kafafuna! kamar maye ya ri’ke ni tsam! yana tsotsar kunnena da gefan fuskata sai so yake ya kamo bakina ina kaucewa.

Kuka na shiga yi ina rokonsa ya sake ni na tashi, da kyar yace.”Kin amince da maganata.”? Da sauri nace”Wace magana.”? A shaqe yace.”Ta aure mana.” naji kamar ya watsa min wuta a jikina, domin ya sake ni nace na amince.”

Ajiyar zuciyarsa naji kafin ya sassauta ri’kon da yayi min. nayi saurin fizge jikina na dira daga gadon ina haki da nishi! dakin na shiga bi da kallo! can na hango wayar da gwaggo take chaza redion ta, ita nai saurin daukowa na nannad’e ta a hannuna, a fusace! nayi kansa da duka! dirgowa yayi da sauri yayi hanyar fita yana dariya, hawaye na zubo min na bishi da duka amma ko d’aya ban sameshi ba abinka da d’an ball tsalle ya buga ya tureni ya fita daga dakin yana dariya.

Zubewa nayi a gurin na dinga kukan bakin ciki ina nadamar abinda ya faru a tsakanina dashi…..ya zama dole nayi nesa da yaron nan kada watarana ya haike min ya rabani da budurcina.

Da kyar na iya wanka nayi sallolina kana na d’ora farar shinkafa tunda inada miya dama haka nake sai nayi miya ta kwana uku ko hudu sai dai kawai na dinga amfanin da ita.

Agogo na duba karfe hudu da rabi na yamma babu labarin gwaggo, al’amarin ya dinga bani mamaki yana daure min kai, kasa daurewa nayi naje na samu Ummatu tana hidimar d’ora abincin dare nace”Ummatu dan Allah ko kin san inda Gwaggo taje.”?

Ba tare data dauki maganata da muhimmacin ba tace”Ni kam ban sani ba.” a sanyaye na fito daga gurin wanda yayi dai-dai da shigowarta. hannunta ri’ke da leda viva.

Kallo na shiga bin ta dashi , ta wani sha kunu da fad’in “Meye kike kallona ko kin aike ni ne.”? Nace.” Gwaggo yanzu dan Allah sai da kika je.”?

Shareni tayi ta shige daki, bayanta nabi naga tana kokarin d’aga gadon karfenta ina tsaye naga ta tusa ledar ciki ta mayar da zanin gadon ta rufe, nace”Ledar me kike ‘boye.”?

A fusace! tace.”Sa’ida ba zaki daina tit*iye ni ba ko.”? Girgiza kaina nayi na rabu da ita, taja tsaki tare da daukar buta ta fita.

‘Daure da alwala ta shigo dakin, na kalli agogo biyar shaura minti biyar nace.”Gwaggo a’ina kika tsaya baki sallah ba duba kiga lokaci fa.”

Ci kanki ba tace dani ba ta gyara dadduma ta tayar da sallah! ajiyar zuciya na sauke na fita daga dakin ina tunanin hanyar da zanbi gurin dauko ledar data ‘boye a ‘kar’kashin gadonta.

“Sa’ida idan kin gama abincin zubo min naci.” muryarta naji daga cikin dakin tana magana. nace.”Bangama ba tukkuna.” Tace .”Salisu mai kanti ya aiko ko.”? nace”Ban sani ba dan nima bacci nayi bayan na dawo daga makaranta.

Tace.”To koma dai ya aiko to sai dai yayi hakuri dan yanda na gaji d’in nan bazan iya tsinana komai ba.” Nace.”Wai dan Allah gwaggo ina kikaje kada kice min kinbi Uwale gurin malami.”

Shuru tayi bata tanka ba, sai nima nayi shuru na kyaleta, abincin na ‘karasa dahuwa na zuba mata da yawa a plate nasa mata miya da kifi na kai mata.

Da sauri tace.”Yawwa babbar mace nagode.” ruwa na d’ebo mata na ajiye mata a gabanta na fita daga dakin, a nan tsakar gidan na zauna naci nawa abincin na gyara gurin tsaf na koma dakin.

Tace.”Haba Jama’a yanzu naji dai-dai.” shuru nai mata na cigaba da abinda nake, a nutse ta kira sunana, na juyo ina kallonta tace.”Naji kina cewa malami me magani zaki ce dan mu ba gurin malamin zaure mukaje ba.”

Nai shuru ina sauraranta ta cigaba da cewa “Na fad’awa mai magani duk abinda yake damunki kuma ya had’o miki magani Sa’ida inaso ki bani had’in kai dan Allah kiyi amfani da maganin nan domin hankalina ya tashi dana ji yace wai ‘bakin aljani ne ya aureki shiyasa bakya so ayi miki maganar aure kuma shine yake shiga tsakaninki da Khalid kuyi ta fad’a kuna samun sa’bani wallahi Sa’ida bakiji yanda hankalina ya tashi ba.”

Cike da mamaki nake kallonta kafin nace”Gwaggo nice nake da ‘bakin aljani.”? da sauri tace.”Eh mana ko kina kokwanto ne.”? nace.”Kwarai kuwa Gwaggo ni ban yarda ina da iska ba saboda haka asarar kudin ki kawai kikayi.”

Marairaice fuska tayi tace”Haba Sa’ida ya zakice baki yarda kina da iskokai ba yanzu shekarunki nawa a duniya kina zaune babu aure duk sa’onin ki sunyi aure sun haihu yaransu sun wayo amma ke kina zaune duk namijin da ya yun’kuro da niyyar auranki sai ya gudu ko kuma a d’aure masa baki a hanashi magana wannan fa duk sharrin iska ne.”

Murmushi takaici nayi nace.”Gwaggo ni abinda na kaddarawa rayuwata shine aure lokaci ne duk yanda naso da nayi aure idan lokacin baiyi ba dole na hakura kuma kina maganar cewa na girma nayi shekaru babu aure ai bani kad’ai bace akwai dubban matan da suke zaune babu aure da yawa daga cikinsu ma sunfi ni girma da shekaru saboda haka ki daina wahalar da kanki akan al’amarina duk ranar da Allah ya kawo lokacin aurena babu mahalukin daya isa ya hana.”

Tace.”Eh duk da haka Sa’ida bakiji bahaushe yana cewa idan kana da kyau ka ‘kara da wanka ba ni na yarda da maganar mai maganin nan domin aljani yana da suddabaru iri-iri saboda haka dan Allah kada ki watsa min ‘kasa a ido.”

Murmushi nayi nace.”Gwaggo kenan dan Allah ki bar maganar nan kinga lokacin sallah yayi kije kiyi alwala ki sallah ki roki Allah ya za’ba min abinda yafi alkairi.”

Tace.”Sallah ko kince nayi ko baki ce nayi ba dole nayi kuma Ubangiji shima ya fad’a cewa bawa ya tashi ya nema shi kuma sai ya taimakeshi.” Nace”Gwaggo ba’a irin wannan al’amari Ubangiji yayi magana ba, Allah yace.” Ko ro’keni ni kuma zan amsa muku amma bece wani bawan sa yaje gurin malamin duba ba.”

A tunzure! tace”Wai Sa’ida waye yace miki gurin malamin duba mukaje.”? Nace.”Gwaggo dan Allah maganar nan ta mutu haka magani dai idan dan ni kike siyo to kinyi asarar kudin ki dan bazan sha ba.”

Ina gama maganata na fita daga dakin na barta tana bina da kallo.

Bayan mun idar da sallar sai ta mike ta fita daga dakin minti biyar ta dawo hannunta dauke da karamin kaskon wuta da garwashi a ciki…….kallo na bita dashi ganin ta d’aga ‘karkashin gadonta tana lalube ledar data shigo da ita ta dauko ta saki zanin gadon ta rufe……..ta shiga zazzage magungunan dake cikin ledar…..Wani tsumma ta kwance naga ta d’ebo maganin dake ciki ta zuba a wutar a take dakin ya turni’ke da haya’ki! tari ya sar’ke ni! haya’kin maganin ya dinga shiga bakina da hancina! a gigice na mi’ke na fita daga d’akin ina tari da rirri’ke kirji, ko gama dawowa hayyacina banyi ba itama ta fito daga dakin ido jazur! sai tari take hawaye na zuba daga idonta……

*Masoya a taimaka da sharing👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR KI BIYA KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE…..VIP #600 NORMAL#300 …..ACCOUNT….. 0542382124….BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*9*
Haka Baba Iro ya fito ya same mu a tsaye muna tari ga haya’ki na fitowa daga cikin dakin. “Gwaggo lafiya me yake faruwa ne.”? Miyau ta had’iya ido jawur tace.” Haya’ki na kunna sai tari ya sar’ke muka fito muna shan iska.” Yace.”Gwaggo wane irin haya’ki ne wannan mai cutarwa.”?

Da sauri tace.”Na mayu ne kwana biyu kasala tana damuna shine Uwale ta kawo min dama kuma ai sa’i da lokaci ina kunnawa .”

Shuru yayi yana kallonta nima na zuba mata ido ina mamakin ‘karyar data shirga. Dakin ya shiga da sauri tabi bayansa tana kallonsa tace.”Ibarahim me kake nema.”? Yace.”Garin haya’kin zan duba nagani.” Tace.”Aa ba sai ka wahalar da kanka ba ai ragowa ne na barbad’a a wuta shine fa ya turnu’ke gidan da haya’ki.”

Yace.”Gwaggo dan Allah ki daina yarda da camfi irin na mutane wane maye ne zai kamaki acikin unguwar nan.”? Tace.”Aa Ibrahim ai shi maye bashi da kama watakila ma ina hurd’a dasu ban sani ba, to dan nayi haya’ki ai ba laifi bane.”

Yace.”Hakane gaskiya to dan Allah gwaggo kisan irin haya’kin da zaki dinga yi duba dai wannan kinsa gashi gabad’aya ya sar’ke muku numfashi.”

Da sauri tace.”Ai yau ne kawai hakan ta faru amma lafiya lau nake haya’kina to tunda ma dai maganin ya ‘kare ai shikkenan.”

Fita yayi daga d’akin ya kalleni cikin taushin murya yace.”Sa’ida ki cigaba da hakuri da halin gwaggo ina nan inayi miki addua akan Allah ya kawo miki miji kiyi auranki.”

Hawaye naji na kokarin kufce min nace.”To Kawu nagode sosai.” Yanda na lura dashi shima yana damuwa da halin mahaifiyar tasa dan dai bashi da yanda zaiyi da ita ne.”

Dakin na shiga na sameta tana gyara shimfid’a k’aurin maganin da haya’kinsa ya dinga sanyawa kaina yana juyawa bana tsammanin zan iya kwanciya a dakin domin kuwa zuciyata in banda tashi babu abinda take.

Tabarma da bargo na dauka na fita daga dakin….shimfid’awa nayi a wani dan loko a tsakar gidan na koma dakin na dauki fillo da wayata, kallo ta bini dashi har na fita daga dakin.

Gwara na kwanta a tsakar gidan yafi min alkairi.” Waya ta na bude ina dubawa naga text d’in Alhaji Nura wai yana nan fa yana jiran amsa daga gare ni, murmushi kawai nayi ba tare dana bashi amsa ba na shiga WhatsApp ina dubawa………Gwaggo da buta hannunta ta fito daga dakin ta nufi bandaki tayi uzirinta ta fito, sai da tazo kusa dani naji tana fad’in ” ‘Dakina ne babu wanda ya isa ya hanani yin abinda naga dama mutum yayi ta kwana a tsakar gida sauro ma ya ishe shi.”

Uffan bance mata ba na cigaba da duba wayata, ta ajiye butar a bakin kofar dakin tace.”Ai tabbacin mutum na tare da iskokai kenan gashinan ai saboda hayak’in yana da k’arfi sun koro ki daga d’akin ai duk abinda zakayi ba zan fasa turara haya’kin nan ba.”

Ta gama surutan ta ban tanka mata ba cikin zuciyata ina ta shawarar matakin da ya kamata na dauka Khalid yana barazana ga rayuwata gwaggo tana kuntukawa zuciyata barina gidan shine yafi alkairi…..”Sa’ida idan kin koma gidan mahaifiyarki anya kuwa ba zaki takura mata ba.”? zuciyata ce take tunasar dani…..Ummana bayan rasuwar mahaifina wanda ta aura babban mutum ne mai iyali itace matarsa ta uku kuma bata dad’e a gidan ba ya cikashe ta hud’un babban gida ne mai d’akuna kowace na rayuwa ita da ‘ya’yanta a dakinta sai dai duk ranar girkinta taje dakin maigidan……Alhaji Shamsu babban mutum ne kuma d’an kasuwa yana da shaguna masu yawa a kanti kwari suna harkar atamfofi tun bayan auransa da Ummana yaso na koma hannunsa Gwaggo tayi ta tsula musu rashin mutunci daga shi har Ummana tace babu wanda ya isa yayi iko dani tana raye jininta ba zaiyi agolanci a wani gidan ba.

Ganin irin rigimar da takeyi ne yasa duk suka hakura hidima sosai mijin Ummana ya dinga yi min duk sabgar karatuna shine ya dauki nauyi kuma duk ranar da naje gidan ziyara yakan bani kudi masu yawa na tabbata a yanzu idan nace zan koma gidan da zama zaiyi farin ciki sosai kuma zai kar’be ni da hannu biyu, tabbas akwai yiwuwar na koma gaban mahaifiyata da zama dan al’amarin gwaggo da Khalid yana nema ya shallake tunani na.

“Sa’ida ya kike kwance a tsakar gida ke kad’ai.”? Muryar Baba Iro naji a kaina. Da sauri na mike zaune da fad’in” Wallahi zafi ne ya isheni na fito amma idan gari ya saki zan koma daki.” Yace.”To shikkenan amma ina fatan sauro baya damun ki.”? Nace.”Eh da sauki tunda na kunna magani.” yace.”To babu damuwa.”

Labulan d’akin Gwaggon ya daga yana dubata. Sunanta ya kira yaji shiru nace.”Ai da alama tayi bacci.” yace.”Eh hakane to sai da safe.” Nace.”To Kawu Allah ya tashe mu lafiya.”

Yana barin gurin na koma na kwanta waya ta na kashe na rufe jikina tare da addua a bakina.

Yana can gurin kallon ball sai kusan sha biyu shaura ya shigo gidan……shuru ko’ina yayi duhu da sauri ya fito da wayarsa ya kunna torchlight idonsa ne ya sauka kanta tana kudindine a cikin bargo garin ya saki ana iska sosai dalilin da yasa kenan cikin bacci taja bargon ta rufe jikinta har kanta.

Tsayawa yayi a kanta yana kallonta tare da haske ta da hasken wayarsa, a hankali ya tsuguna kusa da ita yasa hannu ya bude mata fuska idonsa ne ya sauka kan wayarta da take kusa da ita ya dauka da sauri ya mi’ke daga gurin.

Dakinsa dake cikin gurinsu ya bude ya shiga ya zauna bakin katifarsa a nutse ya kunna wayar ya shiga yi mata binkice, babu wasu tarkacen numbobin maza a ciki yaji dadin hakan Number Alhaji Nura ce kawai itama yana ganinta ya gogeta yana tsaki! yana kokarin kashe wayar text ya shigo.

Da sauri ya shiga yana dubawa, text ne daga Alhaji Nura ga abunda yake cewa.

_Gimbiyar mata kinyi shuru baki bani amsa ba kuma nasan kinga messengers d’ina Sa’ida ko kuma na cire tsammani ne.?_

Ya dinga wani irin huci! kibiyar kishi na sukar sa a ma’kogwaro a duniya nan bashi da babban wanda ya tsana kamar mutumin nan.

Hannu na rawa ya fara bashi amsa kamar haka.

_Alhaji kayi hakuri fa ban san amsar da zan baka ba shiyasa kaji nayi maka shuru to amma yanzu tunda ka tsananta inso na tabbatar maka da cewa ina da miji zamuyi auran zumunci da ‘Dan uwana Khalid saboda haka dan Allah ka daina bibiyar rayuwata haka._

Tura masa text din yayi ya kashe wayar, fulas din abincin sa ya janyo ya bude a nutse ya fara ci bayan ya kammala ya dauki pure water guda yasha ya mike ya fita da wayar a hannunsa

Har yanzu tana kwance a tsakar gidan…..a jiye mata wayar yayi a kusa da ita ya juya da niyyar barin gurin shawara ya sanja ya dawo a da baya.

A hankali ya tsuguna gabanta ‘kasa-‘kasa ya shiga kiran sunanta…..mafarkinsa take gashi wai suna kwance a gado d’aya sun lullu’ba da bargo suna wasu abubuwa masu dad’in gaske, kawai ta dinga jin sautin muryarsa a kanta yana kiran sunanta.

A firgice ta mike zaune tana zazzare ido a kansa “Khalid me kakeyi anan gurin.”? bakinta na fara tayi maganar tana dudduba jikinta addua take Allah yasa mafarkinta ba gaskiya bane.

A tausashe yace.” Babu abinda nake ban jima da shigowa ba na ganki a kwance ke kad’ai aunty Sa’ida akwai sauro ki tashi ki koma a d’aki.”

Shuru tayi masa ta mike da sauri ta fara kwashe kayan shimfid’ar sai ya shiga taimaka mata suka kwashe kayan shimfid’ar a tare, duk shige da ficen da suke Gwaggo nacan tana shirgar baccinta.

Fitowa tayi da niyyar kama ruwa, kawai sai ta ganshi a tsaye a jikin bango(Garu) gabanta ya fad’i! tai saurin dauke kanta hannunta ri’ke da buta ta nufi bandakin.

Koda ta fito yana nan tsaye a inda yake……Sai tasha jinin jikinta cikin sauri tayi nufin shiga dakin ya tare mata hanya…… shuru tai tana kallonsa yasa kirjinsa ya danne nata sai ta jingina jikin bango(garu) bata so tayi magana jama’ar gidan su tashi in banda Kawu Iro babu wanda zai yarda da ita Ummatu da Gwaggo zasu ce sharri tayi masa.

Yasa hannunsa ya zagaye ‘kugunta dashi sosai ya matseta a kirjinsa yana sakin wani irin nishi kafin yayi magana da wani irin voice “Auntyna dan Allah ki taimaka ki bani bakinki nasha kinji ko.”

Shuru nayi masa ya dinga wasu irin sambatu yana ya mutse min jikina……”Khalid kafi karfina sharrin ka ya girmi tunani zan had’aka da Allah yayi min maganinka.” cikin rawar murya nayi maganar.

Jikinsa na kyarma ya tallafo fuskata a hankali yace.”Auntyna kada ki had’ani da Allah idan na lalace kema kin lalace aunty Sa’ida bani da laifi kaunarki ta riga ta gama kassara ni mutukar zan gan ki nakan rasa nutsuwata dan Allah da darajar Annabi Muhammad (SAW) ki amince da soyayyata.”

Girgiza kaina kawai nakeyi hawaye bakin ciki da takaici na kwararo min…..Harshensa yasa ya shiga lashe hawayen yana tsotsar kumatuna kokarinsa ya kamo bakina na fuzge fuskata da sauri nasa ‘karfi na tureshi yayi taga-taga zai fad’i! da sauri ya fizgo hannuna a lokacin da nake kokarin shiga dakin kawai na jini a kwance a kirjinsa……..Bakinsa yasa a daidai kunnena yana sakin wani irin nishi kafin yasa hak’ori ya d’an ciji fatar kunnena da fad’in “Kina so rayuwata ta salanwace ko aunty Sa’ida mutukar baki amshi soyayyata ba zan iya rungumar transformer ta tashi dani na bar duniya.”

Ji nayi kamar na shaqe masa wuya saboda takaici na sake yunkurin tureshi ya ri’ke ni gam! gam! yana shanshana jikina tsigar jikina ta dinga tashi………….”Kada dai wannan yarinyar bata shigo ba.” Muryar Gwaggo ce ta doki kunnuwanmu da sauri muka kalli bakin kofar d’akin hasken torchlight d’inta dalll! da alama fitowa tsakar gidan take kokarin yi da sauri ya sake ni yayi gaggawar shiga gurinsu, ni kuma jikina na rawa na d’auki butar dake ajiye a bakin kofa….ta fito daga dakin tana surutai gani na yasa ta dauke kanta ta nuna kamar bata damu ba nima bance mata komai ba na mika mata butar ta ta kar’ba da sauri na shige dakin ita kuma ta nufi bandaki…

*Masoya a takaima da sharing👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE….VIP GROUP #600 NORMAL GROUP…. #300…..ACCOUNT… 0542382124…..BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

_*Free pege ya kusa ‘karewa kuyi maza ku hanzarto domin ku biya kudin karatu🥰🤝🏻 Masu tambayata na turo musu littafin su biya kudinsu sai a sasu a gruop😊 Sannan dan Allah masu plashing su bari! idan kin san ba siyan book d’in nan zakiyi kada ki dauki number ta kiyi min magana dan Allah mu muntuna junanmu🤝🏻 Masoya masu kaunar cigabana ina sauraranku fa💃🏻 Free Pege ya kusa ‘karewa ku hanzarto!!!!*_

*10*
Na jima kafin bacci ya dauke ni. Da safe kuma na tashi da wata irin kasala da damuwa dan ina idar da sallar asubahi ko hijabin jikina ban cire ba na kwanta kan daddumar. idona kawai na rufe ba don nayi bacci ba sai dan tunanin yanayin rayuwa hakika abunda ya faru tsakanina da Khalid ya tsaya min a raina na rasa yanda zanyi na tunkari gwaggo da maganar gashi ina jin kunyar Baba Iro na ce masa d’ansa yana min me? al’amarin da akwai nauyi da kuma kunya idan ya yarda to na tabbata Gwaggo da mahaifiyarsa Ummatu ba zasu yarda ba zasu ce nai masa sharri ne, amma haki’kanin gaskiya lamarin da akwai ban tsoro da firgici a ciki ina tsoron ranar da zai samu galaba akaina to kuwa tun kafin zuwan ranar gwara na nemawa kaina mafita.

Idona a rufe na soma jin ‘kaurin maganin jiya a hancina. da sauri na bude idona na mike zaune ina kallonta tana tsaye a kaina da ‘karamin kasko a hannunta tana turare ni haya’ki.

Da saurin gaske na miqe dan har sai dana bugeta waje na fita na tsaya a tsakar gida ina mayar da numfashi wani irin jiri da ciwon kai ne yake taso min.

Fitowa tayi da haya’kin tana fad’in “Sai dai idan waje zaki fita amma duk inda zaki shiga a gidan nan sai na turara miki haya’kin nan dan ba zanyi asarar kudina a banza ba.”

Ido jawur na kalleta tana sake kusanto inda nake da haya’kin nace.”Gwaggo Kina so ‘bakin cikin ku ya kasheni ko.”? Shuru tayi min ta cigaba da turo kaskon haya’kin inda nake.

Takalma na nasa da sauri na kama hanyar fita daga gidan kamar wata zararriya. tace.”Au! futar zakiyi kuwa.”? ko kallonta banyi ba nasa kai na fita daga gidan.

Karo muka buga a lokacin da yake kokarin shigowa hannunsa rike da wata k’aramar bakar leda.

Yanda yaga jikinta na rawa yasa yayi saurin rike hannunta a nutse yace.”Aunty Sa’ida ina zaki da sassafe haka? yau asabar babu makaranta.”

Zuciyata ta karye na daure ban bari hawayen sun zuba ba nace.”Khalid Sake ni.” Girgiza kansa yayi a tausashe yace.”Ba zan sake ki ba aunty dan na lura bakya hayyacinki.”

Ido na tsira masa shima ya tsira min nasa, a haka Baba Iro ya shigo ya same mu….Gyaran muryar da yayi itace tasa muka ankara da shigowarsa yace.”Lafiya na ganku a tsaye a soro.”?

Hannuna dake cikin nasa ya sake ri’kewa yace.”Baba da alama babu lafiya dan nima nazo shigowa mukayi karo da ita zata fita a gigice.”

A nutse ya kalleni da fadin”Sa’ida me yake faruwa ne.”? Hawayen da nake kokarin dannewa suka kucfe nace .”Kawu maganar dai guda d’aya ce.”

Yace.”Gwaggo ce ko.”? kaina na d’aga nace”Eh tun jiya ta hanani zaman lafiya a dakinta tace aljanu ne dani kawai yanzu ina kwance na ganta a kaina tana bunka min haya’ki.”

Baba Iro ya shiga girgiza kansa yana mamakin halin rigima irin na mahaifiyarsa. yace.”Sa’ida kiyi hakuri kinji ko mu shiga gidan za’a sasanta.”

Nace.”Kawu nifa idan ba haya’kin nan ta daina bunkawa ba ba zan shiga dakinta ba.”

Khalid yace.”Muje duk inda haya’kin yake zan daukeshi na yar dashi.”
Jin abinda yace yasa na yarda muka shiga gidan a tare.

Suna tsaye ita da Ummatu suna magana……”Wallahi ajanu ne da ita gashinan daga jiya zuwa yau duk ta kasa nutsuwa sakamakon turaran da nake mata kinga yanzu tayi waje a gigice.” Ummatu tace.”To ai kuwa tunda dai an gano bakin zaren sai a cigaba da nema mata magani…..shigowarmu yasa duk suka kallemu.

Khalid kai tsaye dakin ya nufa yana neman maganin Gwaggo kamar ta sani ta dauka ta bawa Ummatu ta ‘boye mata….Kawu Iro yace “Gwaggo wannan wace irin rayuwa ce dan Allah ya kike nema ki furgita yarinya kina cewa tana da aljanu a ina suke? Gwaggo na fad’a miki ki daina yarda da surutan mutane akan yarinyar nan shi aure lokaci ne dashi idan lokacinta yayi za tayi aure amma dan Allah ki daina d’ora mata lalura yanzu ina amfanin abinda kikayi Gwaggo da sassafe kin bunka a haya’ki a gida kin firgita yarinya tunda tace bata so ba sai ki k’yaleta ba.”

“Kai Ibrahim ba fa zanyi asarar kudina ba dole sai nayi haya’kin nan tunda d’akina ne kuma idan ba aljanun ne da ita ba me yasa take guduwa mu da muke shak’ar haya’kin me yayi mana saboda haka ba zan fasa abinda nayi niyya ba idan tana da inda za taje ta tafi.”

Khalid ya fito daga dakin fuska a murtuke yace.”Gwaggo ina haya’kin naga irinsa.” Kallonsa tayi lokaci guda ta fahimci abinda yake da akwai tace.” Babu sauransa kenan nasa a wuta.”

Kawu Iro yace.”Gwaggo jiya ma fa haka kika ce sai gashi kuma yau da safe kin kuma kunnawa.” Kuka ta fashe dashi tace.”Yanzu dai kunyi min taron dangi kenan kuna kokarin ‘karyata ni ko.”?

Kawu Iro hankalinsa ya tashi ya dinga rarrashinta tace.”Oh!oh! Ibrahim ai ‘yar d’an uwanka ta fini a gurinka tunda gashinan a kanta kana nema ka ‘kure ni.”

Yace.”Aa Gwaggo wallahi ba haka bane ina ni ina ‘kure ki nayi laifi ki yafe mun.” Ba tare da tace komai ba ta shiga dakinta ta bar mu a tsaye.

Kallonsa nayi naga duk hankalinsa ya tashi nace.”Kawu ka kwantar da hankalin ka insha Allahu zan cigaba da hakuri da halinta.” Yace.”Yawwa Sa’ida dama abinda nake so kenan naji daga gurinki kiyi ta addua kinji ko komai mai wuce wa ne.” Cikin dauriya nace.”To Kawu nagode.” Gurinsu ya nufa ya barmu nida Khalid a tsaye…..Yace.”Aunty Sa’ida kada ki damu duk inda ta ‘boye haya’kin zan bincika a dakin.”

Nace.”Khalid kyaleta dakinta ne fa tayi duk abinda take so da abunta.” “Eh d’akina ne Sa’ida idan kinyi zuciya kada ki sake shigowa.” Tana daga cikin dakin take magana.

Yace.”Gwaggo wace irin magana ce wannan.”?

“Haba Jarumi ai dole raina ya ‘baci akan al’amarin nan ranar da naje ‘karbo maganin nan sai da na yini banci ba bansha ba salloli na ma sai had’asu nayi amma saboda wukalancin Sa’ida ta dinga kokarin watsa min ‘kasa a ido.

Yace.” To wai waye ya saki ne? sai fa da nace dake kada kije okey to zanje har gidan ita Uwalen da take janki yawon gurin masu magani na gargad’eta akan hakan ni idan kinyi min baki ba zai kamani ba tunda dai ni ba Baba Iro ba ne.”

Kuka tasa daga cikin dakin take fad’in “Khalid kada kaje kaci mutuncin Uwale bata cancanci hakaba.” Ya d’aga labulan d’akin da fad’in.”To idan bakya so naje gidan Uwale dauko min haya’kin.”

Tace.”Shigo ka kar’ba.” da sauri ya shiga dakin nima naji wani sanyi a cikin raina…….Wani tsohon magani ta d’auko masa a ‘karkashin gadonta a daure a wata tsuhowar leda ta mika masa da fad’in”Gashinan wannan jaraba ta isheni haka.”
Kar’ba yayi ba tare da ya tanka mata ba ya fito daga dakin.

Yana fitowa yace.” Ki kwantar da hankalinki ga maganin nan a hannuna zan fita dashi na zubar.”

Hannunsa na kalla a take na gane ba maganin bane domin wancan a k’ulle yake b’akar leda wannan kuwa ledarsa yaluwa ce…..girgiza kaina kawai nayi na wuce na barshi a gurin, dakin na shiga na sameta tana murd’a redion ta ta dago kanta ta kalleni ta dauke kai tana cigaba da abinda take……gurin dana kwanta na nufa na dauki wayata na nemi gefan gado na zauna wayar na kunna na fara dube dube a ciki…….Ummatu ce ta shigo da jug d’in kunu da mai daidaiciyar silba da ‘kosai a ciki.

Abin mamaki cikin mutuncin Gwaggo ta kar’ba “Sannu ‘yar albarka ai Ibrahim yayi sa’ar mata Rabi wallahi ina jin dadin zama dake sabida kina mutunta ni Allah yayi miki albarka.”

Ita kanta Ummatu sai da tayi mamaki da yake tasan halin Gwaggo sai tayi dariya kawai ta girgiza kanta ta fita daga dakin….Nima dana san dani take ban tanka mata ba na cigaba da duba text d’in da Alhaji Nura ya turo ina mamakin al’amarin…..Kiran wayarsa ne ya katseni da sauri na d’aga nasa a kunnena.

Yanda ya amsa gaisuwata yasa naji jikina yayi sanyi nace.”Alhaji naga text dinka amma kuma ban fahimci abinda kake nufi ba.”

A d’an fusace! yace.”Sa’ida kada ki mayar dani ‘karamin yaro mana, jiya kin turo min text din daya hanani bacci amma yanzu kina wata magana.”

A nutse nace.”Alhaji kayi hakuri kayi min bayanin da zan fahimta na dai ga text d’inka amma ban mayar maka da replay ba.”

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Haba Sa’ida kada kiyi wasa da hankalina mana, nifa ba yaro bane ballanatana kizo min da wasa da gaske nake auranki zanyi amma me yasa kin san akwai al’kawarin aure a tsakaninki da yaron nan Khalid kikayi wasa da hankalina.”

Jikina yayi sanyi nace.”Wace irin magana ce wannan waye kuma Khalid.”? Lokacin da nayi maganar tayi daidai da lokacin daya shigo dakin shida Gwaggon suka zuba min ido….na cigaba da cewa.”Alhaji ina tambayarka kayi shuru waye Khalid da har kake wata magana akansa yanzu a duniya na rasa mijin aure sai Khalid dan Allah ka daina wannan maganar sannan kuma text d’in daka gani mybe shine ya dauki wayata a bayan idona ya turo maka amma ni da hannuna wallahi ban tura maka wani text ba.”

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Okey to har naji dadi a cikin zuciyata yanzu a’ina maganarmu ta kwana.”? nace.”Insha Allahu yau ko gobe zan yanke shawara.” Yace.”Haba Sa’ida wace irin shawara ce wannan da har yanzu ba’ai yanke ba.”?
Nace.”Alhaji ka ‘kara hakuri dan Allah.” Yace.”Shikkenan tom ina sauraranki.” Sallama mukayi na kashe wayata rai a ‘bace na kalleshi yana tsaye idonsa ya kad’a yayi jajazur!! sai wani irin kallo yake min.

“Khalid waye ya baka izinin d’aukar min waya.”? Kai tsaye yace.” Ni ne na bawa kaina izini ko kina da abinda zakiyi ne.”? Cike da mamaki! nake kallonsa.

Ya zare min manyan idonsa da suka rine da ‘bacin rai da ‘bakin kishi yace.”Ni kike ciwa fuska ko.”? Nace.”Meye abin cin fuska sarkin tsaurin ido ina kai ina Alhaji Nura da har zaka dauki wayata ka rubuta masa text kasan dai ya kusa haifarka ko.”?

Yana ‘kokarin magana Gwaggo tace.”To daya kusa haifarsa mai zai nuna masa? namiji yake shima namiji yake sannan duk abinda yake dashi shima yana dashi sai me kuma.”?

Kallonta nayi tace.”Mara mutunci wacce bata san mai sonta ba, dame Alhaji Nuran yafi Khalid da har zaki dinga ci masa fuska.”

Nace.”Kinga Gwaggo ki cire kanki daga cikin wannan maganarki babu ruwanki ni babu wanda ya isa yayi min dole a gidan nan wanda nake so zan aura bana auran ‘karamin yaro a kyaleni.”

Gwaggo ta fashe da kuka had’e da fad’in “Zagi na Zakiyi ne naga kina zaburowa ko kuma dukana zakiyi butulu kawai.”

Hawaye suka shararo min nace.”Me nayi na butulci kuma? ina zaune a gado na mahaifina ina ciyar da kaina sai me? me nayi na butulci da har kike kirana da kalmar.”

Jikinta ne kuma yayi sanyi ganin ina kuka…..Girgiza kansa yayi ya fita daga d’akin zuciyarsa kamar ta babbake saboda ‘bacin rai.

Bayan fitarsa na share hawaye mi’kewa nayi na fara had’a kayan wanki, sai naga tana satar kallona cigaba nayi da abinda nake tace.”Sa’ida kinga yau ‘kosan yayi kyau gashi da zafinsa ki zuba kunun kisha sai kiyi wanki.”

Nace.”Aa Gwaggo ba zan sha kunu ba kisha kawai.” Shuru tai tana kallona tsaf na gama had’a wankin na fita dashi can bakin rijiya na zubesu komawa dakin nayi na dauko indomee biyu ‘karamin gas d’ina na kunna na d’ora tukunya da ruwa akai na zuba indomee a ciki…..ina zaune a gurin ta dahu na juye a plate kana na kashe gas d’in. Nan tsakar gidan na zauna a nutse naci na fara ci ina Nazarin rayuwa wai ni Gwaggo take kira da Butulu hummm! rayuwa kenan.

*Masoya a taimaka da sharing👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE…..VIP GRUOP#600 NORMAL GROUP #300 ACCOUNT… 0542382124…..BINTA UMAR GTBANK….IDAN KATI ZAKI TURO #400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_

*13*
A daran ranar Gwaggo kasa rintsawa tayi asubar fari ta tashi tai alwala tayi sallah da carbi a hannunta ta fito kai tsaye gurin baba iro ta nufa ta shiga bubbuga musu kofa. Lokacin shi yana massalaci bai shigo ba, bugun kofar da take ya tashi khalid a firgice ya mike zaune dama shima sai dab da asubah baccin ya daukeshi agogon da yake kafe a bangon dakin ya kalla shida da rabi da sauri ya dauki brush dinsa ya fito…..kallo ta bishi dashi da fadin.”Kada dai kace sai yanzu ka tashi.”? kansa ya daga mata ya ratseta ya wuce bayansa tabi da kallo kafin tace.”Khalid me yasa kake wasa da sallah ne.”? ba tare da ya tanka mata ba ya dauki buta ya shiga bandaki, sai itama ta bar gurin ta nufi dakinta ta zauna cikin alhini da damuwa.

Baba Iro ne ya shigo dakin da carbi a hannunsa suka gaisa yace.”Gwaggo ya kike ganin za’ayi ne.”? Tace.”Ibrahim ni da kaina zani gidan Alhaji Shamsun dan bana tantama can ta nufa kome suke ji dashi na rantse ni nafi karfinsu Sa’ida ikona ce dan haka tilas ta dawo gabana ta cigaba da zama.”

Yace.”Gwaggo kada ki fusata komai cikin nutsuwa za’ayi Alhaji Shamsu babban mutum ne mai mutunci bai kamata kije har gidansa gaban iyalinsa kici masa mutunci ba.”

“Ibrahim bafa zan zauna nayi lako-lako ba wato ka manta irin d’auki ba dad’in da mukayi dasu a wacan karon ko wane irin abune baiyi ba akan lallai Sai Sa’ida ta zauna a hannunsa to wannan karon ma ko yafi ‘kuda naci ba zata zauna a gidansa ba domin bamu gaza dayi mata komai ba.”

Baba Iro yayi shuru yana mamakin halin mahaifiyarsa yasan halinta da rashin tsinkaye da hangen nesa zata iya zuwa gidan mutum gaban iyalinsa ta tsinka shi wannan dalilin yasa yayi wani tunani…..”Gwaggo ki nutsu ki kwantar da hankalin ki insha Allahu Sa’ida zata dawo gida da kaina nake so naje gidan mu tattauna da Alhajin yana ganin mutuncina sosai itama Sa’idar haka da yardar Allah tare da ita zan dawo gida.”

“Aa Iro gwara mu tafi tare ayi komai a gabana wallahi nake fada maka jiya kewarta hana ni rintsawa tayi.” Yace.” Ai bake kad’ai ba Gwaggo ni kaina banyi bacci ba amma insha Allah komai zai zo da sauki kiyi hakuri naje ni kad’ai din.”

Shuru tayi alamar bata gamsu da maganarsa ba…Khalid ya shigo dakin suka gaisa da mahaifin nasa tace.”Khalid kaje ka aro adaidaita sahun abokin ka kazo ka dauke ni ka kai ni gidan Alhaji Shamsu.”

Babu walwala a fuskarsa yace.”Me zakije kiyi.”? da sauri tace.”Zanje na dauko Sa’ida ne.” Yace.”Gwaggo babu inda zakije aunty Sa’ida zata dawo da kafafunta bayan haka kuma shi wanda zai bani aron adaidaita sahun nasa ya fita aiki da ita saboda haka ki zauna a gida zamuje nida Baba.”

Da sauri tace.”Zakuwa ku gan ni a gidan domin kuwa Allah ya hore min kudin mota.”

Baba Iro cikin rarrashi yace.”Gwaggo abinda nutsuwa bata bayar ba to tashin hankali ma ba zai bayar dashi ba dan Allah ki nutsu kada kizo ki aikata abu daga baya kizo kina jin kunya Alhaji Shamsu bai cancanci tozarci a gurin mu ba yana kuma da ikon ri’ke Sa’ida a hannunsa tunda yana matsayin mijin mahaifiyarta.

Tace.”Ai kaji abinda nake gudu dama nasan ko kaje ba wani mataki zaka dauka ba karshe ma ka dawo gida kai kadai ba tare da ita ba to sai naje na fada maka.”

Khalid yace.”To kije d’in kina shiga gate din zan sa masu gadi su saki karnuka kin san zan iya ko.” shuru tayi tana kallonsa, Yace.”An fada miki cewa komai a hankali da nutsuwa ake binsa amma kin kasa ganewa.” tasa kuka da fad’in “Khalid bana son Sa’ida tayi nesa dani shiyasa kaga duk hankalina ya tashi bana so wannan karon Alhaji Shamsu ya samu galaba akan mu.”

Yace.”Ba zai samu ba insha Allahu.” hawaye ta share tace.”Khalid shiyasa nake so ka aureta na dinga ganinku a gabana inaso ku haifa min zuria mai yawa.”

Tausayi ta bashi yace.”To Allah ya amsa adduarki ina fata dai yanzu kin janye maganarki ta zuwa gidan.” Tace.”Tunda kunfi karfina na hakura ina zuba ido kuje ku dauko min ita.”

Baba Iro yace.”To Alhamdulillahi bari na kimtsa na fito, yana kokarin fita ta kira sunansa, juyowa yayi yana kallonta tace.”Maganar Rabi baka ce min komai ba.”

Yace.”Tun jiya tana gidansu ai.” girgiza kanta tayi tace.”To wannan hukuncin daka yanke ni yayi min daidai na kuma ji dadi gobe ma sai ta sake aikatawa amma inaso yau idan Sa’ida ta dawo gida kaje kayo bikon matarka.”

Yace.”To Gwaggo yanda kika ce hakan za’ayi.” ya juya da niyar fita sai ya tsaya da fad’in .”Me zaki karya dashi na aika a siyo miki.” Tace.”Ibrahim ba sai kayi asarar kudin ka ba ina da d’umame gashi can a jibge yanzu zan d’umama kafin ku tafi sai kuci.”

Yace.”To shikkenan Gwaggo.” Bayan fitarsa daga dakin sai ta fara janyo kwanukan abincin tana dubawa doyar babu abinda tayi sannan itama farar shinkafar da Ummatu ta dafa a daran ranar ba tayi komai ba ta mike ta fita da kwanukan abincin a hannunta tana fad’in “Ruwan zafi kawai zan sa na turara shinkafar tunda da abincin ai ba sai anyi hidimar siyan wani abu ba.”

Tsaf ta gyara abincin ya dawo tamkar sabo ta dauko ta kawo daki….cikin plate ta zuba masa ta zuba masa miyar nama da yawa…..yace.” Gwaggo a’ina kuka samu nama haka.”?

Tace.”Kasan duk sati Alhaji Nura yakan kawo mana cefane to jiya da ya kawo sai Sa’ida tayi mana miya harda kayan shayi ma watakila ta tafi da abunta.”

‘Bata fuska yayi yace.”Gwaggo nayi sha’awar abinci amma ba zanci ba.” tace.”Sabida me Khalid.”? Hankalinsa nakan wayarsa yace.”Saboda ina kishin mutumin na tsaneshi wallahi.”

Tace.”Khalid ka kwantar da hankalinka kai zaka auri Sa’ida Alhaji Nura kuwa shi yaga zai iya wahalar da kansa mu dai duk abinda ya kawo hannu biyu zamu sa mu ‘karba.

Yace.”Gwaggo idan kina bukatar farin ciki na to ki daina cin abinda mutumin zai kawo wa aunty Sa’ida wannan shine abinda nake bukata dake.”

Shuru tayi tana girgiza kanta bata tsammanin zata daina cin kayan dad’in da Alhaji Nura zai kawo musu amma saboda ta kwantar masa da hankali tace.”To shikkenan tunda baka so na daina.”

Mikewa yayi zai fita tace.”Yanzu Khalid kana kallon abinci da kyau amma kace ba zaka ci ba.” Girgiza kansa yayi yana ta’be bakinsa yasa takalmansa ya fita……….Baba Iro ya shiga dakin cikin shiri yace.”Ina Khalid din.” tana tsotse ‘kashin hannunta tace.” Wata’kila ya tafi gurin mai shayi.” da mamaki a tare dashi yace.”Wannan abincin fa.”?

Tace.”Ibrahim kasan Khalid da zuciya da kishin kansa wai ba zai ci ba saboda yana kishi da wanda ya kawo cefanan.”

Baba Iro ya zauna kusa da ita yana girgiza kansa mamaki yake sosai akan irin tarangahumar d’an nasa in banda abinsa inashi ina Sa’ida ko da yake Namiji komai ‘kan’kantarsa mutukar ya balaga to mace duk girma da shekarunta bata gagararsa…..Gwaggo ta zuba masa abincin tasa masa miya da uban nama akai.” Yace.”Gwaggo ki rage naman.” Tace.”Ibrahim kaci ka ‘koshi ka barshi.”

Bisimillah yayi ya fara cin abincin. dakin yayi shuru na tsayin minti biyar yace.”Gwaggo ya kamata mu samu zama da mutumin nan idan da gaske yake akan yarinyar nan ya fito ayi abinda za’ayi.”

Da sauri tace.”Ko da gaske yake ba zamu bashi Sa’ida ba tunda Khalid ya nuna yana so hausawa na cewa gida bai koshi ba ba za’a kai dawa ba.”

Yace.”Gwaggo duk da Sa’ida budurwa ce to bai cancanci ayi mata dole ba shin da bakinta kinji ta furta tana san auran Khalid.”?

Girgiza kanta tayi tace.”Aa bata furta ba asali ma kullum cikin fad’a da juna suke sam basa jituwa dalilin ma kenan da yasa naje na kar’bo taimaiko gurin mai magani Ibrahim yarinyar nan Sa’ida na tare da iskokai kaga kuwa idan ba na gida ne ya aureta ba to babu shakka akwai matsala shiyasa kaga sam! bana sha’awar wani na waje ya aure ta.”

Baba Iro shuru kawai yayi ya cigaba da cin abincinsa, shi kam ba zai iya da rigimar mahaifiyarsa ba mutukar shine madaurin auran Sa’ida to ba zai daura mata aure da wanda bata so ba.

To Cikin nutsuwar zuciya na wayi gari a gidan mahaifiyata, sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina sannan ta shigo dakin fuska a sake tace.”Sa’ida kinji shuru ko.” Murmushi kawai nayi nace.”Umma ai nasan inda kike ina fata kin tashi lafiya.”?

Tace.”Lafiya kalau alhamdulillahi Jiya duk na shedawa Alhaji abinda yake faruwa shima al’amarin bai masa dadi ba ko kad’an dan haka ya yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan sai kin kwana biyu anan kin samu nutsuwa tukkuna.”

Ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata ina jin dadin hukuncin da ya yanke. tace.”Ki tashi kije ku gaisa dan fita zaiyi bayan kin fito daga dakin nasa sai ki shiga dakin matan gidan ku gaisa.”

Nace.”To shikkenan Umma.” hanyar fita ta nufa da fad’in “Bari na shiga kicin na taimakawa Asabe da aiki kada ya yara su makara a makaranta.” Nace.”Umma ai yau Lahadi babu skull.” tace.”Ai yaran gidan nan suna zuwa islamiyya tahafiz in suka tafi sai yamma suke dawowa.”

Bayanta nabi da fad’in “To bari nima nazo ayi aikin dani.” Mirmushi tayi ba tare data ce komai ba ta nufi hanyar babban kicin din nasu dake tsakar gidan.

A nutse nayi sallama cikin dakin nasa……Ya amsa min tare da kiran sunana.” Na karasa cikin dakin sosai ina amsawa har ‘kasa na tsuguna na gaishe shi. Ya amsa cikin sakin fuska da kulawa ya d’ora da fad’in “Sa’ida jiya mahaifiyarki duk tayi min bayanin abinda ke faruwa da rayuwarki naji rashin dad’i sosai kuma raina ya ‘baci dalilin da yasa ma kenan na yanke hukuncin kan cewa ko zaki koma can gidan to ba yanzu ba sai kin samu nutsuwa saboda haka ina so ki kwantar da hankalinki ki cire duk wata damuwa dake ranki insha Allahu Allah zai kawo miki miji nagari ki aure.”

Cikin rauni gami da tausayin kaina nace”Nagode Alhaji insha Allahu kuma zan cire al’amarin daga cikin raina.”

Yace.”To Alhamdulillahi ya aikin ki ina fatan komai lafiya.”? nace.”Alhamdulillahi komai lafiya Alhaji.”‘ Yace.”To masha Allah Allah ya taimaka.” Na amsa da ameeen tare da kokarin mikewa yace.”Kyace ina kiran mahaifiyar taki.” Nace.”Tom zan fada mata yanzu.

Ina fita na nufi kicin din na sheda mata kiran da yake mata, cikin sakin fuska muka gaisa da mai aikinsu Asabe har tana tambayata yaushe nazo. nace “Shigowar dare nayi shiyasa ba kowane yasan da zuwana ba.”

Sai bayan mun kammala aikin ne na samu nutsuwar shiga d’akunan abokan zaman nata muka gaisa dasu cikin mutunci da girmamawa Famliy d’in Alhaji Shamsu suna da kirki sosai Mussaman Babban d’ansa Mai suna Aminu mun saba dashi sosai yana da kirki da saukin kai kud’in sa sam bai rufe masa ido ba babbar matsalar Yaya Aminu rashin aure anyi anyi dashi yayi aure ya’ki ga uban kudi da yake samu dan kasuwa ta nayi dashi sosai yake fita ‘kasashe ya shigo da kaya amma duk kudinsa da tsayin shekarunsa bashi da mace… mahaifiyarsa har magunguna take ‘karbo masa cikin dubara take bashi a ganinta ko bashi da lafiya shiyasa baya sha’awar auran shi kuwa ba tare da yasan maganin menene ba zai kar’ba yasha tunda yasan mahaifiyarsa ce ba zata cutar dashi ba.

To Alhaji Shamsu na fita da kamar minti ashirin su Khalid suka isa gidan…..su gaisa da maigadi cikin mutunci Baba Iro yace “Munzo gurin maigidan ne.” Maigadi yace.”Ayya wallahi kun doki gurbi Alhajin bai jima da fita ba sai dai idan kasuwa zaku bishi.”

Gabad’ayansu jikinsu yayi sanyi….Baba Iro yace.”Babu damuwa insha Allahu zamu dawo da daddare ko kuma gobe da safe idan yaso idan ya dawo sai ka sheda masa zuwanmu.”

Maigadi yace.”To shikkenan babu damuwa wane suna za’a fad’a masa.”? Yace.”Kace masa Ibrahim ne Kawun Sa’ida daga Mandawari.”

Yace.”To shikkenan za’a fada masa insha Allah.”

Sallama sukayi da juna Maigadin ya rufe gate din….Khalid a sanyaye yace.”Baba mai zai hana mu bishi kasuwar.”? Baba Iro ya girgiza kansa da Fad’in “Khalid al’amarin yana bukatar sirri bai kamata mu bishi gurin sana’arsa ba tunda dai maigadinsa yasan da zuwanmu nasan idan ya dawo zai fada masa.”

Jiki a mace yace.”Hakane.” Adaidaita sahu suka shiga Baba iro yace.”Ni Kasuwa zan wuce yanzu yana da kyau kazo muje .” Jim! yayi yana nazari kafin yace.”Baba kasan gobe zan koma skull so inaso na koma gida nayi shirye-shirye.” Yace.”To shikkenan Khalid idan ka koma gida ka taushi zuciyar Gwaggo nasan dai yau akwai rigima a gidan amma kai tunda taku tazo da d’aya ka rarrasheta kafin na dawo.”

Yace.”To shikkenan Baba.” Direban yace.” Ina zan kaiku ne naga kamar tafiyar taku ta bambamta.” Khalid yace.” Kasuwar sabon gari zaka kaishi ni kuma Mandawari.” Direban yace.”Ai hanyar ta baud’e ni yanzu kai tsaye Sabon gari na nufa.”

Yace.”Okey to sauke ni na samu wata.” ya tsayar da babur din ya fito hannu yasa a aljihu ya dauko kudi ya mik’a masa……Baba Iro yace.”Kana da kudi wadatacce a jikinka ne.”?

Yace.”Eh baba kada ka damu Kuje kawai Allah ya kiyaye.” Direban yayi saurin sa kudin cikin d’an bankin dake gaban babur din yaja da sauri suka bar gurin.

Ajiyar zuciya ya sauke bayan barin su a gurin ya tari wani babur din gidan Alhaji Shamsun zai koma.

Maigadi ya bude karamar kofa yana tambayar waye ganin Khalid yasa yace ”Ka dawo kenan.”? Khalid yace.”Inaso zanyi magana ne da Auntyna Sa’ida.”

Jim! yayi kafin yace.”Khalid kayi hakuri da abinda zan fada maka Alhaji ya hana kowane namiji shiga cikin gidansa ko masu yi musu hidima iyakar su bakin gate saboda haka nake baka shawarar kiranta a waya ita sai ta fito ku gaisa.”

Yace.”Okey to bude min na zauna a gurin zamanka sai na kira wayar tata.” Maigadin ya bude masa ya shiga ya zauna kan kujerarsa shi kuma ya mayar da gate din ya rufe…

*Masoya a taimaka da Sharing🥰👏🏼*

*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE……VIP GRUOP#600….NORMAL GRUOP#300…..ACCOUNT…..0542382124…..BINTA UMAR GTBANK…..IDAN KATI ZAKI TURO…#400 NE SAI KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBER*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*12*
Cikin ikon Allah ina tsayuwa a bakin titin wani adaidaita sahu ya tsaya a gabana. “Hajiya ina zakije.”? Ya fad’a yana dan le’ko da kansa. Da sauri nace.”Hotoro zaka kai ni.” Jim yayi kafin yace.”Okey to nawa zaki biya.”? ‘Kugin da naji a bayana yasa nai saurin juyawa Khalid ne da Salim cikin a daidaita sahu suna kokarin shiga layin….Da sauri na dauki jakata na fad’a babur da fad’in “Muje ko nawa ne zan baka.” babur din ya buga da sauri muka bar gurin….Sai da naga munyi nisa sosai hankalina ya kwanta a nutse na fito da wayata daga cikin jaka number ta na shiga nema inaso na sanar da ita cewa gani nan a kan hanya.

A tsanake muka gaisa nace.”Umma gani nan a kan hanyar zuwa.” Tace.”Da daddare nan Sa’ida ina fata dai lafiya.”? Cikin rauni nace.”Lafiya Umma.” Ta amsa da to “Alhamdulillahi sai kin ‘karaso.” Kashe wayar nayi nasa a jaka kana nayi saurin sa gefan hijabina na goge hawayen da ya fara zuba a fuskata.

Cikin magagin bacci ta tashi tana lalu’ben torchlight d’inta ta kunna tana haske d’akin da fad’in “Sa’ida Ibrahim din be shigo bane.”? Shurun da taji yasa tayi saurin kallon inda take kwanciya taga wayam! sai tai zargin ko tana bandaki redion ta ta dauka ta fara kokarin kunnawa wasu tashoshin sun rufe da kyar ta lalubi freedom redio lokacin suma daf suke da rufewa. kimanin minti goma tana zaune ba taji motsinta ba sai ta mike ta fito bakin band’akin ta tsaya tana kiran sunanta. shurun da taji yasa gabanta fad’uwa tana kokarin barin gurin ya shigo gidan ganinta a tsaye a bakin bandaki yasa yace.” Gwaggo lafiya me kike anan gurin.”?

Murya na rawa tace.”Khalid Sa’ida bata gidan nan.” gabansa ya fad’i da sauri yace.”Gwaggo bangane bata gidan nan ba.” ? Ajiyar zuciya ta sauke tana kokarin barin gurin tace.”Jeka kira min babanka idan ma yayi bacci ka taso shi.”

Khalid da sauri ya nufi gurin nasu itama ta nufi dakinta tana haske haske da torchlight nan taga babu jakar kayanta sai ta sake karaya a sanyaye ta zauna kan shimfid’arta tana fad’in “Wannan yarinya bata da hankali ashe.”

Baba Iro da Khalid suka shiga dakin a tare……Tace.”Ibrahim matarka ta tunzura Sa’ida ta had’a kayanta ta gudu.”

Kawu Iro yace.”Gwaggo wace irin magana ce wannan.”? Fashewa tayi da kuka tace.”Iro d’azu Rabi ta zauna ta ‘karewa Sa’ida cin mutunci tana kiranta da Karuwa tsohuwar guzuma saboda kawai ina maganar auransu da Khalid shine fa ta fito tayi mata wannan cin mutuncin a cewarta wai d’anta ba zai auri lalatacciya ba wannan dalilin ya fusata zuciyarta ta had’a kayanta ta gudu.”

Baba Iro yayi shuru yana jimanta al’amarin! tace.”Yanzu ni babban tashin hankalina da damuwa ta inda ta nufa a cikin daran nan.”

Yace.”Gwaggo hakika raina ya ‘baci da wannan al’amarin kuma duk irin hukuncin dana dauka akan Rabi kada kice don me ta riga ta gama fusata ni ace wai ‘yar d’an uwana na jini take kira da Karuwa.”

Gwaggo tace.”Ibrahim ba zan hana ka ka dauki mataki akan Rabi ba domin ko baka dauka ba ni zan dauka ba zata dinga la’antar zuria ta ba.”

Yana kokarin fita daga d’akin Khalid ya dafa kafad’arsa a tausashe yace.”Baba kada ka yanke hukunci cikin fushi Annabi ya hana.”

Rai a ‘bace! yace.”Saboda mahaifiyarka ce ko? yanzu kai a tunaninka abinda ta aikata tayi daidai.”?

Kansa ya girgiza a sanyaye yace.”Nima banji dadin al’amarin ba amma dan Allah kayi hakuri.” Ba tare da yace masa komai ba ya bar gurun.

Khalid dakin ya shiga jikinsa duk a mace babu shakka yasan wannan hargitsin dake faruwa shine sila da baya shiga sabgar auntyn nasa da mahaifiyartasa ba zata samu hanyar zaginta ba.

Number ya nemo a wayarsa ya fara kira, Gwaggo tace.”Yawwa dama yanzu zance ka kira ta a waya mu ta fad’a mana inda ta nufa duk da dai nasan watakila tana can gurin uwarta mai hure mata kunne.”

Jin wayar tana shiga yasa da sauri ya d’aga mata hannu. shuru tayi tana kallonsa, wayar ta ‘karaci ringing ta katse bata dauka ba.

Hannu na rawa ya sake kira nan ma babu amsa Khalid ya dinga kiran wayar tana katsewa ya kai sai goma, jiki a sanyaye ya kalleta da fad’in “Gwaggo aunty Sa’ida tayi zuciya taki daukar wayar.”

A sanyaye tace.”Khalid dole tayi fushi! bayan fitarka Uwarka sata tayi a gaba taci mutuncinta ta dinga zaginta tana kiranta karuwa.” Tana share hawaye take maganar ta cigaba da cewa”Wai yau zuria ta Rabi takewa wannan cin mutuncin.”

Yace.”Gwaggo idan Ummatu tana da laifi kema kina dashi kada fa ki manta irin takura mata da kikeyi Gwaggo keda Ummatu kune kuka kori auntyna Sa’ida daga gidan nan.”

Shuru tayi tana share hawaye tace.”Dan Allah sake kiran wayar ko zata dauka idan kuma bata daga ba ka kira wayar uwartata idan kana da number ta.”

Yace.”Ni bani da Number Ummah Habiba amma bari na sake kira naji ko zata dauka…sake kiran wayar yayi har sau biyu babu amsa, ya sauke nannauyan ajiyar zuciya yana tunanin yanda za’ayi…….”Khalid ka fito kaje gidansu abokinka ka kar’bo mukkulin adaidaita sahunsa ka kai ni babban gida.” Muryar mahaifiyarsa ta katse masa tunani.

Da sauri ya mike ya fita sai ya ganta a tsaye da hijabi a jikinta. agogon dake daure a hannunsa ya duba sha d’aya shaura yace.”Ummatu me zakije kiyi a babban gida da daddare haka.”

hawaye ta share tace.”Babanka ya kore ni a gidan wai naci mutuncin ‘yar d’an uwansa har ta gudu sabida haka nima ba zan kwana a gidan ba.”

Khalid jikinsa yayi bala’in mutuwa da saurin ya jingina jikin bango (garu) Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un ya shiga kira yana jimanta masifar dake kokarin kunno musu….Gwaggo kuwa tana cikin dakinta a zaune tana jin duk abinda ke faruwa ko gezau ba tayi ba tana zaune babu abinda ya dameta.

Yace.”Ummatu ba zaki je ko’ina ba ina zuwa.” da sauri ya nufi gurin nasu hankalinsa duk a tashe…..a kwance ya samu mahaifin nasa a tsakar gidan ya tsuguna gefansa hade da fad’in “Baba dan Allah kayi hakuri matakin daka dauka akan Ummatu bai dace ba.”

Hannu ya d’aga masa rai a ‘bace yace.”Khalid tashi ka bani guri bana bukarar jin wata magana daga gareka, Rabi ta kaini karshe kuma dama ba tun yau ba nasan da cewar bata kaunar yarinyar nan Sa’ida alhalin abinda yayi ubanta shi yayi ni mu biyu kacal iyayenmu suka haifa muka haifeku me zai sanya ta d’orawa yarinya karan tsana akan wane dalili? ita ko tausayin maraicinta ba tayi to shikkenan yanda tayi sanadin barinta gidan itama sai ta barshi idan kaga mahaifiyarka ta dawo gidan nan to ka tabbata cewa Sa’ida ce ta dawo.”

Khalid jikinsa yayi sanyi yace.”To Baba dan Allah kayi hakuri dare ne yanzu ka bari da safe kome zai faru sai ya faru.” cikin tsawa! yace.” Khalid ba zaka tashi ka bani guri ba.”?

Mikewa yayi ya fita daga gurin ransa a tsananin ‘bace…Babu Ummatu a gurin da sauri ya le’ka dakin Gwaggon yana tambayarta tace itama bata san inda take ba, fita yayi da saurin gaske.

Can ya hangota tana tafiya yabi bayanta da sauri yana kiranta, tsayawa tayi ya karaso gurin yaga tana share hawaye yace.”Ummatu kiyi hakuri dan Allah ki daina kukan nan bari na shiga gidansu Salim d’in na kar’bo key din.”

Kanta kawai ta d’aga masa zuciyarta na tafarfasa tunda tayi aure tsayin shekara ashirin da biyar wani sa’bani mai muni bai ta’ba shiga tsakaninta da mijinta ba, sai gashi yau akan Sa’ida yarinyar tayi sanadin da mijinta ya koreta daga gidan auranta.

Khalid ya karaso gurin cikin adaidaita sahun a sanyaye ta shiga ta zauna yaja babur din suka tafi.

Sai da suka hau titi sosai ta sauke ajiyar zuciya da fad’in “Khalid kaga irin tozarcin da mahaifinka yayi min akan Sa’ida ko.”?

Yace.” Ummatu kiyi hakuri amma kema mai yasa kika zageta ki ka kuma yi mata kazafi na zina.”

Cikin ‘bacin rai tace.”Ai ba sharri nayi mata ba gaskiya na fad’a me yasa kun san gaskiya amma gabad’ayanku kuke kareta ni nasan Sa’ida mazinaciya ce.”

Yaji kansa ya sara! gumi na yanko masa yace.” Ummatu zuciya takan dauki zafi a duk lokacin da zaki jefi Auntyn Sa’ida da wannan kalmar wallahi ita d’in kamila ce bata bin mazan banza a waje.”

Tace.”To shikkenan tunda kana jin zafi sai ka dauki mataki a kaina kamar yanda ubanka ya dauka wallahi Khalid mutukar ni na haifeka to ba zaka auri Sa’ida ba dan duk na gane take-taken ka.”

Shuru yayi wani irin gumi! yana tsatstsafo masa .

Tace.”Idan ka bijirewa umarnina ka auri yarinyar sai nayi maka baki ka lalace gwara tun wuri ka cireta daga cikin zuciyarka.”

Murya na rawa yace.”Ummatu me yasa kike wannan maganar me yasa kika dauki zafi da al’amarin nan kada kiyi min haka dan Allah aunty Sa’ida itace farin cikina.”

Tace”Humm! dama abinda nake so na gazgata kena gashinan kuma ka furta da bakin ka saboda haka daga yau sai yau na rabaka da yarinyar nan wallahi tallahi ka sakeyi mata magana Allah ya isa.”!

Ji yayi kansa yana juyowa kan babur din na nema ya kufce daga hannunsa da kyar ya aro dauriya yasa a ransa ya cigaba da driving din yana nanata kalmar innalillahi wa’ina ilaihi raji’un.!

“Hakika Sa’ida banji dad’in wannan abubuwan da suke faruwa da rayuwarki ba amma kuma bai kamata ki yanke wannan hukuncin ba dalili kuwa shine kin san halin Gwaggo baud’ad’d’iyar macace zata iya zargina kan cewa ni nake zugaki ki bijire musu.”

Ajiyar zuciya na sauke a raunane nace”Umma wallahi hakuri na ya ‘kare a gidan nan dan saboda bana so watarana su tunzura zuciyata na fad’a musu magana mara dad’i shiyasa kawai na yanke wannan hukuncin.”

Girgixa kanta tayi tace.”To shikkenan ai Allah yasa hakan shi yafi alkairi bari da safe sai na shedawa Alhaji halin da ake ciki idan yaso duk hukuncin da ya yanke miki sai kiyi hakuri dashi.”

A sanyaye Nace.”Tom shikkenan Umma Allah ya kaimu lafiya.” kallona tayi cikin tausayawa tace.”Naga duk kin rame ko duk fargabar ce.”? Murmushin takaici nayi nace.”Umma zama da Gwaggo da Ummatu ai sai jarumi mai kuma hakuri sosai suke takurawa rayuwata.”

Murmushi tayi tace.”Ba tun yau ba na san halin Gwaggo macace wata iri wacce baka gane gabanta da bayanta haka nima nai hakurin zama da ita Ummatu kuwa dama can ba muyi wani zaman arziki da ita ba.”

Nace.”Hakane Umma tace.” to saboda haka sai kiyi hakuri ki cire damuwa daga cikin ranki ki fuskanci abinda yake gabanki aure idan Allah ya kawo lokacinsa babu wanda ya isa ya hana.”

Nace.”Kwarai kuwa hakane.” Ta kalli kwanukan abincin dake gabana a nutse tace.”Da alama ba ki bude abincin nan ba.”? Nace.”Eh ban ci ba tukunna.” Tace.”To ni zan shige na tafi dakin Alhaji sai ki nutsu kici abincin ki kwanta.” nace.”Tom shikkenan Umma sai da safe.” Ta mike a nutse ta fita daga dakin, cikin nutsuwa na bud’e kwanukan abincin towon farar shinkafa ne da miyar taushe taji gyada sai kamshi take…..dama tsabar fargaba da tashin hankali bata bari naci wani abincin kirki ba saboda haka lokaci guda yunwa ta taso min nasa towon a plate na zuba miya akai a nutse na fara ci ina tunanin halin da Gwaggo zata shiga idan ta farka daga bacci taga bana nan…..

*Masoya a taimaka da sharing👏🏼🥰*

*IDAN KINA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA YANDA ABIN YAKE….VIP GRUOP#600 NORMAL GROUP #300 ACCOUNT… 0542382124…..BINTA UMAR GTBANK…IDAN KATI ZAKI TURO #400 SAI KIYI MIN MAGANA TA WHATSAPP DA WANNAN NUMBER.*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/6, 2:04 PM] Umm Muhammad: *GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*11*
Ina zaune da plate din indomee a gabana ya shigo gidan, kallo guda nayi masa na kauda kaina, gani nayi ya tsaya yana kallon kayan wanki na dana jibge a bakin rijiya, minti biyu ya wuce daga gurin….. mikewa na share tsakar gidan sannan na shiga dakin na harhad’o kayan wanke-wanke na fito dashi bakin rija. d’akin na koma na sameta ta fara kad’in lagwani nace.” Gwaggo zan fara wanki inaso na share miki dakin.” Tace.”Kije kiyi wankin ki idan na tashi na share.” Ba tare da nace mata komai ba na fita daga dakin, samun sa nayi zaune a bakin rijiya daga shi sai gajeran wando yana wanke kayan ball d’insa.

Tsigar jikina ta tashi na tsani na ganshi babu suttura a jikinsa nakan ji wani irin yanayi a tare dani, kamar na koma d’aki na zauna idan ya gama abinda yake nazo nayi wankin, sai dai na daure kawai naja bokiti da ruwa a ciki na zuba omo na sunkuya na fara cud’a wankin….Shuru gurin yayi yana ta cud’a kayansa nima ina cud’a nawa.

Sunkuyo na d’an gyara karaf! na kama shi yana satar kallon kirjina. cikin dubara na duba sai naga ashe gurin sunkuyo din wuyan rigata ya zame gabad’aya breast dina ana ganinsu.

Girgiza kaina kawai nayi na mi’ke. kujera ‘yar tsuguno naje na dauko na zauna akai na cigaba da abinda nake…….. Hannunsa ya mi’ka ya d’auki briziyata yasa a cikin ruwan omon dake gabansa ya fara cud’awa.

Rai a ‘bace! na kalleshi da fad’in “Ranka zai ‘baci idan baka mi’ko min rigar nan ba.”

Uffan bai ce min ba ya cigaba da cud’a breziyar yana gyarata, Nace.”Khalid ko bakyaji abinda nace ba.”? Babu walwala a tare dashi yace.”Naji ashe akwai sauran wani abu da zakiyi min bayan wanda kikayi min d’azu.”

A zafafe! Nace.”Nayi maka d’in ai kai ka janyo meye ruwanka da wayata ko kuma Alhaji Nuran sa’anka ne wallahi ka nutsu ka shiga hankalinka idan ba hakaba kana tare da ‘bacin rai.”

Cike da nuna rashin damuwa yace.”Mutukar akanki ne a shirye nake da kowane irin ‘bacin rai kuma wallahi sai inda karfina ya ‘kare zaki gane baki da wayo.”

Da sauri nace.” Ni kake fad’awa wannan maganar.”? Shiru yayi ya cigaba da abinda yake a fusace! na kai hannu zan fuzge rigar ya murd’e min hannu har sai da yayi ‘kas! cike da mamaki nake kallonsa! Yace.”Ki kyaleni na cigaba da wankewa hakan na rage min rad’ad’i!

Gabana ya fad’i! wanke breziyya har wani jin dad’i ne lallai Khalid fitinanne ne……..Kallona yayi da wani munafikin murmushi a fuskarsa yace.”Naga kamar ma tayi miki kad’an idan na tashi had’a miki lefe wacce ta fita girma zan sa miki.”

Naji wani irin takaici ya rufe ni wai ni ya zanyi da yaron nan ne? shamtarsa nayi na zubar da ruwan oman dake gabansa.

Sai yayi murmushi ya cire breziyar a cikin bokitin kawai naga yana marmatsa ‘ko’konta kamar yana ta’ba nono sai lumshe ido yake yana cizar lips d’insa….Ruwan Oman dake gabana na d’aga na kwara masa a jikinsa, hakan yayi daidai da fitowar Ummatu daga gurinta, ya mi’ke tsaye da breziyyar a hannunsa…..Ganin mahaifiyarsa yasa yayi saurin mayar da fuskarsa ta salihai “Aunty Sa’ida me nai miki kika watsa min ruwan wanki.”

Shuru nayi jikina yayi sanyi da irin kallon banzan da mahaifiyarsa keyi min….ta kalleshi rai a ‘bace tace.”Khalid meye wannan a hannunka.”? da sauri ya kalli hannunsa sai kuma ya jefo min breziyyar da fad’in.”Ummatu ban san na rike ba mybe a cikin ruwan wanki data watsa min ta had’o da ita.”

Ta kalleni da rai a ‘bace “Sa’ida wane tsabar rashin mutunci ne wannan? me yayi miki dan wulakanci zaki watsa masa ruwan wanki a jiki.”

Shuru nai mata ba wai dan bani da amsar da zan bata ba sai dan sanin da nayi cewa duk abinda zan fad’a mata yayi min ba yarda za tayi ba.

Gwaggo ta fito daga dakin tana fad’in “Me kuma yake faruwa nake jin hayaniya.”? Ummatu da sauri tace.” Gwaggo duba jikin Khalid ki gani sabida tsabar ita ta cika ishashshiya ta dauki ruwan wankinta ta watsa masa a jikinsa.

Gwaggo da sauri ta kalli Khalid jikinsa jagab! da ruwan daud’a! cike da mamaki! tace.”Jarumi me ya had’a ku nasan dai ruwa baya tsami banza.”?

Girgiza kansa yayi yace.”Gwaggo daka kawai zan taimaka mata da wanki shine tayi min wannan wulakancin.”

Tace.”Haba Sa’ida me yasa kika aikata haka.”? Rai a ‘bace na d’ago ina kallonsu nace.” Lokacib dana fito da wanki na bance kowa ya taimaka min ba akan me zai zo yasa min hannu sai kace sa’arsa dan wulakaci ya d’auki breziyata yace zai wanke.”

Gwaggo ta ri’ke bakinta tana yi masa wani irin kallo mai kama da harara…..Ummatu tace”Ke Sa’ida kada kiyi masa sharri yaushe ya dauki rigar nonan naki bayan ke kika watsa masa ruwan daud’a da ita a ciki.”

Nace.”Ummatu kenan ba sharri nai masa ba da idonki fa kin gani amma zaki ce nai masa sharri.”

Gwaggo tace.”To duk dai magana ta wuce kada a ‘kara tayar da ita kai kuma Khalid babu ruwanka da ita.” Yace.”Yanzu ke Gwaggo kin yarda zan aikata hakan? okey idan ma breziyar ta na d’auka domin na wanke mata meye a ciki? ai ba k’irjinta na ta’ba ba ballantana tayi min sharri .” Gwaggo tace.”Aikuwa dai babu laifi a ciki tunda tace bata so sai ka kyaleta.

Tsaki yaja ya bar gurin yana fad’in “Daga Abin alkairi sharri ya biyo baya wataran ma cewa zakiyi na turmushe ki.” Ummatu tayi saurin fad’in “Allah ya kiyaye.” Bayansa tabi tana surutai itama Gwaggo dakinta ta koma ta cigaba da abinda take.

Tana zaune a d’an tsakar gidanta ya fito daga dakinsa cikin shirin fita yayi gayu cikin ‘kananun kaya sai kamshin turare yake, Khalid akwai tsabta da kwalisa kayansa kullum a goge gashi bai yarda da fesa turare me arha ba.

“Khalid zo nan ina so nai magana da kai.” A nutse yaje ya samu gefanta ya zauna. tace.” Kana jina ko.”? yace.”Eh Umma ina jinki.” Tace.”Ni ba zan raba ka da ‘yar uwarka Sa’ida ba amma inaso kayi nesa da ita dan gabad’aya ni yarinyar bata kwanta min a raina ba ina jin tsoro taje tayi lalata a waje ta laqaba maka sharri ka daina shiga sabgarta.”

A sanyaye yace.”Ummatu me yasa kike mata irin wannan zargin.” ? Tace.”Kai Khalid yaro ne kai baka san me duniya take ciki ba gabad’aya jama’ar gari kallon lalatacciya suke mata dan ni akwai wacce ta kawo min magana kancewa babu irin lalatar da ba tayi da maza a gurin aikinta wannan dalilin yasa nace kayi nesa da ita bana so taje tayo cikin shege ta d’ora maka.”

Cike da mamaki! yake kallonta kafin yace.”Ummatu amma banji dadin wannan magana ba dan Allah ki daina yarda da surutan mutane bana tsammanin Aunty Sa’ida zata zubar da martabar gidan nan.”

Tace.”Oho! dai Sa’ida tana bin maza bata bin maza ni dai nace ka rabu da ita dan naga kaima tana so taja hankali ka gashinan baka san laifinta.”

Shuru yayi yana girgiza kansa! Tace.”Yaushe ne zaku koma makaranta.”? Yace.”Ai kin san da tuni mun koma wannan yajin aikin da aka tafi ne ya janyo amma naji gwamnati tayi magana cewa kowane dalibi ya koma makaranta ranar mondy.”

Tace.”Jibi kenan zaka tafi.”? Yace.”Eh insha Allahu.” Tace.”To shikkenan kafin ka tafi kaje can babban gida ka gaishe su.” Yana kokarin mi’kewa yace “To insha Allahu zanje.”

‘Kamshin turaransa ne yasa nayi saurin juyowa muka had’a ido dashi, saurin dauke kaina nayi ina mamakin a’inda ya samu kudi ya siyi turare mai tsada irin wannan nafi jin ‘kamshinsa a jikin Alhaji Nura. Cigaba da shanya kayana nayi har ya fice daga gidan sai kawai na tsinci kaina da bin bayansa da kallo gaskiya dressing din yayi masa kyau sosai. kawar da tunaninsa nayi daga cikin raina na cigaba da abinda yake gabana.

Ina tsaka da share inda nayi wanki yaro ya shigo.”Wai Salisu mai kanti yace a bashi lagwanin.” Nace.”Shiga dakin ka fad’a mata. muryarta naji tana fad’in “Bama sai ya shigo ba naji bari na kawo maka ka kai masa.”

Yaron yace.”To gwaggo.” ta fito hannunta rike da leda viva ta mika masa da fadin”Kace dan Allah yayi hakuri banyi masa akan lokaci ba.” Yace.”To Gwaggo zan fada masa.”

Fita yaron yayi ta kalleni da fadin”Sa’ida yau sha’awar sakwara nake ko zakiyi mana da ragowar doyar can.” Nace.”Banda kudi da zan sarrafa.”

Tace.” ‘Dari biyu zata isa ayi miyar.”? Kaina na girgiza mata alamun ba zata isa ba, tace.”Aikuwa dari biyu zan iya bayarwa ayi cefane.” tafada tana kokarin shiga daki sallamar Almajirin gidan Alhaji Nura ta dakatar da ita.
Washe bakinta tayi tana kallonsa ya ‘karaso inda nake hannunsa ri’ke da ledoji yace.”Aunty Sa’ida ina wuni.”? na amsa ina kokarin wanke hannuna yace.”Daga kasuwa nake Alhaji yace na kawo miki wannan.” Hannu nasa na kar’bi ledojin da fadin.”To Rabi’u kace masa nagode sosai.” Ya amsa da ameen tare da juyawa Gwaggo tace.” Rabi’u babu gaisuwa ka shigo kawai ka wuce gurin uwar dakinka.”Murmushi yayi yana kallonta yace.”Gwaggo Dan Allah kiyi hakuri wallahi hankalina ne yayi gaba ina fatan kin wuni lafiya.”?

Tace.”Lafiya lau Rabi’u ya Alhajin ina fata dai lafiya dan Allah kace masa muna godiya da hidima.” Rabi’u yace.”Insha Allah zan fad’a masa.”

Yana fita ta karaso inda nake tana fad’in “Kai amma naji dad’in wannan aiken wallahi nasan harda nama da kayan miya a ciki kinga na huta ‘batar da kudina.

A nutse nace.” Gwaggo wai dan Allah me yasa kike da san abin duniya ne inace d’azu kika gama zagin mutumin nan amma yanzu kinga kayansa duk kin gigice.”

“Sa’ida kada ki fad’a min magana mana kin san dai ba zan bar nawa na na za’be shi ba, ni nafi kaunar ki auri Khalid amma da babu maganarsa a tsakani zan baki goyan baya d’ari bisa d’ari ki auri Alhaji Nura domin ya cancanta.”

Nace.”Wallahi har mamaki kike bani idan naji kina cewa wai na auri Khalid gwaggo kina tunanin ko maza sun’kare a duniya zan auri wannan yaron……..”Shima ba zai aureki ba tsohuwar guzama dake.” Muryar Ummatu ce ta katse maganar da nake. duk muka juya muna kallonta….Fuska a murtuke ta karaso inda muke tsaye tace.”Sa’ida ke har wata cikakkiya ce da har zaki dinga k’yamatar auran Khalid me kike dashi na matantaka bayan duk kin gama rabawa abokanan aikin ki maza.”

Gwaggo tace.”Rabi wannan wace irin banzar magana ce.”? Da sauri tace.”Gwaggo ranar wanka fa ba’a ‘boyan cibi ke kin sani kuma kin fad’a da bakinki hakanan kuma jama’ar gari sun sani Sa’ida bata da kamun kai to me zai sanya kice lallai sai Khalid ya aureta.”

Rai a ‘bace Gwaggo tace.”Rabi kada ki ‘kara yi mata ‘kazafi ni kaf zuriyata babu lalatacce idan Allah ya kaddara auran Sa’ida da Khalid babu yanda zakiyi sai hakuri.”

Murmushi takaici tayi tace.”Gwaggo sai dai kuwa idan bani na haifi Khalid ba.” Tana gama maganarta ta bar gurin tana wani irin huci!

Ido jawur! na kalleta nace.”Kinga abinda kika janyo min ko.”? ”Kinga Sa’ida rabu da Rabi bata da cikakken hankali kuma wallahi sai na fad’awa Ibrahim ayi muku tsakani da ita kada ta ‘kara jifanki da mummunar kalma.”

Nace.”Gwaggo da Ummatu ba taji kina fad’a min haka ba to ba zata fad’a ba tun farko ke kika nuna kina zargina da iskanci a gurinki taji gashinan kin janyo min cin mutumci.”

Tace.”Kiyi hakuri na fad’a miki zan had’ata da Ibrahim zata gane bata da wayo.” nace”Gwaggo kada ki had’ata da mijinta a kaina ki kyaleta kawai ni zan yanke hukunci da zakuyi farin ciki.”

Tace.”Sa’ida wane irin hukunci zaki yanke.”? Murmushin takaici nayi nace.”Idan na yanke zaki gani.” barin gurin nayi naje ina duba abinda yake cikin ledojin …..kayan tea ne komai da komai sai uban kayan miya da nama mai yawan gaske a cikin wata katuwar takarda.
Kallonta nayi nace.” Kinga nayi wanki na gaji ba zan iya dukan sakwara ba zan dafa miki ita kawai kici da miya.”

Tace.”To shikkenan had’a kayan miyan ni da kaina sai na miqa markad’an gidan Lubabatu.” Mi’kewa nayi na dauko d’an maidaidaicin baho da wuka na zauna ina gyara kayan miya ta nufi daki tana fadin” bari na ‘karasa d’an abinda nake kafin ki gama.”

To duk k’ulafucin Gwaggo ba taci doyar da yawa ba duka -duka uku taci ta ajiye wa mutumin nata miya cikin silba duk ta kwashe masa naman ‘kyaleta kawai nayi domin ni nasan abinda na shirya mata.

Ganin tana gyangyad’i nace.”Gwaggo ki gyara kwanciyarki mana.” Da sauri ta bude ido tana kallona tace.”Ina jiran Ibrahim ya shigo ne shiyasa ki kaga bankwanta.”

Nace.”Gwaggo Ummatu ni ta ciwa fuska kuma gani tayi ki nayi min saboda haka dan Allah kada kice zaki fad’awa mijinta ki had’asu.” Ta’be bakinta tayi tace.”Ai sai kiyi Sa’ida Sai fa na fad’a masa fa Ummatu zata san da ni take zancan.”
Shuru nai ina kallonta………ta cigaba da gyangyadin tana nema ta tintsira nace.”To ki kwanta idan ya shigo zan tashe ki.” Ajiyar zuciya ta sauke tace.”To mi’ko min fillo na d’an matse.” da sauri na mi’ka mata ta kwanta tana kiran sunan Allah.

Shuru dakin yayi na tsayin minti goma sha biyar na tabbatar tayi bacci na mike a tsanake nasa hijabina jakar dana san na had’a dukkanin kayana na dauka a hankali na fita daga d’akin…….Kai tsaye babban titi na nufa ina addua a kan Allah yasa ina fita na samu adaidaita sahun da zai kaini hotoro gidan Mahaifiyata……

?‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_

*14&15*
Wayarsa ya d’auko daga aljihun shart din dake jikinsa sai ya nemo number ta ya shiga kira.

lokacin ni kadaice zaune a falon Ummah ina karyawa, jin kira ya shigo wayata dake gefena a ajiye yasa da sauri na kai hannuna kan wayar kwata-kwata ban kawo shi bane sai da na duba naga number sa akan wayar. tsaki naja na mayar da ita na ajiye a nutse na cigaba da abinda nake.

Ya kira kusan sau hudu bata dauka ba jikinsa yayi sanyi sosai kuma ransa ya ‘baci da abinda tai masa yanke shawarar tura mata text yayi kamar haka.”

_*Aunty Sa’ida ina fatan kin tashi lafiya na kira wayarki babu adadi sabida wulakanci kin’ki dauka kin tafi kin bar baya da kura a gida saboda ke Baba ya kori Ummatu gidansu bayan haka kuma Gwaggo tana nan cikin damuwa ko abinci ta kasa ci kiyi hakuri ki dawo gida idan ni nake takura miki to ina mai tabbatar miki da cewa gobe i yanzu ina skull saboda haka ki dawo gida saboda farin cikin masu kaunarki.*_

Text din na duba jikina yayi sanyi jin cewar Ummatu na gidansu me yayi zafi da Kawu Iro zai yanke irin wannan hukuncin sai duk naji banji dadin al’amarin ba.

Dakin ta shigo ta sameni a zaune ga kayan break din a gabana na kasa ci tace.”Lafiya kika zabga tagumi haka.”?

A sanyaye nace.”Umma wai kinji Ummatu tana gidansu saboda abinda tayi min Kawu Iro ya yanke mata wannan hukuncin.”

Cikin rashin jin dadi tace.”Ikon Allah me yayi zafi shi kuwa da zai yanke irin wannan hukuncin a gaskiya ban Ji dadi ba wallahi.”

Nace.”Nima gabadaya jikina ya mutu wallahi a cewarsa wai ba zata dawo ba har sai na koma gidan.”

Umma shuru tayi tana girgiza kanta kafin tace.”A gaskiya Ibrahim ya yanke hukuncin da bai da dace ba ai bai kamata da girmanta da komai yayi mata haka ba.”A sanyaye nace.” Nima dai haka na gani.” tana kokarin bud’e wardrobe d’inta tace.”To Allah ya shiga cikin al’amarin ya sasanta tsakaninsu.” na amsa da “ameeen ya Allah.”

Khalid kai tsaye can babban gida ya nufa gidansu mahaifiyar tasa dake unguwar dala gidan yawa ne irin na gado duk wanda ya tashi a gidan yake aure ya zauna kafin Allah yayi masa nasa shiyasa gidan kullum yake a cike da yara kowanne da nasa .

Kai tsaye bangaran su Mahaifiyarsa ya nufa ya same su suna karyawa da koko da awara zama yayi kusa da kakarsa mai suna Baito yana tsokanarta ganin yanda ta tasa bokitin koko a gabanta tana sha. Tace.”Kai ma idan kana sha sai na zuba maka badan halin Ubanka ba.”

Yace.”Aa bana shan koko kashe min jiki yake.” shuru tayi ta cigaba da kur’bar kokonta yace.”Baito naga kamar haushina kike ji.”

A fusace! tace” Ba dole naji haushi ba Khalid jiya da bakin cikin kakarka da babanka na kwana saboda tsabar rashin mutunci su koro min yarinya cikin dare mai tayi musu da zafi da har zasu yanke mata wannan hukuncin.”?

Yace.”Baito dan Allah ki samu nutsuwa muyi magana ta fahimta yanzu ina Ummatu take.”?

Tace.”Tana Bandaki.” shuru yayi na minti biyu kafin yace.” Baito Ummatu bata fad’a miki laifinta ba ko.”?

Tace.”Ta fad’a min akan wannan lalatacciyar yarinyar ubanka ya koro ta.”

Khalid yaji kamar ta soka masa wu’ka a ma’koshi yace.”Baito bai kamata ba abinda kukeyi kuma fa kun haifa kina da ‘ya’ya da jikoki bai kamata ki dinga aibata d’an wani ba yau ko gaskiya ne zargin da kukewa auntyn Sa’ida bai kamata ku dinga zaginta kuna la’antar ta ba kamata yayi kuyi mata adduar shiriya.”

“Allahu akbar! Khalid ka gama nasihar ko baka gama ba.”? Tafad’a tana masa wani kallo. yace.” Da alama maganata bata gamsar dake ba.”

Da sauri tace.”Ta ina kuwa zata gamsar dani bayan nasan karya kake kana fada ne kawai dan ka kareta nan Jamila take sheda mana irin lalatar da takeyi da maza a makarantarsu saboda haka maganar Jamila ba karya bace Sa’ida bata da kintsi da kamun kai.”

Jamila ‘yar yayan Ummatu ce da suke zaune a cikin gidan Jamila budurwace ‘yar kimanin shekara goma sha takwas tana zuwa makarantar da Sa’ida take koyarwa ta *Hajara Buhari* dake goran dutse.

Khalid yace.”Jamilan ce tazo tana fad’in wannan maganar.”? Baito na kokarin yin magana Ummatu ta karaso gurin da sauri tace.”Rabi kinga Khalid daga zuwansa ya soma kalubalantata akan na fadi gaskiya ashe har Sa’ida ta fiki kima da mutumci a gurinsa.”

Ummatu ta ajiye butar dake hannunta rai a ‘bace tace.”Baito aini tuntuni na gama magana wallahi tallahi duk ranar da yaron nan ya sake shiga sabgar Sa’ida to sai yaga abinda zai faru dashi.”

Khalid yace.”Ummatu dan Allah ki daina wannan maganar aunty Sa’ida ‘yar uwata ce bai kamata ki raba zumuncin dake tsakanina da ita ba.”

Tace.”Ai nima dama ba zumuncin ku nace zan raba ba abinda nake nufi shine ka raba kanka da ita tunda duk wasu alamu ka nuna kana sonta in banda rashin hankali irin naka Khalid me zakayi da wannan yarinyar tsohuwa gata mara daraja da kamun kai kai yanzu ba zakaji kunyar auranta ba.”

Yace.”Ummatu babu kunya a cikin abinda ya zamanto halas dan aunty Sa’ida ta girme ni hakan ba zai hanani na aureta ba tunda ba haramun bane.”

Baito tace.”To ba zaka aureta ba d’in Khalid ba zaka lalata mana zuria ba kaje ka nemo wata ka aura idan baka samu ba kazo gida ka duba gamu nan da ‘yan mata kyawawa masu da kyau da duk abinda ake bukata.”

Shuru yayi ransa duk a ‘bace ya tsani yaga suna nuna k’yamarsu akan auntynsa a ganinsa sam bata cancanci haka a gurinsu ba.

A cunkushe yace.”Dama ni nazo ne domin nayi muku sallama idan Allah ya kaimu gobe zan koma makaranta”

Baito tace.”Wace makaranta kuma? dama baka gama karatun ba.”?

Yace.” Akwai sauran kad’an.” Tace.”To Ubangiji Allah yasa daga ka gama ka samu aiki kaga sai kayi auranka da hujja ni nafi so ma kazo gida ka duba wallahi ina yi maka sha’awar Jamila.” tana ‘yar dariya ta ‘karasa maganar.

Hararar gefan ido yayi mata yana kokarin mi’kewa yace.”Baito ni dai Namiji ne babu wanda zai yi min auran dole.”

Ummatu tace.”Khalid magana kake so ka fad’a mata saboda baka da kunya.”?

Girgiza kansa yayi yace.”Aa Ummatu kiyi hakuri dan Allah abar maganar amma ni kada a ‘kara yi min maganar wata Jamila bana ra’ayinta.”

Ummatu ta fusata sosai tace.” ‘Yar d’an uwan nawa kake k’yamata? meye aibun Jamila yarinya kyakykyawa fara mai kuruciya a jika.”

Shuru yayi bai tanka ba yasa takalmansa Baito tace.”Ai ni mamaki ma ya hana ni magana ‘kiri-‘kiri yaron nan yana nuna yafi kaunar dangin Ubansa akan na uwarsa.”

Khalid dai baice komai ba ya kama hanya ya fita daga gidan gabad’ayansu suka bishi da kallon mamaki!! bayan fitarsa Baito tace.”Rabi hak’ika zama bai ganki ba tilas ki fara neman taimako akan yaron nan idan ba hakaba anan gaba cewa zaiyi ba ke kika haifeshi ba.”

Ummatu ta sunkuyar da kanta ranta idan yayi dubu ya ‘baci tace.”Baito maganarki gaskiya ce Khalid kwata-kwata baya ganina da mutunci baya jin maganata sai ta kakarsa duk abinda Gwaggo tace shine daidai a gurinsa ni ya raina ni alhalin ni na haifeshi kuma mutukar za’a zagi Sa’ida a gabansa sai ya nuna ‘bacin ransa saboda haka dole na nemi taimako a gurin malamai su karkarto da hankalinsa kaina dan na rantse ba zai auri Yarinyar nan ba.”

Baito tace.”Abinda ya kamata kiyi kenan kada kiyi sanya idan anjima ki shirya sai muje gurin Malam Saminu zai taimaka miki akan lamarin.”

_Allah kasa mu dace jama’a wai uwa ce take d’ora ‘yarta a hanyar zuwa gurin malami a maimakon tayi wa d’anta kyakykyawar addua sai mugun baki take masa ‘karshe ma zata kaishi gurin malami Allah ya kyauta yasa mu gane_

Khalid na daf da fita sukayi karo da Jamila zata shiga gidan washe baki tayi da fadin”Laa Yaya Khalid ina wuni.”? Kallon banza yayi mata kafin ya ratseta ya wuce ba tare da ya amsa gaisuwarta ba, haushinta yake ji sosai akan k’azafin da tayi wa auntynsa…..Jamila a sanyaye tabi bayansa da kallo gabanta na faduwa itakam ya zatayi ne Allah ya d’ora mata kaunarsa a cikin ranta…jiki a mace ta shiga cikin gidan.

Gwaggo na zaune a tsakar gida ita kad’ai tayi suguri abin duniya duk ya isheta Sa’ida kawai take tunani idonta akan kofar shigowa gidan daga taji motsi zata zabura ta kalli kofa…..Uwale ta rangad’a sallama cikin gidan.

Gwaggo ta amsa mata tare da gyara mata gefanta ta zauna suka shiga gaisawa….Uwale tace.”Dama nazo ne naji inda aka kwana shin ina fatan kuna ganin kyawun maganin nan.”?

Gwaggo ta sauke ajiyar zuciya rai a ‘bace! tace.” Ai Uwale Yarinyar nan ta’ki bani had’in kai wallahi da ‘kyar ma ta bari aka turara maganin sau biyu daga nasa turaran a wuta zata dinga masifa ta fita daga dakin ta barni a ciki ina shakar haya’kin ke a takaice ma ta gudu daga gidan tun jiya.”

Uwale ta rike ha’ba cikin mamaki tace.”Kinji ko ai alamun da akwai iska a tare da ita kenan tunda gashi sun hanata zama a gidan saboda turaran da kikeyi musu.”

Gwaggo tace.”To hakan zata iya kasancewa amma ni ina tunanin abinda Rabi tai mata ne yasa ta tattara kayanta ta gudu.”

Cikin son jin gulma Uwale tace.”Oh! me kuma Rabin take mata.”? Gwaggo ta shiga bata labarin abinda ya faru…Uwale tace.”Ai kinga Rabi ko gado tayi dan mahaifiyarta Baito mara mutunci ce babu irin sharri da kazafin da ba tayi wa kishiyoyinta ba ni dama tuntuni nasan Baito ba mutuniyar kirki bace.”

Gwaggo tace.”Kice dai Rabi gadon mugun hali tayi.”? Uwale ta ‘bantari gora ta mi’ke kafarta a kan tabarmar tace”Wallahi kuwa Sau nawa muna had’uwa da ita a zauran malam ai shiyasa kullum nake fad’a miki cewar sai kin tashi a tsaye akan Rabi domin ita da mahaifiyarta biye-biyen malamai suke.”

Gwaggo tayi shuru tana jimanta al’marin…..Uwale ta yunkura da fad’in “Gwaggo ni zan tafi dama unguwa zani nace bari na shigo mu gaisa na kuma tambayeki halin da ake ciki.”

Gwaggo tace.”To Uwale nagode sosai sai kin dawo nazo gidan naki domin mu yanke shawarar yanda za’ayi domi gaskiya maganar Rabi da mahaifiyarta ya tsaya min a rai.”

Uwale tace.”To shikkenan ai babu damuwa sai kinzo din.” Sallama sukayi da juna…Uwale na kokarin fita daga gidan Khalid ya shigo da kyar ya gaisheta yana dauke kansa ya shige gidan.

Gwaggo na ganinsa shi kadai fuskarsa kuma babu annuri sai tasha jinin jikinta…..Ya zaune kusa da ita yana matse gumin goshinta a sanyaye tace.”Jarumi ya ake ciki ne ina Sa’idar.”?

Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace.”Gwaggo lokacin da muka isa gidan Alhajin ya fita sai na yanke shawarar kiran wayarta Gwaggo nayi nayi ta daga ta’ki haka na hakura na kyaleta.

Tace.”Yanzu dai baku samu nasarar daukota ba.” Kansa kawai ya daga mata ya lumshe idonsa damuwa ce mai tsanani take damunsa.

Gwaggo shuru tayi na minti biyu kafin tace.”Idan anjima da yamma zanje gidan ayi wacce za’ayi.”

Idonsa ya bude da sauri yace.”Kada kije musu gida ki bari Baba yace zai koma da daddare insha Allahu komai zaizo da sauki amma ni bana so kije gidan kiyi wani abu suji haushinki ko kuma daga baya kiyi nadama kiyi hakuri abi komai a hankali.”

Shuru tayi ba dan maganarsa ta gamsar da ita ba, yace.” kin san gobe ni zan koma skull ko.”? Girgiza kanta tayi tace.”Bani da labari aini na dauka ka gama karatun ganin wannan karan ka dade a gida.”

Yace.”Yajin aiki malamai suka tafi karatu kuma da yardar Allah na kusa kammalawa ki cigaba dayi min addua idan na gama na samu aiki.”

Tace.”Insha Allahu zan cigaba dayi maka addua.”

Mikewa yake kokarin yi tace.”Zaka ci abinci ko.”? kallonta yayi kafin yace.”Idan yanzu kika girka zanci.” Tace.”Sai dai na dauki taliya d’aya a cikin kayan abincin Sa’ida nayi maka dafaduka da daddawa irin wacce kakeso.”

Girgiza kansa yayi yace.”Kada ki ta’ba mata kayan abinci bari nai wanka na fita na siyo sai kiyi min.” Tace.”Khalid kada ka ‘batar da kudinka zasuyi maka amfani a makaranta ka bari a d’auka tunda da akwai.”

Yace.”Gwaggo bana bukata na fad’a miki ki kyaleni naci aljihuna bana fatan wata mace ta ciyar dani.” Tace.”To shikkenan bari naje na siyo kayan miyar da zanyi maka girkin.”

Yace.”Ki zauna ki huta duk zan had’o komai da zaki bukata gurin girkin.” Shuru tayi tana kallonsa har ya shige gurinsu….Ta sauke ajiyar zuciya cikin ranta take masa fatan alkairi.

Tsaf tayi masa jallop din taliya irin ta mutanan da taji daddawa da manja da kifi sosai yaji dadin abincin ya dinga ci yana santi ita kuma sai dariya take masa dama haka take so ya sake ya cika cikinsa da abinci……Bayan ya kammala cin abincin a nutse ya kalleta da fad’in “Gwaggo ni zan fita nayi sallama da abokaina dan gobe da wuri nake so na tafi.”

Tace.”To shikkenan Jarumi sai ka dawo.” Khalid yasa takalmansa ya fice daga gidan ita kuma ta juye ruwan zafin dake kan wuta ta surka ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje ta shirya jikinta cikin atamfa (nicam) riga da zani da mayafi ta daura dankwalin (disco) a kanta pose dinta da dan mukkuli ta dauka ta fito ta kulle dakin takalmanta na dan’ko tasa a ‘kafafunta ta fita daga gidan……Bakin titi ta fita tana addua akan Allah yasa kada ta hadu da Khalid din cikin ikon Allah kuwa har ta shiga adaidaita sahu bata ganshi ba.

Har bakin gate din gidan Alhaji Shamsu aka ajiyeta ta fito tana gyara lullu’bin mayafin atamfar dake jikinta, Pose din ta bude ta dauko dari biyu ta mika masa ya kar’ba tare da dauko hamsin ya bata a matsayin canjin ta.. karba tayi da sauri tasa a cikin jakarta tana masa godiya yaja babur dinsa yayi gaba.

Gate din gidan ta nufa ta bubbuga maigadin ya bude ganin kamar yasan fuskarta yasa ya gaisheta tace.”Ina fata ka sheda ni ko.”? Maigadin yace.”Eh na sheda ki Gwaggo bisimillah shigo mana.”

Gwaggo ta shiga gidan tana hamdala a cikin zuciyarta……………Gyaran kayan miya mukeyi da Asabe kawai naji sallamarta nai saurin daga kaina ina kallon bakin kofa. Ido muka had’a da ita tace.”Babu shakka Sa’ida wato ke kina nan hankalin ki a kwance kin bar mu cikin damuwa ko.”?

Bagarar da maganarta nayi nace.”Gwaggo sannu da zuwa ki shigo mana.” Tace.”Ai ko baki fad’a ba.” Asabe na murmushi ta gaisheta ta amsa tana bin gurin da kallo sai ta’be baki take.

Sanin halinta yasa nayi saurin mi’kewa da fad’in “Shigo mana.” Ba tare da tace komai ba ta biyo bayana…Ummah kawai sai ganin mu tayi a tare.

Da sauri tace.”Gwaggo kece kike tafe da yamma haka.”?

Tana kokarin cire takalmanta domin shiga falon tace.”Aikuwa dai nice nake tafe ko dai ba’a maraba dani.”?

Ummah Habiba tace.”Aa Gwaggo ana maraba dake shigo ga guri ki zauna.” Ta shiga ta zauna kan kujera tana gyara yafan mayafinta.

Cikin mutunci da girmawa Ummah ta gaisheta ta amsa babu cikakkiyar walwala a tare da ita.

Nace.”Gwaggo sannu da hanya.” tayi saurin fad’in “Ai bazan amsa gaisuwarki ba Sa’ida tunda kin nuna mana iyakarmu.”

Nace.”Gwaggo wace irin magana ce wannan.”? Fashawa tayi da kuka tace.”Wato Sa’ida saboda Ibrahim bashi da kudi baya baki shayi da biredi baya siyo kayan miya da nama shine kika tattaro kayan ki kika gudo gidan mijin mahaifiyarki to komai talaucin mu mune gatanki sabida haka ‘kafata k’afarki zamu koma gida dan ba zan zauna ayi min ‘karfa-‘karfa ba.”

Cikin aljabi da mamaki nake kallonta lallai Gwaggo ta iya sauya lamari wato tanan ta ‘bullo kenan.”

Umma Habiba tace.”Haba Gwaggo banji dad’in wannan magana ba wallahi Sa’ida bata da gata sai ku kuma duk rashi da taulacin Kawunta bai gaza da ita ba yana iyakacin bakin kokarinsa akanta to me zai sanya kiyi wannan maganar.”

Shuru tayi bata tanka ba.Umma Habiba ta cigaba da cewa” Sa’ida tazo gidan nan jiya da daddare cikin damuwa da tashin hankali ta sheda min irin cin mutuncin da Ummatu take mata wannan dalilin yasa nace ta zauna ta huta idan ta samu nutsuwa sai ta koma.”

Gwaggo tace.”Eh hakane abinda tazo ta fad’a miki Ummatu taci mutuncin ta amma kuma Kawunta Ibrahim ya dauki mataki dan yanzu zancan da nake miki Rabi tana gidansu kuma yace ba zata dawo ba sai Sa’ida ta dawo saboda haka idan ke ‘yar halak ce sai ki had’a kayanki mu tafi gida idan kuma kikayi sanadiyar raba auran Ibrahim da matarsa to zaki shiga bakin duniya.”

Sa’ida da mahaifiyarta jikinsu yayi sanyi! Gwaggo ganin duk jikinsu ya mutu sai taji dadin hakan ta cigaba da zuzuta al’amarin…..Ummah Habiba tace.”To shikkenan Gwaggo magana ta ‘kare Sa’ida zata biki amma sai mun jira Maigidan ya dawo.”

Gwaggo wani irin kallo ta watsa mata a fusace tace…..
*GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*

*MUTANAN NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA NUMBER DA ZAKU NEMA……22790899076*

*SADAUKAWA NE GA IYAYE BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

_*Hakika ina alfahari dadu Iyayena🤝🏻🥰*_

*16&17*
*’KARSHEN FREE PEGE*
“Wane irin sai maigidan ya dawo kuma Habiba kina nufin zanyi ta zama a gidan nan har sai mijinki ya dawo ya bada umarni.”? ta’karashe maganar tana hararar ta.

Umma Habiba taji rashin dadin maganar Gwaggon amma sai ta daure ko a fuska bata nuna ba tace.”Gwaggo abinda nake nufi kenan a bari ya dawo a bashi hakkinsa a matsayinsa na mijina tunda tamkar uba yake a gurinta saboda haka dan Allah kiyi hakuri kada ki dauki maganata da wata manufa ta daban.”

Ta’be bakinta tayi tace.”Saboda kawai nice sarkin zargi sai na dauki maganarki da wata manufa shikkenan ai tunda kince haka sai na zauna na jira shi ya dawo na dai fad’a miki ‘kafata ‘kafar Sa’ida dan ba zan yarda da raina da lafiyata jinina yayi agolanci a wani guri ba.”

Cikin takaici nace.”Wai Gwaggo wace irin magana ce wannan kike yi dan Allah kiyi shuru haka ki daina d’aga mirya da tada jijiyar wuya magana ta ‘kare zan koma gidan ko dan saboda Ummatu ta dawo d’akinta.”

Shuru tayi min ba tanka ba. Umma ta sauke ajiyar zuciya da fad’in “Ai maigidan ma yana kan hanya shida na yamma suke dawowa daga kasuwa.”

Tace.”To Allah ya kawo su lafiya.” Umma Habiba ta amsa da “ameen tare da mi’kewa domin fita daga falon Gwaggo ta dakatar da ita, da fadin ” Nace ko kina da goro ki bani wallahi garin sauri na manta nawa a gida.” Tace.”Gwaggo ni bana cin goro amma bari na tambayar miki Hajia Hansatu.” tana nufin uwargidansu. tace.”To nagode Habiba ina jira wallahi sha’awar cinsa ce ta taso min a yanzu idan ma babu a gurinta ga kudina a siyo min.”

Umma Habiba tace.”Ba za’a rasa ba insha Allahu bari na tambayar miki ita.” Fita tayi daga dakin da sauri.

Nace.”Gwaggo ba zaki daina cin goro ba ko.”? Kallona tayi cikin kulawa tace.”Sa’ida ai ina jin sai ranar da numfashi ya bar gangar jikina zan hakura da goro ya zame min masifa ni kaina so nake na daina amma na kasa.”

Nace.”Abu ne da kuka sanyawa ranku wanda kuke ganin idan baku ci ba wata matsalar zata iya faruwa daku kuma ba haka bane da zaku yi sati guda baku ci ba babu abinda zai same ku sai ma lafiya da kuzari da zakuyi amma dan jaraba kuyi ta cin abinda zai cutar daku.”

Shuru tayi bata ce komai ba. nasan duk surutan da zanyi akan al’amarin ba zata d’auka ba cin goro ya zame mata jinin jikinta.

“Gwaggo zan koma gida amma da akwai sharad’i.” Da sauri ta kalleni, na sha kunu da fad’in “Kiyi min tsakani da Khalid babu ni babu shi yaron bai da kirki da tarbiya akwai abubuwan da suka faru a tsakaninmu wanda idan na fito na fad’a miki hankalinki zai tashi ko kuma ma kice nai masa sharri to wannan dalilin yasa nayi shuru da bakina inaso ki zauna dashi kija masa kunne sosai ya fita daga sabgata maganar yana sona ya ajiyeta a gefe guda dan na rantse ba zan aureshi ba koda kuwa zan rasa mijin aure keda kike goya masa baya akan lamarin ki cire kanki domin ke zakiji kunya. abu na biyu kuma kina d’ora min lalurar aljanu ni lafiyata kalau kamar yanda nasha fada miki aure lokaci ne sabida haka Uwale ta daina janki gurin masu magani kina asarar kud’in ki bayan haka kuma idan kin san akwai ragowar wannan turaran da kike turnuk’awa a daki to da mun koma ki zubar dashi dan wallahi duk ranar da kika sake kunnawa zan bar gidan kuma komai abinki ba zan dawo ba guduwa ma zanyi ku rasa inda na nake.

Gwaggo gabanta ya fad’i! ta tsira min ido nace.” Wallahi Gwaggo wannan maganar da nake miki har cikin zuciyata nake miki ita Khalid ba tsaran aure na bane ki daina tatsuniya ba zan aureshi ba sannan ni lafiyata kalau aure kuma lokaci ne insha Allah cikin satin nan Alhaji Nura zai turo da magabatansa.

“Sa’ida meye aibun Khalid da zaki dinga gudunsa ko dan bashi da kudi ne.”? A sanyaye take magana dan na lura jikinta yayi sanyi da maganata.

Girgixa kaina nayi ina kokarin magana Umma ta shigo falon hannunta da farar leda cike da goro manya masu kyau Gwaggo da sauri tasa hannu ta kar’ba da fad’in ” Kai amma naji dadi sosai Habiba Allah yayi miki albarka.”

Umma Habiba ta amsa da “ameeen ya Allah.” Ta fita daga falon.

Ledar ta kwance ta dauko daya ta ‘bantara ta fara taunawa. Nace.”Gwaggo Khalid ko ya kai *Dangwate* kud’i a duniya baya cikin tsarina yaje can ya auri daidai dashi nima na auri daidai dani magana ta mutu a gidan nan kada ki Sake yi min maganar Khalid.”

Tace.”Ai shikkenan Sa’ida tunda kinqi Khalid har kina kokarin yi masa sharri zanyi masa magana ya rabu dake tunda bakye kad’ai ce autar mata ba insha Allahu Allah zai bashi wacce ta fiki kyau da ‘kuruciya.”

Nace “Nima zan taya shi da adduar samun macan data fini.”

Shuru tayi min ta cigaba da tauna goronta kallonta kawai nayi na gane maganata ta kashe mata jikinta, nace.”Ko na kawo miki abinci.”?

Girgiza kanta tayi tace.”Bana bukata saboda inda na baro da akwai abinci.” Nasan magana ta fad’a min a fakaice oho! ni dai na fad’a mata abinda yake raina sabida haka ita da Khalid din duk su shiga hankalinsu.

Tace.”Khalid d’in ma gobe zai koma makaranta.” Nace.”Allah ya bada sa’a.” ta amsa da “ameeen ya Allah.”

Umma ce ta shigo dakin da fad’in “Gwaggo Alhajin ya dawo tashi muje nayi miki jagora ku gaisa.” Da sauri ta miqe tana gyara yafan mayafinta suka fita tare.

Alhaji Shamsu yana zaune a kan kujera yana lissafi da wayar hannunsa sukayi sallama a dakin nasa….cikin kulawa ya amsa da fad’in”Gwaggo sannu da zuwa ga guri nan zauna.”yafada yana nuna mata kujerar dake kallonsa

Gwaggo ta zauna kan kujerar tana amsawa tare da fad’in “Ai na jima a gidan ina jiranka da fatan ka dawo lafiya.”? Yace.” Lafiya lau gwaggo ai ban sani ba da tuntuni na dawo gidan sabida ke koda na shigo ma maigadi yake sanar dani zuwan Ibrahim bayan fita ta hakika banji dadin faruwar hakan ba.”

Tace.”Aikam dole kaji rashin dadi dan muma jiya haka muka kwana zuciyoyinmu Babu dadi wannan dalilin ne ma yasa shi Ibrahim dako sammako yazo gurinka domin ku tattauna magana sai kuma akayi rashin sa’a ka fita kasuwa shine nace to ni bari idan rana tayi sanyi sai nazo gidan na sameka mu tattauna maganar dan nazo tafiya da Sa’ida ne matarka Habiba tace lallai sai ka dawo ka bada umarni shine nace to komai dare kuwa zan zauna har ka dawo domin naji uzirinka akan yarinyar.”

Alhaji Shamsu yayi gyaran murya yana kallonta ya riga yasan halinta ‘yar taratsatsi ce yace.”Hakane Gwaggo Sa’ida tazo gidan nan cikin halin damuwa tana kuka ta sheda mana abinda yake faruwa acan gidan al’amarin ya tayar min da hankalina sosai Gwaggo shi ai aure lokaci gareshi mai zai sanya ku tayar da hankalinku akan yarinyar nan har ku dinga d’ora mata lalura irin ta aljanu bayan haka kuma har a samu masu yi mata ‘kazafi na zina wannan al’amari baiyi min dadi ba gaskiyar lamari raina ya ‘baci dajin wannan magana shine dalilin da yasa ma na yanke hukunci kancewa ba zata koma gidan ba sai an kwana biyu kuma dole ne mu samu zama dashi Ibrahim din akan maganar yana da kyau ya jawa matarsa kunne ta guji jifan yarinyar nan da muna nan kalamai domin hakan bai dace ba.”

Gwaggo tace.”To ai Alhaji Ibrahim ya tauna tsakuwa dan aya taji tsoro inaso na sheda maka cewar duk yanda kake kaunar yarinyar ba kamar shi ba tunda Ubanta ne ya saki nono shi ya kuma ya kama kaga dole yayi kishinta ya kuma nunawa matarsa ‘bacin rai dan yanzu maganar da nake maka Rabi tana gidansu tun jiya ya koreta daga gidansa yace mutukar ba Sa’ida ce ta dawo gidan ba to ya gama zama da ita.”

Alhaji Shamsu yace.”Subahanallahi Me yayi zafi Ibrahim zai yanke wannan hukunci.” Ummah Habibatan tace.”Nima haka na gani Alhaji Iro ya yanke hukuncin da bai kamata ba ai komai a sannu a hankali ake binsa.”

Gwaggo tace.”To ai shine nake so ku fahimta Ibrahim zai iya rabuwa da matarsa akan yarinyar nan to tun kafin hakan ta faru yasa nazo domin tafiya da ita.”

Hankali a tashe ya dauki wayarsa da fad’in “Bari na kira wayarsa idan da hali sai yazo domin mu tattauna maganar a tsakanina dashi amma banji dadin wannan lamari ba.”
Gwaggo tace.”To shikkenan ai yanzu nasan ya dawo daga kasuwa idan ma bai dawo ba to babu shakka yana kan hanya.

Kawu Iro na adaidaita sahu kira ya shigo wayarsa ganin number Alhajin yasa da sauri ya daga suka gaisa a tsanake Alhaji Shamsu ya sheda masa uzirinsa….Kawu Iro yace.”To babu damuwa Alhaji ganin zuwa insha Allahu.” Wayar ya kashe ya umarci direban daya juya baya ya kaishi hotoro. Yace.”Amma dai zaka ‘kara min kudi ko.”? Kawu Iro yace.”Eh ‘kwarai kuwa idan ma ka samu fasinja ka dauka.” yace.”to shikkenan.

Sai magariba Kawu Iro ya isa gidan kuma basu samu zama ba sai da suka gabatar da sallah tukkuna suka fito daga massalaci a tare wani ‘kebantacan guri suka samu suka zauna suka sake gaisawa cikin mutumci kana suka shiga tattauna abinda ya had’asu.

Kawu Iro ya sauke ajiyar zuciya da fad’in “Alhaji ka kwantar da hankalinka insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba maganar mai d’akina kuma ni a ganina hukuncin dana dauka a kanta shine daidai kaga gaba zata kiyaye jifan yarinyar nan da wata mummunar kalma.”

Alhaji Shamsu yace.”Hakane Ibrahim to amma inaso dan Allah ka sake sanya ido akan yarinyar nan sannan idan da wani wanda kaga alamun da gaske yake sonta to kayi masa magana ya fito kawai domin hakan shine ya dace.”

Kawu Iro yace.”Insha Allahu hakan za’ayi akwai wani mutumin anan gaban inda muke yana son ta koga yanayin hidimar da yake mata to saboda haka idan na koma gida zan sameshi da maganar domin mu tattauna.”

Alhaji Shamsu yace.”To Alhamdulillahi Allah yasa sanya alkairi.” Kawu Iro ya amsa da ameeen ya rabbi.”

To muna zaune a falo har gwaggon muna hira ya shigo. gwaggo tayi saurin fad’in “Ina fatan Ibrahim din yazo.” Yace.”Eh Gwaggo yazo ina fita da niyyar shiga massalaci na hangi zuwansa tare ma mukayi sallah masha Allah mun tattauna magana dashi ta fahinta saboda haka ke Sa’ida zaki koma gida magana ta wuce insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba sannan kuma Ibrahim ya sheda min cewa akwai wani mutumi da yake sonki a Cikin unguwar to nace masa yayi magana dashi idan da gaske yake sai yayi magana ayi abinda za’ayi.”
Gwaggo har ta bud’e baki za tayi magana sai kuma ta fasa.

Yace.”Gwaggo kamar akwai magana a bakinki.” girgixa kanta tayi tace.”Aa babu magana Alhaji.” Ya kalleni da fad’in “Kinji hukuncin dana yanke ko.”? Nace.” Eh naji Alhaji dama nima inaso nayi masa magana kan cewa ya turo magabatansa ayi maganar aure idan da gaske yake.”

Alhaji yace.”To Alhamdulillahi hakan yayi kiyi masa magana shima Ibrahim din yayi masa sai ya dauki maganar da muhimmanci.” Nace.”To shikkenan Alhaji.” hannu yasa a aljihu ya dauko kudi kimanin dubu biyar ya mikawa Gwaggo da fadin “Gashi kya sayi goro.” Babu yabo babu fallasa ta kar’bi kudin dan Taji masifar haushin yanda yake nuna ikonsa akan Jikarta wai duk muna nan maganganun data ya’ba masa ba suyi masa zafi ba sai wani za’kal’kalewa yake.

Bayan fitarsa daga falon Ummah Habiba tace”Gwaggo bari na kawo miki abinci kici sai ku taf……tun kafin ta ‘karasa tayi saurin katseta da fad’in “Bayan wanda naci d’azu kuma zaki sake d’ubga min wani Aa bana bukata tafiya za muyi.” kana jin yanda tayi maganar kasan a fusace take……mi’kewa tayi tana gyara yafan mayafinta, nida Umma muka bita da kallon mamaki.

A cunkushe tace.”To gimbiya ina jakar kayan naki take na d’aukar miki.” Murmushi takaici nayi ba tare dana tanka mata ba na mi’ke Umma ma ta mi’ke tana ‘yar dariya nasan ita da gwaggo ne….Hijabina na gyara na dauki jakar kayana na ri’ke ta ta’be bakinta tai tayi gaba tana surutai! Umma tace.”Gwaggo ga mayafi da takalmi kayi amfani dasu.”

Juyowa tayi tana kallon ledar hannunta murmshi tayi wanda be kai ciki ba tace.”Habiba kin manta ni tunda jajayen sawuna bana yafa wani gyale idan ba na atamfa ba.”

Umma tace.”Kwarai hakane na manta wallahi to ki kar’ba dai ko kyautarsa sai kiyi…..Nace.”Umma ki ajiye mayafin ki zaiyi miki amfani idan ta kar’ba ma munaf*ckar matar nan zata bawa Uwale.”

Umma ta ri’ke bakinta cikin mamaki tana kallon Gwaggo tace.”GwaggoAshe har yau kina tare da Uwale.”?

Da sauri tace.” ‘Kwarai kuwa ba kuma mai rabani da ita sai mutuwa.” Tana gama maganarta tasa takalmanta ta fita ta barmu…Umma tace.”Sa’ida ki cigaba da hakuri kinji ko watarana sai labari.” Nace.”Umma Insha Allah zan cigaba dayi nasan Allah yana kallo.”

Ta mi’ka min ledar da fad’in ” ‘Karbi ki ri’ke mata tunda nayi niyya bazan fasa ba babu ruwanki da wanda zata bawa.” ledar na kar’ba da fad’in “To shikkenan.” sallama mukayi da ita tace.”Lallai idan na fita na shiga d’akunan kishiyoyinta nai musu sallama.
Nace.”To insha Allah zan shiga.

bakin gate na same su a tsaye ita da Baba Iro suna jiran fitowa ta ina ta kici-kici da jakar kayana yazo ya kar’bi jakar yana fad’in ” Sai kiji da ledojin hannunki.” Nace.”Haba dai Kawu dan Allah ka ba kawo dik zan iya ri’kewa.” Gwaggo tace.”Au! ashe kayan naki suna da yawa tunda ga wasu nan a ledoji.”

Nace”Aa wannan ledar taki ce su kuma wannan yanzu akayi min kyautarsu amma ni ba dasu nazo ba.” hannu ta mik’a ta kar’bi ledar kayanta tayi gaba nabi bayanta ina mamakin ‘karfin halinta.

Direba ya kar’bi jakar kayana yasa a bayan mota Gwaggo ta shiga ta zauna Kawu ya zauna kusa da direba ina kokarin shiga……..Motarsa ta shigo gidan tsayawa nayi har direbansa yayi parking ya fito a nutse cikakken mutum kamili dogo ba’ki da kyau daidai misali saboda yanayin hutu da jin dadi yasa bakar fatarshi tayi wani freesh sai daukar ido take…… kwata-kwata Yaya Aminu baida izzah irin ta masu kudi dalilin ma da yasa kenan nake ‘kara mutunta shi.

Fuska a sake ya ‘karaso inda nake yace.”Ranki ya dade dama kina nan.”? murmushi nayi a nutse nace.”Ina nan Yaya Aminu ya kake ya al’amura.”? Yana min wani irin duba yace.”Alhamdulillah wato dai ba zaki tambaye ni Iyali ba ko.”?

Dariya na d’anyi nace.”Yaya Aminu kenan to Ya Iyali.” Cikin sigar tsokana nayi maganar ya amsa min da “Suna nan lafiya kalau kamar gaske.

Dariya nasa ina kallonsa shima sai yasa dariyar Gwaggo ta le’ko kanta da fad’in ” Wannan kuma waye kike ta ya’ke masa baki.”

Da Sauri nace.”Yaya Aminu ne babban yaron Alhaji.” “Au! koda naji.” abinda ta fada kenan ta dauke kanta……Motar ya dafa cikin nutsuwa ya gaisheta ta amsa kamar bata so Ya mi’kawa Kawu Ibrahim hannu suka gaisa a mutunce, Ya dawo da hankalinsa kaina da fad’in “Tafiya zakuyi ne.”? Nace.” Eh wallahi.”
Jim! yayi kamar da magana a bakinsa kawai ya basar yasa hannu cikin aljihu sabbin kudi ya dauko ya mi’ko min.

Nace.”Dan Allah ka barshi.” girgiza kansa yayi yace.”Ki kar’ba mana ko katin waya kyasa ko.” hannu biyu nasa na kar’ba da fad’in “Nagode Yaya Aminu Allah ya ‘kara arziki.

A nutse ya amsa da ameeen to sai gani na biyu ko.”? nace” Aikuwa dai tunda kai ganinka ha’bo ne baka zama a gari.”

Yace.”To ya za’ayi Sa’ida taurari na masu zagaye ne nima ba a san raina nake zurga zurga nan ba.

Nace.”Hakane to Allah ya taimaka.” Ya amsa da “ameeen tare da daga min hannu da sauri ya wuce cikin gidan……Ina shiga motar ta rufe ni da fad’a ” Sa’ida wato kin mai damu marasa galihu ko kinga kudi duk kin gigice kin barmu zaune a mota to bari kiji wallahi komai abunki ba zaki sanjawa towo suna ba.”

Uffan bance mata ba ta cigaba da sababi tana fadin” Yana fama da ‘bakar fuska yazo ya tsayawa mutane to idan ma sonki yake sai dai yayi hakuri dan ba zaki aureshi ba ehe! ba naji ubansa na wata magana ba Kai Ibrahim kada ka kuskura ka tunkari Alhaji Nura da wata magana Sa’ida bata da miji sai Khalid da yardar Allah.”

Nida Kawu Iro shiru mukayi mata uffan ba muce ba ta ‘karaci surutan ta ta gaji tayi shuru tana gyangyadi. sai da muka isa gidan na tashe ta ta fito tana mita……Khalida dake can tsallaken gidansu Salim ya karaso gurin, hannunta ya ri’ke suka shiga gidan sai magana take masa ‘kasa-‘kasa…Yace.” To shikkenan Gwaggo magana ta wuce zan fita daga harkarta. har daki ya kaita ya karkade mata shimfidarta ta kwanta tana mita wai kafafunta ciwo suke mata da sauri yace.”Bari naje na siyo Roob sai na shafa miki a kafafun.

Yana kokarin fitowa daga dakin ni kuma ina ‘kokarin shiga mukayi karo dauke kaina nayi tare da bashi hanyar wuce wa…..ba tare da ya kalleni ba ya fice daga gidan.

Tana mitar ciwon kafafu tana fama da redio sai shuuuuuu! takeyi ta’ki kamawa da alama batir din yayi sanyi, da ‘kyar ta yunkura ta mi’ke tsaye da fad’in “Ai dole na fita na siyo batir.” Da sauri na kalleta tana kokarin yafa mayafi nace.”Gwaggo yau d’aya dai ai sai ki hakura kuma yanzu fa Khalid ya fita mai yasa bakice ya siyo miki batir din ba.”

Tace.”Sa’ida bana san takurawa Khalid bashi da kud’i shiyasa bance ya siyo min ba.” Nace”Idan kika bashi kudinki zai siyo miki ba lallai sai da kud’insa ba.” Girgiza kanta tayi tace.”Bai zama lallai ya kar’ba.” Nace.” Ki daiyi hakuri da jin redion ki barwa gobe.”

“Aa ba zan hakura da jin taskar labarai ba.” Hanyar fita ta kama cike da mamaki na bita da kallo maganarta naji a tsakar gida tana fad’in “Eh fita zanyi na siyo batir na redio na yayi sanyi ta’ki kamawa.”

Muryar Kawu naji yana fad’in “To koma ki huta bari naje na siyo miki.” Tace.” To yawwa Ibrahim nagode Allah yayi maka albarka.”

Dakin ta dawo ta zauna tana dai sake mummurd’a redion sai shuuuuuu take amma taki hakura.

Khalid ya shigo dakin da sallama a bakinsa itace ta amsa masa dan ni ko inuwarsa ma ban kalla ba….ya mika mata batir din da fad’in “Gashi Baba yace a kawo miki.” kar’ba tayi ta fara sawa a redion ya zauna kusa da ita tare da mi’kar mata da ‘kafafunta a nutse ya bud’e Roob din ya fara shafa mata. addua ta shiga yi masa kafin naji sun fara magana ‘kasa-‘kasa ‘karamin tsaki naja na fita daga d’akin buta na dauka na shiga band’aki ina jin takaicin abinda suke.

“Gwaggo na fad’a miki fa magana ta ‘kare zan fita daga harkata amma kuma ba zan daina so da kaunarta ba wannan nasan a jinin jikina yake……Tace.” Kuma ka kwantar da hankalinka idan ka koma makaranta kayi karatunka lafiya maganar Alhaji Nura Gaibu ce.
Murmushin takaici yayi yace.”Gwaggo qaddara ma Akawai aure a tsakaninsu to ni kuma mutukar ina raye sai na hanata jin dad’in aure wallahi.”

Shuru tayi ba tace masa komai ba ya mike da fad’in “Ni zan tafi kallon ball.” tace.”To dan Allah kada kayi dare.” yana kokarin fita daga dakin yace.”Da wuri zan shigo gida insha Allahu.

Ri’ke da buta na fito daga band’akin santsin ruwa dana takalmin ‘kafata yayi yun’kurin kayar dani salati nasa nayi saurin ri’ke kyauran bandaki dik da haka sai da nayi zaman da’baro a gurin. ‘Kuguna ya buge sosai na rintse ido ina kiran sunan Allah.

Gurin ya ‘karaso kawai naga ya sunkuya yana kokarin dauka ta….duk yanda naso dana hanashi kasawa nayi saboda naji jiki sosai jikina sai kyarma yake……har bakin kofar dakin ya ajiye ni ba tare da yace min komai ba ya juya ya fita daga gidan.
Jiki a sanyaye na bishi da kallon mamaki!

To washe gari da safe kadaran kadahan muka tashi gaisuwa ce kawai ta had’ani da ita sai da na shirya tafiya makaranta nayi mata magana, tace.”Ba zaki tsaya ki karya ba ga ruwan kunu na d’ora a wuta.”

Nace.”Gwaggo idan na tsaya karyawa zan makara zan samu wani abu naci a ofis.” Tace.”Ai ke idan ba dan kina da kurman jiki ba to da tuni kin zabge kiyi ta zama da yunwa ko damuwa bakya yi.”

Murmushi kawai nayi na gyara jakata dake kafad’a nace”Sai na dawo.” tace.”Allah ya bada sa’a.” na amsa da “ameeen.” Ina kokarin fita yana kokarin shigowa dakin baya na koma na bashi hanya ina d’an satar kallonsa yana sanye da ‘kananun kaya ya goya jaka a bayansa kafarsa sanye da boot ya taje tarin sumar kansa sai kamshin turare mai sanyi yake…..babu walwala a fuskarsa yace.”Auntyna barka da asuba.” Ba tare dana kalleshi ba nace.”Barka kadai ka tashi lafiya.”? a tsanake ya amsa yana kallona da fad’in “Zan koma skull yau.” nace.”Allah ya bada sa’a.” da sauri na fice daga dakin dan bana son wata duguwar magana a tsakaninmu.

Gwaggo kamar za tayi kuka haka sukayi sallama ta rakashi har soro tana ta zabga masa addua…..a daidaita sahun Salim ya shiga yana daga mata hannu shima yasan zaiyi kewar kakar tasa sosai ya sha’ku da ita akan mahaifiyarsa.

*BAYAN KWANA BIYU*
gidan ya samu nutsuwa domin a washe garin ranar dana koma gidan Ummatu ta dawo da daddare babu laifi dai zaman da akeyi a gidan tsakaninta da Gwaggo gaisuwa ce dan har yanzu ta kasa sakewa a gidan ni kuwa kullum idan mun had’u na gaisheta bata amsawa hakan bayayi min ciwo saboda dama tuntuni na riga na saba…..sosai naji dad’in tafiyar Khalid domin na sake a gidan ina abubuwan da raina yake so kai tsaye zanyi daurin kirji na fito tsakar gida ba tare da fargabar wani abu zai faru ba..Gwaggo kuwa ta hakura da turara haya’kin tunda na gargad’e ta a gidan Ummana ta kiyaye muna zaune lafiya yanzu sai dai amma kullum cikin zagin Alhaji Nura take tana kwashe masa albarka idan kuma yayi min ake tare da ita muke cinyewa.

To koda Kawu Iro ya samu Alhaji Nura da maganar sai ya nuna farin cikinsa sosai yace dama shima abinda yake ta sauraro kenan saboda haka tunda lamari ya kasance a haka zai turo da kudin sadaki i dan yaso in ya dawo daga tafiya sai ayi hidimar biki.”

Kawu Iro yace.”Hakan yayi insha Allahu kuma zamu saurari zuwan wakilan ka.” Cikin mutunci suka rabu da juna Kawu Iro ya kira wayar Alhaji Shamsu ya sheda masa duk yanda sukayi dashi…..sosai yaji dadin hakan kuma yayi fatan alkairi tare da jimirin jiran zuwan wakilan nasa.

Gwaggo kuwa a ranar Yini tayi tana sababi! har taso ta saka min ciwon kai ‘bacin ran abinda take yasa na fito na bar mata dakin

Tabarma na shimfida a tsakar gida na zauna ina duba jarrabawar yara kira ya shigo waya ta a nutse na dauka ina dubawa murmushi nayi ganin sunansa akan wayar Alhajin Allah kenan tun ranar da sukayi magana da Kawu Iro yake farin ciki a rana sai ya kira ni sau hudu ko biyar….gaishe shi nayi ya amsa yana tambayata aiki nace.”Alhamdulillahi Alhaji na.” Mirmushi yayi mai sauti da fad’in “Gimbiyar mata ina jin dadin yanda kike kula dani nasan idan aka daura auran zan zama d’angatan ki.”

‘Yar dariya nayi nace.”Aikuwa dai zaka sha lele a hannuna Alhaji saboda ni a rayuwata ina son mutum mai saukin kai ha’kika naji dadi sosai daka amince da maganata inaso ko bayan auranmu na cigaba da aikina ba wai dan ka gaza ba Aa ni kawai ina bukatar naga ana amfanuwa da ilmina.”

Yace.”Kada ki damu gimbiya insha Allahu duk abinda kike so nima inaso zaki cigaba da zuwa aiki da yardar Allah.” Cike da farin ciki nace.”To nagode sosai My love.” sai ya hau ‘ba’b’baka dariya da alama yaji dadin sunan dana kirasa dashi.

To cikin ikon Allah wakilan Alhaji Nura suka kawo kudin Sadaki dubu dari cas Kawu Iro yayi kara da kawaici ya bawa Alhaji Shamsu yace ya rike a gurinsa, aikuwa Alhajin yaji dadin karamcin da yayi masa.

Gwaggo yini tayi tana kuka ko abinci ta’ki taci sai ‘kunci da ‘bacin rai take koda Kawu ya dawo daga kasuwa rufeshi tayi da fad’a! akan lallai sai an mayarwa da Alhaji Nura kud’insa….Kawu ya ‘bata lokaci gurin nusashe ta ya d’ora da fad’in “Wallahi gwaggo idan baki daina adawa da auran nan ba sai rabo ya kashe ki kika san abinda Allah ya lullu’be a cikin alamarin to saboda haka dan Allah ki daina damuwa ki cigaba dayi wa yarinyar nan addua shi kuma Khalid Allah ya bashi daidai shi.”

Gwaggo jikinta yayi sanyi sosai da irin maganganun Kawun sai kawai ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido amma a zahirin gaskiya tana tausayawa khalid ganin yanda ya ‘kwallafa ransa akanta.

Ummatu kuwa kamar ta zuba ruwa a ‘kasa ta sha saboda dadi tunda dai har an riga an kar’bi sadakin Sa’ida sai ta kwantar da hankalinta tasan tayiwa Khalid nisa sai dai ya nemi wata kuma.

Wata shida aka tsayar da maganar daurin aurana da Alhaja Nura wanda kuma a daidai lokacin Khalid zai kammala karatunsa ya dawo gida dan duk wainar da ake toyawa bashi da labari duk da suna waya da mahaifinsa amma ko kad’an bai fad’a masa komai ba.

Ya kasance saura wata biyu daurin auran Alhaji Nura ya tafi Chana domin shigo da kaya kuma a qalla zaiyi kusan wata guda ko fiye da haka sosai naji rashin dadin tafiyarsa dan kusan kullum muna tare da juna a yanzu ni dashi munyi wata irin sha’kuwa kuma ina jin sonsa sosai a cikin raina saboda yana da saukin kai kuma duk abinda nake so to shima yana so wannan dalilin yasa nake marmarin auransa domin ina ganin zan samu duk wasu muradan da nake bukata a gurin d’a namiji.

To koda ya tafi kusan kullum muna tare a waya yana d’auke min duk wata kewarsa dake damuna.

Satinsa Uku da tafiya Khalid ya dira a gida ya dawo cikin farin ciki da nasara dan gabad’aya takardunsa sunyi kyau yanzu abinda ya rage masa aikin yi ne……Khalid ‘bangaran zane-zane ya karanta duk da kafin ya fara karatun sai da aka dinga bashi shawara akan ya canza cos ya’ki yace shi wannan ne ra’ayinsa to yanzu gashi yayi ya gama sai fafutukar neman aiki shin yanzu wane company ne zai d’aukeshi aiki? wannan fargabar tasa tunda ya dawo bai zauna ba kullum yana yawon neman aiki babu labari duk inda ya nufa babu nasara sai kawai ya ajiye takardun abokinsa Salim ya samar masa adaidaita sahu ya fara ja…sai sannan hankalinsa ya kwanta dan ya tsani ya zauna garjeje dashi a gida yana d’orawa mahaifinsa wahala.

*BAYAN SATI UKU*
Da dawowarsa da safe ya fito da shirin fita yana tsaye a kofar dakin Gwaggo suna magana tace.”Khalid sabgogi yasa har yanzu ka kasa zama na sheda maka abinda yake faruwa.”

Ba tare da ya bawa maganarta muhimmanci ba yace.”Me kuma ya faru a gidan bayan bana nan.”? Tace.”Shigo ciki ka zauna muyi maganar. agogon hannunsa ya duba kafin ya tu’be takalminsa ya shiga dakin.

A nutse ta kalleshi tace.”Kasan an kar’bi sadakin auran Sa’ida ko.”? da wani irin sauri ya kalleta bakinsa na rawa……”bangane ba gwaggo.”? Cikin takaici tace.”Alhaji Nura dai ya samu galaba akanka dan wata hudu da suka wuce ya bada sadaki magana tuntuni tayi nisa nake fada maka gobe ma idan Allah ya kaimu zasu kawo lefe.”

Wani irin gumi ne ya tsinke masa ya dinga katse goshinsa yana girgiza kansa yace.”Gwaggo Alhaji Nura bai samu galaba akaina ba wallahi ni nake da galaba akansa.”

A sanyaye tace.”Khalid kayi hakuri ka kwantar da hankalinka kaji ko watakila babu alkairi a tsakaninka da ita shiyasa Allah ya……”Gwaggo ya kike wannan maganar ne? wallahi akwai alkairi a tsakanina da ita ki daina fadar wannan maganar zuciyata zata tarwatse.”

Suguri tayi tana kallonsa jikinsa sai kyarma yake….Alhaji Nura ya bada sadakin auransa da Sa’ida yana zaune lallai dole ya dauki mataki dan yayi rantsuwa sai yayi aika-aika mutukar ba ta janye auran mutumin ba.

Mikewa yayi ya fita Gwaggon nata kiransa ko waiwayowa baiyi ba.

Tunda na doso layin na hangoshi a zaune a kofar gidan gabana yake faduwa na dinga mamakin zaman da yake a gurin shi kad’ai bayan yana da abin yi…..koda na karasa ban kalli inda yake ba na shige soron yayi saurin biyo bayana….hanya ya tare min yana min wani lalataccan kallo.

Rai a ‘bace nace.”Meye haka ko iskancin zaka gwada min.”? girgiza kansa yayi a cunkushe yace.”Soyayyata kika yi wa haka ko? Aunty Sa’ida ni Khalid kika watsa wa ‘kasa a ido ko ashe har kin kar’bi sadakin wancan ‘katon mutumin kin barni ina dakon! soyayyarki a cikin zuciyata aunty Sa’ida ni zaki yaudara ko.”?

A fusace! nace.”Khalid baka da hankali ko? ka dube ni ka dube ka dan Allah dan Annabi me zan samu a tare da kai? nace ka fad’a min idan na aureka me zaka bani!? me kake dashi idan na aure ka!! suwa zan nunawa nace musu wannan ne mijina.”!!? cikin hargagi gami da d’aga murya take maganar tana nunashi da hannunta…..aikuwa a fusace! ya kama hannun ya murd’e! jikinsa na rawa yana huci! da zufa! yace.”Ni kike fadawa wannan maganar ko.”? Hannuna na fizge a tsorace nayi nufin shigewa gida…ya fizgo ni na fad’a saman kirjinsa na dinga jin kirjinsa na sama da ‘kasa! “Wallahi sai na shayar dake ruwan mamaki! sai na karya alkadarin ki aunty Sa’ida kin raina ni ko? har kina nuna ni da hannu kina min kallon ‘kas’kanci to ki rubuta ki ajiye cewar Khalid Namiji ne kuma Jarumi ne a cikin maza.”

Fizgewa nayi daga jikinsa da mugun sauri na shige gidan gabana na dukan uku-uku wannan bala’i da masifar ya isheni.

Zamewa yayi ya zauna a gurin yana huci! da mayar da numfashi babu shakka zai nuna mata shi ba tsaranta bane.

“Ke kuma me ya faru kika shigo kina huci.”! Gwaggo ce take wannan maganar tana bin ta da kallo a lokacin data shigo gidan.

Raina a ‘bace nace.” Gwaggo wato baki dai baki jawa Khalid kunne ba ko.”? da sauri tace.”Wane Khalid kuma Sa’ida a ina kuka had’u bayan tun safe ya bar gidan nan.”

Nace.” Khalid ya dawo daga duk inda yaje sabida ya riski dawowata ya kuma tare ni a soro yana yi min wasu zantukan banza Gwaggo inaso ki ja masa kunne wallahi tallahi idan bai daina yi min shirme ba zan dauki mataki mai tsauri akansa.”

A sanyaye tace.”Mai da wu’kar Hakima kiyi hakuri kada ki dauki mataki akansa idan ya shigo zanyi masa magana.” Ajiyar zuciya na sauke na shige dakin raina duk a ‘bace da irin iskancin da yaron yake min kawai ya dinga da’kumar jikina ba tare da yayi shakka ba.

Sai wajejan goma da rabi ya shigo gidan dan ni har bacci ma ya soma daukata naji muryoyinsu ‘kasa-‘kasa suna magana….”Khalid kasan Alhaji Nura yana da kudi ina jin tsoron ta fada masa ba zaka iya sharia dashi ba.”

Cikin takaici da ba’kin kishi yace.”Ai dama shi yayi kad’an nayi shari’a dashi da Ubansa zanyi.”!

Gwaggo ta bud’e bakinta tana kallonsa da fad’in “Khalid me ya kawo zagi kuma.”? Yace.” Kinga Gwaggo maganar nan ta isa haka Allah ba zan yarda ba.” yana ‘kare maganarsa ya mi’ke ya fita, gurinsu ya nufa yana wani irin tangad’i kamar wanda yasha kayan maye ya bude dakinsa ya fad’a kan katifarsa yana fitar da wani irin numfashi mai wahalar gaske.

Gwaggo kuwa bayan fitarsa daga dakin addua ta shigayi masa muryarta sai rawa tace tace”Allah ka sassautawa yaron nan wannan jarraba Allah ka mu sanya masa da alkairi.”

Tausayi ta bani a lokacin da take adduar nayi shuru ina sauraranta har ta ‘kare kusurkusur d’inta ta kwanta tare da kara redio a kusa da kunnanta.

Washe gari da safe da yake Asabar ce ina karyawa na kwanta sabida na tara bacci inaso na rama….muryarta naji tana fad’in “Sa’ida kin san yau bikin ‘yar gidan Jummai ‘kanwata wacce muke ‘yan maza zur da ita saboda haka ki tashi ki shirya mu tafi ni na gama shiryawa.”

Cikin bacci nace.”Gwaggo kuje kawai da yamma zan shigo gidan bikin inaso nayi bacci ne.” tace.”To ai shikkenan zamu tafi tare da Rabi da Uwale.” nace”To sai nazo.” kwanciyata na gyara na cigaba da baccinta ban san lokacin data gama kujiba-kujibar ta ta fita daga dakin ba.

Rana gatse-gatse ya dawo gidan domin yayi wanka Khalid sam baya son zafi shiyasa kullum sai yayi wanka sau biyu ko sau uku mussaman da zafi ballantana kuma yanzu da yake jan adaidaita sahu……shuru yaji gidan kai tsaye gurinsu ya nufa sai yaga kofar dakin mahaifiyarsa a kulle da ‘kwado jallabiyar jikinsa ya cire ya dauko dan abinda yake sa sabulun wankansa ya duba gabadaya ya manta sabulunsa ya kare hannunsa rike da abun ya fito ya ajiye shi bakin rijiya kai tsaye dakin Gwaggo ya nufa daga shi sai gajeran wandon da ya bari yana so ya dauki sabulunta yayi wankan dashi dan baya so ya ‘kara fita sai yayi wanka……….Gabansa yayi wani irin fad’uwa ganinta a kwance ita kadai a d’akin babu riga a jikinta tayi daurin kirji da zanin atamfa tayi kuma kwanciyar rigingine ta dogare ‘kafafunta a kasa zanin jikinta ya ‘bantare cinyoyinta duk a waje bacci take sosai da mafici a hannunta da alama idan zafi ya farkar da ita take firfita dashi……lafiyayyar ajiyar zuciya ya sauke idonsa ‘kur a kanta yayin da yake jin wani irin abu da jarumarsa take a cikin wando! A yau ne zai nunawa mata shi Namiji ne a yau ne zai wargaza duk wani shiri da sukayi bayan baya nan, wallahi yayi rantsuwa sai ya nuna mata shi ba kanwar lasa bane.
Fita yayi daga dakin da sauri yaje ya rufe babbar kofar gidan ya dawo dakin ya sa sakata kai tsaye ya durfafeta!!!!!!!
*’KARSHEN FREE PEGE🥰🤝🏻*

*TIR’KASHI!!*
*Wai shin me yake shirin faruwa ne? me Khalid zai aikata da ya kulle kofar gidan? 🤔 Tofa!! ni har na rasa bakin magana? Jama’a Khalid zai samu nasara kuwa ko kuma auntyna nasa zata iya kwatar kanta a hannunsa…..Akwai bada’kala Jama’a Khalid fa zaiyi aika-aika bayan da sadakin wani🙆🏼‍♀️…..Idan ha’kansa ya cimma ruwa wane al’amari ne zai faru a gaba shin auntynsa zata janye maganar auran Alhaji Nura ko kuwa? Wane irin matakin nasara Khalid zai taka anan gaba? Jama’a idan Alhaji Nura ya auri Sa’ida da wata matsalar me zai faru a zamantakewar auran nasu? shin anya kuwa Khalid zai iya samun galaba akanta kuwa?😅 ku muje dai zuwa labari yanzu aka fara akwai badakala a gaba…..#400 ko #600 ta biya miki bukata ‘yar uwa kada kiyi ganin kyashi gurin biyan kudin littafin nan domin yana dauke da darrusa masu amfani bayan nishad’antarwa……..Kuyi maza ku garzayo ku biya domin ayi tafiyar tare daku.🤝🏻*

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*18&19*
A hankali ya tsuguna a gabanta ya tsirawa fuskarta idanunsa. ya jima a haka kafin ya d’ora hannunsa saman kirjinta, ajiyar zuciya ya sauke yana sakin wata irin sheshsheka shi dai yana bala’in son breast d’inta suna masifar tayar masa da hankali….Jin yanda Jarumansa take harbi yasa yayi saurin kwanciya a kusa da ita ya wani janyota jikinsa ya matse ya dinga sakar mata zafafan kesses jikinsa na wani irin karkarwa…….A firgice! na bud’e idona ina salati kafin nayi wani yunkuri naji nauyinsa a kaina ya danne ni sosai yana cusa fuskarsa a tsakankanin wuya na.

“Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un.” kalmar dana furta kenan na shiga motsi da ‘kafafuna domin tureshi daga jikina kamar cingum! ya matse ni! cikin tashin hankali mai tsanani nace”Khalid d’aga ni.”? shuru yayi bai tanka min ba bai kuma daina abinda yake ba.

Bakina na bude zan sake magana yayi gaggawar rufeshi da nasa tashin hankali na shiga na rasa yanda zanyi na k’waci kaina a hannunsa gabadaya ya kashe min jikina da nauyin sa.

hawaye masu zafi da rad’ad’i suka shiga zubowa a fuskata babu shakka tsautsayi da qaddara ne ya dawo dani gidan……..Sosai yake sucking din bakinta yana tatta’ba duk inda yake so a jikina ni kuwa hawaye bai fasa zubo min ba, K’arfi na da nasa ba daya bane dan duk wani kokarin da nake akan na kwaci kaina al’amarin yaci tura kawai na rabu dashi yana abinda yake so……Gabadaya ya cire min zani da breziyya sai sarrafa ni yake tamkar matar auransa.

Lokacin da naji saukar hannunsa a pant d’ina wani karfi yazo min na tunkud’eshi saboda rashin kuzari ya fad’i a gefe kamar zautacce ya mike cikin azama yayo kaina.

Fitilar ‘kwan Gwaggo na wawura ina kuka wurjajan nace”Khalid wallahi ka sake ta’ba ni sai nayi maka lahani dan iska kawai.”

Ido jajawur! yace.”Aunty Sa’ida a yau babu wani mahalu’kin da ya isa ya ‘kwace ki a hannuna wallahi sai nayi miki lahani a rayuwarki tunda kika wofintar da soyayya ta har kina nuna ni da hannu kina min kallon ‘kas’kanci da fad’in idan kin aure ni me zaki samu a gurina to babu shakka yau zan nuna miki maza ma suna suka tara.”

Jikina na rawa na matsa gefe ina kare kirjina da zani nace.”Khalid sai Allah ya tsareni daga dukkanin wani sharrin ka.”

Girgiza kansa yai kana ya saki wani mugun murmushi yace.”Ba dai kin za’bi Alhaji Nura ba to shikkenan zai aureki fanko dan wallahi Allah ni zan fara shiga wannan gurin.”

Gabana ya tsananta fad’uwa na dinga kallonsa ina mamakin al’amarin gabadaya ya juye mara imani fuskarsa a murtuke kwayoyin idanunsa sunyi jajawur!

Gani nayi yana ‘kokarin sa’bule gajeran wandonsa da saurin gaske na mike ya sanya hannu ya janyo ni na fad’a jikinsa ban bari yayi wani yunkuri ba na tureshi tare da gaura masa mari a sukwane nayi hanyar fita yasa kafarsa guda ya tad’o ni na fad’i a gurin.

Rumfa yayi min zigidir! dashi haihuwar Uwarsa Jarumarsa mai kauri da tsayi ta mike sam’bal!! na rintse idona da karfi hawaye bakin ciki da takaici na shatata a fuskata.

“Na fad’a miki fa mai ‘kwatar ki a hannuna sai Allah saboda haka ki ma daina wahalar da kanki gurin guduwa .”

Idona na bude ina kauda kai dan bana san kallonsa a haka nace.” Khalid dan Allah kayi hakuri ka mayar da wandon ka.”

Girgiza kansa yayi yasa hannu ya juyo da fuskata muka kalli juna yace.” Anti ba zan mayar da wandona ba sai na gama abinda zanyi inaso ki bani had’in kai sosai kada naji miki ciwo domin zan nuna miki irin ‘kwazo na.”

Hannuna na had’e guri guda mak’ogwaro a bushe nace.”Khalid kada kayi min haka ni ‘yar uwarka ce bai kamata ka tozarta ni ba dan Allah kayi hakuri da kaddara.”

Cikin takaici yace.”Maganar hakuri ta ‘kare aunty Sa’ida baki da imani kuma baki san me sonki ba ni meye laifina da ba zaki aure ni ba ko kuma dan bani da kudi ne? Wallahi idan kin aure ni zan jiyar dake dad’in da baki ta’ba jin irinsa ba aunty Sa’ida ki daina daukata karamin yaro nima NAMIJI ne.”

A sanyaye nace.”Na sani Khalid amma inaso kasan da cewa shi aure rabo ne ka qaddara ni d’in ba matarka bace.”

A zafafe! yace.” Ba zanyi wannan hakurin na son zuciya ba tun yaushe nake rarrashinki akan ki soni ki aure ni kina zagi na kina wulakanta ni saboda kin raina ni ko? to yau zan nuna miki ni ba kanwar lasa bane sai na k’ure zurfin ki sai kuma na kwashe duk Ni’imarki fanko zakije gidan wancan shashashan mutumin.”

Yana k’are maganar ya janyo k’afafuna nayi saurin janyewa ina takure jikina gabad:aya na sare da al’amarin ina zaune haihuwar uwata shima haka ya Allah ka kawo min agaji.

Hannunsa ya d’ora akan breast dina yana wasa dashi ya wani kura min jajayen idanunsa da suke cike da fitina.

Yanda yake murza nipples d’in ne yasa jikina ya sake mutuwa na dinga ture hannunsa ina matsawa baya sai kawai yasa hannu ya tunkud’a ni na fad’i saman shimfid’a ya haye kaina tare da hard’a k’afafuna da nasa.

Bakinsa yasa kan breast d’in ya fara tsotsa yana murza nipples d’in d’ayan na dinga sauke ajiyar zuciya jikina na wani irin karwarwa…….Nishi mai wahala ya shiga saukewa yana gogo jarumarsa a pant d’ina.

Na shiga tashin hankali mai tsanani na kuma tsananta kiran Allah ya kawo min dauki ! cikin ikon Allah na sake samun nasarar bangaje shi ya fad’i wanwar a gurin Jarumarsa na duba naga ta mike sosai tana kallon rufin dakin

Cikin gigita na rarumi zanina na kama hanyar fita….da ‘kyar na zare sakatar na fice a guje! sakatar babbar kofa tana da tauri dama shi ko Kawu sune suka iya bud’ewa cikin kyarmar jiki na dinga kokarin bud’ewa ta’ki buduwa…motsin da naji a bayana ne yasa da mugun sauri na juya shine ya karaso gurin har yanzu babu kaya a jikinsa.

Jikin kofar na ma’kale tare da kwarma ihu! da fad’in “Jama’a kuzo ku taimake ni zaiyi min fyad’e! da yake tsakiyar rana ce babu wanda yaji…….Jikina na ‘bari na rarumi manjagaran gyaran kwata na ri’keshi da kyau a Hannuna ” Wallahi Khalid ka sake ta’bani sai na kasheka.

Murmushi yayi wanda ya tsaya iya fatar bakinsa ya cigaba da zuwa inda nake…..Yana karasowa na daga manjagaran da dukkanin ‘karfina zan kwad’a masa da azama ya ri’ke hannuna manjagaran ya sauka kan kafarsa.

Bai damu ba ya sa’bani a kafad’a tare da tallafe mazaunai na ya nufi cikin gidan dani na dinga kuka ina dukan bayansa ko gezau bai dire ni a ko’ina ba sai saman gadon Gwaggo ya jefar dani yaje ya rufe kofar…..yana juyowa yaji saukar abu a goshinsa ‘kwan fitilar gwaggo na cire na kwad’a masa….goshinsa ya fashe jini ya soma d’iga

Ya tsaya yana kallona da fad’in “Kika futar min da jini.” a zabure! nace.”Kashe ka ma zanyi yanzu Khalid kai annoba ne kuma baragurbi a cikin al’umma.”.

Yana murmushin mugunta yace.”Duk sunan da zaki kira ni dashi na d’auka ni dai ina sonki har karshen rayuwata.”‘

Nace.”Khalid wannan ba so bane da kana sona zaka so duk abinda nake so ya kake so ka haike min bayan kasan da akwai sadakin wani akaina kada fa ka manta abinda kake shirin aikatawa haramun ne.”

Kafad’arsa ya d’aga yace.”Laifi tudu ne ka take naka ka hango na wani duk abinda ya faru a tsakanina dake taurin kanki ne ya janyo miki.”
Yana gama maganarsa ya hayo gadon nayi saurin takurewa a loko jikina na karkarwa. hannuwana nasa na rufe kirjina ina kallonsa sai yasa dariya da fad’in “Okey shine bakya so na ta’ba.”?

Shuru nai ina kallonsa yayi murmushi yana shafa sajensa yace.” Ba zan iya kauda kaina daga kansu ba zan gwada miki k’arfina yanzu.” Ya janyo ni da karfin gaske yasa dukkanin karfinsa akaina kyakykyawar fizga yayi pant din ya yage yasa hannunsa a gurin yana shafawa tsigar jikina ta wani mi’ke…kafin nayi wani yunkuri ya cire hannuna dake kan breast ya fara tsotsarsa yana dan cizan nipples din…gabadaya naji alkadari na ya karye domin yanayin yanda yake wasa da hannunsa a gabana yayi masifar dauke min hankali na dinga jin wata gawurtacciyar sha’awar da ban ta’ba jin irinta ba.
Jin shaid’an na kokarin samun galaba a kaina yasa na dage da addua ina cigaba da kokarin ceton kaina.
Idona a rintse nake jin yanda yake sarrafa ni yana juya ni duk inda ransa yake so nayi masifar galabaita da abinda yake min bayan kokaye-kokayen da mukayi dashi amma dai yanayin rashin ‘kwarin jikin nawa bai hana ni taimakon kaina ba dan da naji abin nasa yayi yawa matse cinyoyina nayi da karfin gaske na hanashi shiga tsakanina……a mutukar d’imauce yake kiran sunana yana lasar fuskata da tsotsar karan hanci na….na bude idanuna da sukayi min mugun nauyi na kalleshi fuskarsa daf da tawa numfashinsa sai sauka yake a fuskata……..”Auntyna dan Allah k…ki taimake ni.” a hard’e yayi maganar yana tsotsar lips d’insa. sai kaje wani maye sai shan yaji yake jikinsa na wani irin karkarwa.

Cikin nishi da rashin ‘kwarin jiki na d’aga hannu da niyyar dukan kirjinsa da yayi min rumfa. ya ri’ke yana girgiza min kai….a raunane yace.”Ki bud’e min kafafu na shiga kinji ko.”

Lafiyayyun hawaye suka sake kwaranyowa a fuskata jiki na rawa yasa harshe yana lashewa! hakan ya bani daman dukan Kirjinsa da mugun karfi!! ya rike kirjin yana tari!! tunkudeshi nayi zan sauka ya had’a kaina da karfen gadon ya bugu! ‘karamar ‘kara nasa ina ri’ke kaina. shuru nayi nai saurin bude idona ido ya tsira min yana tunanin ta inda zai fara…..cikin rawar baki nace. “Khalid inaso kasan da cewa bayan bukatarka ta biya akai to na sai na kasheka sannan na kashe kaina domin bamu da wani amfani a duniya.

Hawaye suka sauka a fuskarsa yace.”Na amince ki kashe ni kinga zunubi na ya rataya a wuyanki dama ni wace rayuwa mai dadi zanyi bayan babu ke.”

rintse idona nayi ina cigaba dajin wani irin nauyin ‘bakin ciki a kirjina. yasa hannunsa ya rike hannuwana tamau! da k’afafunsa ya bud’e cinyoyina ya shiga tsakiyata jin haka yasa na kwarma ihu! “Innalillahi wa’ina ilahi raji’una.”!!! Hannu yasa ya dam’ke min bakina cikin hawaye muka shiga kallon juna kai ya shiga girgiza min idanunsa duk sun shagid’e.

A hankali ya fara wasa da jarumarsa a inda yake muradi na dinga bugunsa da kafafuna amma saboda yafi ni dubara sai da yasan yanda yayi ya shiga jikina sosai kukan nadama ya kucfe min. cikin kukan na soma yi masa magiya da had’ashi da Allah ya rufe idonsa ruf! ya’ki saurarata a lokacin shima hawayen yake fitarwa ya dinga girgiza min kansa yana ciccije le’bunansa a haka ya dinga cuku-cuku har ya samu nasarar hud’a jikina ya shiga sosai! ya manne ni a jikinsa ya ri’ke ‘kam! na tsayin Mintina biyar kafin ya mike da wani irin kuzari a tare dashi ya fara bubbuga jikinsa a nawa.

Tsananin azabar da yaron yake gana min tasa bakina ya mutu jikina ya mace gabad’aya kuzari na ya ‘kare na kasa motsa koda ‘karamin d’an yatsa na wani irin bugu yake min yana ihu! tare da sakin sambatu wanda shi kad’ai yasan abinda yake fad’a gabadaya ya zama tamkar zautacce sai kiran sunana yake yana caccakata kamar zai kai ni lahira

A qallah sai da ya kai kimanin mintina talatin akai na kafin ya zubar da abinda yake mararsa ya ‘kan’kanme ni ‘kam! a jikinsa yana numfarfashi ni dashi gabad’aya gumi ya ji’ka mana jiki

Turesa nayi na fara kokarin mi’kewa ina jin wani irin jiri a saman kaina….hannuna ya rike ya rike yana girgiza min kai mirya na rawa yace.”Kinga rayuwar da kika janyo mana ko.”? nayi wani irin juyi a kid’ime! nayi niyyar kwashe shi da mari ya rike hannuna da fad’in “Kina so kice zaki mare ni wanda ke kanki kin san ba barin ki zanyi ba aunty Sa’ida mutukar kinga na tsaya kin mari fuskata ni nayi ra’ayi a yanzu dai nasan zaki tabbatar da cewa ni ba rago bane kuma na isa namiji tunda na cika miki marar ki na kuma ‘kure zurfin ki a yau kin san waye Khalid kije ki auri Alhaji Nura ni kuma na cigaba da biyayyar rayuwarki mutukar ina raye ba zan barki ki zauna lafiya ba.”

Sauka yayi daga gadon yaje ya dauki gajeran wandonsa yasa yace.”Zan tafi kafin ‘kura ta lafa ki rubuta ki ajiye duk inda nake kina maqale a cikin zuciyata kina da number wayata idan kin janye maganar auran Alhaji Nura sai ki kira ni zan dawo na aureki tunda nasan ni na cancanta dake.” Yana ‘kare maganarsa ya fita daga dakin. ya barni cikin tararrabi da tsantsar tashin hankali da nadamar rayuwa.

*Kuyi hakuri dan girman Allah da Annabi ku kar’bi labarin littafin nan a yanda yake…..idan nace dole zan dauki ra’ayoyinku zan sha wuya daga ‘karshe ma na rasa abinda zan rubuta muku kuyi hakuri ku cigaba da bina a cikin littafin har na samu na isar da sa’ko na👏🏼🥰
*20&21*
Cikin tsinkewar zuciya gami da tarin nadamar abinda ya aikata yayi wanka ya fito a gurguje ya shirya jikinsa. kayan sa ya shiga had’awa cikin ‘yar ‘karamar akwati yana had’a kayan yana jin wani katon abu a tokare a kirjinsa. tun sanda yake raping d’inta yake jin nannauyan abun a cikin kirjinsa amma saboda yasa al’amarin a cikin ransa ya kasa saurara mata duk da irin hakurin da take bashi, hakika bai so wannan mummunan al’amarin ya kasance a tsakaninsu ba yaso suyi mu’amula ta aure mai tsafta sai gashi qaddara ta mai muni ta gifta a tsakaninsu yatsa yasa ya d’auke hawayen daya sauko masa a saman fuskarsa ya cigaba da had’a kayan a gurguje ya fito daga dakin ya kulle da kye babban tsakar gidan ya fito ya d’an tsaya yana kallon kofar dakin. ya kai minti biyar a tsaye a tsakar gidan idonsa akan kofar dakin kafin ya sauke wani gwaron numfashi ya kama hanyar fita zuciyarsa nayi sa’ke-sa’ken inda zai nufa.

Na jima kaina a ‘kasa ina zubar da hawayen bak’in ciki! da takaici! kafin na motsa jikina da niyyar saukar daga gadon naji wani irin mugun zafi a karkashi na sunan Allah na kira tare da sake sunkuyar da kaina ‘kasa hawayen ne dai suke ta zuba kamar an bud’e famfo….zanin atamfar jikina da zanin gadon Gwaggo sunyi kaca-kaca da jin budurci na, Khalid yayi min fyad’e! wace irin rayuwa zan fuskanta anan gaba? dame zan kare kaina a gidan aurena.”? Wannan tunanin shi ya dame ni ya sanya min tsananin ciwon kai da zazza’bi! mai zafin gaske jiki na kyarma na koma na kwanta tare da d’an lullu’be jikina da gefan zanin gadon daya cukurkud’e ya ‘baci da jini……Rufe idanunawa nayi na cigaba nanata kalmar “LA’ILA HA ILLAH ANTA SUBAHANAKA INNI KUNTU MINA ZZALIMIN.” a cikin zuciyata.

“Assalamu alaikum.” Gwaggo ce take sallama a cikin gidan. tana rarraba idonta a tsakar gidan…..Kwata-kwata ta manta bata tafi da gudumawar da zata bawa uwar amarya ba sai da suka je gidan bikin sannan ta tuna shine ta yanke shawarar dawowa gidan ta d’auka.

Labulan d’akin ta d’aga da fad’in “Sa’ida wai har yanzu baccin kike baki tashi ba gashi azahar ta kawo k……Kasa ‘karasawa tayi ganin d’akin nata a hargitse ko ina yayi kaca-kaca! ga fitilar ta a fashe da sauri ta kalli gadon da fad’in ” Ke! Sa’ida waye ya shigo min d’aki yayi min ‘barna haka.”?

Idanuwana na zuba akanta uffan na kasa cewa da ita, cikin fad’uwar gaba ta k:araso gurin tana duddubawa. murya na rawa tace.” Wai Me ya faru ne Sa’ida wannan jinin meye akan gadona.”?

Wasu lafiyayyun hawaye masu zafi da rad’ad’i suka shiga gudana akan fuskata .

Idanunta suka ciko da ruwan hawaye ta zauna gefe na jikinta sai rawa yake Gwaggo dai ba yarinya bace ta fahimci abinda yake faruwa ko ga yanayin yanda taga Sa’idar babu suttura a jikinta.

Cikin tararrabi da tsananin tashin hankali tace.”Khalid ne ko.”? Kaina na d’aga mata murya na rawa nace.”Gwaggo wannan jinin na budurci na ne Khalid ya raba ni dashi bayan fitarku ya dawo gidan ya haike min.”!

Gwaggo da k’arfin gaske tace.”Innalillahi wa’ina ilahi raji’una.”! Sai kawai hawaye ya shiga kwarara a fuskarta jikinta ya dinga kyarma tana dudduba jikina da fad’in “Sa’ida garin ya akayi haka ta faru? ya akayi kika bar shi? ya afka miki! yanzu ashe rashin albarkar da yaron nan zai aikata kenan dama yace zai dauki mataki ashe abinda zaiyi kenan? Sa’ida Khalid ni ya tozarta bake ba ya gur’bata min zuriata *Zina* a gidana kuma akan gado na *Lahaula wala k’u wata illah billahil aliyulazim* cikin tashin hankali take magana.

Na ri’ke hannuwanta ganin tana neman kifawa ‘kasa nace.”Gwaggo ki samu nutsuwa kada wani abu ya sameki Khalid ya aikata hakane domin na janye kudiri na na auran Alhaji Nura saboda wannan dalilin nasa yasa ya cutar dani to bukatarsa ta biya akaina auran Alhaji Nura kuma ba zan janye ba komai abin sa abinda kuma yayi min ya nuna cewa dama ba sona yake tsakani da Allah ba sha’awa ta yake koda na aureshi daga ya biya bukatarsa a kaina shikkenan zai iya rabuwa dani.”

Gwaggo ta shiga girgiza kanta tana share hawaye tace.”Sa’ida nima na gazgata na kuma yarda da cewa Khalid ba son Allah da annabi yake miki ba domin idan son gaskiya yake miki to ba zai ta’ba cutar dake ba wallahi tallahi ban dauka irin wannan matakin zai dauka ba jiya na zaunar dashi nayi masa nasiha kamar ya d’auki maganata ashe ni ya mayar mahaukaciya ya shirya tozarta ni a idon duniya to ai shikkenan tunda bukatarsa ta biya zai shigo gidan ya same ni wallahi sai yaga ‘bacin raina kuma dan dai bana so maganar ta fita waje ne amma da sai nace ki fad’awa mijin mahaifiyarki a bi miki Hakkin ki.”

Murmushin takaici nayi ina kokarin mikewa nace.”Gwaggo duk wani hukunci da za’a dauka akan Khalid ba zai ta’ba goge wannan mummunan tabon da yayi min ba Gwaggo yanzu idan naje gidan mijina mai zance masa idan ya kusance ni yaji ni a bud’e.”

Kuka tasa tace.”Sa’ida ki daina maganar auran wani mutum kuma ai dole A mayarwa da Alhaji Nura kud’insa kiyi hakuri ki auri Khalid asirin mu ya rufu idan kin auri Alhaji Nura ya same ki babu budurci ai mummunan zargi ne zai shiga tsakaninku dama kuma jama’ar gari na munana zaton su akan ki.”

Murmushin takaici nayi nace.”Gwaggo ke yanzu a tunanin ki idan har na auri Khalid auran zaiyi albarka.”?

Shuru tayi tana kallona….nace.”Khalid fa ba sona yake tsakani da Allah ba sha’awata yake yanzu ya samu biyan bukatarsa to me kuma yake nema? babu wani sauran buri a tare dashi dan ko na aure shi ‘bacin rai za mu shiga saboda haka ki daina wannan maganar Khalid ya zalince ni kuma insha Allah sai ubangiji ya saka min.”

Hannu tasa ta goge fuskarta a sanyaye tace.” yanzu yana ina Khalid din.”? Shuru nai mata na fara kokarin sauka daga gadon…ta rirri’ke kafad’una tana taimaka min na mi’ke tsaye daurin zanina ta gyara min kamar ‘yar kaciya haka muka fita tsakar gida…..Ta zaunar dani a kujera ‘yar tsuguno kamar wata maijego mai haihuwar fari da sauri ta koma dakin ta dauko fulas cike da ruwan zafi tana share hawaye ta surka ruwan a buta ta kai min bandaki da fad’in “Shiga kiyi tsarki kafin na d’ora miki wani ruwan ki gasa jikin ki Allah zai saka miki abinda akayi miki.

Daurewa nayi na mike tazo wai zata taimaka min nace.” Ki barshi gwaggo.” gefe ta matsa ni kuma na dafa bango na shiga bandakin ina rintse idona……koda na tsuguna domin wanke najasar dake jikina kuka ne ya ‘kwace min yi nake ina tsarkake jikina tare da yin tasbihi a cikin zuciyata.

Daga bakin kofar bandakin ta tsaya tana miko min zanin atamfa da fad’in “Kar’bi ki daura wannan sai na shigo miki da ruwan zafi ki shiga ki gasa jikinki a ciki.”

Tausayi ta bani ganin yanda duk ta damu da ni banta’ba tsammanin zata yarda da lamarin ba.

Tana can uwar dakin na fito daga bandakin ganin maidaidaicin baho da ruwa a ciki yasa kawai na tattare zani na na shiga ciki….sai bayan dana shiga cikin ruwan kuma na shiga tunanin wanda zai shigo…

Gwaggo tana share hawaye ta cire farin zanin gadonta daya ‘baci ta dinga kiran sunan Allah a cikin zuciyarta tana addua akan Allah ya kauda idanun ‘yan gaza gani a cikin al’amarin…….zanin gadon ta fito dashi ta ajiye bakin kofar shiga gurin Ummatu.

Na bita da kallo ina mamakin abinda take nufi da yin hakan…..Tace.”Sa’ida dole na ajiye sheda iyayen yaron nan su dawo su ga abinda d’ansu ya aikata ba zan shaqi takaici ni kad’ai ba.”

Girgixa kaina nayi nace.”Gwaggo ki dauke zanin gadon nan dan Allah bana so kowa yasan maganar nan.” Da sauri tace.”Sa’ida ko kowa bai sani ba to ya zama lallai Rabi da Ibrahim su sani daga haka sai a rufe magana a gida Khalid kuwa ya nemi gurin kwanciya dan ba zai ‘kara shigowa gidan nan ba.”

Shuru nayi tare da yin ‘kasa da kaina ta juya ta shige dakin tana surutai had’e dayin tur da abinda Khalid din ya aikata…..naji dadin ruwan zafin sosai hakan yasa na karfafa jikina na zubar da ruwan bahon kana na janyo ruwa a rijiya na daura alwala na nufin dakin..

Tsaf ta gyara d’akin ta ta kunna turaran tsinke sai kamshi yake…..dadduma na shimfid’a nasa hijabi cikin karfin hali da yanayi na jin jiri da hajijiya na tayar da sallah…..Itama alwalar ta fita ta d’auro ta dawo dakin.

Koda na idar da sallar kwanciya nayi kan daddumar na rufe idona….har yanzu gabana radad’in zafi yake min inaji kamar an tsaga da reza!! jin hawaye na nema ya kufce min yasa da sauri na shiga nanata kalmar innalillahi wa’ina ilahi raji’una.

A take kuwa na samu sassauci a cikin zuciyata na dinga jin imani da tsoron Allah na ratsa ni zuciyata ta shiga fad’a min cewa wannan al’amari daya faru dake ki daukeshi a matsayin qaddarar da kike tafiya da ita haki’ka duk wani abu da zai same ki a duniya mai dad’i ko mara dad’i a rubuce yake a lauhil mahafuz Allah shine yake zartar da iko akan kowane bawan sa Ki roki Allah ya tsayar miki nan kuma kisa a zuciyarki cewa baki sa’bi Allah da gangan ba sai dai karfi da aka gwada miki….Tsakanin ki da Alhaji Nura kuma fatan alkairi ne.”

Jin irin shawarwarin da zuciya take bani yasa naji wani irin kwari a jikina na mike zaune a ina kallonta da carbi a hannunta tayi zugum! tana kallon guri guda nace”Ba zaki koma gidan bikin bane.”?

Girgixa min kai tayi tace.”Ya za’ayi na kuma fita na barki ya dawo ya ‘karasa ki yaro mara imani yasa miki k’arfi ya fatataka miki budurci na tsorata da jinin da nagani Sa’ida.”

Kaina na sunkuyar k’asa ina tunanin artabun da muka sha ni dashi…. ko da wane ido zai kalli mutane? ko da yake ai mara kunya ne zai iya fittikewa akan ‘karya domin ya kare kansa.

Haka muka kasance a zaune cikin jajantawa juna dan har sai da naso na fita dauriya domin sa’i da lokaci ina hankalce da ita tana sa hannu ta goge hawaye a fuskarta.

Sai yamma Ummatu ta shigo gidan…..bakin kofar dakin ta tsaya da fad’in “Gwaggo lafiya baki koma gidan bikin ba? jama’a sai cigiyarki suke.”

Girgixa kanta tayi tace.”Rabi tashin hankalin dana tarar a gidan nan ne ya hana ni komawa gidan bikin ina fata kinje kinga dakin amarya.”?

Ummatu tace.”Aikuwa ni na wakilce ki dan dani aka kai Suwaiba dakinta ba kiga gidanta ba yayi kyau kuma sosai Jummai tayi kokari dan tayi mata kayan daki masu kyau.”

“Ba shakka.” abinda tace kenan tayi shuru da bakinta…Ummatu tasha jinin jikinta ganin yanayin rashin walwalar dake tare damu sai kawai ta bar gurin tana ta’be bakinta.

Tazo shiga gurinta taga zanin gado a kud’indine kuma kamar an goge jini dashi….cike da mamaki ta dauka tana dubawa wannan zanin gadon ai na Gwaggo ne. sai kawai ta nufi dakin Gwaggon da zanin gadon a hannunta

“Gwaggo wannan ba zanin gwadon da kika siya kwanaki bane.”? tafada tana nuna mata.

” Shine Rabi ki warwareshi sosai ki duba kiga meye a jiki.”

Ummatu tace.”Haba Gwaggo ai ba sai na warware ba gashinan ina ganin jini kaca kaca a jikinsa.”

Murya na rawa tace.”Jinin budurcin Sa’ida ne Khalid ya dawo gidan bayan fitar mu ya haike mata a cewarsa tunda shi bai samu nasarar auranta ba to sai da taje gidan mijinta a fanko.”
Ummatu ta shiga watsa mana wani irin mugun kallo kafin tace…………!
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*22&23*
“Gwaggo wannan wace irin magana ce kikeyi? Ina khalid yake a gidan da har zai aikata wannan mummunan akin! Gwaggo shuru-shuru fa ba tsoro bane gudun magana ne ya za’ayi yarinya tayi fasiqancin ta sannan a laqabawa wanda baya nan Khalid tun karfe bakwai na safe ya fita daga gidan nan ballanatana ayi masa mummunan sharri irin wannan.”

Gwaggo ta nuna kirjinta da fad’in “Rabi ni kike wa rashin kunya har kina fad’in shuru shuru ba tsoro bane to me kike nufi? kin san dai ba zan qi Khalid naso Sa’ida ba tunda duk daya suke a gurina abinda kuma yasa na yarda da al’amarin shine jiya da daddare na jima tare dashi ina tausar zuciyarsa akan auran Sa’ida da Alhaji Nura na dinga kawo masa misalai ina fahimtar dashi cewa shi aure rabo ne Allah ya kaddara cewar Sa’ida ba matar auransa bace dan haka sai ya hakura ya nemi wata…..Idan kikaji irin munanan kalaman da ya dinga yi sai kin riqe baki wannan dalilin yasa na yarda da abinda ya aikata.”

A fusace! tace.”Gwaggo idan duk jikina kunne ne ba zan yarda da wannan k’anzon kuregen ba, a ina Sa’ida taga wani budurci da har jininsa zai ‘bata zanin gado kawai dama dai ta dawo gidan ne da niyyar ta d’ora masa sharri saboda ta tsaneshi.”!

Cikin takaici da ‘bacin rai nace.”Ummatu idan nayi wa Khalid k’azafin zina meye ribata a duniya.”

“Ke! saurara kada ki kuskura ki sake kiran yaro na da wannan sunan Khalid ba mazinaci bane.”! a fusace tayi maganar tana kumfar baki.

Gwaggo ta zabaro! itama a fusace! tace.” To menene shi idan ba mazinacin ba Rabi nace ki fad’a min menene shi Khalid ya cancanta a kirasa da wannan suna tunda har ya iya haikewa ‘yar uwarsa.”

Ummatu ta fashe da kuka da fad’in “Jama’a wannan wace irin masifa ce Gwaggo ashe akwai ranar da zaki goyi da bayan ‘karya akan gaskiya kin fi kowa sanin halin Khalid ba zai aikata wannan mummunan aikin ba.”

Gwaggo ta girgiza kanta cikin takaici da bakin ciki tace.” ‘Dan yau ne fa Rabi ba’a shedar mutum sanin abinda yake zuciya sai Allah amma ko shakka ba nayi Khalid shine yayi wa ‘yar uwarsa fyad’e a tunaninsa idan hakan ta faru sai a janye maganar auran Alhaji Nura ayi dashi.”

Ummatu zaman dirshan! tayi a gurin tana kuka tare da fad’in “Ni kam ba zan yarda da wannan k’azafin ba duk inda za muje a haka nake kuma ina da ‘yan uwan da zasu tsaya min a gaban al’kali amma inaji ina gani ba zan yarda ayiwa yaro na qazafi ba.”

Gwaggo tace.”Ummatu ashe wu’ka zaki d’abawa kanki wane mahaukacin ne ya fad’a miki ana fita da irin wannan sirrin.”?

Shuru tayi tana lalube a wayarta Gwaggo tace.”To Wallahi tallahi kada ki kuskura naji maganar nan a wani guri Rabi idan kika sake kika fad’awa dangin ki abinda yake faruwa to zakiyi nadama mai tsananin gaske.”

Hawaye ta share hannu na rawa tasa wayar a kunnenta tana fara ringing ta katse ta sake kiran wayar ta sake katsewa a sanyaye tace.”Duk inda yake nasan yana kan hanyar dawowa gida gwara yazo ayi komai a gabansa .”

Gwaggo tace.”Ko yazo ko bai zo ba shine munafiki kuma dole ya fuskanci hukunci domin shi da shigowa gidan nan har abadah.”

Saurin kallonta tayi rai a tsananin ‘bace tace.”To idan bai shigo ba ina kike so yaje ya kwana.”? kai tsaye tace.”Ya tafi can dangin ki dama su suke d’aure masa gindi.”

Ummatu ranta ya ‘baci! kawai sai ta shiga farfad’ar bak’aken maganganu wanda Gwaggon ta kasa hakuri itama ta shiga mayar mata da martani suka dinga cacar baki Ummatu ta dage sai rashin kunya takewa Gwaggo……..”To dama me nake samu a gidan idan ba wahala ba lafiya lau aka dauko ni daga gidan ubana da kuzari na da qiba ta amma tsabar wahala da yunwa tasa duk na lalace sai me idan kin sa shi ya sake ni.”
Ummatu ce ke wannan maganar tana sakin wani irin nishi na bacin rai! Gwaggo tace.”Rabi ba zan sa Ibrahim ya sake ki ba amma zan sashi yayi miki kishiya tunda ke baki da mutunci wato dama zuwa kike gidanku kina kwance mana zani ko duk tsiyarki Ibrahim yayi miki abinda uwarki da ubanki ba suyi miki ba.”

Ummatu ta fashe da kuka da fad’in “Ni dai Allah ka jarrabe ni da jarabar Suruka tinda na auri d’anta banji dadi ba.”

Nace.”Gwaggo Ummatu kuyi hakuri dan darajar Allah kada makota su fara shigowa gidan asiri ya tono ni akai wa laifi kuma na barwa Allah.”

Gwaggo tace.”Dama shi ne alkali shi kuma wanda ya aikata zai girbi abinda ya shuka a nan gaba.”

Ummatu da sauri tace.”Insha Allahu zina ba dai a zuria ta b…….Shuru tayi ganin Kawu ya shigo gidan.

Ganin fuskarta jage-jage da hawaye yace.”Me yake faruwa ne.”? Ummatu ta tsuguna gurin tare dasa kuka.

Sai ya daga labulan dakin Gwaggo yana tambayarta…Tace.”Shigo ciki ka samu nutsuwa na sheda maka abinda ya faru a gidan.”

Jikinsa a sanyaye ya cire takalminsa ya shiga dakin ya zauna har lokacin Ummatu kuka take tana girgiza kanta ya ma za’ayi ta yarda da wannan qazafin.

Hankalinsa akan Sa’ida yace.”Me ya samu fuskarki ta kumbura haka ga idanunki sunyi jawur kamar wacce taci kuka ta koshi.”

Zuciya tace ta karye naji hawaye na nema ya kufce min cikin rawar murya nace”Babu komai Kawu.”

Sai ya kalli Gwaggo yana neman ‘karin bayani. tace.”Rabi mi’ko min zanin gadon nan idan kin gama d’ibar albarkar.”

Ummatu a sanyaye ta dauki zanin gadon ta shiga dashi dakin ta miqa mata ta juya zata fita tace.”Aa ai babu inda zakije zauna nan tunda ga Ibrahim din ya dawo ayi magana a gabansa.”

Ummatu gabanta ya buga tana jin tsoro kada ya sake aunata gidansu. jiki a sanyaye ta nemi bakin kofa ta zauna.

Gwaggo ta shiga warware zanin gadon… da sauri nasa hannu na ‘karbe ina girgiza mata kai hawaye na zuba a saman fuskata.

Murya na rawa tace.”Sa’ida ki bari a nuna masa sheda.” nace.”Gwaggo dan Allah dan Annabi maganar nan ta isa haka a barta ni na barwa Allah.” da kyar na’karasa maganar saboda kuka mai karfin daya kufce min na miqe da saurin gaske na fita daga dakin guri na samu na tsuguna na dinga kuka ina kiran kalmar innalillahi wa’ina ilaihi raji’una.”

Baba Ibrahim jiki a mace yace.”Gwaggo dukkanin abinda yake faruwa a gidan nan nake so ki fad’a min dan girman Allah kada ki ‘boye min komai.”

Ta girgiza kai tare da fad’in “Ibrahim ai ranar wanka ba’a ‘boyan cibi wannan lamari ya zama dole ka sanshi domin kana da hakkim sanin abinda d’anka Khalid ya aikata akan marainiyar Allah.”

Hawaye ta share tace.”Ibrahim Khalid tinda ya samu labarin auran Sa’ida da Alhaji Nura ya tayar da hankalinsa ya dinga jifan al’amarin da mugwayen kalmomi tare da yin ikirari mai muni kancewar mutukar ba’a janye maganar auran Alhaji Nura ba to ba zai yarda ba sai ya dauki mataki! jin haka yasa na zaunar dashi na dinga rarrashinsa akan yayi hakuri ya barwa Allah komai na rayuwa rabo ne ashe yaron nan bai dauki nasiha ta ba ya shirya mugun abu…..’Dazu nida Rabi muka tafi gidan bikin ‘yar gidan Jummai muka bar Sa’ida a gidan ita kadai tana bacci to wannan damar khalid ya samu ya haike mata a takaice dai Khalid shi yayiwa Sa’ida fyad’e abinda nake so na fada maka kenan.”

Kawu Iro yayi ‘kasa da kansa wani irin gumi! mai d’umi ya dinga tsatstsafo masa! hular saman kansa ya cire baki a bushe? yace.”Gwaggo Khalid irin tozarcin da xaiyi mana kenan ? me mukayi masa a rayuwa? me kuma Sa’ida tayi masa da zai keta mata rigar mutumci wane irin kallo Alhaji Nura zaiyi mana a matsayin mu na iyayen yarinyar nan Gwaggo da sadakin wani Khalid ya aikata wannan ‘barnar? idan Alhaji Nura ya kusanci yarinyar yaji ba daidai ba wani irin kallo zaiyi mata? me zai biyo baya a zamantakewar auranta.”

Gwaggo ta goge hawaye a sanyaye tace.”Shine dama babban tashin hankali da damuwar ai kawai Ibrahim ka ajiye maganar Alhaji Nura a gefe a mayar masa sa kud’insa Sa’ida babu namijin da zata aura a cikin wannan halin ta samu nutsuwa Khalid din dai shi zamu hakura ta aura asirinmu ya rufu.”

Kawu ya girgiza kansa cikin mugun takaici da nadamar haihuwar yaron yace.”Gwaggo Sa’ida bata dace da macucin yaron nan ba saboda haka ki daina wannan maganar tsayin wattani biyar mun kar’bi sadaki a hannun mutumin nan ya za’ayi ace za mayar masa hakuri kawai za muyi a daura auran mu cigaba da addua kafin muga abinda Allah zaiyi.”

Tace.”To ai shikkenan Ibrahim yanzu wane mataki ka dauka akan Khalid din……Girgiza kansa yayi da fad’in “Kotu zan kai shi Alkali ya yanke masa hukunci daidai da abinda ya aikata wallahi ba zan bari mutucin marainiyar Allah ya tafi a banza ba.

Ummatu ta fashe da kuka da fad’in ” Haba kai kuwa wace irin magana ce wannan? kana nufin d’an cikin ka zaka kai kotu akan abinda baka da tabbas a kansa.”

Ya kalleta yace.”Rabi ke zaki qalubalanci maganar mahaifiyata a gabana me kike nufi? kina so ki fada min cewa Gwaggo sharri tayi wa d’anki kome.”

Girgiza kanta tayi tace.”Aa ni ba haka nake nufi ba naji kana maganar kai shi kotu nace kafin ka yanke wannan hukunci ka tsaurara binkice akan al’amarin.”

Cikin fusata! yace.”Ba zan tsautsara binkicen ba! ni d’an halak ne kuma nasan *ZAMANI* Khalid babu abinda ba zai aikata ba tunda yasa son zuciya a ransa. mahaifiyata ba zata ‘kir’kiri sharri ta d’ora masa ba.”

Tace.”Ai ba haka nake nufi ba ita Sa’idar me yasa bakwa ganin laifinta Khalid fa yaro ne akanta to har yaushe ma zai iya sarrafata ballanatana yayi mata fyad’e.”

Takaici ya cika zuciyar Kawu Iro yace.”Rabi idan baki daina magana anan gurin ba ranki zai mummunan ‘baci! wane irin rashin tarbiya ne wannan a gabana kike kokarin ‘karya ta mahaifiyata.”

Gwaggo tayi murmushi wanda bai kai ciki ba tace.”Ibrahim rabu da ita haka ita ‘karya ai fure take bata ‘ya’ya ita wai tana so ta kare d’anta akan abinda ya aikata idan kin kareshi a duniya a lahira fa.”?

Ummatu tayi shuru tana shaqar hanci….Kawu Iro ya dauki wayarsa yana lalube number Khalid din ya nemo ya shiga kira…..Is swich Up. wayar a kashe take.

Ya dinga kira ana fada masa a kashe take…Gwaggo tace.”Ai dole ya kashe waya tunda yasa abun da ya aikata ai da tuni ya shigo gidan.”

Kawu Iro ya mike da sauri ya fita daga dakin…..tsayuwarsa naji a kaina na dago da sauri ina kallonsa….’bacin rai da damuwar da nagani a fuskarsa yasa wasu hawayen sake yankowa hakika Khalid ya jefa zuciyoyin mu cikin masifar tashin hankali

A sanyaye yace.”Ki daina kuka kinji ko ki barwa Allah zai saka miki sannan inaso ki dauki wannan al’amari a matsayin qaddara wacce ta riga fata insha Allahu Allah zai dubi maraicinki Khalid kuma da ya aikata miki wannan abu ni da kaina zan kaishi a hukuntashi .

“Ajiyar zuciya na sauke ina goge hawayen fuskata nace.” Kawu insha Allahu zan sanyawa raina dangana akan wannan al’amari sannan maganar kai khalid hukuma ka janye nasan tunda zalinci ya aikata sai Allah ya hukuntashi a duniya ko a lahira.”

Girgiza kansa yayi yace.”Sa’ida idan nayi haka naci amanar zumuncin Allah kuma duniya zata zage ni dole ne na dauki mataki akan dukkanin wanda ya ta’ba martabarki.”
Kafin nace wani abu yayi gaggawar fita daga gidan…jiki a mace na bishi da kallo ina girgiza kaina.

Ummatu yun’kurawa tayi zata mi’ke Gwaggo ta dakatar da ita da fad’in “Rabi kin gama koke-koken ne.”? Ummatu ta zuba mata ido tana kallonta, Tace.” To wallahi kada naji da wai! maganar nan ta fita waje al’amarin nan ya zama sirri a tsakaninmu idan kika fad’awa dangin ki maganar nan wallahi kinji na rantse sai kin fi kowa ‘bacin rai.”

Ummatu girgiza kanta tayi ba tare da tace mata komai ba ta kad’a kanta ta fita daga dakin ranta a mugun ‘bace.

Inda nake bata kalla ba ballanatana ta tanka min ta bude kofar gurin ta ta shige tare da bugo kofar da karfin gaske!

A hankali na mi’ke na nufi dakin jiri da hajijiya na neman su kayar dani a gurin.

‘Bangaran Khalid kuwa yana fita kai tsaye can Na’ibawa ‘yan lemo ya nufa gidansu abokinsa Salmanu wanda suka gama karatu a tare tun kafin ya isa gidansu abokin nasa ya kirashi a waya ya sanar masa zuwan nasa sai kawai ya kashe wayarsa yasa a jakar kayansa yasan dole daka gida a nemi inda yake shiyasa ya kashe wayar gabad’aya.

Kawu Iro yana fitowa daga gidan kai tsaye Gidansu Salim ya nufa babban abokin yaron nasa yana kokarin aika yaro gidan Salim din ya fito ganinsa yasa da sauri ya risina yana gaisheshi.

Kawu ya amsa tare da Tambayarsa ina abokinsa yake.

Salim yace.”Wallahi baba nima yanzu na dawo gidan na tarar da key na adaidaita sahu wai d’azu Ya aiko yaro dashi a ajiye min da nazo mahaifiyata take min bayani shine fa yanzu na fito da sauri zan siyi kati nasa a waya na kirashi naji dalilin da yasa ya kawo min key din

Kawu yace.”Ai tuntuni nima nake kiran wayar tasa taqi shiga amma dai jeka siyo katin ka gwada kiransa ko Allah zai sa wayar ta shiga.”

Salim da saurin gaske ya nufi gurin sayar da katin gabadaya hankalinsa a tashe yake da abinda abokinsa ya aikata a daidaita sahu wuya take a gari shi ya samu an bashi sojan gona yana samun kwabo da dari amma saboda bashi da hankali ya dawo da key din.

Kawu Iro kuwa bayan wucewar Salim daga gurin sai ya samu gefan dakalin dake ‘kofar gidan ya zauna yana jiran dawowarsa.
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*24&25*
Jiki a sanyaye ya ‘karaso kofar gidan nasu Kawu Iro na ganin yanayin fuskarsa ya gane akwai matsala Babu walwala a tare dashi yace.”Ka kira wayar ne.”?

Salim ya girgiza kansa da fadin”Wallahi kuwa Na kira ya kai sau bakwai tana katsewa gabadaya hankalina ya tashi da abinda Khalid yayi baba kasan sai da muka sha wuya sosai kafin mu samu adaidaita sahun nan amma kuma Khalid ya dawo da mukkulin babu wani dalili mai k’arfi.”

Kawu Iro ya miqe da fad’in “Salim ka kwantar da hankalinka Khalid dai a yanxu ba za’a kirasa yaro ba yana da hankali yasan abinda yake adaidaita sahu kuma daya dawo maka da ita kansa yayiwa mugunta sai kayi gaggawar mayarwa da mai ita a samu wanda yake bukata a bashi.”

Salim yace.”Kawu kayi hakuri dan Allah zan jira Khalid din ya dawo daga dik inda ya tafi sai naji dalilin da yasa ya aikata hakan.

Kawu Iro ya girgiza kansa cikin takaici yace.”Salim zaka wahalar da kanka domin abokinka yayi nisa saboda yasan rashin kyautawar da yayi sabida haka nake shawartarka da kayi gaggawar mayarwa da mai babur din nan key d’insa.”

Salim a sanyaye yace.”To shikkenan Kawu insha Allahu gobe zanje na kai masa key din.” Kawu ya miqa masa hannu sukayi sallama da juna ya wuce ya barshi a gurin a tsaye yana mamakin maganarsa to wane irin abun kunya abokin nasa ya aikata da har zaiyi nisa da gida.” da yaga bashi da mai bashi amsa sai ya juya jiki a mace ya shiga cikin gidan nasu.

A ranar Ummatu qin d’ora tunkunya tayi har wajen tara na dare babu labari Gwaggo ta hau surutai akan lamarin Ina daga kwance nace.”Gwaggo dan darajar Allah da Annabi kada ki sake tada wata tarzomar ki rabu da ita tunda ba tayi girkin ba ki dauki taliya ki dafa tunda kina da ragowar miya ni dai bana tsammanin zanci wani abu.”

Tace.”Haba Sa’ida ai wannan iskanci ne da wulakanci Ibrahim na iya bakin kokarinsa a gidan nan amma matar nan take kokarin tona masa asiri a unguwa yanzu bayan bakin cikin da muke ciki tana so mu kwanta da yunwa kenan.”

Nace.”Gwaggo ki kyaleta kada ki biye mata kinga rashin kunya take miki ni kuma zuciyata bata dad’i watarana idan ta ‘kure ni dole na mayar mata da martani shiyasa bana so kina biye mata kuna fad’a ma’kota na jinku.”

Tsaki tayi ta girgiza ta fara kokarin mi’kewa……Fita tayi ta dauko ‘yar tukunya ta dawo dakin da fad’in “Ai sai ki kunna min gas din ko.” Motsawa nayi na mike zaune ina ya mutsa fuskata, cikin kulawa tace.”Yana da kyau dai ki sake shiga cikin ruwan d’umi idan kuma baki daina jin zafi ba gobe sai muje asibiti a dubaki dan na lura yaron nan ya gwada miki mugunta.”

Nace.”Gwaggo babu wani asibiti da zanje idan kin sauke kisa min ruwan zafin ya isa.” Tace.”To ai shikkenan Allah ya kyauta.” ciki zuciyata na amsa da ameen tare da kar’bar ashanar hannunta na kunna mata ‘karamin gas din ta dora tukunyar akai.

Tana sa taliyar a cikin kunyar Kawu ya daga labulan dakin. tace.”Ibrahim ka dawo kaga har yanzu ja’irin yaron nan bai shigo gidan ba.”

Yace.”Gwaggo bana tsammanin fa Khalid na kusa dan tun dazu ake kiran wayarsa a kashe abokinsa Salim ya tabbatar min da cewa ya mayar masa da mukkulin adaidaita sahun da ya samo masa shin gwaggo duk me ya janyo haka? Khalid yasan bashi da gaskiya shiyasa ya gudu.”

Tace.”Ka rabu da ja’iri Ibrahim ai duk guje-gujen da zaiyi dole ya dawo gida ya same mu hukunci kuma kada ka fasa yi masa domin ya aikata abinda da ya zama dole a hukunta shi.”

Kawu ya kalli inda nake kwance cikin kulawa yace.”Sa’ida ya jikin naki ina fata dai babu wata matsala.”? Kafin nai magana tace”Tun d’azu take ya mutsa fuska tana tafiya da ‘kyar shine nace gobe muje asibiti a dubata ko yayi mata rauni tace ba za’aje ba xata cigaba da shiga ruwan zafi.”

Shuru yayi yana me sunkuyar da kansa ‘kasa hakika wannan al’amari ya tsaya masa a zuciya….a sanyaye yace.”Sa’ida kiyi hakuri aje asibitin a dubaki kada kuma wata matsalar ta afku.”

Murya na rawa nace.”Kawu ba sai anje asibiti ba insha Allahu babu matsala.” Girgiza kansa yayi yace.”To shikkenan ai dama haka ake so…..Kokarin fita yake sai ya kuma yatsa yana kallon tukunyar dake kan gas yace.”Gwaggo me kuma kike dafawa da dare haka.”?

Da sauri na rigata magana da fad’in “Taliya ce nace ta dafa min ina sha’awa.” Yace.”To na fahimta.” sai da safe yayi mana ya fita daga dakin.

Ummatu na ‘kuryar dakinta tana sa’kawa da kwancewa ya shiga yana kiranta tana jinsa tayi saurin kwanciya tare da rufe jikinta, rufe idonta tayi kamar mai bacci yazo ya tsaya a kanta yana fad’in “Rabi tashi ki dauko min abinci na dawo da yunwa.”

Ta bude ido cikin yanayi na masu bacci tace.”Ai sai dai kayi hakuri dan wannan fargabar ita ta hana ni na shiga kicin nayi wani abin arziki nima a haka zan kwana da yunwa.”

Rai a ‘bace yace.”Saboda ke zaki iya kwanciya da yunwa sai ki azabtar da rayuka tun safe da zan fita na baki kudin cefane bayan tsabar abinci da nake dashi a gidana amma saboda wani dalilin ki na banza da wofi kin ki yin girki a gida kina so nida mahaifiyata mu kwana da yunwa kenan.”

Zaune ta miqe tana kuka tace.”Ibrahim dan Allah ka saurara min haka naji da wannan masifar da take damuna wallahi ina hakuri a gidan nan mahaifiyarka a d’azu babu irin cin mutuncin da ba tayi min ba akan kawai na kare d’ana daga zargin da ake masa ni wallahi har yanzu ban yarda Khalid ne ya aikata abunda kuke zarginsa dashi ba.

Rai a ‘bace yace.”To idan bashi ne ya aikata ba mai ya hana shi dawowa gida? kuma mai yasa ya kashe wayarsa Rabi wai me yasa kike da son zuciya ne yarinyar nan Sa’ida itama haihuwarta akayi mai yasa kike fifita d’anki a kanta kema uwa ce ya kamata ki dinga adalci a cikin al’amuran ki a zahiri yaro ya aikata abu kuma ya nuna kansa amma sabodo son zuciyarki kice baki yarda ba k’azafi akayi masa.”

Komawa tayi ta kwanta tare da juya masa baya alamun duk maganganun da yake basu gamsar da ita ba, Kawu Iro cikin ‘bacin rai ya fita daga dakin kai tsaye hanyar fita daga gidan ya nufa ba zai zauna da yunwa akan yaron da bai ji tausayinsa ba.

Gwaggo ta fito daga bandaki da buta a hannunta tace.”Ibrahim ina kuma zakaje ai na dauka ka shigo gida sai da safe.”

Jim yayi kafin yace.”Gwaggo zan fita na nemi abinda zanci ashe wai Rabi bata baku abinci ba.”? Tace.”Eh ka rabu da ita da halinta kada kaje ko’ina zo muje daki kaci abinci ko baka ga ina dafa taliya ba.”

Yace.”Na gani Gwaggo.” tace.”To muje daki kaci ka koshi ka shareta da bak’in halin ta.” Girgiza kansa yayi yabi bayanta d’akin suna maimaita maganar.

Salmanu shuru yayi kawai ya tsirawa abokin nasa ido yana kallonsa. Khalid yace.”Salmanu ka tsananta lallai sai na fad’a maka damuwata na fad’a maka kuma ka tsira min ido kana kallona.”

Salmanu yace.”Khalid dole na kalleka saboda abinda ka aikata yanzu dan Allah ina soyayya take a nan? ashe dama duk irin haukan da kake a kanta sha’awarta kakeyi yanzu kai baka ji kunyar haike mata ba? bayan kullum kana ikiririn so da ‘kaunarta me zai sa ba zaka so abinda take so ba.”

Gumi ya goge a sanyaye yace.”Salmanu hankalina ya gushe tunani na yayi nisa a lokacin dana aikata wannan al’amarin nasan ban kyauta ba amma ina ganin hakan da nayi shine daidai domin ina tsammanin dole su janye maganar auran da zasuyi mata su nemi inda nake.”

Salmanu yace.”Khalid wannan ba dubara bace komai na rayuwa ana bin sa ne a sannu a hankali ba’a gwaggawa Khalid duk abinda kaga mutum bai samu ba a duniya ba to ba rabonsa bane kai mai yasa baka hakura da qaddara ba kabi son zuciyarka ka aikata abinda zai jefe zuk’atan iyayenka a damuwa kai ma duk da kabi son zuciyarka a yanzu nasan babu wanda ya kai ka nadama gami da damuwa yanzu kasan a wane irin hali na damuwa da bacin rai iyayenka ke ciki a gaskiya ni kam banji dadin wannan abu daya faru ba wallahi kuma ban ta’ba tsammanin zaka iya cutar da aunty Sa’ida ba sabida irin son da kake mata.”

Girgiza kansa kawai yake kafin ya dago kai ido jawur yace.”Salmanu sanin abinda yake cikin zuciyata sai Allah domin shi kad’ai yasan irin son da nake wa Aunty Sa’ida wannan al’amari daya faru tsakanina da ita tsautsayi da qaddara ne a lokacin a fusace! nake da irin abubuwan da take min bayan haka kuma kasan shi so babu abinda ba yasa mutum ya aikata amma bana ta’ba tsammanin zan iya daina sonta har duniya ta nad’e.”

Salmanu yace.”To ai shikkenan yanzu wace shawara ka yanke na ganka da jakar kaya.”

Yace.”So nake na bar garin kano gabadaya idan ‘kura ta lafa sai na dawo.” Salmanu yayi shuru yana nazarin maganar kafin yace.”Eh wannan tunanin yayi kyau kayi nesa da gida kafin zuciyoyinsu suyi sanyi amma ina baka shawara kancewa ka nemi iyayenka a waya ka basu hakuri itama Aunty Sa’idar ka kirata ka bata hakuri ka nuna mata nadamarka.”

Ya sharce gumin goshinsa yace.”Insha Allahu haka za’ayi abokina nagode ‘kwarai da shawararka…….Salmanu yace.”Haba ai babu komai Khalid an riga an zama daya ina jinka tamkar d’an uwana na jini shiyasa gabadaya da naji al’amarin nan hankalina ya tashi.”

Khalid girgiza kansa kawai yayi shima jikinsa duk yayi sanyi da abin kunyar daya tafka tun a mota yake tunanin mawuyacin halin daya bar auntyn nasa a ciki sai kuma fargabar tashin hankalin da iyayensa zasu shiga idan sukaji abinda ya aikata.

Salmanu mi’kewa yayi ya kama hanyar fita da fad’in “Bari na shiga gida na kawo maka abinci.” Khalid ya sauke ajiyar zuciya da fad’in “Nagode abokina.”

Bayan fitar Salmanu da minti uku sai ya bude jakar kayansa ya dauko wayarsa a nutse ya kunna ya nemi number Salim. domin yana so suyi magana a tsakaninsu.”

Salim na kallo a wayarsa yaga kiran abokin nasa da sauri ya daga hannunsa sai kyarma yake yace.”Khalid kana ina ne tun dazu ake ta kiran wayar ka bata shiga mahaifinka ma yazo yana nemanka hankalinsa a tashe.

Khalid yace.” Salim nayi nisa da gida saboda wani dalili shiyasa ma kafin na tafi na kai mukkulin babur gidanku nace a ajiye maka inaso ka mayarwa da mai shi abunsa ya bawa mai bukata sannan don Allah gobe da safe kaje can gida kafin mahaifina ya fita kasuwa kace masa nace dan Allah dukkaninsu su gafarce ni.”

Salim jikinsa yayi sanyi yace.”Khalid wai me yake faruwa ne? yanda naga hankalin mahaifinka a tashe ya dameni gashi kuma kai yanzu kana wasu zantukan da suka sanyayyar min da jiki.”

Murmushi yayi irin na takaici da nadama yace.”Salim kai abokina ne tun na ‘kuruciya kasan halina sannan kasan abinda zanyi da wanda ba zanyi ba qaddara da tsautsayi sun afka min na haikewa Aunty Sa’ida bayan na samu labarin maganar auranta da Alhaji Nura.”

Salim yace.”Khalid magana kake yi a cukurkud’e! ka fito fili kayi min bayanin da zan fahimta ka haikewa aunty Sa’ida to me hakan yake nufi.”

A sanyaye yace.”Ina nufin nayi mata fyad’e a d’azu da rana.” “Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un! Khalid garin ya akayi haka ta faru? A garin ya ka aikata wannan mummunan aikin akan masoyiyarka.”

Yaji hawaye na nema su kufce masa daurewa yayi ya aro dauriya yace.”Tsautsayi da qaddara ne sai kuma son zuciyata nima nasan ban kyauta ba dan Allah ka riqe min sirri na bana so kowa yaji wannan magana salim.”

Salim ya dinga jijjiga kansa gumi! na yanko masa yace.”Wallahi Khalid ko a mafarki ban ta’ba tsammanin zaka aikatawa aunty Sa’ida haka ba me tayi maka mai zafi ashe dama duk ‘karya kake ba sonta kake ba.”

A tunzure! yace.”Wai ya zaku dinga fad’a min wannan banzar maganar ne? Salim me ya janyo hakan idan ba so ba? ka fad’a min maganar da zata sanyaya raina ba irin wannan ba! har abada ba’a sanjawa towo suna wannan abu da ya faru tsakanina da ita ya sake saka min so da kaunarta a cikin zuciyata.”

Salim yace.”Kayi hakuri Khalid naga kamar ranka ya ‘baci amma dai kasan kowaye yaji wannan al’amari dole ya razana dole kuma ya shiga tantama akan son da kake mata amma babu komai qaddara ta riga fata kamar yanda ka fada cewa tsautsayi da qaddara ne ya janyo maka to ina rokon Allah ya kare faruwar wani abu anan gaba.”

Can ‘kasan ma’koshi ya amsa da ameeen ya Allah nagode abokina sai na sake kiran wayarka.” Salim yana kokarin yayi magana Khalid din ya kashe wayarsa yabi wayar da kallon mamaki kafin yayi yunkurin sake kiran sa domin yana so tambayeshi inda yake a halin yanzu yana fara kira a kace masa wayar a kashe take, dan suna gama magana Khalid din ya kashe wayarsa ya mayar da ita cikin jakar kayansa.

Salmanu ne ya shigo dakin hannunsa da fulas ba abinci da maidaidaicin plate da co*kula ya ajiye a gabansa tare da bude karamin firjin dake dakin ya dauko masa ruwa da lemo masu sanyi kallonsa yayi da fad’in “Khalid kaci abinci ka samu nutsuwar zuciya kuskure ne dai ka riga ka tafka sai sa ka kiyayi gaba.”

Yace.”Salmanu bana tsammanin zan iya cin wani abu a halin yanzu cikina a cunkushe nake jin sa bana sha’awar komai.”

Salmanu yace.”Ai dama ba dan dad’i zaka ci abinci ba domin ka kori yunwar dake damun ka ita kanta yunwar wata matsala ce mai zaman kanta saboda haka kaci abinci kawai ka kwanta kaja istgifari akan abinda kayi.”

Yace.”Salmanu Istgifari tun ina kan aikata al’amarin nake yi sai dai kace na d’ora wani akan wanda nake amma ni ma babu shakka nasan nayi kuskure mai muni kuma wallahi sai yanzu nadama da dana sani suka dame ni Salmanu abinda hakuri bai baka ba rashin sa ba zai baka ba, na bi son zuciyata na janyowa iyayena zagi shine babban abinda yake damuna.”

Salmanu yace.”Idan maganar ta tsaya a cikin gidanku ai asiri ya rufu amma kuma gaskiya banji dadin yanda kake nuna rashin damuwarka akan Aunty Sa’idar ba yanda na lura kamar kafi fargabar halin bakin cikin da iyayenka zasu shiga.”

Yace.”Hakane Salmanu ina tausayawa iyayena sosai akan aunty Sa’ida domin ni ina ganin duk abinda ya faru a tsakaninmu itama tana da laifi mai zai sanya ta dinga zagi na tana nuna ban isa ba Salmanu idan kaga irin cin mutuncin da take min sai kayi mamaki wannan dalilin yasa na yanke mata irin wannan hukuncin dan data bini a sannu a hankali duk haka ba zata faru ba.”

Salmanu yace.”Gaskiya ne maganar nima ko kad’an bana son raini su kuma mata daga zarar sun d’an girmaka ko yaya ne sai su rainaka itama abinda tayi maka bata kyauta ba Ai *GA IRINTA NAN!* abu yazo ya faru gabad’aya kai da ita kun fad’a cikin masifa kuncin rayuwa.”

Ajiyar zuciya ya sauke ba tare da ya sake cewa komai ba ya dauki pure water daya yasa a bakinsa sosai yaji dadin ruwan saboda yanda ya sanyaya masa kirji Salmanu ya bude fulas din abinci da kansa ya zuba masa wanda zai isheshi yasa masa co*kali a ciki ya tura masa gabansa…….

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*26&27*
Cikin ikon Allah gami da tasirin addu’oin dana durfafa bacci mai nauyi ya dauke ni tunda na kwanta kuma ban farka ba sai asubah…… da salati a bakina na bude idona lokacin itama Gwaggo ta tashi zaune tana laluben torchlight d’inta. “Sa’ida tashi asubah tayi ina tunanin ma an idar da sallah dan ga gari nan ya fara haske.” Waya ta na laluba na kunna inna duba lokaci shida da kwata ba a jima da idar da sallah ba.

cikin rashin ‘kwarin jiki na mike buta na dauka zan fita tace.”Kada kisa ruwan sanyi a gabanki Sa’ida akwai na zafi a fulas ki surka.”

Ba tare da nace mata komai ba na surka ruwan na fita dashi a hannuna kai tsaye band’akin nayi nufin shiga Ummatu ta fito daga ciki da buta a hannunta.

Sai nayi saurin kaucewa na bata hanya, ta tsaya tana watsa min kallon banza kafin tace.”An dai ji kunya an kuma aikata abin kunya Insha Allahu sai asirinki ya tonu a gari kowa sai ya gane mugun halinki.”

Uffan bance mata ba na shige bandakin ina jin wani irin tsanarsu ita da d’an nata.

Koda na tsuguna domin fitsari sai da na kusa kuka dan gurin rikice min yayi da zafi kamar wanda akasa reza aka tsatstsaga.

Ruwan zafin na fara watsa a gurin ina rintse idona anya kuwa ba zan amince da shawarar Gwaggo ba muje asibiti a duba gurin nan kada yaron nan fa ya jefa ni a matsala.

Idona na rufe ina watsa ruwan a gurin ina tunano irin girman Joystick d’insa babu shakka Allah yay masa hallita sosai tabbas wani abu mai muni yana iya faruwa dani tunda gashinan gurin ya kume! sai zafin azaba yake min

Sai da na ‘karar da zuwan d’umin tas na mike a hankali tare da mayar da wando na na fito lokacin Ummatu ta jima da barin gurin

Daki nayi nufin zuwa na dauko brush ta fito dashi a hannunta. hannu nasa na kar’ba tace.”Ai naga baki dauka ba shine nace ko mantawa kikayi.” A hankali nace mata ina sane ban manta ba.

Hanyar bandaki ta nufa kafin ta shiga sai da ta jima a tsaye a bakin kofar bandakin tana addua sannan ta shiga.

To koda na idar da sallah zamewa nayi na kwanta kan daddumar na shiga tunanin irin rayuwar da zan fuskatanta anan gaba nasan dai dole sai na fuskanci kalubale mai muni tunda nayi rashin babban abu mai muhimmanci a tare dani.

Tana shigowa dakin kira ya shigo waya ta da sauri tace.”Yauwa duba ki gani ko shine.” hannu na mika na dauki wayar ina kallonta nace.”Wa kike nufi.”? Tace.”Khalid mana.” Kawai na tsaya ina mata kallon mamaki kafin nace.” Gwaggo Khalid ya kira ni a waya yace dani me.”?

A sanyaye tace.”Ai ba zai rasa abin fad’a ba dan jiya kwana nayi ina mafarkinsa wai yana cikin mawuyacin hali kuma a mafarkin da nayi dashi ya bani hakuri yana hawaye yace duk abinda ya faru tsautsayi da qaddara ne shiyasa nayi tunanin ko zai kira ki a waya ya baki hakuri.”

Kai na girgiza nace.”Kinga Gwaggo kiyi sallar ki kina ‘batawa kanki lokaci waya ba Khalid ne ya kira ba Alhajina ne.”

Sai tayi min shuru ta hau gyara zaman hijabinta a wuya.

Alhaji Nura wayar ya sake kira bayan katsewarta na d’aga cikin nutsuwa nace.”Ranka ya dade barka da asubah ina fata ka tashi lafiya.”?

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Sa’ida kina ina ne ina kiran waya kusan sau uku tana katsewa.”

Nace.” Bana kusa da wayar ne shiyasa kayi hakuri.” Yace.”Okey babu damuwa ya gida yasu Gwaggo ina fatan kowa lafiya.”?

Nace.”Alhamdulillahi ina lafiya Gwaggo ma haka.” Yace.”To masha Allah nace ya shirye-shirye ina fatan duk wani abu da kike bukata kin rubuta insha Allahu ranar juma’a nake so a kawo lefe idan yaso idan sati ya zagayo a daura auran.”

Naji gabana ya wani irin fad’uwa ! shuru nayi duk na rikice bakina yayi nauyi sai magana yake na kasa bashi amsa ina can ina tunanin yanda zata kaya.

“Gimbiya kina jina ina magana kinyi shuru nace wane shiri da tanadi kika yi min a matsayina na ango.”

A sanyaye nace.”Alhajina kenan kada ka damu nayi maka tanadin alkairai masu yawa ni dai buri na ka ri’ke ni tsakani da Allah da amana kuma kayi adalci a tsakani na da matarka.”

Yace.”In dai wannan ne kada ki damu Sa’ida ni tsayayye ne a gidana matata kuma baki da matsala da ita tana da saukin kai da fahimta inaso idan kinje ku had’e kanku kuma ki bata girmanta.”

Nace.”Insha Allahu zan kiyaye nima sai kace mata ta dauki ni a matsayin ‘yar uwa ba kishiya ba.” Yayi dariya da fad’in “Ai tuntuni da haka ta dauke ki kullum idan zanzo gurinki tana bada sakon gaisuwarta yanzu haka ma tana kusa dani a kwance.'”

Nace.”Naji dadi sosai da irin kulawar da take min dan Allah kace ina gaisheta.” Yace.” Bari kawai na bata wayar ku gaisa.” kafin nace komai naji muryarta ta doki kunnena.

Muryarta naji cikin ‘yar fara’a tace” ‘Kanwata kin tashi lafiya.”?

Cike da kulawa na amsa da “Lafiya kalau Wallahi ya kwanan yara.”? ta sake ‘Yar dariya da fadin.” Yaran ki sun kwana lafiya suna can suna shirin skull.” Nace.”To masha Allahu Allah ya basu ilimi mai amfani.”

Ta amsa da “ameen ‘kanwata ki gaishe min da Gwaggo da kyau.” Nace.”Insha Allahu za taji.” sallama mukayi naji muryarsa yana fad’in “Gimbiya sai an jima ko.”?

Cikin jin nauyi nace.” Eh Alhaji yanzu zanyi shirin makarana ne.” Yace.”Okey to babu damuwa bari na barki ki shirya idan anjima na sake kira.”
Nace.”To shikkenan sai an jima.” da sauri na kashe wayar domin ba naso magana ta cigaba da tsayi a tsakanin mu kodan saboda matarsa dake kusa dashi.

Gyaran muryar ta naji kafin tace.”Amma matar nan tana da kirki da alama kuma zaku zauna lafiya da juna dama ai tuntuni nake samun labarin kirkinta a bakin Uwale tace ai ta fito daga babban gida ne.”

Nace.”Nima nayi mamakin yanda take mu’amula dani da alama tana da sau’kin kai ba kuma ta dauki al’amarin da zafi ba.”

Gwaggo tace.”To Allah ya kauda ‘yan gaza gani akan al’amarin.” Nace.” Ameeen ya Allah.”

Shuru d’akin yayi na minti biyu ta kalle ni da fadin.”Naji kina maganar zuwa makaranta haba Sa’ida yanzu sai ki shiga cikin jama’a kina tale ‘kafafu har yanzu fa tafiyarki bata dawo daidai ba.”

Shuru nayi ina tunanin maganar ta tabbas nima nasan tafiya ta ta sanja domin ina jin jiki gurin taka kafafuna nace.”Gwaggo inaji dai shawararki zan duba.

Kallona tayi, nace.”Idan mun karya zaki raka ni asibiti a duba gurin nan a gani ni kadai nasan azabar da nake ji.”

Tace.”Haba dama ni jikina yayi sanyi da yanayin yanda kike tafiya kafafu a bud’e Allah dai yasa yaron nan bai ‘kara miki kofa ba.”

Gabana ne ya fad’i! na sunkuyar da kaina ina addua Allah yasa kada maganar Gwaggo ta zama gaskiya idan Khalid yayi sanadiyar bud’ewar gabana ai ya cuce ni.

Hankalina ya tashi nace.”Gwaggo tashi ki shirya mu tafi asibitin nan.” Tana kokarin magana Kawu Iro ya daga labulan dakin da alama daga massalaci yake…a nutse suka gaisa da mahaifiyarsa na gasheshi ya amsa cike da kulawa yana tambayar jikina…..A sanyaye nace.”Da sauki Kawu.”

Yayi jim! kafin yace.”Gwaggo yanzu yanzu Salim abokin Khalid ke sheda min cewa jiya ya kirashi a waya sunyi magana da juna.”

Gwaggo da sauri tace.”Yauwwa to Alhamdulillahi me yace dashi dan wallahi jiya kwana nayi ina munanan mafarkai akansa.

Kawu Iro ya girgiza kansa da fadin”Gwaggo dole kiyi munanan mafarkai akan Khalid domin kuwa ya aikata abu yazo ya dameshi a maimakon yazo ya nemi gafara sai kawai ya yanke shawarar barin gari yanzu haka dai ba’a san inda yake ba.

Murya na rawa tace.”Kai jama’a! wannan wace irin masifa ce.”? da sauri yace.”Gwaggo daina kiran masifa shi da ya janyo ta to akansa zata ‘kare.”

Gefan hijabinta tasa ta goge hawaye da fad’in “Wannan yaro Allah dai yasa baiyi nisa da gari ba Ubangiji Allah ya karkato hankalinsa ya dawo gida.

Kawu yace.” Gwaggo Khalid gwara yayi nesa damu domin hakan shine nutsuwa da kwanciyar hankalinmu.”

Tace.”Haba Ibrahim ai hannunka ba zai ru’bewa ka yanke ka yar kayi hakuri ka yafe masa.” Kallonta nayi ina mamakinta wato dai Gwaggo wahainiya ce mai sanjawa a duk sanda ta so jiya babu irin zagin da ba tayi wa Khalid ba amma yau gashi kuka take a kansa duk ta tashi hankalinta har ta manta abinda ya aikata.

Kawu Ibrahim na kokarin barin gurin Ummatu ta karaso hannunta ri’ke da tire na silba mai fadi kayan karin kummalo ne a kai.

Ta shigo dakin tare da ajiye tire din a gabanta a dakile ta gasheta Gwaggo ta shaqi hanci tana amsawa tace.”Rabi bukatar ki ta biya akan Khalid kinyi masa baki ibtila’i ya sauka a kansa *GA IRINTA NAN!* mai afkuwa ta afku ya tattara kayansa ya bar gari gabadaya.”

Ummatu gabanta na faduwa tace.”Gwaggo wace irin magana ce wannan? wane irin baki zan jefi d’an ciki na dashi dan Allah Gwaggo ki dinga tauna magana kafin ki fad’eta.”

Gwaggo a fusace! Tace.”Haba Rabi wallahi ko shakka ba nayi bakin ki ne ya kama yaron nan me yasa kika dinga zaginsa har kina masa Allah ya isa idan ya sake magana da Sa’ida ashe har ke kin isa ki raba shi da ‘yar uwarsa.”?

Ummatu shuru tayi tana nazari! dama tasan tsakaninta da d’anta Babu sirri komai za tayi masa sai yazo ya fad’awa kakarsa ashe zuwa yayi ya fad’a mata gargadin da tayi masa akan Sa’idar.

Gwaggo tace.”Wattanin da suka gabata yaron nan yazo gurina ransa a ‘bace yake sheda min abubuwan da kukayi masa keda mahaifiyarki wato kece harda cewa duk sanda ya sake wata magana da Sa’ida Allah ya isa to gashinan Allah ya isan da kikayi masa ta sauka a kansa Rabi kin cutar da d’anki da kaifin bakin ki.”

Ummatu jikinta yayi la’asar cikin ‘kokarin kare kanta tace.”Aa Gwaggo ki daina wannan magana ni bance masa Allah ya isa ba nasan dai nayi masa fad’a a kancewa kada na sake gani ya shiga sabgar Sa’ida domin ba sa’arsa bace.”

Gwaggo tace.”Ke har kin isa ki raba zumuncin da Allah ya halasta? akan wane dalili zaki raba shi da ‘yar uwarsa.”? jin yanda take daga murya yasa tayi saurin mi’kewa domin fita daga dakin dan bata so mijinta yaji abinda yake faruwa.

Gwaggo cikin masifa tace.”Shashashar uwa kawai wacce bata aiki da ilimin ta haka kawai saboda rashin tsinkaye da tunanin abinda zai faru a gaba kin cutar da danki.”

Ummatu dai uffan ba tace mata ba ta shige gurinta jikinta a masifar sanyaye Khalid ya gudu ya bar gari to ina ya nufa? wasu zafafan hawaye suka shiga sauka a fuskarta ta zauna a d’an tsakar gidanta tana kuka mara sauti tare da nadamar abinda tayi.

*Hattara Iyaye masu kausasa kalma a kan ‘ya’yansu ku kiyaye yi wa ‘ya’yan ku Allah ya isa ko kuma jeka zaka gani wannan kalmar tana da had’ari sosai duk halin da d’anki ya shiga kece sanadi*

Gwaggo bayan fitar Ummatu Kukanta taci ta koshi ina kallonta da mamakin halayyarta da kyar ta iya shan kunu taci kosai uku ta janye tiran daga gabanta…Lokaci ni har na gama shiryawa na kalleta babu walwala a tare dani nace.”Shin zaki raka ni asibitin ko kuma nayi tafiyata.”

Tace.”Zan raka ki mana Sa’ida tashin hankalin tafiyar Khalid ne ya hana ni shiryawa baki ga ma ko karyawa na kasa yi ba.”

Ba tare da na kalleta ba nace.”Ke ki kaga zaki iya.” shuru tayi min ta miqe ta fita minti uku ta dawo dakin ta dauki mai ta shafa a kafafunta hijabin ta tasa da fad’in “Ai asibiti ne ba wata kwalliya ake ba.”

Ba tare da nace komai ba na miqe da jakata a hannuna bayana ta biyo da kwad’o (mukkuli) a hannunta…..kar’ba nayi na kulle kofar dakin. kana muka kama hanya muka tafi.

Pravite hospital mukaje na yanki kati kai tsaye ofis din da aka tura ni na nufa….lokacin akwai wata a ciki sai da ta fito tukkuna na shiga Gwaggo tana kokarin bina nace ta zauna na shiga na fito.

A nutse ta kalleni bayan ta gama sauraran jawabi na tace.”Sa’ida dole zaki kwanta a gado na dubaki dama ai mafi akasari irin haka na kasancewa mussaman a daran farko akan samu matsala irin wannan matsalar.”

Hawaye suka cika idona wai daran farko naji takaicin wannan magana tata, babu kuzari a tare dani na shiga d’an d’akin data nuna min na shiga na kwance zani na tare da cire pant d’ina.

bayan na kwanta a gadon tasa safa a hannuwanta ta shiga duba gurin hawaye masu zafin gaske suka shiga gudana a fuskata wai yau ni Khalid ya janyowa wannan tozarcin.

Kallona ayi tare da fad’in “Ki tashi baki da wata matsala abinda yasa gabanki ya tsatstsage lokacin da mijin naki yazo ka kar’bar hakkinsa kinyi gaddama hakan shi ya janyo miki matsala shiyasa kullum muke fada cewa duk budurwar da mijinta yazo kar’bar hakkinsa a daran farko to yana da kyau ta bashi hadin kai kada tayi wani yunkuri domin ceton kanta dan ko tayi ba zai bari ba daga karshe ma ta janyowa kanta wata matsala amma dai ke gabanki normal yake bai kar’u ba zafi da rad’ad’i kuma zaki daina ji insha Allah yanzu zan rubuta miki magunguna idan kun fita sai ki siya.”

Cikin kokarin danne damuwar dake taso min nace.”Nagode Dr.” safar hannunta ta cire ta watsa a dustbin kafin ta fita daga dakin.

Kati na ta miko min mai dauke da magungunan data rubuta min…na kama hanya zan fita ta dakatar dani. juyawa nayi ina kallonta a tausashe tace.”Sa’ida kada kice naiyi miki katsalandan kamata yayi ace tare da mijin naki ku kazo asibiti.

Kaina na sunkuyar ina nazarin maganar da zan fad’a mata…..”Wallahi tafiya ce ta kama shi a washe garin ranar daurin auran mu shine dalili.”

Kallona naga ta nayi kamar bata yarda da maganata ba, nace.”Dr nagode da kulawarki.” hannu ta d’aga min da sauri na fita daga ofis din ina mamakin bin
diddigi irin na mutane….

*Littafin na kudi ne….kada ki siya ki fita dashi idan kika ganshi kada kiyi sharing…..’yar idan kika karanta min littafi baki biya ba ina bin ki bashi….Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake…….Vip gruop#600….normal gruop#300….account.. 0542382124…Binta umar gtbank…idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*

*28&29*
Tun a cikin adaidaita sahu Gwaggo ke tambayata nace ta kwantar da hankalinta babu matsala, ajiyar zuciya ta sauke tana godewa Allah….har kofar gida nace da direban ya kai mu sai cewa tayi ita ya sauke ta a bakin hanya domin tana so ta shiga gidan Uwale su gaisa.

Nace.”Gwaggo me zakiji kiyi a gidan Uwale da rana gatse-gatse haka.” d’an ‘bata fuska tayi tace.”Zanje ne mu tattauna al’amuran da suka shafe mu Sa’ida kin san abokin kuka shi ake fad’awa mutuwa.”

Idanuwa na suka kawo ruwa nace.”Wallahi Gwaggo kika kuskura kika fad’awa Uwale abinda yake faruwa kin kashe kanki domin dai ni nasan Uwale ba zata ta’ba barin maganar nan a cikin ranta ba sai ta fad’awa wani kinga daga haka shikkenan labarin abinda ya faru ya bazu a duniya ko ya sani.”

Shuru tayi tana nazari tace.”Sa’ida Uwale tana da amana kuma mun jima muna aminta nasan zata ri’ke min amanata.

Nace.”Ni dai dan Allah dan Annabi kada kije gidan matar nan wallahi bata da kirki ko kad’an yanda take kawo miki gulmar mutane haka kema zata kai gulmarki gurin wasu.

Tace.”To naji dan Allah maganar ta isa haka na fasa zuwa shikkenan ko.”

Na kalli direban da fad’in “Shiga damu cikin layin ka ajiye mu a kofar gida.
Da sauri yace.” To hajiya.

Koda muka shiga gidan shuru babu motsin kowa kofar gurin Ummatu a rufe da kwado Gwaggo tace.”Sarkin yawo kenan wato har ta kulle kofa ta fita.”

Nace.”Kika sani ko wani uzirin ne ya fita da ita.” tace.”babu wani uziri ta tafi yawon malamai ne.”

Ashe hakane Ummatu bayan fitarsu gwaggo daga gidan itama sai ta shirya a gurguje ta tafi gurin malamin da suke zuwa gurinsa yana musu duba tana kuka duk ta sheda masa abinda yake faruwa.

Malam Sammani ya jima yana zane-zane kafin ya dago kansa ya kalleta da fadin”Rabi yaron nan naki abinda ya aikata gaskiya ne ba sharri akayi masa ba kamar yanda kike zargi! kuma na duba na gani cewa lallai akwai ibtila’in da zai sameshi a cikin ‘yan kwanakin nan amma kuma akwai wani tauraro da yake haska shi watakila nan gaba akwai wata daukaka da zai samu sannan maganar surukar ki sai dai kiyi hakuri domin ‘kwan’kwaman! da suke kanta sunfi karfin ki itama sunfi ‘karfin ta iyayen aljanu ne a jikinta dole kiyi hakuri da duk abinda za tayi miki sai dai akwai wani taimako da zanyi miki akanta zan gwada daure mata baki mu gani idan zai yuwu.”

Ummatu ta sharce gumin goshinta hankali a tashe tace.”Malam Sammani dan Allah ka taimaka min akan yaron nan hankalina ya tashi da jin abinda kace yayi nisa da gari bayan haka kuma ga ibtila’in da zai hadu dashi ka taimaka min kayi aikin da zai sanya ya dawo gida babu shiri.

Malam Sammani yayi zane-zane a karo na biyu ya duba yaga abinda Allah ya haska masa tabbas duk abinda ya gani a dubansa zai faru amma bari kawai ya sanja mata magana domun ya kar’bi kud’inta ya biya bukatarsa.

“Shikkenan Rabi za’ayi miki kokari akan bukatarki amma kema zaki bayar da sadaka mai auki.”

Tace.” To kamar nawa ne abin sadakar.”? yace.”Dubu bakwai zaki bayar ya isa.” jim tayi tana nazari kafin tace.”Malam a yanzu dai wallahi bani da dubu bakwai bani da dalilinta amma ina da kayan kudi a gida insha Allahu gobe zanzo maka da kudin sai ka fara gudanar da aikin.”

Yace.”To babu damuwa insha Allahu zan ajiye aikin kowa na durfafi naki sabida ni kaina al’amarin ya firgita ni amma babu komai za dage da addua muyi masa kiranye ya dawo gida babu shiri itama surukar taki aiki mai kyau zanyi akanta.

Ummatu ta dinga zabga masa godiya kafin tayi masa sallama ta tafi gida .

*Shashashar Uwa kawai a maimakon ta gyara kuskuranta ta sake tafka wani*

Kafin ta shiga gida sai da ta tsaya gidan Lantana Dillaliyi tayi mata bayani kancewa idan tana son siyan katifar gado tazo ta gani.

Lantana ta kalleta da mamaki a tare da ita tace.”Ke kuwa Rabi me yayi miki zafi zaki siyar da katifar gadon ki shin rashin ci ko rashin sha ne ya janyo haka.”?

Ummatu a sanyaye tace.”Ko d’aya Lantana wata ‘yar matsala ce dani wallahi sabida haka nazo nayi miki tallah idan kina so kawai muje ki gani bana san doguwar magana.”

Lantana ta yafa mahaifinta da fad’in “To shikkenan muje naga katifar.” suka fito daga gidan a tare.

Muna zaune nida Gwaggo a tsakar gida muna hira gwaggo na gyara wake za tayi mana alala Ummatu da Lantana suka shigo…..Lantana cikin mutunci ta tsaya suka gaisa da Gwaggo ita kuwa Ummatu ko kallonmu ba tayi ba ta bude gurinta ta shiga Lantana tabi bayanta.

Gwaggo da bakinta baya shuru tace.”Sa’ida mai Ummatu zata siyar ta kawo dillaliya gidan nan.”?

Nace.”Gwaggo dan Allah ki daina shiga abinda babu ruwan ki kiyi shuru da bakin ki shi yafi miki alkairi.”

Shuru tayi bata sake cewa komai ba sai dai sa’i da lokaci takan daga kai ta kalli kofar Ummatun nasan jira take su fito.

“To shikkenan Lantana sai ki aiko yaro da akori kura ya daukar miki na siyar miki akan dubu ashirin da biyar din.” Ummatu ce ke wannan maganar a lokacin da suke fitowa daga gurin nata.

Lantana tace.”To shikkenan yanzu yanzu ina komawa gida zan turo a dauka tare da kudin naki.” Ummatu tace.”To ina saurare.”

Lantana ta kalli Gwaggo da fad’in “Gwaggo Allah ya bamu alkairi ni na tafi.” Gwaggo tace.”To ki gai da gida.” Lantana na fita Ummatu da sauri ta juya zata bar gurin.

“Rabi.” Gwaggo ta dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta. Fuska a murtuke ta juyo tana amsawa Gwaggo tace.”Me zaki siyar ne.”? Da sauri na kalleta ina jin masifar takaicin abinda take ina ruwanta Ummatu ko kanta da kanta zata siyar ido ne nata.

“Gwaggo ba abinda ya shafeki bane” Ummatu ta mayar mata da amsa daidai da tambayarta. Gwaggo taji ciwo sosai tace.” Duk abinda zaki siyar kije kiyi ta siyarwa ni dai nasan ba za’a zagi Ibrahim ba ace ya gaza a gidansa wannan ai cin mutunci ne rana gatse-gatse kije ki dauko dillaliya ta shigo mana gida me aka gaza dayi miki a gidan.”?

Itama cikin rashin tausasa harshe tace.” Ai dama ni bance Ibrahim ya gaza a gidansa ba tunda daidai gwargwado yana kawo abinci amma kuma suttura sai shekara shekara sannan ni na dauko Lantana ne domin tazo ta siyi katifar gadona saboda inada bukatar kudi.”
Tana gama maganarta ta kad’a kanta ta shige gurinta.

Gwaggo ta bude bakinta cike da mamaki tana kallona.

Nace”Ai dama baki in yasan abinda zai fada bai san abinda za’a mayar masa ba tun farko sai da nace kiyi shuru kika k’i ai gashinan kin janyowa kanki cin mutunci.'”

Tace.”Sa’ida ni ba wannan ne ya dame ni ba saboda cin mutuncin Rabi kuma wane iri ne ban sani ba ko ba kiji abinda tace ba wai zata siyar da katifar gadonta to a ‘ina Ibrahim zai dinga kwanciya.”?

Nace.”Gwaggo babu ruwanki katifa dai ta Ummatu ce baki isa ki hana ta siyarwa ba saboda haka kiyi shuru da bakinki shi yafi miki alkairi Kawu kuma insha Allahu ba zai rasa gurin kwanciya ba ni nayi alkawarin siya masa katifa yasa a dakinsa shikkenan magana ta mutu.”

Girgiza kanta tayi da fad’in “Lallai Rabi tayi nisa ko da yake ai nasan idan ta kar’bi kudin katifar gurin malamai zata kai asararriya kawai.”

Shuru nayi ban tanka mata ba saboda bana so maganar tayi tsayi da dai naji taki tayi shuru sai na mike na shige daki na kwanta ina jira ta gama mana alalan nasha magani bacci mai nauyi ne ya dauke ni.

Gwaggo kuwa har akazo ka dauki katifar ba ta daina surutai ba tamkar ma wacce ake ingizawa Lantana da Ummatu sun sha habaici amma sai akayi sa’a cikinsu babu wacce ta tanka mata Lantana ta tafi da katifa ita kuma Ummatu ta shige gurinta da kudinta a hannu

****
*BAYAN SATI DAYA*
Khalid ya dan samu nutsuwa a gidansu Salmanu sai dai baya sakewa sosai a unguwar gudun kada yaga idon sani kullum yana dakin Salmanu a kwance yana shawarwari da zuciyarsa.

Salmanu ya shigo dakin da fad’in “Khalid ka tashi ga shawara nazo mana da ita.”

Zaune ya miqe yana kallonsa da fadin” Nima kwanciyar nan da nayi shawarwari nake da zuciyata.

Salmanu yace.”Legos zamu tattara mu tafi akwai wata ‘kungiyar ‘yan ball ta ‘yan kano mai taken kano Pillas inaso muje mu fara gudanar da harkokinmu na ball a can Khalid ka iya buga ‘kwallo jikina na bani kana da abinci a harkar.

‘Karamin tsaki yaja yace.”Wallahi na dauka zaka ce akawai company da yake bukatar irinmu a legos din wace irin ball kuma Salmanu mu fuskanci abinda yake gabanmu ina ganin tunda aikin ya’ki samuwa anan me zai hana mu tafi da takardun mu can mu gwada mu gani.”

Salmanu yace.”Eh dama haka za’ayi Khalid ai ba zamu dogara da abu guda ba idan aikin ya’ki samuwa ba sai mu mayar da hankalinmu gurin harkar k’wallo ba ko ya kaga ni.”

Khalid yace.”Salmanu nifa a halin yanzu aikin da zai ri’ke ni nake nema bana so nayi ta zama da girmana wani na dawainiya dani ‘Kwallo tana kawo kudi amma sai mutum yana da hanya a harkar sannan duniya zata san dashi har ya samu wani abu.”

Salmanu yace.”Khalid ka kasa gane maganata dama ai ba wai zamu zauna a guri daya bane idan munje zamu dinga buge-buge nufi na duk inda ta fad’i daidai ne.”

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”To shikkenan Salmanu amma dai akwai guziri mai yawa a gurinka ko dan ni ba wasu kudi masu yawa gare ni ba.

Salmanu yace.”Babu damuwa insha Allahu zan tambayi kanin mahaifina zai taimaka min sannan Mamana ma zata bani goyon baya kuma zata taimaka mana.

Yace.”To shikkenan Allah yasa muje a sa’a.” Salmanu ya amsa da ameeen tare da fadin”Khalid ya kamata ka kunna wayarka ka kira gidanku ka shedawa mahaifinka yasa maka albarka ka kuma nemi gafararsa.

Yace.”Salmanu wallahi tuntuni nake wannan tunanin amma na rasa ta ina zan fara ina jin kunyar abinda na aikata.

Salmanu yace.”Daurewa kawai za kayi ita qaddara ai ba’a guje mata zuwa yanzu dai nasan zuciyoyinsu sunyi sanyi sai ka tausasa harshe gurin neman afuwarsu mussaman ita wacce ka ‘batawa.”

Shuru yayi yana me sunkuyar da kansa, Salmanu yace.”Bari na shiga gida na dauko mana abinci.” Bayan fitar Salmanu daga dakin Khalid ya janyo jakarsa ya bude a nutse ya dauko wayarsa ya kunna kai tsaye number auntyn nasa ya lalubo ya shiga gurin kira.

Lokacin muna hanyar dawowa gida ni da ‘kawata Hauwwa kiran ya shigo waya ta gabadaya hankalina ya dauke gurin hirar da muke shi yasa ban duba mai kiran ba na daga tare da sa wayar a kunne na.

A sanyaye naji maganarsa….”Auntyna barka da rana.” Gabana ya yanke ya fad’i wayar ta kusa su’bcewa daga hannuna…..shuru nayi masa yace.”Ina fatan kin warware ko.”? nayi shuru ban tanka masa ba yayi d’an murmushi da fad’in “Kiyi hakuri sharrin shed’an ne ki gafarce ni dan Allah.”

Ajiyar zuciya na sauke na kashe wayar na ajiye gabadaya yanayi na ya sanja.

Hauwwa na driving ta kalleni da fad’in “Kawata ina fata dai lafiya.” da sauri nace”Lafiya mai kika gani.”?

Tana ‘kokarin magana ya sake kira kamar kada na dauka sai kawai na yanke shawarar dagawa sabida kada ta zargi wani abu.

Zazzafar ajiyar zuciyarsa naji a cikin kunnena kafin yace.”Ya maganar wacan ‘katon mutumin mai k’aton tumbi.” Yana nufin Alhaji Nura. Nace.”Khalid kada ka sake kiran waya ta kaji ko ba kaji ba.”?

Jin sanyayyar muryarta yasa shi sake sauke ajiyar zuciya ya lumshe idonsa yana sake gyara kwanciya ‘kasa-‘kasa yace.”Aunty Sa’ida idan kin janye maganar Alhaji Nura zan dawo gida idan kuma baki janye ba to ina mai tabbatar miki da cewa sai dai kuyi hakuri dani domin zanyi nisa kuma ba zan dawo ba.”

Nace.”Khalid ka tafi ‘karshen duniya kaji ko ba abinda ya dame ni bane aurena da Alhaji Nura yana nan yanda ka sani ranar Juma’a mai zuwa daurin aure.”

Ya fesar da wani zazzafan huci! ya mi’ke zaune gumi! na yanko masa yace.”Okey ina fata dai kin sheda masa cewa saura na zai samu domin duk na kwashe roman sai da ya samu sud’i.”

Da sauri na kashe wayar gabana na dukan uku-uku addua nake a zuciyata akan Allah yasa Hauwwa ba taji komai ba.

Kiran wayar ya sakeyi na dauka da sauri na kasheta gabadaya, Hauwwa tayi dariya da fad’in “Khalid kenan kice dai har yanzu bai hakura ba.”

Cikin basarwa nace” Hauwwa rabu da shashasha dan Allah idan ya gaji zai hakura.”

Tayi dariya da fad’in “Ni kam ina sha’awar yanda yake nuna miki so hakan yana burgeni wallahi.”

Nace.”Hauwwa ke kin fiye budurwar zuciya wallahi ina abun yake a gurin Khalid me ya iya a soyayya sam baya burge ni wallahi.”

Ta kalleni tana so ta gazgata maganata nace.”Kwarai kuwa Hauwwa soyayya sai babban mutum wanda yasan abinda yake amma irin wannan soyayya tasu Khalid ai shirme ce.”

Tace.”Ni kam a gani na Sa’ida soyayya duk soyayya ce babu babba babu yaro a cikin ta na tabbatar da cewa babu abinda Alhaji Nura zai nunawa Khalid d’an zamani ne sai dai ma ya nuna masa wani abun.”

Nace.”Hauwwa wai ko son yaron nan kike ne.” ? tasa dariya da fad’in “Ai abun so ne yaro ingarma namiji mai ‘kwazo ai wallahi ni idan na sameshi to bakina alaikum.”

Na dinga kallonta ina mamakin maganarta ita kuma sai kyalkyala dariya take tana ‘kara tabbatar min da gaskiyar maganarta…

*30&31*
Cikin wani irin yanayi na damuwa Salmanu ya shiga dakin ya same shi…..Ya ajiye fulas din abincin a gabansa da fadin”Abokina yane na ganka a cikin wani irin yanayi dubi yanda kake zabga gumi sai kace wanda yayi tsere.” Ajiyar zuciya ya sauke ido jawur yace.”Salmanu dole ne ma na bar garin kano domin mutukar ina zaune a cikinsa hankalina ba zai ta’ba kwanciya ba yanzu nan na kira aunty Sa’ida a waya ta farfad’a min maganar da take so akan wannan mutumin da zata aura Allah Salmanu yanda na tsani Alhaji Nura haka na tsani mutuwa ta idan ina ganinsa zan iya aikata mummunan abu akansa domin sosai nake kishin sa.”

Salmanu yace.”Dan Allah Khalid ka cire soyayya a cikin ranka kayi abinda yake gabanka wai shin me kake nema ne a gurin aunty Sa’ida bayan ka samu biyan bukatarka duk fa namijin da ya aureta a yanzu sauranka zai samu to meye na damuwa kuma ka cire soyayyarta a ranka ka fuskanci abinda yake gabanka.

“Salmanu bana jin zai ta’ba daina son aunty Sa’ida a cikin jini na yake ko yaya nayi motsi sai na jita a rai na ina yi mata so da kaunar da ban san iya adadinsa ba saboda haka ka daina wannan maganar bana tsammanin zan cire sonta a cikin raina.

Salmanu yace.” To ai aure za tayi bai kamata ka cigaba da bibiyarta ba dan Allah tunda dai ka samu abunda kake so a tare da ita to ka rabu da ita ta zauna da mijinta lafiya.

Murmushin takaici yayi yace.”Idan ni ne na auri mace babu budurci wallahi a daran ranar zan saketa to ina fatan hakan ta kasance a kanta Alhaji Nura ya koro ta gida a daran ranar da aka daura musu aure.”

A tsorace Salmanu yake kallonsa yace.”Khalid wace irin muguwar zuciya gareka wai shin kai baka kaunar zaman lafiya ne kake irin wannan mugwayen kalaman akan ‘yar uwarka gaskiya ba sonta kake ba domin duk wanda kake so ba zaka dinga yi masa mummunan fata irin wannan ba.”

‘Karamin tsaki yaja yace”Salmanu dan Allah maganar nan ta isa haka ni kadai ne nasan abinda yake cikin xuciyata sai kuma wanda ya hallice ni duk da na samu abinda nake so a tare da ita to ba zan daina bibiyar rayuwarta ba.”

Salmanu ya dinga girgiza kansa yana mamakin karfin halin abokin nasa.

Yace.”Kenan yanzu daka kira wayarta ba hakuri ka bata ba.”

Yace.”Ganin ina karyar da kaina gurin bata hakuri yasa ta samu damar fad’a min ba’kar magana wannan dalilin ne yasa ka shigo ka tarar dani a burkice Salmanu wai dan Allah dame Alhaji Nura fini da har zata dinga fifitashi a kaina.”

Salmanu yace.”Watakila kud’insa take so amma bayan haka babu macen da zata dubeka tace bata so Khalid kasan matan yanzu suna so su auri mai kudi ko dan su huta shiyasa kaji nace ka watsar da komai kazo muje mu nemi kudi ko dan mu huce takaici.

“Salmanu bana tsammanin aunty Sa’ida za tayi auran kudi kawai dai nine bata ra’ayi tunda tasha fad’a cewa ita ba zata auri yaro ba sai mai shekaru shin wai wane abu ne take nema da bukata a gurin Alhaji Nura wanda ni bani dashi na zauna nayi tunani sosai na kasa gane mai take hangowa a tattare da mutumin.”

Salmanu yace.”Son sa take shiyasa take ganin kowane namiji a bayansa yake saboda haka ni dai shawarar da zan baka shine ka tattara lamarinta ka watsa a kwandon shara ka fuskanci a binda yake gabanka.
Murmushin takaici kawai yayi yace.”Salmanu duk abinda zan fada maka a yanzu ba zaka gamsu ba saboda kai baka ta’ba soyayya ba sabida haka zanyi kokarin ganin na dauki shawararka amma inaso na sheda maka cewa ba zan ta’ba iya cire son aunty Sa’ida daga zuciyata ba.”

Salmanu yace.”To Allah yayi maka magani abokina.” ya amsa da ameeen yana goge fuskarsa da hankici Salmanu abincin ya zuba musu a plate cikin ikon Allah aka kawo wuta dama zafi ya ishesu sai kawai suka kunna fanka suka fara cin abincin suna tattauna yanda tafiyar tasu zata kasance.

Ina komawa gida na kunna waya ta saboda nasan Alhaji Nura zai iya kirana a cikin ko wane lokaci…..sai da nayi wanka tukkuna na zauna domin cin abinci Gwaggo tace.”Sa’ida yau ma sai hakuri domin dai tun safe Rabi tasa kafa ta fita daga gidan nan bayan fitar mijinta.

Nace.”Ba ayi abinci ba kenan.”? Tace.”Sauran taliyar ki na dauka na dafa gatanan a cikin fulas sai dai babu yaji dan nayi ta neman yaro ya siyo min barkono ban samu ba duk suna makaranta.

Nace.”Gwaggo taliya da man gyada ina laifin da manja.” Tace.”To nima dai har yanzu ban ci ba dan na tsani taliya ina jiran yara su dawo daga makaranta a siyo min d’an wake a gidansu Mamu.”

Nace.”Yau kuma d’an wake kike sha’awa.”‘? Tana cigaba da kad’i tace.Aikam kin san rai da marmari.” Girgiza kaina kawai nayi cikin zuciyata nace.”Gwaggo sar’ka kenan mai rikicin gangan.

Mikewa nayi zan fita tace.”Ina kuma zakije da ina so muyi wata magana mai muhimmanci.

Nace.”Zan duba almajiri ne ya siyo min kayan miya nayi miya dan ba zanci farar taliya da mai ulcer zata tayar min.

Tace.”Yawwa to tunda hakane nima na fasa siyan d’anwaken Allah yasa a samu almajirin.”

Ameen nace na fita daga dakin….daga cikin soron na tsaya ina le’kawa can na hango almajirai su uku hannu na daga musu gabad’ayansu suka ‘karaso inda nake na mikawa daya daga cikinsu dari biyu da fad’in “Dan Allah kayan miya zaku siyo min na duka.”

Da sauri suka ce to suka tafi ni kuma na koma cikin gidan

Tana zaune a inda take na nemi guri na zauna ina kallonta da fad’in ” Wace magana za muyi.”

Ta dago a nutse tace.”Ya jikin naki ina fatan gurin ya daina ciwo.” nace.”Eh alhamdulillahi.” Tace.”Masha Allah haka ake so.”

Dakin yayi shuru na minti biyar kafin tace.” Dazu bayan tafiyar ki makaranta Ina sauraran shirin *TAMBAYA MABUDIN ILIMI* wanda Malam *AMINU DAURAWA* yake gabatarwa a tashar freedom redio naji yana amsa wata tambaya da akayi masa akan budurwar da akayi mata fyad’e ko kuma karuwar da ta tuba ta dawo gida domin tayi tsarkakken aure shine yake cewa ba kai tsaye za’a daura aure ba sai mace tayi tsarki uku an tabbatar da cewa babu ciki a tare da ita sai a d’aura auran wannan shine daidai da abinda addinin musulunci ya tanada sai duk jikina yayi sanyi Sa’ida ina so kiyi tsarkakken aure gashi yau saura kwana biyar daurin auranki yanzu ya kike ganin za’ayi me zamu cewa da Alhaji Nura nasan dai shi yanzu ya gama shirye-shiryensa lokaci kawai yake jira yanzu ya kike ganin za’ayi.”?

Cikin wani irin yanayi nace.”Gwaggo wallahi nima ban san ya za’ayi ba gabad’aya na mance da hakan kinga Amfanin sauraran redio kenan da tuni an daura aure akan kwamacala.”

Tace.” To Sa’ida ai ita redio tamkar makaranta take domin babu abinda basa koyawa mutane wallahi sauraran redio yafi mutum ya kalli akwatin talabijin mutukar ba tashoshin addinin musulunci mutum zai kalla ba.”

Nace.”Hakane maganarki Gwaggo yanzu wace shawara za ‘a yanke.”? Tace.” Bari Babanki Iro ya dawo mu tattauna shima nasan hankalinsa ne ya dauke baiyi tunanin hakan ba nasan idan ya dawo yaji abinda yake da akwai dole a nemo mafita.”

Ajiyar zuciya na sauke nace”Gwaggo Allah yayi mana maganin masifa.” ta amsa da “ameen ‘yan nan.”

To kusan awa guda kenan da aiken da nayi wa almajirai shuru basu dawo ba, Nace”Gwaggo kinga awa guda almajiran nan basu kawo kayan miyan ba.

Tace.”Sa’ida Ai almajiran unguwar nan su zama abinda suka zama Allah yasa dai basu gudu da kudin ba domin sau nawa suka gudar min da kudi shiyasa kika ina zuwa nayi uzirina da kaina.

Girgiza kaina nayi nace.” Allah ya kyauta to.” tace”Sai dai fa kiyi hakuri ki bada wani kudin a siyo kayan miyan.” Nace.”Bani dasu tunda kin san yanzu dai a karshen wata muke ki siyo ai nasan kina da kudi.

Tace.”To bari na ‘karasa abinda nake sai naje na siyo.” Tana rufe baki naji alamar shigowar text wayata daukar wayar nayi ina dubawa, Khalid ne wai dan Allah yana so yayi magana da Gwaggo yanzu zai kira sai na bata wayar. takaici ya sani na kashe wayar gabadaya na ajiyeta.

‘Bangaransa kuwa hankalinsa ne ya tashi sosai lokacin daya kira wayar yaji ta a kashe ya kalli Salmanu a raunane yace.”Kaga ta kashe wayar gabadaya.” Salmanu yace.”Ka kira ta mahaifinka mana.” shiru yayi yana tunani kafin ya yanke hukuncin kiran mahaifin nasa.

Baba Iro yana kasuwa yaga kiran D’an nasa ‘kin daga wayar yayi har ta karaci ringing d’inta ta katse. Khalid sai da ya kira sau kusan biyar Kawu Ibrahim bai daga ba. sai ya yanke shawarar kiran ta mahaifiyarsa a lokacin ta dawo daga zauran Malam Sammani suna tattaunawa da mahaifiyarta Baito ganin Khalid din ke kiranta a waya sai farin ciki ya isheta hakika babu abinda za tace da malam sammani gashi tun kafin aje ko’ina aiki yayi kyau Khalid din ya kira wayarta.

Hannu na rawa ta dauki wayar tasa a kunnenta tana kiran sunansa.

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Ummatu ku gafarce ni.” sai kawai ta fashe da kuka da fadin.”Khalid kana ina ne? me yasa ka gudu bayan baka ka aikata ba nasan ni yaro na kamili ne ba zai aikata abinda ake zarginsa ba.

Yace.”Ummatu ni na aikata ba wani mahaluki ba wallahi nine.” sai hawaye suka ‘kwace mata tana rawar baki tace.”Khalid kaine fa kace.”

Yace.”Eh Ummatu tsautsayi da qaddara ne ku gafarce ni.” hannu tasa ta sharce gumin fuskarta tace.”To yanzu kana ina.”?

Yace.”Ummatu ina gidansu abokina a halin yanzu domin ina jin kunyar sake hada ido da gwaggo da Babana naci amanarsu na tozartasu a idon duniya dalilin da yasa kenan na yanke shawarar barin gari gabadaya.

Gabanta ne ya fad’i da sauri tace.”Khalid ba’a kan ka aka fara ba kuma ba za’a ‘kare a kanka ba saboda haka ka dawo gida shine kwanciyar hankalina.

“Ummatu kiyi hakuri ki gafarce ni ba zan dawo gida na zauna cikin takaici da damuwa ba ki yafe min kuma kiyi min fatan alkairi a duk inda nake.”
Yana gama maganar ya kashe wayar kansa na wani irin sarawa

Ummatu baki a sake take kallon mahaifiyarta Baito tace.”Wai me yake faruwa ne.”?

Bude baki tayi za tayi magana sai kuma kuka ya kufce mata!

baito hankali a tashe ta dinga tambayarta abunda ya faru Ummatu sai da taci kukunta ta koshi ta fada mata yanda sukayi da Khalid din.

Baito tace.”Amma nayi mamakin hakan saboda nasan aikin malam Sammanin kamar yankan wuka haka yake to me yasa wannan karon aikin yayi gardama.”

Ummatu tace.”Ni babban tashin hankalina ma katifa ta dana siyar gashi yaron nan yana tabbatar min da cewa ba zai dawo gida a wannan lokacin ba

Baito tace”Share hawayen ki ki daina kuka akwai malamai a gari saboda haka yanzu sauran kudin da suka rage a hannunki dasu zamuyi amfani zaki tashi yanzu muje mu nemi inda za’ayi aiki mai zafi akan yaron nan.”

Ummatu a sanyaye tace.”To shikkenan Baito Allah yasa a dace.” Baito ta amsa da cewa “Za’a dace da yardar Allah bari na shirya mu tafi.”
Mikewa tayi ta hau shiryawa suna sake tattauna maganar.

Sai daf da magariba suka gama yawace yawacen gurin malaman tun a hanya suka rabu da juna….Ummatu ana kiran sallah ta shigo gidan lokacin Gwaggo na zaune a kan kujera tana alwala sallama tayi Gwaggo ta kalleta kafafunta sunyi fururu! duk tayi firgai-firgai da ita! Gwaggo ta amsa sallamar da fad’in “Rabi daga ina kike haka kinyi fururu dake kamar an haqo ki daga rami.”

Ummatu shuru tayi bata tanka mata ba ta bude kofarta ta shige…Gwaggo ta bita da kallo tana girgiza kanta.

Ummatu abubuwan hannunta ta ajiye da sauri ta fito ta shiga kicin ta hura wuta ta dora tukunya ta fito a gurguje tayi alwala azahur la’asar magriba ta had’a a lokaci guda tana idar da sallar ta mike ta dauko kaskon wuta kicin ta shiga ta d’ebo garwashi da yawa tazo ta bude ledojin data shigo dasu wani magani ta dauko daure a leda ta kwance ai kafin kice kwabo ta rikice da atishawa maganin jajawur dashi kamar barkono tana zabga atishawar ta zuba maganin cikin wutar ta mike da saurin gaske ta fito babban tsakar gidan tasa a tsakiya ta tsaya kan maganin tana kiran sunan Khalid.

Gwaggo dake sallah atishawa da majina suka cika mata hanci hawaye kawai take a jigace! ta idar da sallar ni kuwa tunda na leqa tsakar gidan naga Ummatu a tsaye gaban kaskon sai kace soja na koma dakin na kwanta tare da toshe hancina daya cika da majina tsinkakkiya…..Tana idar da sallar ta hau sababi da fad’in “Wace irin jaraba kuma aka shigo mana da ita gida.” Zaune na mike ina kokarin hana ta fita ta fizge hannunta da fad’in “Ke sakar min hannu na fita naga jarabar da matar nan take.” Fita tayi daga dakin tana surutai….har yanzu Ummatu na tsaye a tsakiyar tsakar gidan da kaskon wuta a gabanta yana hayaki tana kiran sunan Khalid fuskarta tayi gaja-gaja da majina da gumi da hawaye sai nishi take tana sakin atishawa…..Gwaggo da sauri ta ‘karasa gurin tasa kafa tayi wurgi da kaskon wutar da fad’in “Rabi wane irin surkulle ne wannan……..!

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*33&34*
Ummatu da sauri ta d’aga kaskon dake cike da wutar ta gyarashi haya’kin ya cigaba da tashi a gurin tana me cigaba da kiran sunan Khalid a bayyane ………Gwaggo ta tsorata sosai da sauri ta bar gurin tana toshe hancinta dakin ta dawo ta same ni da tissue ina goge hanci gabad’aya majina ta tsinke min wannan wace irin jaraba ce…Hannuna ta kamo muka fito daga dakin har yanzu Ummatu na tsaye akan maganin tana aiki ita kanta sauri take ta gama kiran sunan Khalid din iya adadin da aka gindaya mata .

Kofar gida muka fita muka tsaitsaya muna mayar da numfashi..Gwaggo ta kalli cikin soron gidan tasa gefen hijabinta ta goge hawayen dake sauka a fuskarta tace.”Sa’ida kinga yanda haya’kin nan yake fitowa kuwa.”

Soron na le’ke na gani nace.”Gwaggo matsa daga gurin ki bashi hanya ya fice idan gidan ya sarara sai mu koma.

Kusa dani ta tsaya tana zazzare ido kafin tace.”Sa’ida kiga jaraba mutum da gidansa an koro shi waje kai gaskiya Rabi shaid’aniya ce wallahi tana azabtar damu.”

Nace.”Gwaggo addua zakiyi mata Allah ya shiryeta.” tace.”Sa’ida idan da Rabi zata shiryu da tuntuni ta shiryu kullum fa a tafe take to daga yau ta daina fita daga gida domin zan sa Ibrahim ya gindaya mata sharad’ai.”

Tana rufe bakinta Kawun ya karyo kwana nace”Alhamdulillahi gashinan ma.” Ajiyar zuciya ta sauke dukkaninmu muka tsira masa ido har ya karaso gurin.

Hankali a tashe yace.”Gwaggo lafiya na ganku da magariba a tsaye a waje.”

Da sauri tace.”Ibrahim ai gidan yafi karfin mu le’ka kaga abinda yake fitowa daga cikin gidan.

Le’ka kansa yayi soron ya hango haya’ki da sauri yace.”Subahanallahi Gwaggo ba dai wuta ce ta tashi a gidan ba.” Yana kokarin kutsa kansa gidan yake magana.

Gwaggo ta hana shi shiga da fadin”Oh o! ko d’aya Rabi ce take haya’ki a gidan ko na barkono ne oho! dan a jigace muka fito daga gidan.

Kawu ransa ya ‘baci sosai shi kam Allah ya jarrabeshi da fitinanniyar mata kafin Gwaggo tayi aune ya fad’a cikin gidan.

Lokacin da ya shiga gidan Ummatu ta gama aikin tana sunkuye gaban kaskon wutar tana karkad’eshi duk tayi wujiga wujiga fuskarta tayi jawur! d’ago kan da za tayi sai taga mijin nata a tsaye a kanta shima hawayen haya’kin na zuba a fuskarsa Kawu Iro bai damu ba saboda yasan dole yayi hawaye saboda zafin maganin da yake fitar da haya’kin.

A sanyaye take kallonsa tana share fuska yace.”Rabi wane irin haya’ki ne wannan kika turni’ke gida dashi saboda tsabar iskanci da wulakanci na dawo na tarar da mahaifiyata a waje a tsaye Rabi wai me yasa bakya ganin girman Gwaggo ne me tayi miki kika raina ta.”

Ummatu kuka ta fashe dashi tace.”Wallahi ni bance su fita daga gida ba da kansu suka fita dama nasan dole a k’ulla min sharri a gurinka.

Mari ya kwada mata yace.”Rabi kina nufin mahaifiyata ce za tayi miki sharri.” hannu da dafe da kumatu tace “Aa ni ba haka nake nufi ba. Yace.” To wannan azababben haya’kin na magani da menene.” ?

Tana kuka tace.”Kiranye Malam ya sani nayi wa Khalid saboda d’azu da Rana Ya kira ni a waya yake sheda min cewa shida gida har abadah. shine Baito tace na tashi muje ayi mana taimako akan al’amarin shine wani malami ya had’a min wannan maganin yace nasa a wuta na tsaya a kai na kira sunan Khalid in sau dari ba d’aya.”

Fuskarsa ta sanja da yanayi na ‘bacin rai yace.”Rabi yanzu akan yaron nan Khalid kike nema ki kauce hanya wane irin mushirikin malami ne wannan kikeje gurinsa da ya baki irin wannan hayakin.”?

Tana hawaye tace.” Kandala ‘Kawar Baito ce ta kaimu gurinsa a can cikin k’yauyen Janguza.”

A karaf a kunne gwaggo a lokacin da suke kokarin shiga gidan ita da Sa’ida.

Tace.”Umhum! kaji maganar Uwale ta fito ko Ibrahim.”? da sauri ya juya yana kallonta ta cigaba da cewa.” Ibrahim ba zan ta’ba mantawa ba kafin ka auri Rabi babu irin abinda ba a fada maka ba a kanta da mahaifiyarta amma ka rufe ido to yanzu ai sai ka gazgata maganar mutane tunda gashinan da bakinta tana fada maka cewa ita da mahaifiyarta sukeje Janguza gurin malami.

Kawu Iro jikinsa yayi sanyi tabbas hakane babu irin shawarwarin da ba’a bashi ba akan ya hakura da Rabi ya nemi wata ya rufe idonsa a lokacin saboda masifar son da yake mata ya aureta gashinan tana azbatar masa da mahaifiyarsa.

Yace.”Gwaggo dan Allah kiyi hakuri wallahi tuntuni na gazgata maganar mutane akan Rabi ba mutuniyar kirki bace.”

Tace.”Ai ni tuntuni magana ta wuce a gurina amma inaso na sanar da kai cewa Yau tsayin kwana biyar kenan Kullum matarka bata yini a gida haka take fita tana barin mu da yunwa ga kayan abincin Sa’ida ya kare muyi ta kame-kame! to sabida haka nake umartaka cewa ka hana ta zuwa ko’ina idan kuma ta’ki to ka gindaya mata sharadi cewa duk sanda ta sake fita a bakin auranta.

Ido jawur yake kallon Ummatu da tayi muzu-muzu a tsaye sabida tsabar zurga-zurga har ta rame yace.”Rabi ina kike zuwa babu izini na sannan kuma ina kike kai kudin cefanan da nake baki a kullum.”

Murya na rawa tace.”Wai shin ya za’ayi na zauna a gida na kwantar da hankalina rayuwar yaro na na cikin garari ai dole naje inda za’a taimaka min.”

Gwaggo tace.”Shiyasa kika dauki katifar dake shimfid’e a gadon ki kika siyar saboda kiyi yawon malamai.”

Da sauri Kawu Iro ya kalleta dan shi bai da labarin siyar da katifa tunda a dakinsa yake kwana sai da Ummatun ta kai kanta gurinsa.

Gwaggo tace.”Eh Ibrahim maganata gaskiya ce Kwana hudu da suka wuce Rabi ta siyarwa da Lantana katifar ta…..Kawu Iro kamar yayi kuka yace.”Rabi me na gaza dayi a gidana yunwa ko ishirwa.”? shuru tayi tana dauke kanta

Yace.” To bari kiji Rabi bani kika tozarta ba kanki kika tozarta kuma shi yaron da kike kashe kudi a kansa ko ya dawo ba zai zauna mana a gida ba sai dai ya nemi gurin zama yawon bin malamai kuma kada ki fasa kece a wahale sannan maganata ta karshe dake ita wallahi tallahi duk sanda kika sake fita daga gidan nan bada sani na ba a bakin auranki dan na gaji da wannan munanan d’abi’un naki.”

Ummatu tana kuka na fitar hankali ta shige gurin….Ya juyo cikin tausasawa yake rarrashin mahaifiyartasa Gwaggo tace.”Ibrahim kada ka damu kaji ko kaje kayi sallah nayi abinci kazo kaci mu tattauna muhimmiyar magana.”

Yace.”To shikkenan Gwaggo bari na shiga na daura alwala.” tace”To babu laifi.” Kawu Iro ya bude kofar gurinsu ya shiga ita kuma ta shigo dakin ta sameni a zaune a bakin tabarmar ta.

Zama tayi tana fad’in “Haba jama’a mata duk ta zame mana annoba a gida wallahi Sa’ida da Ibrahim yana da iko aure zan sa shi yayi domin kuwa sam bai dace da mace ta gari ba.”

Nace.”Gwaggo kema fa da laifinki kina shiga abin da babu ruwanki a gaskiyar magana Ummatu tana hakuri dake da halin ki shiyasa wani lokacin idan tana mayar miki da magana bana jin haushi sabida nasan ke kika janyo.”

Tace.”Sa’ida nifa ba zan ga ba daidai ba nayi shuru haka halina yake tunda can bana shuru kawai na zuba ido akan mutum yana abinda yake so ban gyara masa kuskuransa ba.”

Nace.”To Gwaggo kada dai kisa Kawu yayi wani aure a yanzu dan Allah ki kyaleshi yaji da d’aya idan ya ‘karo aure gidan nan sansanin ya’ki zai zama gaki ke kuma a gefe kina ‘kara ruru wutar al’amarin sabida haka ki kyautata zamanki da surukar ki shima Kawu Ibrahim sai yaji dadin tafiya neman sa.”

Tace.”To ai shikkenan Sa’ida tunda laifi na kike gani a kan na Rabi.” Nace.”Aa Gwaggo bance ke kadai kike da laifi kowa yana dashi.”

Shuru tayi bata tanka ba ta dauki redio tana murdawa. Kawu ya shigo dakin na gaisheshi a nutse ya amsa Gwaggo ta ajiye redion a kusa da ita bayan ta kama tashar da take so.

Abincin ta zuba masa tasa masa da yawa, yaci ya koshi yasha ruwa. tace.”Ka gani sai Rabi taci kayanta idan ta dafa dan Allah Ibrahim ko tayi maka tayi kada kaci ka nuna mata kuskuranta.”…….kallonta nayi ina mamakin ‘karfin halinta ko waye ya fad’a mata ana shiga tsakanin miji da mata oho.

Zamansa ya gyara da fad’in”Gwaggo kada ki damu ai sai na sake nuna mata kuskuranta idan na shiga gurin.” Tace.”Yauwa to ka tauna mata tsakuwa sosai.” yace.”Insha Allah Gwaggo ke nake saurare akan maganar da zamu tattauna.

Gyara zama tayi ta fuskance shi sosai tace.”Ibrahim akwai wani bayani dana saurara daga Malam Aminu Daurawa inda yake cewa…………….Bayani tayi masa sosai kamar a gabanta malam din yayi tambihin…Kawu Iro ya dago kansa a hankali yace.”Gwaggo wallahi ni kaina na sha’afa da wannan al’amari nasan tabbas hakane gaskiya malam ya fad’a akan wannan al’amarin kuma dole ne a dakata da daurin aure tukkuna aga abinda ubangiji ya lullube amma ni yanzu tunanin ta inda zan tunkari Alhaji Nura da maganar nake.”

Gwaggo tace.”Muma dai tun dazu muke wannan nazarin mutumin nan fa ya riga ya gama duk wani shirye-shiyen sa lokaci kawai yake jira idan anje masa da wata magana dole yayi zargin wani abu.

Kafin Kawu yace wani abu kira ya shigo waya ta Alhajin ne da sauri na fita daga dakin da wayar a kunnena.

Soro na tsaya muka gaisa kamar ko da yaushe kafin yace.”Sa’ida wasu harkoki ne na kasuwanci suka taso min a yanzu dama kuma tun watanni uku da suka wuce nake tsammanin gudanar da harkokin sai yanzu Allah ya bani iko sabida haka nake baki hakuri akan abinda zakiji na fada miki a yanzu.” a sanyaye nace.”Haba Alhaji ai babu komai ina sauraranka.”

Yace.”Yauwa ‘yar albarka inaso za’a d’aga daurin auran mu sai nan da wata uku ko hudu saboda a cikin satin nan nake so na tafi chana domin company da muke harkokin mu a tare suna bukatata a kusa wannan dalilin yasa nace bari na kira ki a waya na fada miki kafin nazo.” Ajiyar zuciya na sauke ina godewa Allah a raina babu shakka dukkanin abinda yake faruwa da ikon Allah ne.

Nace.”To babu komai Alhaji kada ka damu ai kamar yau ne kaje ka dawo insha Allahu ina zaman jiranka kuma inayi maka fatan alkairi da nasara a rayuwarka.”

cikin jin dadi ya amsa da ameeen Sa’ida insha Allahu a satin dana dawo za’a daura auran ki tare a dakin ki.” mirmushi nayi nace”To Alhaji Allah ya nuna mana lafiya.” Ya amsa da ameeen Gimbiya bari na barki ki huta ko insha Allahu gobe zan shigo da wuri muyi sallama.”

Nace.”To shikkenan sai kazo din a gaishe min da yarana.” ya amsa da fadin”Zasuji da kyau insha Allah.” sallama mukayi da juna na kashe wayar na koma cikin gidan.

Cikin nutsuwa na nemi guri na zauna ina kallonsu duk sun shiga yanayi na damuwa nace.”Gwaggo ku kwantar da hankalin ku Allah ya kawo mana mafita domin kuwa yanzu muka gama waya da Alhaji Nuran yake sheda min cewa tafiya ta taso masa zuwa chana sabida haka za’a daga daurin aure sai bayan ya dawo wata uku zaiyi a can ko hud’u insha Allahu yace cikin satin da ya dawo sai a daura auran.

Gwaggo tace.”Kai alhamdulilahi amma naji dadin wannan magana wallahi dama bayan fitar ki muna ta tararrabin yanda za’ayi a tunkareshi da maganar sai gashi cikin sauki Allah ya kawo mana mafita.”

Kawu yace.”amma kuma kamata yayi yazo ya same ni mu tattauna maganar a tsakaninmu.

Nace.”Eh hakan yace insha Allahu gobe zai zo kuyi maganar.” Gwaggo tace.”To kaga shikkenan sai ka jira zuwansa kada ka fita kuma kuyi sa’bani.”

Yace.”Insha Allahu zan zauna nayi jiran zuwan nasa. Mi’kewa yayi da fad’in zai fita ya sha iska a waje.” Gwaggo tace.”Haba ai zafin ya isa muma yau kwanciyar tsakar gida zamuyi ai.” Kawu yana kokarin saka takalmansa yace.”Hakan yayi gwaggo ke Sa’ida sai ki fito ki dan gyara muku inda zaku kwanta din.” Nace.”To shikkenan.” mikewa nayi na fito tsakar gidan domin na gyara mana inda zamu kwanta.

To kamar yanda dai Alhaji Nura yayi alias a run zuwa gurin Kawu su tattauna maganar haka din ne ya kasance domin Kawu a daran ranar ya kira wayar Alhaji Shamsu mijin mahaifiyata ya sheda masa dukkanin abinda yake da akwai Alhaji Shamsu yace babu damuwa insha Allahu zai fito da wuri ayi zaman dashi.

Sun tattauna abinda ya dace a tsakaninsu tinda dukkaninsu ba yara bane sun san harkokin kasuwanci mussaman Alhaji Shamsu shi ya ‘kara karfafawa Alhaji Nura gwiwa akan tafiyar tasa amma kuma sai yace mai zai hana kawai a daura auran idan yaso in ya dawo sai ayi maganar tarewa.

Lokacin da yayi wannan maganar Kawu Iro hankalinsa ne ya tashi yayi shuru yana sauraran yaji amsar da zai bashi Alhaji Nuran yace yafi so ayi komai a lokacin da yake nan.” Alhaji Shamsun yace to shikkenan babu damuwa Allah yasa hakan shi yafi alkairi.”

Dukkaninsu suka amsa da ameen ya Allah .” suka rabu cikin mutumci da girmama junansu.

****
*Bayan sati biyu*
Khalid da Salmanu mota suka bi da kayansu da kuma guzirin su domin zuwa Lego’s dan su nemi aikin yi su kuma cigaba da gudanar da harkokinsu na buga kwallo a cewarsu duk inda ta fad’i sha ne, Salmanu lafiya lau suka rabu da mahaifiyarsa da da sauran ‘yan uwansa shi kuwa Khalid babu sa albarka uwa da uba ya d’auki irin wannan tafiya aikuwa cikin dare suna tsakiyar titi motarsu na sharara gudu *da’u fataken dare!* (‘Yan fashi) suka tare musu mota yana ganin haka yayi saurin bude wayarsa ya cire sim card dinsa yasa a bakinsa ya danne a kasan harshen sa……’Yan fashin suka dinga sakin harbi! ta ko’ina suka sanya dik wa’inda suke motar mata da maza suka fito suka kwanta a tsakiyar titi duk motar da ta karaso gurin sai sun tsayar da ita sun fito da mutanan ciki…..Daya bayan d’aya suka dinga binsu suna kar’be musu wayoyinsu wa’inda sukayi gardama a cikinsu suyi musu dukan mutuwa ganin haka yasa mutane suka tsorata domin tsira da ransu da lafiyarsu suka dinga mika musu wayoyinsu da jakkunan kayansu da guzurinsu.

Sai da suka kwace musu komai suka loda cikin motocinsu sannan suka dawo gurin da suke kwance suna haskasu………Babban cikinsu ya tsuguna kusa da wata mata ta rungume d’anta sai kuka take ta hada uban gumi jikinta sai karkawa yake.

Fuskarta ya haska sosai yake ‘karewa jikinta kallo ya sauke ajiyar zuciya ganin akwai mamora a jikinta yasa ya kira daya daga cikin ‘yan uwansa ya nuna masa ita da fad’in “Zamuje da ita mu biya bukatarmu.”

Matar ta fashe da kuka tana waiwayen bayanta mijinta take nema can ta hangoshi ya rarrafo gurin cikin fitar hayyaci yace.”Oga dan Allah kada kuyi mata wani mummunan abu ni ne mijinta tunda dai kun samu abunda kuke bukata shikkenan.”

Wani wawan mari ya kwad’a masa a take hancinsa ya fashe da Jini yasa kan bindigar dake hannunsa ya dinga dukan kansa da mugun karfi har sai da yaga galabaitar dashi tukkuna ya kyaleshi ya fad’i a gurin jina jina dashi! matarsa da ‘yarsa sai kuka suke a kansa………Fizgo hannunta yayi ya hau janta a k’asa ta dinga ihu tana fad’in “Ku taimaka min kada ku bari ayi zina dani.” ‘Kwakkwaran motsi babu wanda yayi a gurin mijin nata ya rarrafa ya mike domin ceton matarsa dan fashin ya kai masa wawan duka ya fadi a gurin a sume.

Khalid yayi shahada ya mike da saurin gaske yace.”Kai bawan Allah kaji tsoron Allah kuji tsoron ranar had’uwa dashi shin wai baka san matar aure ce ba kada kuyi zina da ita da nauyin aure a kanta Allah ba zai barku ba.

A sukwane! sukayo kansa dukkaninsu! Salmanu ya shiga tsananin tashin hankali ya dinga jan hannun Khalid din wai ya tsuguna ya basu hakuri Khalid ko gezau beyi ba yana tsaye suka karaso gurin babban cikinsu ya daga hannunsa zai kwada masa mari Khalid da sauri ya rike hannun…….Cike da mamaki jama’ar gurin suke kallonsa. Kafin kiftawar ido yaji saukar wani mugun duka a tsakiyar kansa…ihu! ya kurma yayin da lokaci guda yaji wani dummmm! a kunnesa tangad’i ya farayi Salmanu ya mike a zabure! yayi nufin rikeshi Danfashin da yake bayansa ya bangajeshi ya fad’i! ‘katon dutsen dake hannunsa ya sake bugawa Khalid a kansa a take ya fad’i a gurin ya suma gefen kansa ya fashe sai zubar da jini yake……..Fitilolinsu suka kashe gurin yayi duhu! dumd’um! suka ja matar nan tana kurma ihu! suka sanyata a motarsu suka tafi da ita…..

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*35&36*
Cikin tsananin tashin hankali Salmanu ya nufi inda Khalid ke kwance ya tarairayoshi jikinsa yana kiran sunansa, Jama’ar dake gurin suka rufo kansu gurin ya hargitse da kace nace kowa yana fadar albarkacin bakinsa akan abinda ya faru Salmanu shi dai babban damuwarsa abokinsa ya farfado! direban motar ne ya karaso gurin hannunsa rike da jarkar ruwa ya bude da saurin gaske ya shiga tuttulawa khalid ruwan a jikinsa, yana gamawa dashi da sauri ya karasa inda mijin matar nan yake a kwance shima ya daga jakar ruwan ya kwara masa a jikinsa cikin ikon Allah gabad’ayansu suka farfad’o cikin jigata Khalid ya dinga kiran sunan Allah yana jin yanda kansa ke wani irin sarawa! hannu yasa saman goshinsa ya shafo jini Salmanu yace.”Sannu Khalid ai ka auna arziki.” kallonsa kawai yayi ya juya yana kallon jama’a dake gurin suna surutai da hayaniyar kowa sai gyara jakar kayansa yake Yace.”Salmanu ina matar nan take bana so su cutar da ita.”

Salmanu yace .”Sai dai hakuri ai sun tafi da ita.”

Kansa ya dafe yana kiran sunan Allah! Ihu! mai karfi sukaji da sauri ya dago kansa mijin matar nan ne yake kurma ihu mutane na rirrikeshi wai sai ya tafi neman matarsa jamaa sun hana shi ga ‘yarsa sai sandara ihu take itama.

Khalid cikin karfin hali ya mike Salmanu yace.”Ina zakaje Khalid kai ma fa kana bukatar taimako.

Yace.”Salmanu mutumin can ya bani tausayi zanje na rarrashe ne.”

Kafin Salmanun yayi magana ya bar gurin Salmanu yabi bayansa zuwa inda mutumin ke zaune jamaa sun kewaye shi suna bashi hakuri.

Khalid ya dafa kafad’arsa ya dinga rarrashin sa kancewa yayi hakuri ya barwa Allah insha Allahu Allah ba zai basu nasara akan matarsa ba…..Yana kuka yace.”Matata ciki ne da ita d’an wata uku gashi bata da cikakkiyar lafiya mahaifiyarta na Lego’s ta matsa min da cewa tana so taje ta gaisheta hakika dana san wannan tsautsayin zamu hadu dashi to da ban amince da tafiyar nan ba.

Khalid yace.”Kayi hakuri abokina dukkanin abinda kaga ya faru da kai da matarka rubutacce:ne daga Allah kayi mata addua kawai akan Allah ya ku’btar da ita.

Kansa ya sunkuyar kasa hawaye masu zafin gaske suna zubo masa hakika yana son matarsa so mai tsanani yana jin tsoron ‘yan fashin nan su haike mata su kasheta da wahala.

A firgice ta tashi zaune tana rarraba idanuwanta a dakin kafin ta fara lalube kan shimfid’arta salati takeyi a zuciyarta tana kiran sunan Allah.

Fitilar ta ta kunna dakin yayi haske jiki a sanyaye ta mike ta dauki buta ta fita bandaki ta shiga ta kama ruwa ta fito garin yayi tsit Allah yana saukar da ikonsa.

Alwala ta d’aura ta shiga dakin ta gyara dadduma ta tayar da sallah.

Nafila tayi raka’a biyu tayi sallama sai ta daga hannunta sama hawaye ya ‘kwace mata tana kuka take fad’in “Ya Ubangiji Allah ka karkato da hankalin yaron nan gida Allah ka yafe masa kada ka d’ora masa mummunar kaddara Allah Khalidu mai laifi ne a gurinka Allah ka sassauta masa Allah kada ka jarrabe mu da abinda ba zamu iya ba.” Kuka ne yaci k’arfinta hannuwanta a sama ta kasa saukewa.

A tsorace na mike zaune ina kallonta gabana na faduwa nace”Gwaggo lafiya meye kike kuka me ya faru.”?

Adduar ta shafa a fuskarta murya a dushe tace.”Sa’ida dan Allah da Annabi ki yafe wa Khalid abinda yayi miki kaddara ce ki yafewa dan uwanki ko ya samu sassauci.

A sanyaye nace.”Gwaggo me ya faru dashi.?

Tana rawar murya tace.”Mummunan mafarki nayi dashi Sa’ida amma kafin na farka daga baccin na manta ni dai nasan na ganshi cikin mawuyacin hali jina jina da jini.

Gabana ya fad’i! nace.”Gwaggo mafarki ba gaskiya bane ki daina gazgazata shi.” Girgiza kanta tayi tace.”Sa’ida ni bazan kira kaina waliyyiya ba ba kuma zan kira kaina ‘yar baiwa ba amma Allah yakan nuna min abu a mafarkina mai dadi ko mara dadi kuma mafarkin yakan zama gaskiya ko mutuwa za’ayi Allah yakan nuna min a mafarkina shiyasa hankalina ya tashi da yin wannan mummunan mafarkin.

Shuru nayi har yanzu kuma ban daina jin faduwar gaba. ta cigaba da cewa “Dan Allah kice kin yafe masa ko ya samu sassauci.” A sanyaye nace”Gwaggo tuntuni na yafe masa ki kwantar da hankalin ki.”

Tace.”To nagode sosai Allah yayi miki albarka na amsa da ameeen ya rabbi.

Kasa komawa bacci mukayi har asubah tayi mukayi sallah muna idarwa tace lallai wai sai na kira mata shi a waya, to nima nawa ‘bangaran jikina yayi sanyi da al’amarin ban yi mata musu ba na kunna wayata na fara laluben number sa.

Na kira sau kusan biyar bata shiga, nace”Gwaggo kin dai ji da kunnanki wayar taki shiga ko.”

A sanyaye tace.”Watak’ila sun kashe shi.” naji gabana ya yanke ya fad’i!

Kallonta nayi hawaye na kwarara a fuskarta tace.”Sa’ida na d’an tuno mafarkin ganin sa nayi wasu mutane masu baka’ken kaya sun zagaye shi da bundigogi a hannunsu suna ta dukansa.”

Nace”Gwaggo ki samu nutsuwa dan Allah in sha Allahu Khalid na raye cikin koshin lafiya.”

“Kayya! Sa’ida bana tsammanin yaron nan nada rai.” nace” Bari gari ya waye sai a sake kiran wayar tashi.”

Tace.”to shikkenan.” tagumi! ta zabga har yanzu hawaye take cikin zuciyata nace ko wane irin so da kauna take masa…..Nace”Gwaggo yau ba zaki kunna redio ba.”?

Kanta ta girgiza min na dauki redion na kunna mata na ajiye mata kusa da ita.

Dauka tayi tana kokarin kashewa tace.”Sa’ida rabu dani nayi salati a zuciyata yau bana sha’awar jin redio nafi bukatar na samu nutsuwar zuciya nayi wa yaron nan addua.

Nace”Hakane Allah ya kare shi.” ta amsa da ameeen ya rabbi.” Mikewa nayi na fita tsakar gida domin d’ora ruwan wanka, sai naji motsin fitowarta na jiyo ina kallonta naga tana sa takalmanta da kudi a hannunta.

Nace”Ina kuma zakije da sassafe haka” Tace.”Zanje gidan Marka mai waina na siya domin nayi wa almajirai sadaka.”

Shuru nai ina kallonta har ta fita daga gidan na girgiza kaina tare da cigaba da abinda nake.

Har nayi wanka na fito nasa kaya na Gwaggo bata dawo gidan ba, na zauna cikin damuwa na dauki mai ina shafawa a jikina Kawu Iro ya daga labulan dakin, da sauri na gaisheshi ya amsa cikin kulawa yana fad’in “Gwaggo tana bandaki ne.”?

Nace.” Aa ta d’an jima da fita wai taje gidan Marka siyo wainar gero.”

Yana kokarin magana ta shigo gidan. Kawu Iro Kallo guda yayi wa mahaifiyar tasa jikinsa ya mutu ganin yanda ta zabge idunuwanta sunyi fululu.

Yace.”Gwaggo lafiya me yake faruwa.”? Hawaye suka ‘kwace mata tace.”Ibrahim babu lafiya domin kuwa Jiya a zaune na kwana tunda nayi mummunan mafarki da yaron nan Khalid na kasa rintsawa.

Yace.”Gwaggo dan Allah ki cire damuwar Khalid daga cikin ranki kada ki janyo wa kanki ciwo mai tsanani.

Tace.”Ibrahim idan kaga na cire Khalid a raina to mutuwa nayi amma ba zan ta’ba daina damuwa dashi ba.”

Tana gama maganarta ta wuce gurin Ummatu.

Ummatu na tsaka da dama kunu ta ganta ta shigo kicin din, gabanta ya fadi! tunda suke a gidan sai ta irga iya adadin shigowarta gurinta bai fi uku ko hudu ba Allah dai yasa ba wata masifar bace.

“Gwaggo ina kwana.”? tafada babu cikakkiyar sakewa.

Gwaggo cikin kulawa ta amsa da fadin” Rabi gurin ki nazo.” Ummatu ta saki ludayin da take dama kunu dashi tana kallonta .

Gwaggo ta ‘kas’kantar da kanta da fad’in “Dan Allah Rabi’atu ki gafarci yaron nan kiyi hakuri ki masa addua Akan Allah ya sassauta masa domin jiya ni nasan mummunan halin dana ganshi a mafarkina.

Ummatu jikinta yayi sanyi tace.” Gwaggo dama ai ni ban ‘kullaci Khalid ba tunda dama ban yarda da zargin da kuke masa ba.

Tace.”To hakane to amma dan Allah ki dage dayi masa addua saboda bakin uwa albarka gare shi ki daina zuwa kina asarar kudin ki a banza addua zaki masa da kyakykyawan fata.”

Ummatu tace.”To shikkenan Gwaggo insha Allahu zan cigaba dayi masa addua.

Tace.”Bari na tsaya na tafi da kunun tunda naga kin gama damawa.” Ummatu tace.”Aa Gwaggo kije kawai zan kawo muku.” Gwaggo ‘kin tafiya tayi har sai da Ummatu ta zuba musu kunun a jug ta zuba musu awara mai yawa a silba Gwaggo ta dinga shi mata albarka kamar basu ta’ba samun sa’bani da juna ba Ummatu ta dinga mamakin al’amarin domin tunda suke da Gwaggon bata ta’ba kwantar mata da kai irin yau ba gashi har da ya sanya mata albarka gaskiya dole al’amarin ya bata mamaki.

‘Dakin ta shigo ta same ni na gama shiryawa tace.”Sa’ida ga kunu nan da zafin sa ki zauna kisha kafin ki tafi.”

Da mamaki! a tare dani nake kallonta kafin nace.”Yau da kanki kika kar’bo kunun.”? Tace.”Eh gani nayi ta gama damawa shiyasa na tsaya na tawo dashi.

Shuru nayi na samu cup na tsiyayi kad’an a warar ma uku na dauka na zauna ina kur’ba, tace”Ki sake kiran wayar tasa mana.

Ba tare dana ce komai ba na dauki wayar na shiga duba number tashi….Kamar dazu wayar ta katse ta’ki shiga.

Nace.”Gwaggo sai dai kiyi hakuri fa domin wayar nan ta’ki shiga.kallona take nace.” Dan Allah ki daina wannan kukan Gwaggo mutuwa dai ake Jin tsoro idan Kwanan sa ne ya ‘kare Allah ya jikansa.

Tace.”Sa’ida amma baki da tausayi da imani yanzu sai kiso Khalid ya mutu a wani guri ai idan ma lokacinsa ne yazo nafi bukatar ya mutu a gabana hankali na sai yafi kwanciya idan naga gawarsa.

Nace.”Yanzu ma idan mutuwar yayi kina zaune labari zai same ki kuma za’a kawo miki gawar sa har gida.

Ta dinga kuka tana watsa min harara, dariya na kunshe a gurguje na gama abinda nake nayi mata sallama uffan ba tace min ba har na fita daga gidan.

Sai da gari ya waye tukkuna suka samu damar komawa cikin motar kowa ya zauna a gurin zamansa jikinsu duk yayi sanyi da irin ‘barnar da ‘yan fashi sukayi musu Khalid baiji takaici sosai ba saboda yasan ya tsira da sim card dinsa da ‘yan tufafinsa amma duk guzurin kudin da Sukayi shi da Salmanu ‘Yan fashin nan sun hargitsa musu kaya sun kwashe a yanzu ko sun sauka a garin na legos sai Sunyi fafutuka tukkuna.

Motar tayi shuru kowa na sake-sake a cikin ransa yayin da direben ke ta sharara guda akan kwalta, tun kafin su karasa inda matar take kwance a gefen titi Mijin nata yake ihu! da fadin”Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un gatacan a kwance sun kasheta.”

Direban suna karasawa inda take ya fara kokarin parking ko kafin ya ‘karasa mutumin ya fit ya fito a take ya gangara k’asan wani rami mai Mugun zurfi! gaske.

Hankalin su Khalid ya tashi mutuka hakika tunda yake bai ta’ba ganin masifa da tashin hankali irin na yau ba wannan mugun ramin da mutumin ya fad’a ciki ai sai dai wani kuma, wasu suka nufi inda matar take kwance wasu kuma Sukayi dafifi! a bakin ramin da mutumin ke ciki sai salati suke suna tunanin ita ina zasu taimakeshi.

Khalid yayi masifar tsorata da ganin matar da babu rai a tare da ita har ta fara kumbura ga jini duk ya bushe a jikinta kud’aje da ‘kwarika sai bin jikinta sukeyi…….Yarinyar ta na gani uwarta sai ta tsandara ihu!! ta shiga tsakanin mutanan tana so taje inda take…Khalid yayi gaggawar daukarta yana rarrashin ta hawayen tausayi na nema ya kufce masa..

Da yake sun shiga cikin gari yasa basu sha wata wahala ba mazauna gurin suka kawo musu dauki ‘yan agaji suka shiga cikin ramin suka fito da mutumin a mace duk ya karkarye, da yawa daga cikin mutanan gurin sai da suka tsorata da wannan tashin hankali masu rauni a ciki suka dinga faduwa suna suma wasu kuwa gefe suke nema su zauna suyi ta share hawaye suna kad’aita Allah shi d’aya.

Khalid wata irin nadama mai tsanani ta rufe shi ya dinga jin kamar ya juya ya koma gida ya nemi gafarar iyayensa da wacce ya zalin ta yanzu idan da ‘karar kwana da tuni shima ya zama tarihi ya mutu da fushin iyaye a tare dashi.

Jakar mutumin aka duba akayi sa’ar samun wallet dinsa nan Suka shiga binkicen in da yake a jikin IDcard d’insa aka samu cikakken address dinsa da inda yake aiki. Mutumin dai dan kano ne kuma yana aiki asibitin Koroda dake karkashin gomnati. ba tare da ‘bata lokaci ba jami’an tsaron dake gurin suka shiga aikinsu Gawarwakin aka d’aure suka sa a mota suka dauki hanya Khalid ya dinga jin kamar ya tsayar dasu ya bisu ya koma gida suna tsaye a gurin har motar Police din ta ‘bacewa ganinsu kafin su koma cikin motar ko wanne da mataccan jiki motar tayi tsit! shima direban duk da ya saba ganin tashin hankali irin wannan amma gaskiya wannan karon ya firgita mutuka jiki a mace ya shiga ya zauna ya kunna motar suka bar gurin…
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_

*37&38*
Khalid da Salmanu sun sha matukar wahala kafin wani bayerabe ya tausaya musu ya basu gurin kwana a jikin gidansa, tunda suka sauka a garin suke buge-buge a kasuwanni domin su samu abinda zasu ci idan dare yayi su shiga ‘kar’kashin gada su kwanta asuba nayi suke futowa daga karkashin gadar suyi sallah su shiga buge-buge kamar yanda suka saba Akande beyerabe ne kullum yana ganinsu a kasuwa suna bulayi da daukar dako sai ya tausaya musu ya dinga jansu a jikinsa yana nuna musu gurin da zasu shiga su samu aiki cikin ikon Allah kuwa suka kutsa cikin kasuwar su shiga cikin kanikawa masu gyaran abubuwan hawa suka fara taimaka musu da yake duk yawanci masu aiki a gurin ‘yan jahar kano ne shiyasa suka saki jikinsu dasu suka basu gurin zama suna nuna musu yanda zasuyi sati hudu sun zama ‘yan gari domin gyaran mota kona babur babu wanda basu iya ba.
Idan sun tashi daga aiki sai su nufi shagon da suke kwana wanda yake jikin gidan Akande, watansu biyu a legos suka siyi waya Khalid yasa Sim card dinsa a wayar shi kuwa Salmanu sai da ya siyi wani akai masa rigistar Allah yasa yana da number wayar mahaifiyarsa saboda haka kai tsaye ita ya fara kira.

Khalid kuwa babu wanda yayi tunanin kira sai aunty shi domin kullum da ita yake kwana a cikin ransa zuciyarsa na fada masa cewa ta riga tayi auranta fa sai dai ka hakura duk sanda zuciyarsa tayi masa wannan tunin yini yake cikin damuwa da bakin kishi.

Muna tare da Hauwwa a gidanta mai lalle nayi min na biki kiran wayar tashi ya shigo waya ta a lokacin da naga sunansa yana yawo a fuskar waya ta sai da na zabura! mai lallen tayi saurin rike kafata nace.”Dan saurara na amsa waya.

Kafata ta saki na kalli Hauwwa a sanyaye nace.”Khalid ne.”? Baki ta bude da sauri tace.”Ikon Allah dama yana raye a duniya.?

Hannu na daga mata nasa wayar a kunnena.

sanyayyar ajiyar zuciyarsa naji a kunnena kafin naji sautin muryarsa yana kiran sunana.

Na amsa a nutse da fad’in “Khalid tsayin wattanin hudu kana ina ne? shin kasan halin damuwar ka jefe iyayen ka a ciki kuwa? Uwa uba Gwaggo na nan ta’ki lafiya kullum sai tayi kuka kafin ta kwanta bacci tana ganin kamar baka raye a duniya dan Allah ka dawo gida ni idan saboda ni ka tafi to ka dawo na yafe maka.”

A sanyaye yace.” Aunty Sa’ida idan na dawo gida zaki aure ni.”? Gabana ya fad’i nace.”Khalid ashe har yau baka daina wannan tatsuniyar ba.”?

Ransa ya ‘baci yace.”Ki daina kiran soyayyata da ta tsuniya insha Allahu sai ta zama gaske.”

Nace.”Okey to naji yanzu dai yaushe zaka dawo gida.”? Yace.”Kina so na dawo ne.”? Nace.”Eh ka dawo ka nemi afuwar iyayenka ni kuma na yafe maka.”

Yace.”Aunt Sa’ida idan na dawo gida zan takura miki fa.” Nace.”Khalid na amince zan aureka ka dawo gida.”

Da sauri yace.”Da gaske kike.”? Ajiyar zuciya na sauke cikin yaudara nace “Eh da gaske nake kana dawowa za’a daura aure.”

Yana dariyar farin ciki yace.”Okey ki bani Gwaggo mu gaisa insha Allahu zan dawo gida a satin nan.

Nace.”To yanzu dai bana gida ina gidan ‘kawata Hauwwa insha Allahu idan na koma gida zan kira ka sai ku gaisa.”

Yace.”Nagode auntyna insha Allahu zakiyi alfaharin aurena zan jiyar dake dadin duniya auntyna zan kula dake zan zama bawanki zan kwanta ki taka ni zan zama d’an aiken ki zan……Katse shi nayi nace.”To duk naji na kuma gamsu da maganarka Ka bari idan ka dawo sai ka ‘karasa.

Yar dariya yayi yace.”Okey to shikkenan zan kira anjima idan kin koma gida.” Ina kokarin kashe wayar nace”babu damuwa.

Hauwwa ta zuba min ido tana kallona tace.”Sa’ida babu kyau yaudara fa ban so kikayi masa haka ba ya za’ayi kice zaki aureshi bayan kin san gobe daurin auranki.”?

A sanyaye nace.”Hauwwa ni nasan halin Khalid idan ba haka nai masa ba wallahi ba zai dawo ba ga Gwaggo taki kwantar da hankalinta dan har fargaba nake na tafi na barta cikin halin damuwa kullum da daddare sai na lalla’bata take bacci.’

Hauwwa tace.”To yanzu idan yazo ya tarar kinyi aure fa wane hali kike so ya shiga.”?

Kai tsaye nace.”Sai yayi hakuri ya kaddara cewa ni d’in ba matarsa bace.”

Hauwwa tace.” A gaskiya da kamar wuya ya iya wannan hakurin dan yaron yana miki mahaukacin so.” Nace.”To hauwwa idan ba zai yi hakuri ba sai yayi abinda zaiyi.” ta bini da kallon mamaki! na Kalli mai kunshin nace.”Baiwar Allah ki cigaba.” Ta kama kafata da sauri ta cigaba da akinta.

Khalid cike da farin ciki yake shedawa abokinsa Salmanu abinda ke faruwa. Salmanu na washe baki yace.”Kai amma naji dadi wallahi to yanzu ya za’ayi naji kace a cikin wannan satin zaka tafi kuma gashi zamu fara buga wasa a Club kasan kana da mutukar mahimmanci a ‘kungiyar nan ko zaka bari mu gama wasan in yaso wani satin sai ka tafi.”

Girgixa kansa yayi yace.”Salmanu hankalina gabadaya yayi gida wallahi kafin na tafi zan nemi shugaban kungiyar na fada masa uziri na idan za’a d’aga wasan nan da sati uku sai ayi min uziri idan kuma yana ganin da akwai wanda zai kawo a madadi na sai ya kawo dan gaskiya babu abinda zai hana ni tafiya gida.

Salmanu jikinsa yayi sanyi sam baya so abokin nasa ya tafi yana ganin kamar damar da suka samu zata iya kufcewa gashi ogan nasu kullum sukaje training yakan fad’a musu cewa yana so su mayar da hankali sosai domin a wannan karon ne yake so ya za’bi za’kwa’kurai a cikinsu da zasuje america su buga wasa to
wannan dalilin yasa gabad’aya Salmanu baya so a bokin nasa ya tafi domin jikinsa na bashi kamar zasu samu nasara.

Khalid yace.”Tashi ma muje chamber d’in Allah yasa mu sameshi.” Salmanu ya mike yana kokarin cire kayan jikinsa ya sanja wasu.

Sun ci sa’a sun sameshi yana horar da wasu suka samu kujeru suka zauna bayan sun gaisa….Oga Labaran yace.”Khalid me yasa yau baku shigo da wuri ba.”?

Yace.”Wallahi oga mun je gurin aiki ne kasan dama sai da mukayi maka bayani cewa asabar da lahadi ba zamu dinga zuwa da wuri ba saboda muna zuwa gurin aiki da wuri.

Oga Labaran yace.”Eh hakane na manta da wannan bayanin dama inaso kuzo mu tattauna ina fata dai kuna cigaba da shirye-shirye kamar dai yanda na fada muku cewa Mr William zai zo a ranar da zamu buga wasa na k’arshe kuma a ranar za’a za’bi muzakkarai a cikinku domin kuje ku fatata da ‘yan wasan dake can america.

Khalid yace.”Oga sai da ni ayi min uziri wallahi cikin satin nan nake so naje ganin gida.”

Oga Labaran da sauri ya kalleshi cikin yanayi na damuwa yace.”Khalid me yasa zakayi mana haka? kana fa d’aya daga cikin ‘yan wasan da nake alfahari dasu, ka iya buga ‘kwallo sosai shiyasa nake so kai ka zama zakaran gwajin dafi nasan ko munje america ba zaka bani kunya ba sai kuma kazo min da wannan maganar.””

Yace.”Oga wallahi uziri babba ne zai kai ni gida ayi min alfarma.” Oga Labaran ya girgixa kansa da fad’in “Khalid dole fa kayi hakuri domin ba zaka sa nayi asara ba ka bari muyi wasan nan mu gama lafiya a za’bi wanda suka dace ayi dasu in yaso sai ka tafi kafin lokacin tafiya american ya tashi.”

Khalid yayi shuru tare da sunkuyar da kansa tunani yake akan lamarin…..Yana son aunty Sa’ida baya so ta kufce masa gefe guda kuma ga wata babbar dama ta same shi wacce yake saka ran samun nasara wai shin ya zaiyi ne?

Oga Labaran ya kalleshi da fad’in “Khalid kayi shuru kada fa ka bani kunya khalid.”

Ya dago kansa da fad’in “Oga zanyi nazari akan al’amarin insha Allahu kafin lokacin zan yanke shawara.” Yace.”To shikkenan Allah yasa naji alkairi.”

Har sun miqe da niyyar tafiya ya hana su yace su sanya kaya suyi wasa. ba tare da ‘bata lokaci ba suka bi umarninsa suka shiga d’akin da suke shiryawa suka sako kayan kwallo suka fito kai tsaye filin wasa suka nufa su shiga shiga cikin ‘yan uwansu Oga Labaran ya mike yana zagaye gurin tare da addua akan Allah ya daukaka ‘kungiyarsa ta Kano pillas.

****
Ina komawa gida na fad’awa Gwaggo cewa Khalid ya kira waya sai ta kwantar da hankalinta yana raye bai mutu ba, ba tare da tace min komai ba naga ta mike ta dauki buta ta fita, alwala ta dauro ta dawo dakin ta gyara dadduma ta tayar da sallah, ina zaune ina kallonta tayi raka biyu ta jima a sujjadar karshe tana addua kafin ta dago….ko bayan da tayi sallama ma sai da ta daga hannu sama ta dinga godewa Allah tana share hawaye…..na cika da d’umbin mamakin irin kaunar da takewa yaron

Mi’kewa tayi ta fita daga dakin minti uku suka dawo tare da Ummatu tana washe min baki tace.”Sa’ida ashe Khalid ya kira ki a waya ko.”? Nace.”Eh wallahi d’azu da rana mun jima muna waya har yace yana so yayi magana daku nace ya bari na koma gida.

Gwaggo tace”Dan Allah ki kirasa ‘yar albarka so nake naji miryarsa.

Nace.”Gwaggo babu kudi a waya ta bari a samu yaro ya siyo kati.” Da sauri Ummatu tace”Ga dari biyu a siyo katin.” kokarin kwance bakin zaninta take nace”Haba dai bari ba sai kin bada kudi ba bari na duba yaro.” Gwaggo tace.”Sa’ida na dauka gurin siyar da katin babu nisa inace gurin Auwala ne.” Nace.”Eh tace.”To bani na siyo da kaina.” kallonta nayi naga duk ta tashi hankalinta na koma na zauna bakin gado ina gwada siyan kati ta banki babu network ko kad’an na mika mata kudin ta yafa mayafi da sauri ta fita.

Ummatu kuwa tsayawa tayi tana jana da hira na dinga mamakin matar ta saki jikinta dani a yanzu ta daina jin haushina kullum kuma na gaisheta da sauri take amsawa komeye dalili oho.

Gwaggo ta dawo gidan da katin mtn a hannunta da sauri na kar’ba nasa a wayar…….Muryar wani mutum naji a kunne na. nace.”Dan Allah Khalid fa.”? Yace.”A yanzu dai suna filin wasa sai dai idan sun fito.” ko kafin nace komai ya kashe wayar.

Gwaggo a sanyaye tace.”Ya akayi.”? Nace.”Wani mutum ne ya dauki wayar yake cewa wai khalid din yana filin wasa.

Gwaggo da Ummatu suka had’a baki gurin fad’in “Ina ne kuma filin wasa.”? Nace”Watakila gurin ball yake nufi kun san dama Khalid akwai naci ball a lokacin da yake gida.

Gwaggo tace.”Eh hakane kuwa to an jima sai a sake kiran wayar. shuru nayi ina duba waya ta Ummatu tace.” To bari naje na karasa ayyukana.”Gwaggo tace.”To shikkenan daga zarar wayar ta shiga zan fito na fada miki.” Ummatu tace to shikkenan a yayin da take kokarin barin gurin.

Kallonta nayi a nutse nace.”Gwaggo a yau da daddare nake so naje gidan Ummana nayi sallama da ita.” Gwaggo tace.”Ba zaki bari ba gobe idan za’a kai ki dakin ki sai na raka ki.” Nace.”Aa Gwaggo gwara naje yau din.” Tace.”To shikkenan Sa’ida ai ni ban ta’ba ganin biki irin naki ba sam baiyi farin jini ba.

Nace”Saboda me kike ce haka.”? Tace.”Ai gani nayi gidan nan yaki cika da mutane makota ne kawai suke shigowa a tsaitsaye suyi Allah ya sanya alkairi su fita.”

Nace.”Gwaggo wannan kuma kanki zaki tuhuma ina dangin suke.”? Tace.” Sa’ida kenan ai ni dangina duk sun mutu saura qalilan dama bamu da yawan zuria ko baki gani bane.”?

Nace.”Hakane amma ai Ummana tana taro a gidanta ita da ‘yan uwanta” Tace.”Aikuwa mu dai sai gobe idan an daura aure zamuyi namu taron.”

Shuru nayi tace.”Dan Allah ki zauna a dakin mijinki lafiya tunda dai Allah ya had’aki da kishiya mai mutunci to ki ‘ki ji ki ‘ki gani babu ruwanki da ‘yan bani na iya kada ‘kawar data zugaki ki dauka.

Nace.”Insha Allahu Gwaggo zan bawa mara d’a kunya.” Tace.”Allah ya sanya alkairi Ya bada zuria dayyu’ba.” a zuciya na amsa da ameeen.

Dakin yayi shuru na minti biyu kafin tace.”Sa’ida Alhaji Shamsu mutumin kirki ne kwarai duk hidimar kayan daki ya dauke ya hana Ibrahim siyan komai duk abinda kika gani a dakin ki to Alhaji Shamsu ne ya siya miki saboda haka ki rike shi da kyau kinji ko.”

Nace.”To Gwaggo insha Allahu…..Ta dauki goro ta gutsira tana taunawa tace.”Oh! yau dai zanji muryar Khalid a kunnena wallahi ni kadai nasan halin damuwar da nake ciki akansa, gashi lokaci guda Allah ya amsa addua ta.

Nace.”Gwaggo kin san wani abu.”? Girgiza kanta tayi tana kallona, nace.”Khalid nayi masa dubara kancewa ya idan ya dawo gida zan aureshi koda zaiyi miki maganar to ki nuna masa hakane.

Shuru tayi tana kallona kafin tace.”Sa’ida me yasa kike yaudareshi gobe fa za’a daura miki aure.”

Nace.”Gwaggo Khalid fa idan ba haka akayi masa ba ba zai dawo gida ba zai bar zuciyoyinku cikin damuwa shiyasa nayi masa haka.

Shuru tayi na minti biyu kafin tace.”To Allah ya sanyaya masa zuciyarsa idan ya dawo ya iske abinda ba shikkenan ba.

Nace.”Ameeen ya rabbi sai ki zaunar dashi ki rarrashe shi ki nuna masa cewa samu da rashi duk na Allah ne idan yayi hakuri sai Allah ya bashi wacce ta fini.

Tace.”Zanyi iyakacin bakin kokarina Sa’ida Allah ya sanya masa dangana.” na amsa da ameeen ina kokarin fita daga dakin.

*Littafin na kudi ne….Kada ki siya ki fita dashi…idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing……Idan kika karanta baki biya ba na biki bashi…..Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake… Vip gruop#600 normal gruop#300…account.. 0542382124…Binta umar gtbank….Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*39&40*
Sai daf da magariba Khalid suka fito daga filin wasa, hannunsa rike da karamin towel yana goge zufar dake jikinsa ya nemi guri ya zauna yana mayar da numfashi, Salmanu ya zauna kusa dashi shima da k’aramin towel din a hannunsa yana goge fuskarsa, Oga Labaran ya karaso gurin fuskarsa yawalce da fara’a yace.”Khalid a gaskiya kana burgeni da kwazon ka babu shakka nan gaba kad’an za kayi fice a duniya zata san da zamanka.”

Khalid murmushi kawai yayi ya kar’bi goran ruwan faro dake hannunsa ya bude ya sha ya mikawa Salmanu sauran. Oga Labaran ya mika masa wayarsa da fad’in “Kana filin wasa aka kira wayar ka ka duba ka gani.”

Da sauri ya kar’bi wayar yana dubawa ganin sunan auntynsa yasa shi sakin murmushi ya mike da sauri ya bar gurin, Salmanu ya bishi da kallo yana girgiza kansa.

Number ta ya shiga kira cikin zumud’i da bukatar son yaji muryarta.

Lokacin da ya kira wayar tana sallah Gwaggo kuma ta idar da tana jan carbi, da sauri ta dauko wayar tana dawurwura domin bata san inda zata ta’ba ba.

Sai kawai tasa wayar a kunnanta ta dinga zabga sallama tana fad’in ” Halo Khalid kana jina ko? Halo Khalid nice Gwaggon ka nake magana.” Da karfi take maganar gashi wayar sai ‘kara take yi kafin kiran ya katse! ta shiga duba fuskar wayar tana surutai da fad’in “To ko dai babu nethook ne.” Saura kad’an dariya ta su’bcewa Sa’ida da sauri ta kori shed’an ta cigaba da sallarta.

Gwaggo ta cigaba da surutai da fad’in “Babu shakka yaron nan ne ya kira waya amma saboda abin nasara bashi da tabbas yayi mana rashin mutunci.

Tana rufe bakinta wani kiran ya sake shigowa, da sauri tasa wayar a kunnanta ba tare da ta ta’ba wani guri ba Fad’i take.”Halo Khalid kayi min magana mana nice Gwaggonka.”

Ummatu dake gurin ta a zaune ta dinga jin shouting din Gwaggo tana kiran sunan Khalid da saurin gaske ta fito ta tsaya a bakin kofar dakin tana fadin”Gwaggo Khalid din ne.”?

Da sauri ta mika mata wayar da fad’in “Eh ina tsammanin shine kinga tun dazu yake kira inata magana babu amsa shine nace ko matsalar nethook ne.”

Itama Ummatu sai da ta kusa dariya ta kar’bi wayar tana fad’in “Gwaggo ai baki d’aga wayar ba ba zaiji maganarki ba.”

Tace.”Ayya to ya ake yi.”? Ummatu na kokarin magana Na idar da sallar wanda kuma yayi daidai da sake shigowar wani kiran.

Ta miko min wayar da sauri! Kar’ba nayi na d’aga tare da sawa a kunnena.

A dan sanyaye yace.”Aunty barka da dare ina ta kiran waya baki daga ba.” nace.”Barka dai Khalid ina sallah ne.” Yace.”Okey to ina Gwaggo.”? Nace.”Gata a zaune ita da Ummatu.” Kafin yayi magana na mikawa Gwaggo wayar yaji sautin muryarta a kunnansa.

Ajiyar zuciya mai sanyi ya sauke yace.”Gwaggo ki gafarce ni akan abinda nai muku.” Murya na rawa tace.”Khalid mun yafe maka dan Allah ka dawo gida gabad’aya mun galabaita da rashin ka.”

Yace.”Gwaggo insha Allahu sati mai zuwa zan zo gida amma hakan ba yana nufin na dawo kenan ba zan koma insha Allahu.”

Tace.”Khalid yanzu kana wane gari ne.”? Yace.”Ina legos kuma na samu aiki Gwaggo kada ku damu akwai alamun nasara a inda nake.

Tace.”Khalid daka hakura da Lego’s din nan ka dawo gida ka cigaba da harkokin ka dan d’azu da Sa’ida ta kira wayarka wani ‘katon mutum ya dauka yake fadin wai kana filin wasa Khalid kasan na tsani buga ‘kwallon nan ko.”

Yace.”Gwaggo idan anan abinci na yake dole kiyi hakuri dan babu irin fafutukar da banyi ba akan na samu aiki abun yaci tura dole tasa na mayar da hankalina gurin buga kwallo.

Tace.”To ka dawo gida kayi anan mana.” Yace.”Gwaggo zan duba maganarki.” Tace.”To shikkenan ga mahaifiyarka ma tana so tayi magana da kai.”

Ummatu hannu na rawa ta kar’bi wayar tasa a kunnenta,

Gaisheta yayi ta amsa a sanyaye tana jin kewarsa tace.”Khalid me yasa ka aikata wannan abu.” A raunane yace.” Ummatu rashin jin magana ne kin gargade ni akan na fita harkar aunty Sa’ida ni kuma na’ki bin umarninki shiyasa Allah ya jarrabe ni nima nayi nadama.”

Hawaye ta share tace.”Khalid ka dawo gida nima bana son zaman Lego’s din nan.”

Yace.”Ummatu zan dawo gida amma kiyi min alkawarin amince min auran Auntyna.”

Magana za tayi Gwaggo ta d’aga mata hannu, da yake wayar handsfree take duk muna jin maganarsa.

Gwaggo a hankali tace “Kice masa kin amince.”

Ummatu ta dinga kallonta tana mamakin maganarta wace irin magana ce wannan bayan gobe daurin auranta

Yace.”Ummatu kinyi shuru har yanzu baki bani amsa ba.” a sanyaye tace.”Khalid ka dawo na amince maka.

Hamdala yayi ga Allah cikin tsananin farin ciki yace.”Nagode Umma Allah ya tabbatar mana da alkairi.” a sanyaye ta amsa da ameeen tana mamakin al’amarin ko me yasa Gwaggon ta fadi haka.

Bayan sunyi sallama sai ta mikawa Sa’ida wayar da fadin”Gwaggo nifa wallahi duk jikina yayi sanyi da wannan maganar taki gobe i yanzu Sa’ida na dakinta ya za’ayi kuma a yaudari yaron nan yanzu idan ya zo ya tarar tayi aure mai zai biyo baya.

Gwaggo tace.”Rabi komai mai sauki ne mutukar dai an samu ya dawo gida ai ni a ganina duk abinda zai biyo baya mai sauki ne ni zan zauna dashi na rarrashe shi ya hakura da kaddara matar mutum kabarin sa.”

A sanyaye Ummatu tace.”To shikkenan Allah ya kawo shi lafiya yasa kuma ya d’auki kaddara kamar yanda itama Sa’idan ta dauka.” Gwaggo ta amsa da ameeen ya Allah. Ummatu sallama tayi mana ta nufi gurin ta tana dan jin sassauci a cikin zuciyarta.

Gwaggo bata kwanta bacci ba har sai da Kawu ya shigo ta sheda masa abunda yake faruwa. to shima da yake ya huce fushinsa akan d’an nasa sai yayi ta murna da farin ciki yana adduar Allah ya dawo dashi gidan lafiya.

****
To cikin ikon Allah da hukuncinsa a ka daura auran Sa’ida da Alhaji Nura daurin auran da ya samu hallatar mutane da dama ta ‘bangaran Ango da kuma Alhaji Shamsu da Kawu Ibrahim anyi taro an gama lafiya amarya tayi ado sosai tai kyau k’awayenta na gurin aiki sunyi mata kara sun hallaci taron bikin sunyi mata gudumawa sosai mussaman Hauwwa dan itace ta dauki nauyin gyara mata jikinta da nau’in magungunan mata masu kyawun gaske mahaifiyarta ma tayi nata kokarin dan tun kafin bikin take gyara ta ita dai Sa’ida kallonsu kawai take fargabar abunda zai biyo baya kawai ke damunta tabbas tasan idan Alhaji Nura ya fuskanci ita din ba budurwa bace dole ya tuhumeta wannan dalilin yasa har aka gama taron bikin aka kaita dakinta ta kasa sakewa bini bini gabanta zai fad’i….Yanzu ma tana zaune ita kadai a dakinta bayan tafiyar Hauwwa sai tunanin yanda zata kaya take tasan Alhaji Nura yana sonta watakila idan ta fada masa abinda ta tanada ba zai kalubanceta ba.

Ya shigo dakin cikin manyan kaya kamshin turaransa ya game dakin ledojin hannunsa ya ajiye kan teble tun kafin ya zauna a kusa da ita ya cire babbar rigar jikinsa da murmushi a fuskarsa ya kira sunanta had’e dayi mata kirarin da ya saba. “Amarya bakya laifi ko da kin kashe d’an masu gida.”

Mayafin dake rufe da fuskarta ta cire tana d’an mirmushi tace.”Alhaji kenan.” yace.”Aa inaso ki kira ni da angon gimbiya Sa’ida.”

‘yar dariya tayi cikin jin nauyi ta kauda kanta yace.”Alhamdulillahi nagode Allah daya nuna min wannan rana Sa’ida auran nan namu anyi kamar ba za’ayi ba sai gashi Alkwarin Allah ya cika.”

Tace.”Hakane Alhaji dama komai yana da lokacinsa ina rokon Allah ya tabbatar mana da alkairi.”

Ya amsa da ameeen ya rabbi yanzu zaki tashi muje falo domin inaso na zauna daku keda ‘Yar uwarki.”

Nace.”To shikkenan.” kokarin mikewa nake ya rike hannuna muka mike a tare falon muka fito ya zaunar dani akan kujera da fadin.”Bari na kira ta ko.” kai kurrum na daga masa na bishi da kallo a lokacin da yake kokarin hawa sama.

Tv na tsirawa ido ina kallon film din da akeyi a tashar Mbc action………..Ina zaune tsayi mintina talatin ina tsammanin su shuru babu labari na dauke kaina daga kan tv din na tsirawa matattakalar benan ido jikina yayi bala’in mutuwa da al’amarin anya kuwa mutumin nan zai fito minti arba’in ko motsinsu nayi kasa da kaina hawayen takaici na nema ya kufce min…………Motsinsu naji da sauri na daga kaina ina kallon steps din ya riko hannunta suna saukowa na dauke kaina raina yayi masifar ‘baci da abinda sukayi min.

A nutse ta zauna kan kujera shima ya zauna kusa da ita da fad’in “Sa’ida kinji shuru ko afuwa tana d’an uziri ne shiyasa na jira ta gama.

Yanda ya fadi maganar kai tsaye babu kulawa yasa naji wani irin sam bai saba yi min magana gatsar-gatsar ba tunda nake dashi idan zaiyi min magana ko a waya ne sai ya tausasa murya amma yanzu magana yake min kamar baya so.

Cikin kokarin danne damuwa ta nace ” Ayya ai babu damuwa. kallonta nayi a nutse nace.”Aunt Murja ina fata kin wuni lafiya.”?

A sake ta amsa min da “Lafiya lau Alhamdulillahi Sa’ida ya taro.”? Nace.”Alhamdulillahi.” falon yayi shuru na minti biyu kafin yayi gyaran murya kamar me tsoron magana yace.”Sa’ida ga Uwargidana Murja Uwar Yasir da Yusura kenan inaso ki zauna da ita lafiya ki mutuntata a matsayinta na uwargidanki kada naji kada na gani tunda nake da ita wani sa’bani bai ta’ba shiga tsakaninmu ba sabida haka bana so zuwanki ya hargitsa min gidana kada kiyi kishi da ita tunda itama ba tayi dake ki dauketa a matsayin ‘yar uwa kamar yanda ta daukeki.”

Kaina ya dinga juyawa ina jin maganganunsa suna amsa kuwwa! a kunnena……..Wannan wasu irin banzayen maganganu ne.”?

“Sa’ida ko bakya ji ne.” Muryarsa ta dawo dani hayyacina, nace.” Naji Alhaji Allah ya sa’ba halaye a tsakaninmu.” Ya amsa da ameeen ya Allah.

Muryart a naji tana fad’in “Abban Yusura ni zan shiga na kwanta .” da sauri ya mike da fadin” Haba gimbiya ai ni zan mayar dake d’akin ki kamar yanda na dauko ki.”

Kafin na ankara naga ya rike k’ugunta sun fara hawa steps suna magana ‘kasa-‘kasa, kaina ya dinga juyawa a gurin na nemi yawun a bakina na rasa hawayen dai da nake dannewa sai da suka kufce na mike da saurin gaske na shiga dakina na zauna bakin gado hawaye masu zafin gaske suna shatata a fuskata….”Shin ni d’in wace irin amarya ce ne? tambayar kaina nake Wace irin wulakantacciyar amarya ce wacce ba’a zumud’in ta? ashe Alhaji Nura mijin tace ne a gidansa? shin me hakan yake nufi ne ? yana so ya nuna min cewa matarsa ta fini daraja a gurinsa? tambayoyin da nake tayi wa kaina kenan ina wani irin kukan bakin ciki a yanzu Alhaji Nura ya fifita matarsa a kaina to kuma ina ga ya fahimci abinda yake lullu’be! innalillahi wa’ina ilahi raji’un!
Ita na dinga nanatawa a cikin raina ina addua akan Allah yasa duk abunda zai faru dani na kaddara yazo min da sauki tabbas nasan zan fuskanci tashin hankali a zamantakewar aurana.

Dakin ya shigo kamar wani mutumin kirki ya mayar da kofa ya rufe dauke kaina nayi har ya karaso kusa dani ya tsaya da fadin”Gimbiyar mata kiyi hakuri na barki ke kadai ko Maman Yusura ce take fama da mura shiyasa na dan jima a gurinta na tabbatar tasha magani ta kwanta.

Shuru nai masa yace.” Ki tashi kije ki dauro alwala mu gabatar da sallar godiya ga Allah.” ba tare da nace komai ba na mike na nufi toilet din dake cikin dakin, ina daura alwalar ya shigo na dauke kaina ina gamawa na fita na bashi guri.

Addua yayi sosai muka shafa na mike na koma bakin gado na zauna…ledojin da ya shigo dasu ya hau budewa da fadin” Amarya ki sauki kici abinci ko.”

Nace.”A koshe nake ni.” jim yayi yana kallona kafin yace.”Kin san fa yau tsakanina dake a kwai harka yana da kyau ki cika cikin ki kada ki galabaita.”

Dauke kaina nayi bance masa komai ba, yayi murmushi a nutse ya fara cin kazar amarcin yana hadawa da lemo, cikinsa ya cika sosai kafin ya d’an gyara gurin duk ina zaune ina kallonsa ya nufi toilet ya wanke bakinsa ya fito..

Hasken dakin ya kashe ya mayar dashi Dark gabana ya tsananta faduwa ganin ya cire rigar shaddar jikinsa ya hayo gadon na dan ja baya ina kallonsa ya janyo ni jikinsa yana kokarin cire mayafin jikina.

Jikina ya dinga karkarwa na dinga no’kewa ina kare jikina, Alhaji Nura gabadaya ficewa yayi daga hayyacinsa ganin zahirin ta sai ya shiga sambatu yana wasa da sassan jikinta mussaman Brest d’inta da suke masifar tafiya da imaninsa.

Ni dai ina kwance ina kallonsa da jinsa yana sarrafa ni gabana na cigaba da faduwar abinda zai faru, jin yana karanto adduar saduwa da iyali yasa na rintse idona kawai sai jikina ya shiga karkawa tun kafin ya shige ni na fara zubar da hawayen bakin ciki da takaici.

Ya jima kafin ya shiga ramin amma duk da hakan sai da ya gane matar tasa ba budurwa bace, ransa idan yayi dubu ya ‘baci! ya cigaba da abinda yake yi yana bukatar ya samu satisfaction ya sauka a gaskiya yayi mamakin yarinyar ashe dai duk irin maganganun da ake kawo masa akanta gaskiya ne gashi yanzu ya gazagata tunda ya sameta a bude.

Ni’imar ta da dad’in ta sune suka sanya yaji dan sassauci a cikin ransa amma dai duk da haka sai ya tuhumeta akan cin amanarsa da tayi……sau biyu yana kawo wa amma abin mamaki a duk kawowar da zaiyi baya ta’ba yarda yayi a cikin ramin fita yake da jijiyar tasa ya zubar da sperm din a kan bedshirt kafin ya koma ya cigaba da biyan bukatarsa, shin to meye manufarsa tayi hakan.?

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*41&42*
Cikin tsananin bushewar ma’kogwaro na mike zaune tare da kare jikina da bedshirt din daya cukurkud’e sabida dabdalar da akayi akansa. Gajeran wandonsa ya dauka yasa a jikinsa ba tare da ya ko kalli inda nake ba ya sauka daga gadon bandaki ya nufa

Cikin mutuwar jiki gami da nadamar rayuwa nabi bayansa da kallo wata masifaffiyar fargaba ce ta tsaya min a raina hakika ya fahimci abinda yake da akwai ko ga yanayin yanda ya sauka daga gadon yana d’acin rai.

Motsin fitowarsa naji daga toilet din sai nayi saurin sunkuyar da kaina kasa jikina duk ya mutu tsabar nadama da kunya tasa kwata-kwata bana kaunar na hada ido dashi.

Ganin ya nufi wardorbe ne yasa na mike a hankali na nufi toilet jikina duk a sab’ule… Tsuganawa nayi na takure kaina guri guda mahaukacin kuka ya kufce min. hannu nasa na rufe bakina ina so na had’iye kukan amma yaki haka na hakura nayi tayi ina shar’be majina Khalid Khalid ya cuce ni ya kassara min rayuwa wannan rana itace ranar da ko wace mace take alfahari da ita mutukar ta yarda da kanta ita din cikakkiya budurwa ce dole tayi tunkaho da ranar daran amarcinta amma ni na kasance cikin kunci da bakin ciki sakamakon abinda Dan uwana na jini yayi min Khalid baya sona domin da yana sona ba zai keta min rigar mutunci ba.

Na jima tsugune a toilet din ina kuka kafin nayi wankan tsarki na fito na samu dakin duhu sosai ya kashe hasken. da lalube na dauki waya ta kan mirror na kunna toch sai na ganshi kwance a kan gadon ya jefar da bedshirt din ya ‘bata a kasa ya shimfida wani.

Babu kuzari a tare dani na duba doguwar rigar bacci mai hula nasa a jikina tare da pant. a sanyaye naje na kwanta kusa dashi sai ya matsa can gefe tare da juya min baya.

Na tsirawa bayan nasa ido ina ayyana abubuwa masu yawa yanzu ko wane irin hukunci zai yanke akaina tabbas al’amarin yayi masa zafi koga yanayin yanda yayi shakulatun ‘bangaro dani ko banza nasan da ya samu budurci a tare dani zai taimaka min da wani abu amma saboda yasan ban cika mace ba ya biya bukatarsa ya juya min baya banga laifinsa ba akan abinda yake ko wane namiji abinda yake kulafuci kenan mutukar yasan budurwa ya aura zai so ace shine zai fasa tantanin budurcinta.

zazzafar ajiyar zuciya na sauke na gyara kwanciya tare da tsirawa rufin dakin do.

Yanda naga dare haka naga rana tsabar fargaba ta hana ni rintsawa shi kuwa baccin sa kawai yake yana sakin munshari babu abinda ya dameshi.

Asubah nayi ya tashi ko gefe na bai kallah ba ya sauka daga gadon ya shiga bandaki, na mike zaune tare da saukar da kafafuna kasa, ido muka hada a lokacin da ya fito nayi gaggawar yin kasa da kaina kunyarsa nake Ji wallahi.

Fita yayi daga dakin daure da alwala. na sauke ajiyar zuciya jiki a mace na mike na nufi toilet domin na daura alwala.

To har gari ya waye sosai nayi wanka na shirya jikina babu labarinsa na daga kaina na kalli agogon bangon dake kafe a dakin tara da rabi na safe tunda ya fita sallah bai dawo ba. cikin rauni da sarewa na sauke kaina kasa ina addua a cikin zuciya ta akan Allah ya sassauta min.

Da sauri na dago kaina jin motsin shigowarsa dakin. wannan karon dakewa nayi a lokacin da muka hada ido dashi ban nuna tsorona ba, har ya karaso inda nake ban dauke idona daga kansa ba mamaki nake lokacin da ya fita daga dakin jallabiya ce a jikinsa amma abin mamaki yanzu ya shigo cikin sabuwar shadda(wagambari) sai zabga kamshi yake yi shin a ina yayi wanka ya kimtsa? zuciyata ce keyi min wannan tambayar.

Kusa dani ya zauna yana yi min wani irin kallo jikina ya sake mutuwa a hankali nace.”Alhaji Barka da asubah fatan ka tashi lafiya.”?

Bai amsa ba kuma bai fasa watsa min kallon tuhuma ba.

Sai kawai na shiga wasa da hannuwana ina jiran abunda zai biyo bayan kallon.

“Sa’ida mai yasa kika yaudare ni kika sa na aure ki a matsayin budurwa.” ? tambayar da yayi min kenan wacce ta kusa sa zuciyata ta faso kirjina ta fito waje.
jarumta na aro nace.”Alhaji wace irin magana ce wannan.”? Ido ya zuba min fuskarsa a had’e yace.” Kada ki mayar dani shashasha mana ba’a kanki na fara auran budurwa ba matata Murja da budurci na aureta kuma akanta nasan ya yake saboda haka jiya na tabbatar da cewa ke ba cikakkiya bace dan duk wasu gyare-gyare da kikayi a gurin sai da na gane budurci ya bambamta da komai.”

Zafafan hawaye suka kwace min murya na rawa nace.”Haba Alhaji shedar da za kayi min kenan? ashe shiyasa naga kana ta ‘kunci ka tashi ka fita tun asubah baka shigo ba sai yanzu to inaso ka sani ni ba ‘yar iska bace ballanatana kayi zargin ko gurin yawon ta zubar na sarayar da mutunci na. Sabida haka ni ban san wata magana ba budurci na kai ne ka kar’ba ba wani ba.” Cikin kame-kame nake magana gabana kuma na cigaba da faduwa

Yace.”Ki saurare ni da kyau kiji abinda zan fada miki.” Na kalleshi ina goge hawaye ya cigaba da cewa”Tun kafin na aureki jama’a suke kawo min suka akan ki cewa babu abinda kikeyi a gurin aiki sai lalata da maza wannan dalilin yasa na sake gazgata maganar mutane tunda naga zahiri kada ki mayar dani yaro nasan komai kin cuce ni kin yaudare ni ashe kin san baki da kamun kai kika sa na tsaya na ‘batawa kaina lokaci gurin auranki.”!

Ina wani irin kuka na zube gabansa hannunsa na rike nace.”Wallahi Alhaji duk k’arya ce kada ka gazgata maganar mutane akaina sharri sukai min amma ni bana bin maza zan iya rantse maka da al’kur’ani ni ba karuwa bace budurci kuma da kake magana akansa watakila ya fita ne saboda tsayin lokacin dana dauka banyi aure ba bayan haka kuma kaga kullum bana zama ina zurga zurga zuwa gurin aiki hawa babur da Napep hakan zai iya janyowa na rasa budurcina.

Shuru yayi yana kallona da akwai alamun sassauci a tare dashi a sanyaye nace.”Dan Allah ka yarda da maganata Alhaji ban yaudare ka ba kada ka amince da maganganun mutane a kaina sharri sukayi min.”

Hannu yasa ya d’ago ni na zauna kusa dashi yace.”Naji maganarki kuma na gamsu tabbas zaki iya rasa budurcin ki ta wad’annan hanyoyin da kike fad’a sabida haka ki share hawayen ki na amince da maganarki.

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Nagode sosai mijina ina rokon Allah ya kauda idanun makiya akanmu.” ya amsa da ameeen yana kokarin miqewa yace.”Ni zan tafi kasuwa saboda kin san bamu jima da shigo da kaya ba bana zama a gida sosai dan haka kina iya zuwa kiyi breakfast d’in ki.”

A sanyaye nace”To shikkenan sai ka dawo Allah ya bada sa’a.” ya amsa da ameeen ya kama hanya ya fice daga dakin.

Ajiyar zuciya na dinga saukewa ina godewa Allah da yasa ya yarda da maganata yanzu dama ashe kallon karuwa mutane keyi min? shin me nakeyi a makaranta da har mutane zasu sanya min ido su dinga zargi na da aikata fasikanci.” hawaye na share a fili nace.”Ya Allah kabi min hakkina akan dukkanin wanda ya d’ora min kazafi na zina.

Fuskata na wanke na d’an shafa hoda nasa kwalli a idanuwana kana na fita falon……a hakimce akan kujera na sameta tayi ado sosai kamar itace amaryar tafkekiyar wayarta ce a hannunta tana dubawa.

Gani na yasa ta saki fuskarta tana murmushi ta nuna min kusa da ita na zauna a nutse muna gaisawa.

Yaran na tambaya tace.”Sun tafi makaranta sai biyar da rabi zasu dawo ai da har sun zauna suna jiran fitowarki sai kuma direbansu yazo daukarsu da kyar na lallabasu suka tafi.

Murmushi nayi nace.”Ai idan sun dawo zamu gaisa da kyau.” Tana tauna cingum! din bakinta tace.” Kwarai hakane.

Falon ya sake daukar shuru na ‘yan mintina kafin tayi magana “Sa’ida kije kiyi breakfast mana.” Murmushi nayi ba tare da nace komai ba. tace.”Dan Allah ki saki jikin ki dani ni bana kishi irin na jahilci kanwata na dauke ki.”

Nace.”Nagode kwarai auntyn Murja. ” tace.”Nima nagode da kika fahimce ni saboda haka sai ki tashi kije ki karya ko.” ba tare da nayi mata musu ba na mike a nutse na nufi gurin cin abincin.

A ranar haka muka yini da Aunty Murja muna hira na dinga mamakin saukin halinta kamar bata da damuwa akaina domin daidai da ‘kwayar zarrah banga ta nuna wani kishi a kaina ba wannan dalilin yasa na saki jikina da ita sosai muka shiga kicin a tare mukayi aiki tsaf muka kammala komai muna hira cikin fahimtar juna

Koda yaran suka dawo daga makaranta a daki suka sameni ina shiryawa suka gaisheni suna nuna farin cikin su da zuwana cikinsu nima na dinga jansu a jikina ina duba litattafansu na makaranta.

Sai da mukayi sallar isha’i tukkuna suka fita suka barni ni kadai a dakin…..sai kawai na yanke shawarar fita falon. abin mamaki da al’ajabi maigidan na samu zaune a gurin cin abinci iyalin nasa suna zaune ko wanne da kujerarsa suna cin abinci….sosai na shiga mamakin al’amarin yaushe ya shigo gidan babu labari kuma me yasa basu nemi ni gurin cin abincin ba.?

Gwiwa a sanyaye na juya zan koma daki muryar Yusura ta daki kunnena….”Aunty kizo muci abinci.” a sanyaye na juyo ina kallonsu naga shi gogan ko kallona ma beyi ba sai abincinsa yake ci itama aunty Murjar haka…. hakan da sukayi sai ya nuna min cewa basa bukatata a gurin…..jiki a mace na bude kofar dakina na shiga na rufe tare da jingina jikina jikin kofar gabana sai wani irin faduwa yake….wace irin rayuwa ce wannan? shin wai me Alhaji Nura yake nufi dani ne? ganin bani da mai bani amsa yasa na sulale nayi zaman durshan a gurin hawayen bakin ciki ya shiga karakaina a fuskata.

Na jima a zaune a bakin kofar dakin ina kuka kafin na bawa kaina hakuri na mike a sanyaye na shiga bandaki na wanke fuskata na fito ina kallon agogo goma har ta gota bai shigo dakin ba ga yunwa na kokarin cinye min ‘ya’yan hanji a sanyaye na mike na fita falon sai na gansu a zaune yaran suna kasan kafet suna duba littafansu na makaranta su kuma suna zaune a kan kujera a tare yana nane da jikinta sai soyayya sukeyi. fitowa ta bai hana su abinda sukeyi ba, ta kalle ni na kalleta ina mamakin iya sharrin ta wai ni za tayi wa dariya na tsaya kawai ina kallonta da jin abinda take fad’a….”Sa’ida kina ji Yusura nayi miki maganar abinci kika share ta.”

Kai tsaye nace.”Aunt Murja naga kamar bakwa bukatata a gurin ne.”

‘Yar dariya tayi tana kallonsa tace.”Abban Yusura kaji amaryar ka da wata magana ko.”?

Murmushi yayi irin na dole yace.” Ina jinta ai na fahimci neman fitina take.”

Kallon banza na watsa masa a zuciyata nace”Lusari mijin tace kawai.”
Daga ita har shi sunga abinda nayi kuma na lura sunyi mamaki. nace.”Ai idan an damu da naci abincin kira na Za’ayi ba kawai sai na fito na tarar daku kuna ci ba.”

Fuskarta ce ta sanja da yanayi na ‘bacin rai kafin tayi magana ya rigata da fad’in “Ke wace irin banzar magana ce wannan? kina so ki rusa min tsarin gidana ne.”? shuru nayi masa ya cigaba da fuff*cka yana kumfar baki.

Nace.” Dan Allah kayi hakuri naga kamar maganata ta fusata ka kasan ita gaskiya d’aci gareta.”

Da sauri tace.”Sa’ida kiyi hakuri anyi miki ba daidai ba kai kuma ka daina wannan kumfar bakin haka.” Kamar anyi ruwa an dauke yayi shuru sai wani muzurai yake…..naja tsaki cikin raina na bar gurun

Gurin cin abincin na zauna na zuba daidai cikina naci na tashi na bar gurin……nesa dasu na tsaya da fad’in “Aunt Murja sai da safe.” Fuskarta kamar gonar audiga ta amsa da fad’in “Allah ya tashe mu lafiya.

Dakina na bude na shiga takaici kamar ya kashe ni cikakken mutum a zahiri mai haiba da kamala uwa uba kudi amma saboda lusaranci mace na juya shi a gida wani irin tsanarsa naji a cikin raina.

Wanka nayi na shirya jikina na kwanta kan gado da waya ta a hannuna…….Misscall din Khalid na gani gabana ya fadi da sauri na mike zaune hannuna sai rawa yake.

Wani kiran ne ya sake shigowa, kamar kada na daga sai wata zuciyar tace ” ki daga kiji abinda zai ce.”

A hankali nayi sallama naji sanyayar muryarsa yana amsa wa. kafin yace.”Aunty ya kike ina fatan kin wuni lafiya.” ?

Nace.”Lafiya khalid fadi abinda yake bakin ka inada uzuri.” murmushi yayi wanda yasa tsigar jikina tashi. na lumshe idona ina sauraransa.

Yace.”Wato aunty Sa’ida idan bani na kira wayarki ba ban isa ki kira ni kiji lafiya ta ba ko.”?

Shuru nai masa yace.”Yau so nake nayi hira dake inaso na rage feeling’s ne auntyna ina nan sha’awar ki duk ta addabe ni kiyi min wani taimako mana.” yakarasa maganar a sanyaye.

Wani irin yanayi na shiga na tsantsar tashin hankali da fargaba nace.”Khalid yaushe zaka dawo gida.” Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Na fada miki cikin satin nan zan zo kuma da sadaki na domin ba zan koma ba sai an daura mana aure.

Shuru nayi kaina yana wani irin sarawa nace.”To kayi kokari ka dawo kaji ko.” Yace.”Insha Allahu ki bani Gwaggo mu gaisa.” da sauri nace.”Ta riga tayi bacci.” yace.”Okey da safe zamu gaisa insha Allahu yanzu meye labari auntyna ki fad’a min kinyi kewa ta ko.”?

Ina kokarin magana ya shigo dakin, da sauri na datse wayar na ajiyeta, ya karaso kusa dani a daida lokacin da ya ‘kara kira, sai kawai na dauki wayar na kashe ta gabadaya na ajiye saman bedside.

Jallabiyar jikinsa ya cire na dauke kaina daga kansa toilet naga ya nufa da gashi sai gajeran wando naja tsaki da fadin”Shashashan namiji kawai.

Minti biyar ya fito daga toilet din ya kashe wutar dakin, kusa dani ya zauna na sunkuyar da kaina ina jin wani irin haushin sa.

Shuru yayi yana tunanin da abinda zai fara “Sa’ida.” ya kira sunana kallonsa nayi a kaurare yace.”Kada ki sake ganin wani abu a cikin gidan nan ki tanka kome kika gani yana tafiya ne akan tsari mun riga mun tsara gidanmu nida Murja saboda haka abinda kika zo kika tarar dashi zakiyi amfani.”

Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa……”Alhaji wannan ai ba tsari bane kwana na daya kacal gidan ka na fahimci abubuwa da yawa a gaskiya dole da kai da matarka ku canja tsari tunda yanzu na shigo gidan kuma a matsayin matar gida nake.”

Hannu ya d’aga min da fad’in “Bana bukatar canza wani tsari a gidana wanda yake kai shine daidai saboda haka idan kina bukatar zama tare dani dole kibi abinda nace.”

Na dinga kallonsa ina me mamakin al’amarin…. matsowa jikina yayi yasa hannunsa ya janyo ni jikinsa ya matse gam! raina ya ‘baci! nayi yunkurin tureshi ya rike ni sosai ya sa min nauyinsa, hakura nayi na kyaleshi ya cigaba da budurunsa yana sambatu sai lugudar breast d’ina yake yana sha kamar zai tsinke nippels d’in, yanayin jikina gabadaya ya sanja zazzafar sha’awa mai zafi ta taso min.

Sakar masa jikin yayi ya dinga sarrafa ni iya son ransa.. Daf da zan samu satisfied ya zare jijiyar daga ramin ya dinga mutsika brest d’ina yana wani irin sambatu kafin naji saukar ruwa mai d’umi a tsakanin cinyoyina duk ya ‘bata min jiki da sperm d’in shi, kafin nayi wani motsi naji saukarsa daga gadon, cikin mawuyacin hali na bude idona na bishi da wani irin kallon mamaki a lokacin da yake kokarin shiga toilet.

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*43&44*
Wani irin azababben ciwo mara ta take min ta dinga wani irin d’aurewa tana murd’awa . fillo na janyo na matse shi tsam-tsam a kirjina ina cigaba murkususu da birgima a gadon gabad’aya hankali na a tashe yake ina jin wani irin azababben feelings yayin da mara ta ke sake turnukewa da ciwo mai zafi.
Zafafan hawaye ne suka shiga sauka a fuskata na rintse idanuwana ina kiran sunan Allah a fili da zucci motsin sa naji ya fito daga toilet din na bude idona dishi-dishi nake ganinsa sakamakon k’an’kancewar da sukayi,

Ni kaina nasan ina da tsananin bukata shiyasa sam ban fiye kallon india film ba dan wannan rungume rungumen da suke yakan tayar min da hankali na uwa uba kuma a yanzu na kai matakin da dole sai da d’a namiji zanyi rayuwa kamata yayi ace na samu jarumin namiji da zai dauke min dukkanin lalurata ta tsayin shekarun da nayi babu aure kwata-kwata ban tsammaci haka daga gurin Alhaji Nura ba saboda ni inayi masa kallon namiji cikakke wanda zai biya min bukatuna ashe ba haka bane *Kallon kitse na kewa rogo* Alhaji Nura ta ko’ina yana da matsala mai girma.

Zaman sa kusa dani yasa na kalleshi naga yana jan bargo zai kwanta duk ya tuje bedshirt din da ya ‘bata yana so ya kwanta kan katifar a haka, raina ne ya ‘baci na miqe zaune ina kallonsa.

Ya kalle ni babu wata cikakkiyar kulawa yace.”Ko da akwai wata bukatar ne.”? Kai tsaye nace.”Eh da akwai.” yace.”Okey bukata mutukar ta kudi ce ki fada kawai.”

Jikina yayi sanyi da jin maganarsa nace”Ni bana bukatar kudi Alhaji.” kallona yayi yana neman ‘karin bayani.

Kunya da tsoro na cire nace “Alhaji ni fa
Bangane abinda kake nufi ba.”

Yayi shuru yana kallona na cigaba da cewa” Me yasa kake min haka ne sai ina daf da samun satisfaction sai ka rabu dani jiya haka kayi yau ma haka meye amfanin zubar da sperm din da kake a waje.”

Jim yayi kafin yayi gyaran murya da fad’in “Sa’ida bana bukatar haihuwa a yanzu Yusura da Yasir sun ishe mu itama Murja abinda mukeyi kenan ni da ita tuntuni mukayi tsarin mu.

Raina ne ya ‘baci nace.” To ni me kake nufi dani kenan kana nufin ba zaka haihu dani ba.”?

Ba tare da damuwar komai ba yace.”Eh haka nake nufi ai na fada miki yara biyu kacal sun isheni rayuwa ga Murja nan munfi shekara bakwai muna haka da ita bata samu ciki ba kuma ba ta ta’ba cewa bata gamsuwa ba sai ke sarkin jaraba ko.”

Hawaye suka zubo min nace.” Alhaji wannan Wace irin magana ce ni kake kira da jarababbiya.”

Yace.”To idan ba ita bace me yasa zaki sani a gaba kina min kuka okey kina so na jigata kaina a kanki ko? na yini a kasuwa ina nema da daddare sai na ‘kare a gindin ki ko ? to ni ba haka nake ba idan nayi sau d’aya shikkenan na gamsu matata Murja bata da matsala dani .

Wani irin kallo nake masa ina mamakin maganganunsa wato dai Alhaji Nura yaudarata yayi Ashe bashi da mutunci dama.”? Zuciya tace “Aa Sa’ida ke kika cutar da kanki yanzu da Khalid kika aura ai bakin ki alaikum zai cika miki mara ya dauke miki dukkanin bukatunki.

Ajiyar zuciya na sauke na kalleshi ya juya min baya ya rufe jikinsa da bargo babu abinda ya dameshi baccin sa kawai yake.

A tsananin bukace na matsa kusa dashi ina dan shafa jikinsa, ya juyo da saurin gaske ya ture ni da fad’in ” Sa’ida bafa ki isa kisa nayi abinda banyi niyya ba ni na gaji ki kyale ni nayi bacci na huta gajiya.”

Sakato nayi da baki ina kallonsa yaja tsaki mai karfi ya koma ya kwanta.

Shuru nayi a zaune a gadon ina sa’kawa da kwancewa, nafi karfin rabin a wa a zaune ina tunani shin ya za’ayi na warware wannan gagarimar matsalar da nake fuskanta. Hakuri kawai na bawa kaina na cire abin daga raina na mike da mataccen jiki na shiga bandaki na tsarkake kaina har na fito daga toilet din gabana bai daina tsut-tsut ba babu shakka har yanzu gurin bai daina bukatar a gaji ba.

Ban kwanta kusa dashi ba sai na dauki fillo na ajiye kasan kafet na kwanta na takure jikina cikin hijab ina addua akan Allah yasa bacci ya dauke ni……Cikin ikon Allah kuwa bacci mai nauyin gaske ya dauke ni.

Sai wajejen shida na safe na tashi, lokacin shi tuni ya fice daga dakin na dinga mamakin yanda akayi bai tashe ni nayi sallah ba. a sanyaye na mike na shiga bandaki wanka nayi a gurguje na daura alwala na fito sai da nayi sallah tukkuna na shirya jikina gabad’aya auran Alhaji Nura ya fice min daga raina, gefan gado na zauna na kunna waya ta ina dube dube so nake na kira k’awata Hauwwa na fada mata halin da nake ciki ko da akwai shawarar da zata bani….Ina kokarin kiran wayar ta Khalid ya kira babu kwari na daga wayar gami da sawa kunnena.

“Auntyna kin tashi lafiya.” A sanyaye nace.”Lafiya Khalid.” Yace.”Ya na jiki wani iri ko baki da lafiya ne.”? ‘Kwallah ce take kokarin zubo min na daure nace.”Lafiya ta lau.” Yace.”Okey ki bawa Gwaggo mu gaisa a gurguje zan fita gurin wasa ne.” Nace.”Khalid Gwaggo tana bacci.” Jim yayi kafin yace.” Tunda nake banta’ba ganin Gwaggo na bacci da safe ba a daidai wannan lokacin take zaman kad’i tana sauraran redio aunt Sa’ida ko dai da akwai abinda kike ‘boye min.”?

Nace.”Khalid Gwaggo ba ta jin dadi ne shiyasa tana karya kummalo tasha magani ta kwanta bacci ya dauketa.” Cikin jimami yace.”Allah sarki Gwaggo ki gaishe min da ita idan mun fito daga wasa zan sake kira.” Nace.”Tom shikkenan.” Kokarin kashe wayar nake ya shigo dakin cikin dakakkiyar shaddar galila kamshin turaransa ya game ko’ina har ya karaso inda nake ban dauke idona daga kansa ba cikin zuciyata nace”A zahiri cikakken mutum amma a bad’ini malalaci ne.

Gaishe shi nayi ba tare dana kalleshi ba, ya amsa yana duba agogon hannunsa da fad’in “Dawa kike waya ne.”? Gabana ne ya fad’i ! nace” Khalid ne.”? Jim! yayi yana kallona da fad’in “Menene zai kira ki da sassafe haka.”? Nace.” Wai yana so su gaisa da Gwaggo ne.” Yace.”Ita Gwaggon bata da waya.”? kaina na daga masa.

Ya wani ‘bata rai da fad’in “Kada ki kuskura ki sake d’aga wayarsa a cikin gidana.” Kai tsaye nace “Sabida me.”? yace.” Tambaya ta kike.”? na kalleshi ido cikin ido nace.”Eh.” girgiza kansa yayi yace.”Yaron nan fa nasan mun had’a takara dashi gurin neman auranki to mai zai sanya na zuba ido na barki kina mu’amula dashi.”

Cikin takaici Nace.”Alhaji da kuka had’a takara da Khalid wa na za’ba a cikin ku.”? ‘Kirjinsa ya nuna da hannu da fad’in “Ni kika za’ba.”

Nace.”To meye naka na kishi da damuwa Khalid dan uwana ne na jini ba zaka rabamu ba.”

Rai a ‘bace yace.”Yanzu dai nasan kin san da cewa a karkashina kike ko.”? Nace.”Eh yace.”To idan na isa kada ki sake daga wayar yaron nan.” cike da d’umbin mamaki nake kallonsa. ya girgiza kansa da fad’in “Ni zan tafi kasuwa.” shuru nai masa. yayi murmushi wanda shi kadai yasan manufarsa ya kama hanya ya fita daga dakin ya barni cikin d’umbun mamakin sa.

Bayan fitar sa na jima
ina sa’ke-sa’ke kafin na yanke shawarar kiran Hauwwa a waya idan da hali tazo mu tattauna domin a gaskiya ina bukatar mai bani shawara akan wannan gagarimar matsalar

Jin yanda nake magana a sanyaye yasa itama tasha jinin jikinta tace.”Sa’ida lafiyarki kalau kuwa.” Nace.”Hauwwa lafiya ba lafiya ba dan Allah idan an tashi kizo zamuyi magana.”

Tace.”Sa’ida kina ganin babu matsala ko? bana so ina zuwa gidan mata biyu gudun zargi kin san dai yanda rayuwar nan take wata matsalar tana iya faruwa ace ni ce”

Nace.”Haba Hauwwa wace irin magana ce wannan me zai faru da har sunanki zai fito dan Allah kizo babu damuwa Aunty Murja tana da saukin kai.

Tace.”To shikkenan idan an tashi zan shigo.” nace.”Okey to ina sauraranki.”

Kashe wayar nayi na ajiyeta kan mirror na futa falon, shuru babu kowa da alama yaran sun tafi makaranta tunda litinin ce. gurin cin abinci na nufa naja kujera na zauna wato dai nice bare a gidan nice wacce bata da mutunci da galihu ban isa a zauna tare dani a ciki abinci ba tabbas badan kada na cutar da kaina da yunwa ba to da babu abinda zai sanya na zauna naci abincin gidan amma babu komai karshen wata na dauki albashina zan sayi komai nawa na dinga ciyar da kaina wannan shawarar na yanke a cikin raina.

To har na gama breakfast din Aunty Murja bata sauko ba sai kawai na yanke shawarar hawa saman na gaisheta.

Na jima a bakin kofar ina knocking kafin naji motsinta ta bude kofar dakin muka had’a ido da juna.

Fuskarta a sake tace.”Aa Sa’ida kece ashe shigo mana.” Kasa shiga nayi sabida nauyi tana sanye da wani gajeran wando da riga mai kamar breziya da madauri a wuya nonowanta duk a waje bayan ta ma haka.

Na tsaya daga bakin kofar da fadin”Dama naji shuru baki sauko ba nace bari nazo mu gaisa.” Murmushi tayi tace.”Kin ga ni wallahi tunda nasha maganin mura ya kashe min jiki nake ta bacci mijinki ma ban san lokacin daya fita ba.”

Nace.”Ayya sannu Allah ya sawa’ke.” ta amsa da “ameeen da fad’in ” Ki shigo mana.” cikin ya’ke nace”Aa aunty zanje nayi ayyuka a dakina ne anjima idan na gama sai nazo muyi hira.”

Tace.”Tom shikkenan babu damuwa.” sallama nayi mata na sauka ina kokarin shiga dakina naji sallama da sauri na juya domin na dauka Hauwwa ce. wata hamsha’kiyar mata ce taci kwalliya har ta gaji kana kallonta kasan naira ta zauna..

Nace”Sannu da zuwa hajiya.” ta amsa fuska a sake tana min wani irin kallo kafin tace.”Kece amaryar Murja ko.”? nace.”Eh nice amma ke d’in ‘yar uwarta ce ko dan naga kuna kama.”

‘Yar dariya tayi tace”Haka mutane suke fada Aa Murja ba ‘yar uwata bace ta jini ‘Kawata ce dai.” Nace.”Ayya sannu da zuwa tana sama sai ki hau ki sameta.”

Tace.”Okey babu damuwa.” Juyawa nayi domin bude dakina naga ta bini da kallo tana murmushi, al’amarin ya dinga bani mamaki! irin murmushin da Aunt Murja takeyi min matar ma irinsa take……..Gefen gado na zauna abun na cigaba daure min kai.

‘Karfe biyu shaura Hauwwa ta karaso gidan, bayan mun gaisa ta dinga bina da kallo tana girgiza kanta kafin tace.”Sa’ida kwana biyu kacal naga duk kin sanja kin wani hargitse dan Allah me yake damunki.’?

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Hauwwa matsala mai girma nake fuskata a gidan nan.” Zama ta gyara tana kallona, idanuwa na suka ciko da ruwan hawaye na shiga bata labarin abunda ke faruwa.

Kanta kawai take girgizawa kafin tace.” *AI GA IRINTA NAN!* Sa’ida babu irin shawarar da ban baki ba akan mutumin nan kika rufe idonki kika aureshi gashinan kwana biyu kacal ya nuna miki akuyanci me ake da auran irinsu Alhaji Nura kayan ba’kin ciki da takaici ai wallahi gwara na auri ‘karamin yaro na raine shi nasan komai rintsi ni zan mora amma duba dan Allah kwana biyu da yin aure kin zama tamkar wata zautacciya.”

Nace.”Hauwwa dan Allah ki bar wannan maganar Alhaji Nura fa lafiyarsa lau tsabar iskanci ne da wulakanci yasa yake min haka tunda ai na fad’a miki hujjarsa ta ‘kin sakin jiki dani saboda kada na haihu bayan sun tsara rayuwarsu shi da matarsa.”

Tsaki taja tace.”Eh ai na fahimta mayaudarin banza da wofi kawai to ke yanzu wace shawara kika yankewa kanki ko kina nufin a haka zaki cigaba da zama da sha’awa.”

Nace.”Shine ai na kira ki domin ki bani shawara.”

Shuru tayi na minti biyu kafin tace.” Sa’ida ki rabu da mutumin nan shine alkairi a gare ki ni dai wannan shawarar ita zan baki.”

Gabana na wani irin fad’uwa nace.”Hauwwa wace irin magana ce wannan? aure kwana biyu ki fadi irin wannan maganar gaskiya bata dace ba ki bani shawarar arziki mana.”

Dariya tayi tace.”Duk wata shawarar da zan baki bayan wannan take wallahi idan kika cigaba da zama da mutumin nan zuciyarki sai ta buga irinsu suna nan da yawa masu kashe matansu da bakin cikin su.”

Shiru nayi ina kallonta tace.”Idan kuma kinga ba zaki rabu dashi ba to sai ki dauki tsatstsauran mataki a duk lokacin daya kusance ki sai ki hana shi tunda zalinci baya barin sa ya biya miki bukatar ki.”

Nace.”To kinga wannan shawarar ita zan duba a cikin shawarwarin ki amma maganar kashe aure sam bata taso ba.”

Tace.”Tom shikkenan sai ki kwada ki gani mybe idan kikayi masa butsu ta wannan hanyar zai dinga dogon zango a kanki tunda kin ce lafiyarsa lau ba rashin kuzari bane wulakanci ne irin nasa.

Murmushi nayi nace.”Hakane Hauwwa Alhaji Nura ragal yake kawai ‘keta ce nima kuwa zan gwada masa tawa.” Dariya tasa ta bani hannu muka tafa.

Sai da tayi sallah la’asar muka ci abinci sannan tayi shirin tafiya, tare muka fito falo wanda yayi daidai da saukowarsu daga sama.

Nace.”Hauwwa ki tsaya ku gaisa da aunt Murja ko.” Tace.”Okey babu damuwa.

Muna tsaye suka ‘karaso dukkaninsu fuskarsu a sake da walwala aunty Murja tace.”Ashe kema bakuwa kikayi.”? Nace.”Eh wallahi ‘kawata ce Hauwwa gurin aikin mu daya.”

Tace.”Ayya Sannu.” Hauwa ta amsa da “yawwa aunty ya gida ya yara.”? tace.”Alhamdulillahi.” Hajiya Aziza na murmushi tace.”Ai sai muje na rage miki hanya ko.”?

Hauwwa tace.”Nagoda hajiya amma nima ina da abin hawa.” Tace.”Okey to babu damuwa sai mu fita tare ko.” Tace.”Eh hakan yayi.” Ta kalleni da fad’in “Sa’ida sai munyi waya kenan amma yaushe zaki koma gurin aiki.”? Nace.” Insha Allahu sati na sama.” tace.”Tom shikkenan Allah ya bamu alkairi.” Nace.”Ameeen ya Allah nagode k’awata.” Aunt Murja tace.”Muje mu taka musu.” bayansu muka bi kowacce ta shiga motar ta suka fita daga gidan muna daga musu hannu da fatan alkairi.

Tare muka koma gidan ita ta hau sama ni kuma na bude dakina na shiga ina tunanin shawarar da na yanke akan abinda yake faruwa.

To yau ma dai ban san lokacin da ya dawo ba sai da na fito falo na same shi a zaune suna hira da ita ga yaran su suna wasa, tsabar haushi da takaici ya hana ni kulashi ballantana nai masa sannu da zuwa.

Gurin cin abinci na zauna naci na koshi na bar gurin ita kanta aunty Murjan haushinta nake ji sabida na gane itama fuska biyu gareta.

Sai da bacci ya soma daukata ya shigo dakin, na dinga kallonsa ina daga kwance har ya gama shirye shiryen sa yazo ya tsaya a kaina…..”Sa’ida wacece tazo d’azu.”? tambayar da yayi min kenan….Na mike zaune ina kallonsa ya sake maimaimata maganarsa.” Wacece tazo gurin ki d’azu.”? Nace.”Kai waye ya fad’a maka wata tazo.”? a fusace! ya daga min hannu da fad’in “Wace irin magana ce wannan a maimakon ki bani amsar tambayata sai kuma ki tambaye ni..

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_

*45&46*
Raina ne ya ‘baci ganin yanda yake daga murya sama kamar zai doke ni nace.”Kayi hakuri dan Allah ni banga abin daukar zafi ba idan kana so kasan wacce tazo guri na sai kaje ka tambayi wacce ta fada maka cewa yau nayi bakuwa.”
Wani irin kallo yake min yana girgiza kansa yace.”Sa’ida ashe baki da kunya dama? ni kike fadawa wannan maganar?
Hawaye na share nace.”Alhaji wace magana na fada maka mai zafi! al’amarin ne ai ya bani mamaki kuma banta’ba tsammanin aunty Murja fuska biyu gare ta ba.”
Yace.”Okey yanzu mai kike nufi.”? kai tsaye nace.”Ina nufin abubuwa da yawa.” Girgiza kansa yayi kafin yace.”Ni ban hana wani naki yazo gidan nan ba kawai dai sintiri ne bana so inace duka-duka yau kwanan ki biyu da tarewa a gidan nan mai zai sanya a fara yi min sallama a gida.

Fuskata na goge nace.”Babu wanda zan hana shi zuwa cikin gidan nan tunda dai kasan ina da jama’a bayan haka kuma ina da ‘yan uwa da dangi masu yawa saboda haka ni dik wanda yazo gurina ina maraba dashi.”

Rai a ‘bace yace.”Ni kike d’aga wa murya ko.”? shuru nayi yace.”To bari ki ji abinda baki sani ba Murja da kike gani ta fiki ‘yan uwa da dangi da jama’a amma saboda tana bukatar zaman lafiya dani tabi doka ta a kan dauki dogon lokacin kafin kiga wani dan uwanta a cikin gidan nan saboda haka kema yana da kyau ki kiyaye.

Nace.” ‘Karya take aunt Murjan.” cike da mamaki yake kallona.

Na cigaba da cewa” D’azu itama ai tayi bak’uwa mai yasa bata fada maka ba saboda ita ta cika munaf*ckace magulmaciya.”

“Murjar kike kira da wannan sunaye.” ? a hasale nace.”Eh ita din fa ai ta amsa duka sunayen.”

Rai a ‘bace ya juya ya fita daga dakin. tsaki naja mai karfi da fadin”Mijin tace kawai.”

Koda ya fita daga dakin kai tsaye bene ya hau ya sameta a kwance da wayarta a hannunta tana latsawa, ganin shigowarsa yasa tayi saurin kashe wayar ta ajiyeta ta mike zaune tana kallonsa.

Zama yayi kusa da ita rai a dagule! ta dafa kafadarsa da fadin “Abban Yusura ya akayi ne naga ka shigo fuska a ‘bace.”

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Murja na lura yarinyar nan Sa’ida bata shigo gidan nan da sigar son zaman lafiya ba kamar ni zata tsaya tana jayayya dani akan hukuncin dana yanke a gidana saboda na kawo mata misali dake shine take zagin ki.”

Murmushi tayi alamun abun bai mata ciwo ba tace.”Sai hakuri Abban Yusura kasan ko wace mace da irin halinta wallahi nima yau haka ta yini tana yar min da habaici ban san meye dalili ba amma dai ka cigaba da hakuri da halinta.”

Yace.”Ai kuwa zata gane kuskuranta Murja babu wata mace da zan aura ta taka martabarki ban nuna mata kuskuranta ba saboda haka na bar dakinta har sai na koya mata hankali.”

Murmushin samun nasara tayi tace.”Haba Abban Yusura kayi hakuri dan Allah ka koma dakin kaga amarya ce ka cigaba da rarrashinta.

Hannu ya daga mata yace.”Murja kin san bana magana biyu ko saboda haka ki bar maganar kawai ni nake auran Sa’ida ba ita ke aurena ba dan haka zan nuna mata cewa ni cikakken namiji ne.”

Tace.”To shikkenan tunda kace haka sai dai nace Allah ya kyauta ya rufa asiri.” shuru yayi bai amsa ba ya nata wani muzurai kamar gaske.

Nayi ta tsammanin dawowarsa dakin naji shuru cikin takaici da bakin ciki na kwanta da kyar bacci ya dauke ni.

Na d’auka da safe zai shigo mu gaisa naji shuru har goma da rabi babu labarinsa, falon na fita shuru matar gidan na sama yara kuma sun tafi makaranta.

Jiki a sa’bule na zauna gurin cikin abincin.

haka na yini cikin ‘kunci da damuwa ga Khalid ya ishe ni da kiran waya lallai sai na bashi Gwaggo sun gaisa sai da nayi masa jan ido sannan ya rabu dani muka rabu cikin Jin haushin juna.

Haka na cigaba da kasancewa a gidan Alhaji Nura tsayin sati guda babu wani zaman Arziki a tsakanina dashi, tun ranar da mukayi musayar yawu dashi bai sake shigowa dakina ba haka nan kuma idan zan ganshi a falo na gaishe shi baya ko kallon inda nake ballantana ya amsa min gaisuwata.

Sosai na shiga cikin tsaka mai wuya nadama mara amfani duk ta buwaye ni gabadaya kaina ya kulle na rasa wane irin tunani zanyi.

Ranar Lahadi nasan baya fita kasuwa da wuri sai na fito falon na samesu suna zaune suna hira na zauna kan kujerar dake fuskantarsu a nutse nace.”Aunty Murja kin tashi lafiya ya kwanan su Yusura.”
Ta amsa fuska a sake kamar ko da yaushe….kallonsa nayi yana duba jarida wanda zama na a gurin ne yasa shi daukar jaridar “Barka da asubah Alhaji.”
Ciki ciki ya amsa hankalinsa nakan jaridar nace.”Ina so zanyi magana da kai.” ba tare da ya kalle ni ba yace.”Ki fada ina sauraranki.

Shuru nayi na minti biyu kafin nace.”Akan maganar aiki na ne dama hutun sati biyu suka bani to kaga yau sati na uku ban je ba shine nake so insha Allahu gobe zan koma bakin aiki.”

Ba tare da ya kalleni ba yace.”Babu maganar aiki a gidana tunda da ban gaza da komai ba saboda haka ki ajiye maganar aiki a gefe mutukar ni nake auranki na soke maganar zuwa gurin aiki.”

Wani irin gumi! ya shiga yanko min murya na rawa nace.”Alhaji wannan wace irin magana ce? kada ka zama ‘karamin mutum mai magana biyu mana ya za’ayi muyi da wajewa da kai kafin muyi aure amma sai bayan bukatarka ta biya sai kuma ka sanja magana.”

A fusace! ya daga min hannu da fad’in “Sa’ida me kike so ki mayar dani ne? wato nine ma nake magana biyu.”? Cikin rawar baki nace” Eh hak…….’Barin makauniya yayi a fuskata! nasa hannu na dafe kumatuna ina mamakin sanda yazo inda nake har ya samu nasarar mari na.

Yana tsaye a kaina yana huci da kumfar baki sai bambami yake Ita kuma gwanar tasa tana rirrikeshi tana bashi hakuri da fad’in “Haba Sa’ida ashe haka kike da tsayayya me ya sanya zaki dinga jayayya da mijinki.”

Cikin b’acin rai na mike tsaye da fad’in “Kinga saurara aunty Murja nifa ba ‘kan’kanuwar yarinya bace ballanatana ki dinga wasa da hankalina duk abinda yake faruwa a gidan nan da sanya hannuki a ciki saboda haka kiyi shuru da bakin ki bana son munafurci.”

Kalar tausayi ta koma da fad’in “Sa’ida ni kike kira munaf*cka.” Cikin rawa murya nace.”Idan ba ita bace mecec….Marin dai ya k’ara kawo min na kauce da sauri ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata nace.”Wallahi dana san kai mijin tace ne a gidanka da ban aureka ba.”

Yana numfarfashi yace.”Ki fice min daga gidana.” da sauri tace.”Subahanallahi Abban Yusura kada ka yanke wannan hukuncin.

Rai a ‘bace yace.”Murja na fada miki babu wata mace da zan aura ta ta’ba martabarki na ‘kyaleta saboda haka mutukar Sa’ida tana bukatar ta zauna lafiya dani to sai ta baki hakuri.”

Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa wato sai na bata hakuri sannan zai zauna dani lafiya. kallona yayi yace.”Ki bata hakuri ko bakya ji ne.”

Kaina kawai na girgiza ba tare da nace komai ba na kad’a kaina na bar gurin.

Dakina na shiga na samu gefan gado na zauna kuke ne ya ‘kwace min na dinga yi ina girgiza kaina wannan takaici da bakin ciki har inaa! lallai babu shakka dole na bar masa gidansa domin ba zan zauna bawa wata ‘yar iska hakuri ba.

Sai da naci kuka na na koshi tukkuna na shiga toilet na wanke fuskata kaya na na hada cikin akwati nasa hijabi na na fito.

Har yanzu suna zaune a falon suna mayar da magana kai tsaye hanyar fita na nufa. ina kokarin bude kofa tazo ta rike akwatin hannuna. “Haba Sa’ida mai yayi zafi haka dan Allah kiyi hakuri kada ki tafi abun kunya ne ace aure sati uku kacal har an fara yaji sam bai dace ba.

Akwatin kaya na na fizge daga hannunta nace.” Aunty Murja ai zama da Alhaji Nura sai ke kamar yanda ya fada cewa komai naku a tsare yake keda shi to bai kamata wani yazo ya rusa muku tsari ba kamata yayi ace ku biyu kacal zaku zauna sai ‘ya’yanku.

Girgiza kanta ta shiga yi kamar wata mutuniyar arziki sai hakuri take bani shi kuma yana zaune ‘kwam akan kujera na d’an hango nadama a fuskarsa amma tsabar girman kai ya hanashi yayi magana.

Ganin ta juya ta nai masa magana yasa da sauri na kwace akwatina a hannunta na bude kofa da sauri na fita.

Gwaggo na zaune a tsakar gida da kayan kad’i a gabanta gefe guda kuma tana sauraran redio tashar freedom suna gabatar da shirin barka da hantsi….Ummatu na bakin rijiya tana wanke-wanke suna hira yanzu tsakanin Gwaggo da Ummatu an samu daidaito sun daina fad’a kullum suka zauna hirar Khalid da Sa’ida suke gabadayansu suna cikin alhinin rabuwa dasu…….Gwara Khalid suna gaisawa dashi dan da ya gaji da kiran wayar Sa’ida tana yi masa yawo da hankali kawai sai ya yanke shawarar kiran wayar mahaifiyarsa su gaisa sannan ta bawa Gwaggo itama su gaisa.

Khalid bai samu damar zuwa gidan ba sabida yanda Oga Laraban da sauran abokanansa suka taushe shi gami da nuna masa muhimmacin abinda ke gabansu, a cikin satin daya gabata Mr William yazo daga america aka gabatar da shahararran wasan daya daukaka ‘kungiyar kano pillars Khalid dashi da Ahamad Musa sunyi kokari sosai kuma sun zama zakaran gwajin dafi domin sune suka cinye kofin da ko wane team suke ‘kwa’kwa Oga Laraban tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha sabida tsabar murna da farin cikin kungiyarsa ta cinye kofi……To wannan dalilin ne yasa bai samu damar zuwa gidan ba a lokacin daya fad’a zai zo sai yanzu da hankalinsu ya kwanta suka shirya tafiyar shida Salmanu.

Sallamar ta a cikin gidan itace ta katse musu hirar da suke. gabadaya suka bita da kallo a lokacin da take shiga gidan da akwatin kayanta a hannunta.

Gwaggo a sa’bule ta amsa sallamar ta cigaba da bin ta da kallo har ta cire takalmanta ta shiga daki ba tare da tace musu komai ba.

Ummatu tace.”Gwaggo anya lafiya kuwa Sa’ida ta shigo jiki a sab’ule ga kuma a kwati a hannunta.

Gwaggo ta ajiye makad’in hannunta ta yunkura da nufin mi’kewa tace”Aa Rabi ai wannan zuwan na Sa’ida ba na lafiya bane kina ganin ta shigo gidan kai tsaye ta shiga daki bari nabi bayanta.

Ummatu shuru tayi jikinta duk ya mutu……..Kuka ta shiga ta same ni inayi. a sanyaye ta tsaya kaina da fad’in “Sa’ida me yake faruwa? kada kice min Alhaji Nura ya sake ki bayan ya tabbatar da babu budurci a tare dake.”?

Kaina na girgiza nace.” Gwaggo Alhaji Nura Bashi da kirki ashe mijin tace ne a gidansa sai abinda matarsa tace dashi.”

Ajiyar zuciya ta sauke ta nemi guri ta zauna da fad’in “Wallahi na dauka ko saboda rashin budurci ne ya koro ki gida ashe ba wannan matsalar bace.”

Girgiza kaina nayi nace” Ba wannan matsalar bace Gwaggo……..Tiryan tiryan na fad’a mata dukkanin abubuwan da suke faruwa ban rage mata komai ba

Gwaggo ta dinga mamaki tana girgiza kanta tace.”Ashe duk kirkin matar nan da jama’a suke fad’a na gaibu ne ashe fuska biyu gare ta.”

Nace.”Wallahi kuwa Gwaggo aunty Murja muguwar makira ce shi kuma kamar tsoronta yake duk abinda tace shine daidai wai dole sai na bata hakuri sannan zan zauna a gidan Gwaggo babban abinda yafi tayar min da hankalina shine maganar gurin aikina wai bai yarda na k’ara zuwa ba.”
Gwaggo shuru tayi tana girgiza kanta gami da jajanta al’amarin.

*Kuyi manege babu yawa ana bikin ‘yar yar Mamana sannan yau ma kuyi min uziri ba zaku samu na dare ba nagode*
*47&48*
Gwaggo tace.”Yanzu dai kiyi hakuri ki daina kuka zamu jira Ibrahim ya dawo domin muji hukuncin da zai yanke amma gaskiya Alhaji Nura ya bani mamaki ashe mace ke juya shi.” Nace.”Gwaggo ai ba kiji mamaki da takaici ba sai kinga abin da idonki.” Tace.”To Allah ya sawake yasa ya zama jajurtacce a gidansa.
shuru kawai nayi ina tunanin abinda zai biyo baya.

To koda Kawu ya dawo ya samu labarin a binda yake faruwa shima ransa ya ‘baci sosai da irin abinda Alhaji Nuran yake a gidansa ya kalleni cikin kulawa yace.”Kiyi hakuri kinji ko yanzu za mu jira zuwan sa domin shime muji da abinda zai zo amma maganar zuwa aiki ki ajiye ta tunda dai baya so sai ki hakura.”

Cikin kuka nace.”Kawu ya za’ayi na saki aiki na bayan kafin auranmu sai da mukayi da wajewa dashi ya amince zan cigaba da aiki na sai kuma yanzu yazo ya sanja magana.”

Yace.”Sa’ida aikin nan ba dole bane tunda Allah ya rufawa mijinki asiri baki da wata matsala sai ki hakura ki zauna kiyi zaman auranki lafiya.”

Hawaye na share ina jin wani irin d’aci a ma’kogwarona anya kuwa zan iya hakura da aiki na kuwa.”

Washe gari da sassafe Ummatu ta shigo da waya a hannunta tana fad’in “Gwaggo Khalid ne ya kira yanzu yanzu yake sheda min cewa yana kan hanya.”

Cikin farin ciki ta mike zaune tare da kar’bar wayar tana dubawa kamar wacce za ta ganshi a cikin wayar sai washe baki take da fadin”Allah ya sauke shi lafiya kamo min shi mu gaisa.” Ummatu ta karbi wayar da fadin”Lokacin da ya kira babu network sosai da ‘kyar ma naji abinda yake fada amma bari na sake kiransa naji.

Wayar ta dinga katsewa ta kalleta da fadin” Taqi shiga wayar bari idan anjima sai mu sake gwada kiransa.” Tace.”To shikkenan.” Ummatu fita tayi daga dakin cike da farin ciki. Ita kuma ta shiga kiran sunana “Sa’ida kina ji ko Khalid na kan hanya.” Shuru nayi mata gabana in banda faduwa babu abinda yake sam! bana so yaron nan yazo ya same ni a gidan ba.

Ido na bude da fadin”Gwaggo naji Allah ya kawoshi lafiya.” Ta amsa tana ‘yar dariya had’e da fadin “Ni kuwa dame zan tar’bi yaron nan.”?

Shuru nayi mata tace.” Sa’ida kina jina ina magana ko nace me kike gani zan shiryawa Khalid na tar’ba.”?

Nace”Kiyi masa girki mai dadi mana amma kisa nama kin san halinsa kamar kure haka yake.”

Dariya tasa da fad’in “Ni kuwa yaushe zan kasa fito da kudi na siyi naman miya bari anjima kadan sai naje gurin Isiyaku mai kayan miya nayi cefane.”

Cikin zuciya ta nace.”Aiki ya same ki. Kawu ne ya daga labulan dakin da sallama a bakinsa gabad’aya muka amsa na mike zaune ina gaisheshi so kawai nake naji yayi magana akan Alhaji Nura.

Kayan tea din dake Hannunsa ya ajiye kusa da Gwaggo da fadin” Gwaggo ga kayan shayi nan yanzu Rabi zata kawo muku ruwan zafin sai ku had’a ku karya.

Tace.”Ibrahim me zai sanya kayi asarar kudin ka kasan ni fa bana ra’ayin cin wannan fulawar d’aure min ciki take.”

Yace.”Gwaggo yau dai d’aya ai sai ki daure kisha saboda Sa’ida yasa nace yau Rabi tayi muku shayi.”

Nace.”Kawu nima zanfi sha’awar kunun ai.” Yace.”To babu laifi Allah ya kaimu gobe sai ayi miki.”

Kokarin fita yake Gwaggo tace.” Ibrahim d’azu Khalid fa ya kira wayar uwarsa yace yana kan hanya.”

Babu yabo babu fallasa yace.”To Allah ya sauke su lafiya.” ta amsa da ameen tana dariyar farin ciki. har ya fita daga dakin ba tayi masa maganar data dangance ni da aurena ba, raina ya ‘baci sosai da kyar na iya had’a tea din nasha na koma na kwanta ina tunanin mafita………Wato dai dama Alhaji Nura ba wani sona yake ba sha’awata yake tunda gashi tun ba’aje ko’ina ba har gishiri ya salance daga jiki kaza, zuciyata tace dani yanzu da ya samu budurcin ki ma wannan wulakancin zaiyi miki, kawai sai naji ina jin dadi da Allah yasa bashi ya samu budurcina ba domin akwai takaici ace ya samu abu mai muhimmanci a tare dani amma ya dinga wulakanta ni akan matarsa.

Ina can duniyar tunani Gwaggo ta gama kujigaba-kujigabarta tasa hijabi ta tafi cefane, sai fitowa tsakar gida nayi na sameta ta baza kayan miya a gaba gefe guda kuma ta hura huta a kurfoti (mangal) ta d’ora kasko tana ta soya nama. cikin takaici da bacin rai na dauki buta na shiga bandaki nayi uzirina na fito ta kalleni da fadin”Sa’ida kina gani aiki ya cakud’e min ba zaki taimaka min ba.”

Ba tare dana kalleta ba nace.”Gwaggo kaina ne yake ciwo.” bina tayi da kallo kafin tace.”Dole kanki yayi ciwo mana tun jiya kike kuka sai kace Alhaji Nura ne autan maza a duniya duk kin damu kan ki.”

Nace.”Gwaggo dole nayi kuka na shiga damuwa mana tun jiya mutumin nan bai kira waya ba kuma bai zo ba ai dole hankalina ya tashi gashi Kawu yace dole sai na hakura da aikina.”

Tace.” Sa’ida nifa wani sa’in bana jin haushin abinda Alhaji Nura yayi miki dama hausawa suna cewa duk wanda ya sayi rariya yasan zata zubda ruwa haka kurrum kika ‘ki d’an uwanki kika za’be shi *AI GA IRINTA NAN!* Tun kafin aje ko’ina ya nuna miki halinsa.”

Hawaye na share nace”Gwaggo dan Allah ki daina wannan maganar kada ki sake tunzura min zuciyata Khalid yana d’aya daga cikin mutanan da suka hana ni samun kwanciyar hankali a gidan aure na.”

Kallonta tayi baki a bude tace.”Au! tana nan kuma kika ‘bullo.”? Da sauri nace.”Eh Mana Gwaggo da Khalid bai raba ni da martaba ta ba, to bana tsammanin Alhaji Nura zai yi min irin wannan wulakancin.”

Shuru tayi ba tace komai ba ta cigaba da gyara kayan miya, labulan dakin na daga na shiga na zaune tare da daukar waya ta ina duba gurin text burina kawai naga wani sa’ko daya dangace shi, abin takaici text din Khalid na gani har biyu inda yake sheda min cewa zuwa La’asar zasu sauka.
Ajiye wayar nayi ba tare dana bashi amsa ba.

Kafin La’asar Gwaggo da Ummatu sun gama aiki tsaf sun shirya masa abinci har kala uku da zo’bo wanda suka sa masa k’ankara Gwaggo sabbin kwanikan ta na silba ta dauko aka jere masa kayan abincin a guri guda yanzu shi kadai kawai ake jira…..Al’amarin ya dinga bani mamaki yana daure min kai ganin yanda suka shirya masa guri sai kace wani cikakken mutun magidanci gabadaya tsabar haushi da kishi naji zaman gidan ya fita min a rai sai kawai na hau shirye shirye ta kalle ni da fad’in “Ina kuma zakije da yamma.”?

Nace.” Zanje can gidan Ummana ne.” Girgiza kanta tayi fuska a ‘bace tace.”Aa Sa’ida ba zaki mayar damu ‘kananun mutane ba da auran mutum akanki ki dinga yawo.”

Nace.”Gwaggo gidan Ummana fa nace zani ba wani guri ba.”

Tace.”Eh ai na fahimta babu inda zakije har sai munji ta bakin mijinki tukkuna.”

Takaici yasa kawai na zuba mata ido ina kallonta. Kayan kad’inta ta dauka tana gyarawa mukaji sallamar yara a cikin gidan.

Gwaggo da sauri ta amsa tare da daga labulan dakin……..Yaran sun kai su hudu biyu buhu ne a kawunan su biyu kuma jarkokin manja da man gyada ne a hannuwansu.

Gwaggo tace.”Waye ya aiko ko da wa’innan kayan.” Daya daga cikinsu yace.”Khalid ne ya dawo yana waje shida abokanansa.”

Da sauri ta cilar da kayan kad’in ta miqe tana fadin”Alhamdullilahi Allah nagode maka.” Hijabi tasa ta kama hanyar fita Nace.”Gwaggo ai kya bari ya shigo ko.”

“Aa Sa’ida gwara naje na tar’beshi.” tafada tana kokarin fita, kallo na bita dashi ina girgixa kaina.

Gwaggo na kokarin fita suka buga karo. rungumeshi tayi sai kuma ta fashe da kuka tana kiran sunansa….Hannunta ya rik’e yana rarrashinta suka shiga gidan

Ummatu na tsaye a bakin kofar ta fuskarta yawalce da fara’a take kallon yaron nata sai taga duk ya sanja ya kara girma da hasken fata….Yace.”Ummana kina mamakin ganina ko.” Murmushi tayi tace.”Khalid dole nayi mamaki.” Cikin jin nauyi ya sunkuyar da kansa kasa yana gaisheta ta amsa cike da kulawa.

Ya shiga gogewa gwaggo hawaye yana fad’in “Gwaggo dan Allah ki daina kuka haka ai gani na dawo cikin koshin lafiya dan Allah ku gafarce ni.”

Ta dinga kallonsa tana girgiza kai tace.”Khalid na kuwa sheda haka tunda gashinan na ganka kayi girma ka sanja kayi haske sosai kamar wanda yake cikin hutu.”

Murmushi yayi yace.”Gwaggo godiyar Allah ce kawai da kuma tasirin adduoin da kuke min shi ya janyo haka.” Tace.”To Alhamdulillahi Khalid naji dadin ganin ka cikin koshin lafiya gashinan harda abin arziki.” Tafada tana bin kayan dake jibge a tsakar gidan.

Yace.”Gwaggo na san ki da son doya shiyasa na siyo miki buhu guda.” Dariya tasa da fadin”Aikuwa naji dadi d’an albarka Allah ya ‘kara maka wadata.” ya amsa da ameeen ya rabbi.

Tace.”Muje daki kaci abinci ka huta ko.”? yace.”To uwagidana.” murmushi tayi ta rike hannunsa suka kama hanyar dakin….Ummatu kuwa murmushi tayi cike da farin ciki ta shiga gurinta.

Jin motsin shigowarsu dakin yasa da sauri na daidaita nutsuwata ba tare dana dago kaina ba na amsa sallamar shi.

A jikina naji cewar kallona yake a fizge na daga kaina na kalleshi yana sanye da k’ananun kaya kamar ko da yaushe sai kawai na tsinci kaina da kasa dauke idona daka kansa mamakin girmansa nake wata biyar kacal yaro ya sanja ya zama ‘kato dashi da gaske ya sake girma da hasken fata.

A nutse ya zauna inda aka tanadar masa Gwaggo sai wani ji dashi take tana gyara masa gurin zama, shi kuma gabadaya hankalinsa na kaina ina kallonsa ta gefan ido sai kallona yake.

“Auntyna ba zakiyi min barka da zuwa.” maganarsa naji ta daki kunnena.

Na kalleshi babu yabo babu fallasa nace.”Khalid ya hanya.”? fuska a sake yace.”Alhmdulillahi aunty ya fargaba da alhinin dana tafi na barki dashi.”?

Share maganar nayi na dauki waya ta ina dubawa.

Gwaggo ta hau bude kwanunkan dake gabansa tana fad’in “Jarumi kaci abinci gashinan.” Yace.”Gwaggo duk wannan nau’in abincin duk ni kadai.”

Tana mirmushi tace.”Khalid kafi karfin komai a gurina burina kullum ka kasance cikin farin ciki.”

Yace.”To gwaggo naji dadi sosai ina rokon Allah yaja min da ranki.” Tana kokarin zuba masa abincin a plate ta amsa da ameen d’an albarka.

Abincin ta zuba masa da yawa tasa masa miya da uban nama. yace.”Gwaggo abincin nan yayi min yawa.” Tace.”Ka dai ci ka koshi.”

Kallona yayi cikin kulawa yace.”Auntyna zo ki taya ni ci.” Ko kallonsa banyi ba ballanatana na bashi amsa.

Tace.”Khalid rabu da ita don Allah kaci abincin ka.”

Girgiza kansa yayi yace.”Gwaggo ya za’ayi amaryata tana fushi kice na rabu da ita ko dai kishi kike.”?

Bani kadai ba Ita kanta Gwaggo sai da gabanta ya fadi! shuru tayi jikinta duk ya mutu data tuna da yaudarar da akayi masa.

Gani tayi ya mike daga inda yake ya dawo kusa dani ya zauna. ni da ita dik jikinmu ya mutu. a sanyaye yace.”Auntyna menene? ki fad’a min matsalarki gani na dawo na share miki hawaye.”

Kallonsa nayi zuciyata ta dinga tafarfasa! ina tuna irin cin mutuncin da yayi min a ranar da zai gudu! ‘kwalla ta cika kwarmin idona! kansa ya girgiza min cikin sigar rarrashi yace.”Kada kiyi min asarar hawaye domin yana da mutukar daraja a gurina ki gafarce ni auntyna nasan dole idan kika kalli fuskata ki tuna abinda nayi miki na rashin kyautawa.”

Bude baki nayi zanyi magana sai kuma kuka ya kufce min nasa hannu na gumtse bakina hawaye na shatata! jikinsa na wani irin rawa janyo ni jikinsa sosai ya rik’e ni yana kokarin goge min hawayen fuskata…Gwaggo tace.”Khalid sakar mata jiki kada kasa mu shiga fushin ubangiji kayi maza!maza ka sakar mata jiki.”
Da karfi take maganar tana kokarin mikewa tsaye!
Kasa’ke yayi yana kallonta hakan ya bani damar mi’kewa daga kusa dashi naje na samu wani gurin na zauna ina goge fuskata.

Yace.”Gwaggo wace irin magana ce wannan.”?

Girgiza kanta ta shiga yi tace.”Khalid da naso ka zauna kaci abinci ka samu nutsuwa in yaso sai na zaunar da kai na fada maka abinda yake faruwa amma yanzu tunda hakan be samu ba dole na fada maka halin da ake ciki…..A yanzu dai Sa’ida tana da aure kuma ba kowa take aure ba face Alhaji Nura wannan dalilin yasa kaga hankalina ya tashi a lokacin daka ri’keta a jikinka.”

Wani irin jiri ya dinga yi a zaune kansa ya dinga juyawa gabadaya ya nemi yawu ya rasa a bakinsa auntynsa tana da aure amma ta yaudare shi a waya tace ya dawo gida zata aureshi shin meye manufarta nayin wasa da hankalinsa.

Mi’kewa tsaye yayi jikinsa na wani irin rawa ya dumfari inda take zaune!…..tsorata nayi da ganin yanda ya tunkaro ni na mi’ke da saurin gaske Gwaggo na kokarin tare masa hanya da sauri ya kauce mata wuyana ya sha’ko ya had’a ni da bango (garu) ya matse ni sosai! ido jajawur! yace.”Ni zaki yaudara ko.”? Gwaggo hankalinta a tashe tazo tana kokarin janyeshi tana fadin.”Haba Jarumi ka sassautawa zuciyarka mana.” hannu ya daga mata a fusace! yace.”Gwaggo ki ‘kyaleni na kashe wannan mara imanin gwara na aika da ita barzahu tun kafin ta aika dani.” Yana gama maganarsa ya sake matse wuya na da jikin bangon.”

Gwaggo ta fashe da kuka hankali a tashe! ta fita daga dakin…………Khalid dai da gaske so yake ya kasheni dan yanda ya matse min wuya gabadaya ya hana ni fitar da numfashi, sai kawai na rintse idanuwana zafafan hawaye suka shiga kwaranyo wa a saman fuskata.

*49&50*
Hawayen dake sharara a saman fuskata bai sanya shi ya sassauta matsar da yayi wa wuyana ba, yana wani irin huci da zufa! yace.”Ni zaki yi wa haka ko? me yasa kin san an daura miki aure da wani zaki yaudare ni! kin mayar dani shakatafe sabida kina ganin ina sonki ko to wallahi ki rubuta ki ajiye sai na hana ki jin dadin rayuwa yanda kika hautsina min lissafi kema sai na hautsina naki sai na hana ki zaman aure da kowane mahaluki.” Yana maganar yana matse ni a jikin bango had’e da bubbuga kaina yanda jikinsa yake rawa sai ka dauka tsumin ‘yan bori yasha hannu nasa akan nasa ina k’okarin cire hannunsa ya sake shaqe ni da kyar nace.”Kashe ni kake so kayi ko.”?

Ido jawur! yace.”Meye amfanin mayaudariya kashe ki zanyi dan baki da wani amfani.” ya ‘karasa maganar yana sake ma’kure ni a jikin bango(Garu) Gwaggo da Ummatu suka shigo dakin hankalinsu a tashe.

Ganin yanda nayi wujiga-wujiga a hannunsa ya tsorata su Ummatu tazo tana janyeshi had’e da bashi baki ya sake ni! kansa ya sunkuyar k’asa tare da sassauta matsar da yayi min amma bai sake ni gabadaya ba.

Gwaggo tazo ta rike hannunsa a sanyaye tace.”Haba Jarumi ka zama mai hakuri da yarda da kaddara mana me yasa zaka aikata haka ka duba kaga yanda duk ka galabaitar da ita kayi hakuri ka saketa komai kaga yana faruwa to dama can haka Allah ya shirya.”

Ya kalleta da jajayen idanunsa yace.”Gwaggo wato har dake za’a hada baki a yaudare ni ko? me yasa kin san tayi aure baki fada min ba bayan kullum muna waya dake.”

Kallona tayi tana so tayi magana sai ta kasa nace.”Me yasa zakiyi shuru Gwaggo ki fada masa cewa nice na tsara haka in yaso sai ya dauko wuka ya soka min a ma’koshi.”
Raina a ‘bace nake magana.

Matse wuya na ya sakeyi ya tsira min rikitattun idanunsa, da ‘kyar nace.”Khalid ka kashe ni mana mai ka tsaya jira ne.” Shuru yayi bai ce komai ba ya dai zuba min idanunsa da nake hango ruwan hawaye a cikinsu.

Ummatu tazo ta cire hannunsa daga wuyana ai banyi wata-wata ba na fitar da hannu a zafafe zan kai masa mari!

Hannun ya rike ya murd’e da mugun karfi na saki ihu! ya yarfar min da hannuna yana huci! ya matsa daga gurin.

Tsugunawa nayi a gurin hawaye masu zafi na zubo min hannuna kawai nake dubawa kamar wacce tayi targade sabida zafi.

Gabad’ayansu kansa suka rufu suna bashi baki babu wacce tabi ta kaina. raina ya ‘baci sosai na kalli gefe na kwalbar cocar colar da Gwaggo kesa maganin sauro a kai na dauka a fusace na kai masa jifa da ita. cikin zafin nama ya kauce yana kallona.

Murya na rawa nace.”Wallahi sai kasan wanda kayi wa wannan iskanci Khalid sai na fad’awa Kawu yayi min tsakani da kai shashasha mara hankali kawai.”

Gwaggo a fusace! tace.”Wato ba zaki daina zaginsa ba ko.”

Nima a fusace! Nace.” Gwaggo abinda yafi zagi zanyi masa mutukar bai fita daga dakin nan ba.”

Tace.” ba zai fita ba din sai dai ke ki fita dama ai rashin hakurin ki ne yasa mijin naki ya koro ki gida.””

Cikin takaici da mugun bakin ciki nace.”Haka zaki ce ko.”? Da sauri tace.”Eh mana ai gaskiya ce ya za’ayi ki yaudari yaro bayan kin san ba auransa za kiyi ba shiyasa lokacin da kika zo da maganar hankalina bai kwanta da ita ba saboda nasan halin Khalid da zafin zuciya.

Nace.”A lokacin da nazo da maganar gabad’ayan ku kuna neman hanyar da zaku bi kuga ya dawo gida kun rasa me yasa dana kawo shawarar hakan kuka amince sai yanzu kuma ki goya masa baya to bari kaji da kai da Gwaggo a yanzu koda aurena zai mutu ba zan aureka ba kaje can ka nemi daidai da kai.” na ‘karashe maganar idona a tsaye a kansa.

Gwaggo tace.”To dama me zaiyi dake kuma ai shi sabuwar budurwa zai aura mai jini ajika.

Kallonta nayi zuciyata na ingiza ni akan na tashi na hada kayana na bar gidan wata zuciyar tace ki zauna dai har Kawu ya dawo ya yanke hukunci.

Ummatu tace.”Ke Sa’ida magana ta mutu dan kyautawa baki kyauta ba kai kuma Khalid ka shiga hankalinka ka gane samu da rashi duk na Allah ne.

Yace.”Ummatu wallahi hakkina ba zai bar wannan mayaudariyar ba ta cuce ni.”

Nace.”Kai har kana da bakin wata magana akaina ko.”? Gwaggo da sauri tace.”Magana dai a barta ni bana son wani tashin tashina.”

Girgixa kaina nayi cikin tsantsar takaici na kalleshi nace.”Hakki ko.”?

Kallona yake babu kiftawa nace.”To ina rokon Allah ya gaggauta bi maka hakkinka a kaina idan kuma ni nake da hakki Allah ya gaggauta bi min akanka.”

Ina k’are magana ta na fita tsakar gida na zauna dandaryar ‘kasa tunanin mafita kawai nake.

Gwaggo da Ummatu da ‘kyar suka rarrasheshi ya tsakuri abinci kadan yace ya koshi! mikewa yayi ya fita ya barsu a dakin suna tattaunawa.

Bayansa nabi da kallo a lokacin da yake kokarin fita daga gidan, daidai bakin kofa ya yanke jiki ya fadi.

Gabana yayi wani irin fad’uwa! “Gwaggo.” da karfi na kwala mata kira.”

Tare suka fito ita da Ummatu na nuna musu inda yake kwance tamkar mara rai.

Gwaggo salati ta rafka hankali a tashe ta kamfato ruwa ta kuza masa a jikinsa, tsayuwa sukayi kansa suna kuka Gwaggo fadi take “Sa’ida kinga masifar da kika janyo mana ko zaki kasheshi ki huta ai.

Daki na shiga na dauko waya ta hannuna sai rawa yake na marasa wanda zan kira a wayar.

Ummatu ta tsuguna kusa dashi tana masa firfita hade da kiran sunansa.

Idonsa ya bude a jigace yake kokarin tashi zaune kansa na wani irin sarawa hakika al’amarin yayi masifar firgitashi da sashi cikin tashin hankali .

Gwaggo hannunsa ta rike sai sannu take masa tana yi masa firfita da mahuci.

Kawu ne ya shigo gidan hannunsa rike da ledoji ganinsu sun masa rumfa da mafici a hannu yasa ya tsaya yana tambayar abinda ke faruwa.

Gwaggo hawaye ta share tace.”Faduwa yayi ya suma bayan ya samu labarin auran Sa’ida yanzu yanzu ya farfado.

Kawu bece komai ba ya tsallakesu ya shige ciki

Kallona yayi cikin kulawa nace.”Kawu Sannu da zuwa.” yana sake nazari na yace.”Sa’ida kiyi hakuri da rayuwa kinji ko.” hawaye suka zubo min hannu nasa na goge nace.”To Kawu insha Allah. Har yayi nufin wuce wa gurinsu sai ya tsaya da fad’in “Har yanzu dai Alhaji Nura beyi magana ba ni kuma bana so na tunkareshi da maganar sabida kada yaga kamar wani abu dole dai zamu cigaba da sauraransa daga nan zuwa gobe idan beyi magana ba to zan samu Alhaji Shamsu da maganar muji hukuncin da zai yanke.

A raunane nace.” To shikkenan Kawu.”

Gurinsu ya shige ba tare daya waiwayi su Gwaggo ba haushin Khalid din ya shafe su ya lura wani lokacin mahaifiyar tasa ce take d’aurewa yaron gindi yake iskancin da yake so.

Nima mi’kewa nayi na shiga daki na bar su a gurfane a gabansa suna rarrashinsa mussaman Gwaggo da duk ta fita daga hayyacinta, shima abinda ya gani kenan yasa ya sassautawa zuciyarsa ya daure ya mike tsaye, Gwaggo tace ka shiga dakinka ka kwanta ka huta kaji ko Khalid dan Allah dan Annabi ka cire Sa’ida daga cikin ranka idan ka mutu mune mukayi asara ba wani ba.

Kansa kawai ya daga mata ya bar gurin kallo suka bishi dashi suna jimanta abinda ya faru.

To sai da na bari Kawu ya ci abinci ya nutsu tukkuna na shiga gurin na same shi a kashingid’e akan dadduma yana hutawa.

Gaishe shi na sakeyi ya amsa cike da kulawa da fadin “Sa’ida akwai magana a tare dake ko.”?

Nace.” Eh Kawu nazo ne akan inaso kayi min tsakani da Khalid ya fita daga harkata tunda dai ni ba sa’arsa bace Kawu wai kamar ni Khalid zai shaqewa ma’kogwaro kuma su Gwaggo suna gani sun kasa daukar mataki.”

Kawu Iro ya mike zaune ransa a bace yace.”Wato Khalid din daga zuwan sa da abinda ya fara kenan me kikayi masa da zaiyi yun’kurin kasheki.

Hawaye na share nace.”Sabida kawai anyi masa dubara akan idan ya dawo gida za’a daura mana aure shi ne daya samu labarin aurena da Alhaji Nura ya yanke min wannan hukuncin.”

Kawu na kokarin yayi magana ya fito daga dakinsa, a kaina ya tsaya kamar zai mangare ni yace.”Ni yaro ne da zakiyi mun dubara mai yasa baki fada min gaskiya ba kika yaudare ni shin kin san halin da nake ciki a yanzu.”?

Kawu ya buga masa tsawa da fad’in “Yanzu daka tsaya a kanta dukan ta za kayi kome.”?

Sunkuyar da kansa yayi ya nemi gefe ya tsuguna yana watsa min harara! al’amarin ya dinga bani mamaki da tsoro yanzu gabad’aya tsoronsa nake ji sabida dazu nayi masifar galabaita a hannunsa.

Kawu ya kalleshi rai a ‘bace murya a kausashe yace.” Khalid wallahi ka fita daga idona na rufe kabar ganin duk abinda kayi Gwaggo tana daure maka gindi wallahi ka guji fushi na wato har ka manta laifinka ko ka dawo zaka yi rashin mutunci da rashin arziki ko? Yanzu Sa’ida sa’arka ce da zaka dinga dukan ta.”?

Yace.”Kawu ka gafarce ni dan Allah ni wallahi ‘karya take min ban doke taba.”

Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa wai yau yaron dana sharewa majina shine yake ‘karyata ni.”

Kawu ya cigaba da cewa.” Kayi yun’kurin kasheta ta hanyar matse mata ma’kogwaro kana nufin idan ka kasheta za’a saurara maka.”? shuru yayi Kawun ya cigaba da cewa”Yarinya tace bata sonka bata sonka amma saboda naci ka nace sai ta aureka waye ya fada maka a nai wa so dole ne.”?

Khalid ya dinga jin wani maqaqin bakin ciki a cikin ranshi! Kawu Iro ya cigaba da watsa masa ‘bakar magana iya yanda ransa yake so tas yayi masa wankin babban bargo dama haushinsa yake ji! Khalid ya rasa inda zai sanya kasa sabida bakin ciki da takaici babu shakka da yasan wannan bakin cikin zai zo ya tarar to da yayi zamansa a inda yake.

Kawu Iro ya cigaba da cewa”To wannan ce maganata da kai ta ‘karshe Khalid nayi maka tsakani da Sa’ida babu kai babu ita babu kuma maganar so Sa’ida ta girme maka a yanzu tunda tanada aure sabida haka kada na ‘kara jin ka furta mata kalmar so gaisuwar mutunci ce a tsakaninku.
Kaji ko ba kaji ba.?
Cikin Jin mugun ciwon kai yace.” Naji Kawu.” Ya kalleni da fad’in “Ki tashi kije ki kwanta ki huta insha Allah itama Gwaggon gobe zan zauna da ita akan wannan matsalar.” Cikin jin dadin abinda yayi wa Khalid din nayi masa sallama na tafi zuciyata fes nasan tunda mahaifinsa yaja masa kunne dole ya fita daga harkata.

.🥰🤝🏻💜_*
*51&52*
Ko dana koma d’akin Gwaggo ‘kin sakar mata fuska nayi duk wani abu dana san zanyi a dakin nayi na fito nayi shimfida a tsakar gida nayi kwanciyata itama uffan ba tace dani ba, tsakanin ni da ita ban san waye yafi jin haushin wani ba.

Ummatu kuwa itama da bakin ciki ta kwana dan bayan fita ta daga gurin Kawu Iro kiranta yayi itama ya ‘kare mata tanadi yace kuma ta jawa Khalid kunne ya shiga hankalinsa idan kuma yasan neman fitina ne ya dawo dashi to sawun sa a likkafa ya koma inda ya fito baya bukatarsa a cikin gidansa….Ummatu taci kukanta ta koshi ba tare da tace masa komai ba ta bar gurin tare da kudirin wani abu ranta.

Khalid yana kwance a d’aki! yaji duk irin cin mutuncin da Kawun kewa mahaifiyarsa ransa ya sake ‘baci ya sake ‘kullatar Auntyn nasa yana tunanin irin hukuncin da zai yanke mata.

Da zazzafan zazza’bi da ciwon kai ya kwana dan haka yana dawowa daga sallah ya shiga dakinsa ya kulle k’ofa ya kwanta ba tare da yayi tunanin zuwa ya duba Gwaggo mutuniyar tasa ba.

Cikin baccin daya soma fizgarsa ya dinga jin bugu ana kiran sunansa.

Mikewa yayi yaje ya bude kofar dakin, Ummatu ce ya bata hanya ta shiga dakin ta mayar da kofar ta rufe.

Gefan katifarsa ya zauna yana gaisheta ta amsa tana kokarin ajiye fulas din shayin dake hannunta.

Tace.”Khalid ina fata jiya duk kaji irin cin mutumcin da mahaifinka yayi min ko.”?

A sanyaye yace.”Eh Umma naji kiyi hakuri dan Allah kin san halin baba be iya ‘bacin rai ba.”

Girgixa kanta tayi cikin takaici tace.” Ba haka bane Khalid dama haka halin mahaifinka yake wani lokacin idan yayi ra’ayi haka zai zauna yaci mutuncina iya yanda ransa yake so akan wannan yarinyar Sa’ida babu abinda ba zai iya aikatawa ba.”

Yace.”Ummatu kiyi hakuri ki saba da halinsa idan kuma nine nake janyo muku sa’bani insha Allahu zan koma inda na fito kamar yanda naji yana fada jiya.

Tace.”Khalid idan kai ka cika dan halak ne to dan Allah ka rabu da Sa’ida bafa ita kadai ce ‘ya mace a duniya ba shin wai me ka hango a tattare da ita kake kulafunci.

Kansa ya sunkuyar kasa ta cigaba da cewa” A matsayina na mahaifiyarka nake umartarka a karo na biyu ka fita daga sabgar Sa’ida idan kana so kayi albarka a rayuwarka.”

Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta a raunane yace.”Umma ki taya ni addua akan abinda ke damuna a zuciyata insha Allahu zanyi kokarin ganin na cire aunt Sa’ida daga rayuwata.”

Tace.”To shikkenan Khalid zan cigaba dayi maka addua sannan inaso ka auri Jamila ‘yar ‘kanina Garba.”

Ya kalleta cikin wani irin yanayi yace.”Ummatu ki ajiye maganar Jamila a gefe guda ni bana ra’ayinta.

Tace.”Khalid tuntuni fa na fahimci cewa baka kaunar dangi na kafi kaunar dangin mahaifinka yanzu meye aibun Jamila kasan dai tafi Sa’ida kyau ko gata yarinya daidai da kai.”

Yace.”Umma kin san shi so babu ruwan sa da wani kyau ko muni duk kyawun Jamila bata burge ni ba kuma bana jin sonta ko kadan a cikin raina.

Tace.”Ni dai umarni nake baka ba za’bi ba saboda haka idan kana so kayi albarka to kabi umarnina.”

Ya jima kansa a kasa kafin yace.”Shikkenan Umma zanyi miki biyayya akan abinda kike so.” murmushin jin dadi tayi tace.”Insha Allahu kuwa zakayi alfahari da auran Jamila.

Shuru yayi bai ce mata komai ba tace.”Ga ruwan shayi nan a fulas bari na kawo maka awara da sauran kayan shayin.”

Yace.”Nagode Ummana.” fita tayi daga dakin ranta fari sol babu shakka za tayi farin ciki idan al’amarin nan ya tabbata.
3qutar ne a jikinsa sai kawai ya sanya k’aramar
T-shirt a jikinsa ya fito daga dakin nasa a daidai lokacin da Kawu ya fito daga nasa d’akin da shirin tafiya kasuwa.

‘Dan risinawa yayi yace.”Kawu barka da asubah.” Ba tare da ya kalleshi ba ya amsa da “Barka dai.” ya d’aga labulan d’akin Ummatu yana mata magana. ganin haka yasa da sauri ya fita daga gurun.

Gwaggo na kokarin fitowa daga d’akin ya shiga tace.”Ai dama yanzu nake maganarka ina cewa ko da kaina zan shiga gurin naku na dubaka naga baka shigo mun gaisa ba.”

D’akin ya shiga babu walwala a tare dashi yace.” Na d’an yi bacci ne.”

Tace.”Koda naji nima nace ko bacci kakeyi to zauna ga guri mu gaisa a nutse.” gefanta take karkad’e masa tana marmatsar da abubuwa sai kace barasake ne zai zauna a gurun.

Hankalinsa akanta tana bacci a gadon ba tare da tasan ya shigo dakin ba….Gwaggo ta lura da irin kallon ‘kurrular da yake mata sai duk jikinta yayi sanyi itakam wannan jaraba ta isheta wai shin wane irin so yaron nan yake wa Sa’ida.

Labari take bashi wai dan duk ta dauke masa hankali jinta kawai yake amma gabadaya hankalinsa da tunaninsa baya kanta yana can tunani akan Sa’ida duk da yasan ya ga mai mata illah amma yana bala’in kishin Alhaji Nura akanta shi kad’ai yake so ya cigaba da dabdala a wannan ramin amma wani katon banza ya shigar masa gona.

Gwaggo haushi ya bata ganin ya’ki barin abinda yake tace.”Ni kam banta’ba ganin mara zuciya irinka ba.”

Sumar kansa ya shafa babu sukuni yace.”Me nayi miki kuma.”? Tsaki taja tace.”Tunda ka shigo kake kallon Sa’ida alhalin bacci take yi ko gaisawa ba muyi ba hankalinka gabadaya yana kanta to ka dai kiyaye kada ka jefa kanta a matsala domin naga idanuwanka sunyi ja.”

Murmushi yayi yana kallonta yace.”Waye yace miki ita nake kallo.”? Tace.”Ai makauniya ce ni.” Dariya yasa yana sosa kansa tace.”Ka karya kummalo.”?

Girgiza kansa yayi tace.”To bari na zuba maka abinci.” Yace.”Gwaggo ba zanci abinci da safe ba ki bani ruwan shayi.” Tace.”Aa Ni yau kunu nasha ruwan shayi ka tambayi mahaifiyarka.”

Yace.” Okey na manta ma da akwai a fulas a dakina idan nasha zanzo naci abincin.” Tace.”To shikkenan.

D’akin ne yayi shuru na minti biyu ya cigaba da satar kallon Sa’ida ta ‘kasan ido Gwaggon ta kalleshi tana girgiza kanta Hankali tace.”Kasan abinda yake faruwa ko.”?

Girgiza kansa yayi yana d’an ya mutsa fuskarsa yace.”Sai kin fad’a.”

Juyawa tayi ta d’an kalli inda take kwance ta dawo da hankalinta kansa ‘kasa-‘kasa tace.”Ai *GA IRINTA NAN!* ta guje ka ta auri wanda take so gashinan tana fuskantar matsala a gurinsa da matarsa ya hanata komawa gurin aiki kuma baya biya mata bukatarta.”

Jim yayi yana kallonta kafin yace.”Gwaggo ban gane baya biya mata bukata ba.”?

Waiwaya wa tayi ta sake kallon inda take kwance tayi ‘kasa da murya tace.”Bukatarta ta gurin auratayya mana wai baya son haihuwa shine yake inzali a waje ma’ana yana zubar da ‘kwayoyin haihuwarsa.”

Cike da mamaki yake kallonta! tana so ta ‘kara tabbatar masa da maganar na tashi zaune duk sai suka diririce mussaman Gwaggo da gabadaya yanayin ta ya nuna na marasa gaskiya.

Yi nayi tamkar ban fahimci abinda suke ba na mike na fita, brush nayi na dawo d’akin na tarar dasu suna wata hirar.

Ta kalleni da fad’in ‘”Ga kayan karin kummalo nan.” Ba tare da nace mata komai ba na hau bud’e kwanukan………..dakin yayi shuru na minti biyu kafin naji sautin muryarsa da fadin” Kin tashi lafiya.”?

Kaina a kasa na amsa da lafiya lau.” Gwaggo tace.”Kina bacci dazu da safe aka kira wayarki kin san ni ban iya dauka ba shiyasa na barta ta katse.”

Hannu na mika na dauki wayar ina dubawa Alhaji Nura ne sai naji wani sanyi a cikin raina text d’inshi na gani da sauri na shiga ina dubawa……Hakuri yake bani akan abinda ya faru wai nayi hakuri insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba kuma idan anjima zai zo ya daukeni.

Zuciyata tayi sanyi kad’an amma dai duk da haka idan na koma sai na nuna masa ‘bacin raina.

A nutse nace.”Gwaggo Alhaji Nura ne yake baku hakuri akan abinda ya faru yace insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba kuma anjima da daddare zai zo mu tafi.”

Ta’be bakinta tayi tace.”Ai sai ki zuba ruwa a ‘kasa kisha saboda murna.”

Kallonta nayi ta gyda min kai da fad’in “Eh mana ai kinga kuka da damuwa ya ‘kare zaki koma d’akin ki tunda anan akan qaya kike.”

Takaici ya hanani ce mata komai kawai na d’auki kofin kunu na fara kur’ba ina duba wayata.

Katsaham! naji maganarsa a kunnena” Aunty Sa’ida idan kin koma gidan mutumin nan waye zai dauke miki bukatunki na yau da kullum.

Babu walwala a tare dani nake kallonsa, shima ya ‘bata rai da fad’in ”Kin kawo ‘kararsa akan baya biya miki bukatarki ta aure sannan baya so ya haihu dake amma sabida rashin sanin ciwon kai zaki koma gidanshi meye amfanin zama dashi a haka kodai kwad’ayin kud’insa kike.”?

Na dinga jin wani irin gumi mai zafi na tsatstsafo min a jikina shin ko dama maganar da sukeyi kenan a lokacin da na tashi na ga sun nuna alamun rashin gaskiya! “Yanzu Gwaggo meye amfanin yin wannan maganar da Khalid? me ya shafe shi a ciki da har zaki zauna kina fada masa halin da nake ciki a gidan aurena.”

Shuru tayi bata tanka min ba, naji wasu hawaye masu zafi suna kokarin zubo min na kalleshi raina a ‘bace nace.”Wato dai ba kaji gargadin da mahaifinka yayi maka ba ko.”

Cikin rashin tsoro yace.”Ai magana ta wuce aunty Sa’ida na rabu dake kije kiyi rayuwar auranki wannan magana kuma da ki kaga nayi miki ba wai da wata manufa nayi miki ba ina jin tausayin halin da zaki shiga anan gaba.”

Nace.”To ina ruwan ka da dukkanin halin da zan shiga a gidan aurena bana so ka nasa bakin ka akan al’amuran da suka shafe ni ka tsaya a matsayin ka.”

ta’be bakinsa yayi yace.” To shikkenan aunty Babbah na daina saka bakina akan abinda ya shafe ki tunda bakya bukata.”

Nace.”Hakan shi zai fi maka alkairi.” Shuru dakin yayi kowa yana sabgar gabansa…..Yace.”Gwaggo kin san wata yarinya Jamila ‘yar Kawu Garba ‘kanin Ummatu.”

Da sauri tace.”Eh kwarai kuwa nasan yarinyar ko ba wata ‘yar fara siririya ba.”

Yace.”Eh ita ce Ummatu take fada wai na nemi auranta.”

Gwaggo ta rangwad’a buda tana washe baki da fad’in “Kai Alhamdulillahi amma naji dadin wannan al’amari tabbas wani hanin ga Allah baiwa ne Khalid nima na goyi da bayan ka auri Jamila domin ta cancanta.

Murmushi yayi yace.” To shikkenan Gwaggo ku cigaba dayi min addua akan Allah ya tabbatar mana da alkairi.” ta amsa da ameeeen ya rabbi.
Gabad’aya ji nayi na kasa nutsuwa a gurin jikina yayi bala’in sanyi jin maganar da sukeyi fita nayi na bar musu dakin na zauna baki soro ina dube-dube a wayata gabadaya na rasa abinda yake min dadi.

To koda Kawu ya dawo da yamma na fada masa sa’kon Alhaji Nura sai yace.”To Alhamdulillhi dama jiya na fada miki cewa yau ne karshe idan baiyi magana ba zamu tattauna da Alhaji Shamsu to tunda yace zai zo ya daukeki zan zauna zaman jiran zuwan nasa.

Nace.”To shikkenan Kawu……..Bayan sallar isha’i Alhaji Nura yayi parking din motarsa a kofar gidan ya fito daga motar cikin lafiyayyar shadda sai maiko take yana baza ‘kamshin turarensa Khalid dake zaune cikin abokinsa ya dauke kansa dan koda Alhaji Nuran ya ‘karaso gurin yana musu sallama bai amsa ba su Salim ne suka amsa Ya kalli Khalid da fad’in ”Ko zaka kira min Sa’ida ne.” Kai tsaye yace.”Alhaji ka kirata a waya mana.”

Ya duba wayar hannunsa da fad’in “Tun kafin na karaso nake kiran wayarta bata daga ba mybe tana wani uziri ne.”

Jim yayi na minti biyu kafin ya miqe ya shiga gidan…..Lokacin na fito daga wanka ya tsaya yana kallona tsaki naja zan wuce shi yace.” Sai kiyi maza ki kimtsa wancan lusarin mijin naki yazo yana jiran ki a waje.”
Uffan bance masa ba na wuce shi na barshi a gurin a tsaye. dakin na shiga a gurguje na soma shirya jikina…
*52&53*
“Mijin naki ne yazo ne.”? Gwaggo ce ke magana tana zaune akan dadduma da carbi a hannunta. A nutse nace.” Eh shine yazo yanzu.” shuru tayi ba ta sake tankawa ba har na gama abinda nake na fita daga dakin.
Yana tsaye a soro kamshin turaransa duk ya game gurun. babu walwala a tare dani na gaishe shi. sai naga ya saki fuskarsa yana amsawa sai kallona yake yana murmushi.
Shuru gurin yayi na ‘yan mintina kafin yace.”Sa’ida ina fatan kinyi hakuri akan abinda ya faru tsakanina dake sharrin shed’an ne kuma bana fatan wani sa’bani mai muni ya sake had’a mu.”

Murmushin takaici nayi nace.” To naji dadin maganarka kuma ina fata har cikin zuciyarka kake maganar domin ni tuntuni na dawo daga rakiyar ka.”

D’an murmushi yayi yana kallona yace.”Kada ki damu Sa’ida wannan magana har cikin raina nakeyi miki insha Allahu zan gyara kuskure na.”

Ajiyar zuciya na sauke ina jin sassauci a cikin zuciyata nace.”To ya maganar aikin nawa.”

Shuru yayi kansa a kasa yace.”Sa’ida ki ajiye batun aiki a gefe kwata-kwata bana ra’ayin matata ta dinga yawo a gari inada kishi mai tsanani.”

Na bude baki kenan zanyi magana Kawu ya shigo soron ganinmu a tsaye yasa ya tsaya babu yabo babu fallasa suka gaisa a tsakaninsu.

Kawu yace.”Alhaji ai tun shekaran jiya muke tsammanin zuwanka shuru babu kai babu labarinka.”

Cikin jin nauyi yace.”Malam Ibrahim a gafarce ni wallahi uzirurru ne sukayi yawa.”

Kawu yace.”To babu laifi ai Allah ya taimaka.” ya amsa da ameeen ya Allah”

Kawu yace.” Sa’ida tazo mana da magana tana kuka wannan dalilin yasa nace tayi hakuri a saurari zuwanka domin kaima muji ta bakinka.

Yace.”Malam Ibrahim d’an sa’bani ne muka samu ni da ita wanda ya sanya ta yanke hukuncin zuwa gida a gaskiya al’amarin beyi min dadi ba ko kadan.”

Kawu yace.”Yanzu kana nufin dama ba kai kace tazo gida ba.” ? Ko kunyata beji ba yace.”Kwarai kuwa ni dai bance tazo gida ba nayi mata fada da nasiha akan abinda tayi min na rashin kyautawa.”

Kawu ya juyo da sauri yana kallona a lokacin da nake mamakin ‘karyar da mutumin nan ya shirga da girmansa da komai amma baya jin kunyar karya.

Kawu yace “Sa’ida ina gargadi akan duk irin sa’banin da zaki samu da mijinki kada ki sake cewa zaki dawo gida ki zauna ki bashi hakuri ku fuskanci juna aiki kuma tunda yace baya so sai ki hakura.”A sanyaye nace.” To shikkenan Kawu duk abinda kace haka za’ayi.

Ya juya yana kallonsa da fadin”Alhaji a kara hakuri da lamarin mata dan Allah ku zauna lafiya da iyalanka.”

Ya amsa da ameen insha Allahu zanyi kokarin ganin na kawo daidaito da zaman lafiya a gidana.

Cikin farin ciki Kawu yace.”Yanzu zaku tafi kenan.

Yace.”Eh kwarai kuwa.” ya kalleni da fadin “Kiyi maza kije kuyi sallama da mutan gidan yana tsaye yana jiranki.”

Amsawa nayi da to Kawu da sauri na shiga gidan domin dauko jakar kayana

Yana dogare a bakin kofar dakin Gwaggo suna magana na shiga gidan har na karasa bakin kofar bai kauce min hanya ba sai da nayi masa magana tukkuna ya dan matsa hanyar na duba naga ba tada da spece gurin wuce wa jikinmu zai iya had’uwa.

Kallonsa nayi yana duba wayarsa ya wani murtuke fuska nace.”Khalid ko ba kaji ne ka matsa ka bani hanya na wuce.” Gwaggo da sauri tace.”Ke kam Sa’ida kin fiye neman fituna wace hanya zai baki bayan wacce ya matsa miki.

Nace.”Gwaggo duba da kyau ki gani a bakin kofa ya tsaya hanyar ba zata isheni ba.

Gurin take kalla kafin tace.”Jarumi bata guri ta wuce kada tayi maka wani sharrin.” Ba tare da yace uffan ba ya shiga dakin ya zauna a kusa da ita suka cigaba da magana.

Kallonta nayi da jakar kayana a hannuna nace.”Gwaggo ni zan koma.” baki a bude tace.”Ke kadai zaki koma dakin naki babu dan rakiya kuma saboda ke ki ke iko da kanki ba zaki tsaya Kawunki ya dawo su tattauna magana ba.

Nace.”Gwaggo yanzu haka Kawu da Alhaji suna tare kuma sun tattauna dik maganar data cancanta.”

Shuru tayi tana kallona kafin tace.”Ashe ni ban isa ya shigo ya gaishe ni ba kenan.” Tunda tafadi wannan maganar nasan neman magana take sai kawai na kama hanyar fita ba tare da nace mata komai ba.

Tace.”Ai shikkenan Allah ya sa’ba halaye sai ki cigaba da hakuri tunda ke ki kaga zaki iya.” shuru nayi mata nasa takalmana gurin Ummatu na nufa nayi mata sallama na fito.

Khalid kuwa kasa sukuni yayi ya rasa abinda ke damunsa kishi mai zafi ya dinga taso masa Gwaggo data fuskanci yana cikin damuwa sai ta dinga rarrashinsa tana tausar zuciyarsa jinta kawai yake da kunnensa amma sam baya fahimtar abinda take fada.

Tun a mota yake jana da hira ni dai jinsa kawai nake da kunne dan na kasa sakin jikina dashi kafin mu shiga gidan sai da ya tsaya ya sayi kaji da yoghot masu sanyin gaske.

Aunty Murja ita da yaran suna zaune a falo suna kallo muka shiga muka samesu.

Babu yabo babu fallasa ta amsa gaisuwata gabadaya ta rage walwala komeye dalili oho.

Nima ban wani zauna a falon ba na mike da jakar kayana na bude dakina na shiga……to har nayi shirin kwanciya bai shigo ba raina ya ‘baci sosai dan koda ya shigo dakin sai da ya fahimci hakan sai ya shiga bani hakuri yana inda-inda nace.”Alhaji wallahi idan ba kayi da gaske ba aunty Murja zata kai ka wuta gabadaya na lura tsoronta kake ji shin wai itace take auranka ko kaine kake auranta.”?

‘Bata rai yayi yace.”Sa’ida kada ki fada min maganar banza mana ni akwai wata mace data isa naji tsoronta.”

Kallonsa nayi ina mamakinsa. ya cigaba da bambami yana kumfar baki. cikin zuciyata nace”Ni ka raina ai shiyasa ka zauna kana min masifa ita aunty Murjan da yake kana tsoronta ai ladabi kake mata. Ajiyar zuciya na sauke nace.”Kayi hakuri dan Allah fadan ya isa haka na amince kai tsayayyan namiji ne a gidanka.
Shuru yayi yana kokarin cire rigar shaddar jikinsa. kallonsa nake wani irin feelings na taso min ya mike ya nufi toilet nace yau kenan anga damar yin wanka a dakina.

Ina zaune ina sa’ke sa’ke ya fito da babban towel a jikinsa na kara jin sha’awata na karuwa a zahirin gaskiya Alhaji Nura yana da suffa ta mazantaka wannan dalilin yana daya daga cikin abinda ya sani sha’awar auransa domin ya cika namijin da kowace mace za tayi sha’awar auransa.

Jallabiya da gajeran wando yasa ya juyo yana kallona da fad’in “Ki bude ledojin dana shigo miki dasu idan kina bukatar abinci.

A sanyaye nace.”A koshe nake.” bece komai ba ya kashe hasken dakin ya hayo gadon.

Janyo ni yayi jikinsa a fara wasa da sassan jikina na dinga sauke ajiyar zuciya ina langwabewa a jikinsa kafatanin sha’awata ta tashi wannan dalilin yasa na dinga bashi kwarin gwiwa ina taimaka masa.

Yau yayi dogon zango akai na yana aikin sosai na dinga jin dadin hakan na sakar masa jikina yana abinda yake so dashi jin ya fara sakin nishi da gurnani yana kokarin raba jikinsa da nawa yasa da wani mahaukacin sauri na ri’ke ‘kugunsa tsam na hana shi sauka! ya dinga dukan katifar gadon yana ihu! nima ina nawa! wani mugun dadi ne naji ya tawo kafin nayi aune ya fizge jikinsa daga nawa yayi rufda ciki a gadon yana turje-turje da kafafunsa

Kuka nasa na raromoshi murya na rawa nace”Ya kake tauye min hakki ne Alhaji wannan wace irin rayuwa ce dan Allah ka biya min bukatata kada ka jefeni a masifa.

Shuru yayi min bai tanka ba, na matsa jikinsa sosai ina shashshafa bayansa.

Zaune ya mike yana kallona da jajayen idanunsa yace.”Wai kina nufin baki gamsu ba har yanzu.”?

A marairaice nace.”Eh wallahi ina daf da samun satisfaction ka katse min hanzari.”

Kallona yayi da mamaki a tare dashi yace.”Sa’ida shin ke d’in wace irin macace mai nisan sha’awa na kusa min talatin a kanki amma kice baki gamsu ba.

A sanyaye nace.”Kasan ko wace mace da irin hallitar ta ni ina da nisa sosai kafin na gamsu shine dalili.”

Tsaki yaja da fad’in “A gaskiya ni yanzu bani da wani kuzarin kirki ki bari da safe idan naji kwarin jikina kafin na fita sai nayi miki.”

Wani kuttun bakin ciki yazo ya tokare min a ma’koshi nace.”Ba zan iya daurewa ba Alhaji marata ciwo kawai take min dan Allah ka daure kaji.”

Kwanciya yayi yana tsaki! na matsa kusa dashi tare da dafa kirjinsa. yace.”Ai sai dai ke kiyi da kanki domin na fada miki uzirina.”

Ba tare da nace masa komai na dora hannuna akan jarumar tashi na fara wasa da ita a hannuna, yana kwance kamar wani mushe ni nake kid’a na kuma nake rawa ta babu wani taimako da yayi min da kyar da sid’in goshi na samu satisfaction ko second guda bai k’ara ba ya mike yana mita ya nufu toilet
Kuka naci na koshi sabida tsabar takaicin wannan al’amarin.

To haka rayuwa ta cigaba da tafiya a gidan na samu sassaucin wasu abubuwan wasu kuma sai godiyar Allah , bangaran aunty Murja kuwa kadaran kadahan muke zaune da ita babu sawa babu hanawa Yaran ta suna ganin girmana duk ranar da basu da makaranta na kan zauna na duba littafansu…..Sai dai yawan sintirin da Hajiya Aziza take a gidan yana bani mamaki a sati sai tazo sau uku sau hudu kuma idan suka hau sama basa saukowa sai yamma al’amarin ya dinga bani mamaki yana d’aure min kai! Zargi dai haram ne koda kuwa ya kasance gaskiya ne amma ha’kikanin gaskiya ina zargin akwai wata ‘boyayyar alaqa tsakaninsu.

Akwai ranar da aunty Murja ta tafi unguwa ya kasance sai ni kad’ai a gidan koda na gama ayyukan gidan daki na shiga na kwanta bacci mai nauyin gaske ya d’auke ni……..Cikin baccin na dinga jin tafiyar tsutsa a tafin kafata ga wani masifaffan kamshin turare da nake ji a hancina a furgice na mike zaune ina salati……Hajiya Aziza na gani a zaune a kusa dani da wannan d’an iskan murmushin a fuskarta.

Cikin mamaki nake kallonta kafin nace.”Hajiya yaushe kika shigo gidan.”?

Ajiyar zuciya ta sauke idanunta ‘kur a kaina tace.”Na jima da shigowa ina ta sallama shuru babu amsa na hau sama ban samu Murja ba shine na yanke shawarar shigowa gurinki sai na sameki kina bacci.”

Nace.”Wallahi kam ban jima da kwanciya ba bacci ya dauke ni aunty Murja kuma taje gidan biki.”

Tace.” Kinga kuma ta manta ba tafada min za taje unguwa ba.” Nace.”Aikam sai ki bita can tunda a famliy house d’insu ake bikin.”

‘Yar dariya tayi tace.”Aa babu inda zanje ai tunda na sameki magana ta ‘kare.”

Ba tare da na fahimci inda maganarta ta dosa ba nace.”Eh hakane hajiya bari na shiga toilet na fito.

Tace.”Okey to sai kin fito.” na sauka daga gadon na nufin toilet din gabana na fad’uwa da zuwan matar.

Uziri na nayi a toilet din na dauro alwala na fito…….Subahannallahi! samun ta nayi a kwance a gadona tsirara haihuwar uwarta ta d’aga kafafunta sama tana lumshe ido hannunta kan nononta tana murzawa.

Da karfin gaske nace.”Azubillahi minashaid’anirajim.” ta mike zaune tana kallona da shegun idanunta tace.”Haba Sa’ida meye na firgita kada dai kice min baki san abinda yake tsakani na da kishiyarki ba.”

Kaina na kautar domin bana bukatar ganin tsaraicinta nace”Hajia dan darajar Allah da Annabi ki suturta jikinki kada kisa ‘kasa ta girgiza.”

Dariya tasa da fadin”Sa’ida kenan da ‘kasa zata girgiza ai da tuni ta girgiza wannan harkar ba sabon abu bane saboda haka dan Allah ki saki jikin ki mu more rayuwarmu.

Baki na rawa nace.”Hajiya Aziza kiji tsoron Allah kiji tsoron ranar haduwa dashi fisabilillahi yanzu meye amfanin *Madigo* da kuke me kuke ji a jikin jununaku.”?

Murmushi tayi ta mike ta dunfaro inda nake. rintse idona nayi ina korar shed’an yayin da zuciyata ke azalzala ni akan nayi mata rashin mutunci tunda ta kasance tunkiya mara kamun kai.

bude idona nayi jin ta tsaya daf dani na kalleta ta kalleni kafin nayi aune naji saukar hannunta kan nonona. Bahagon mari na kwad’a mata a fuska da saurin gaske na janye jikina ina tsuma! nace”Wallahi yanzu zanci uwarki na yaga miki rigar mutunci ni zaki zowa da wannan yahudancin.

Hannunta dafe da kumatunta tace.”Sa’ida kin san kuwa ni wacece da zaki fitar da hannu ki mare ni.”? A zafafe nace.”Bana bukatar nasan ko wacece ke ki fice min daga Daki ko na rotsa miki kai shegiya ba’kar daga.”

Tana wani irin huci! tace.”Zaki gane baki da wayo yarinya wallahi sai na d’aure ki sai nayi miki rashin mutunci.

Nace.”Ki daure ni ni kuma na tona miki asiri a duniya domin duk wannan abunda ya faru nayi video a waya ta.” Na fadi hakane domin na razana ta da yake gaula ce sai ta soma waige-waige a dakin nayi dariya da fadin”Ai ba zaki ga inda wayar take ba ballanatana ki dauka wallahi sai kin tozarta da yardar Allah.”

Kayan ta tasa jiki a sanyaye ta dauki jakarta ta kama hanyar fita nace.” Ubangiji Allah ya shiryeki dake da masu mugun hali irin naki.” da saurin gaske ta bude kofa ta fita ba tare da tace wani abu ba.

K
*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*54&55*
A ranar yini nayi da fargaba mai tsananin gaske. koda auntyn Murjan ta dawo sama-sama mukayi magana da juna na bar mata falon na koma daki na zauna ina tunanin rayuwa, Yusura ce ta shigo da fad’in “Auntynmu wai kizo muci abinci.” Kallonta nayi da fad’in.”Babanku ya dawo ne.”? kanta ta daga min alamar Eh. to sanin da nayi bani nake da girki ba yasa ban damu ba, nace.”Kije kice gani nan fitowa.” Yarinyar ta juya da sauri ta fita.
A maimakon na tashi naje gurin cin abincin sai na nemi guri na kwanta daidai da ‘kwayar zarrah bana so na had’a numfashi da ita wani irin tsanarta nake ji a cikin zuciyata.
Motsin shigowarsa dakin yasa ni saurin kallon kofa….jikinsa sanye da jallabiya ruwan toka ya karaso kusa dani.
Zaune na mike ina gyara daurin dankwali na nace.”Barka da dare ina fatan ka dawo lafiya.”?

Babu sukuni a tare dashi ya amsa da “yawwa zaman me ki keyi ne tun dazu na aiko kizo muci abinci baki fito ba idan kuma ba’a kira ki ba kice anyi miki laifi.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Bana d’an jin dadin jikina ne shiyasa ban fito bs babu damuwa kuna iya cin abincin ku.”

Idonsa akaina yace.”Me yake damun ki domin Murja ta sheda min cewa tunda ta dawo daga gidan biki kika kulle kan ki a daki Sa’ida bana son neman fitina a gidana.

Nace.”Yanzu shikkenan bani da damar da zan zauna a daki nayi tunanin rayuwa sai a zargi wani abu har kullum idan na kira Aunty Murja munaf*cka kana jin haushina to wallahi kayi takatsantsan da ita domin abunda take aikatawa ya sa’bawa addinin Musulunci”

“Kinga ni ba wata magana na nema ba shin rashin lafiyar gaske kike ko kuma ta ‘karya kika ‘kir’kira domin ki tayar mana da husuma a gida.”

Cikin takaici nace.”Ni lafiyata lau husuma kuma da kake magana a kai Allah ya tsare mu da ita dalilin da yasa na zauna a daki mai k’arfi ne wanda nake tunanin koda na fada maka bai zama lallai ka yarda ba.

Yace.”Ai fad’ar shi yafi alkairi domin ni a rayuwata na tsani ‘kumbiya-‘kumbiya.” Na bude baki kenan zanyi magana Yusura ta shigo, duk sai muka bita da kallo tace.”Abbah kazo inji mommy.” Da sauri yace.”gani nan zuwa.” Yarinyar na fita yabi bayanta kallo na bishi dashi ina mamakin halayyarsa.

Sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina na daidaici cewar sun bar daining din sannan na fita falon kai tsaye gurin cin abincin na nufa ba tare dana tanka musu ba.

Ina kokarin zama naji tana fad’in “Sa’ida yau Hajia Aziza tazo ko.”? Nace.”Eh tazo.” Tace.”Wallahi sai da na fita na tuna ashe ban fada mata zani unguwa ba kuma nayi ta kiran wayarta domin na sheda mata wayar ta’ki shiga.”

Nace.”Eh itama haka tace har nace ta biki gidan biki tace Aa ba zataje ba.”

D’an murmushi tayi da fad’in “Hajiya Aziza kenan.” cikin zuciyata nace “Gafalallu insha Allahu sai Allah ya tona muku asiri.

Mintina goma sha biyar na kammala cin abincina na mike a nutse na bar gurin. dakina na nufa Yusura tace.” Aunty yanzu zasu saka *TARKO KAUNA* Naga zaki shiga daki yau ba zaki kalla ba.” Ba tare dana juyo ba nace.”Yusura yau bacci nake ji na kalli maimaici ranar lahadi.” Tace.”To shikkenan aunty Sai da safe.” na amsa da Allah ya tashemu lafiya.

Ina kokarin shiga bargo ya shigo dakin ya tsaya a kaina zaune na mike ina kallonsa yace.”Wulakancin naki har akan ‘ya’yana zaki gwada.

Nace.”Ban fahimci maganarka ba.” A hasale yace.”Yarinyar nan Yusura tana miki magana sabida kina ji da isa da iko ki gagara kallon inda take shin dame kike takama ne.”?

Murmushin takaici nayi nace.”Bana takama da kowa sai Allah da ma’aiki” Da sauri yace.”Ki kiyaye b’ata ran d’aya daga cikin iyalina kinji ko baki ji ba.”

Nace.”Naji yanzu Ita Yusuran ce ta turo ka kazo ka sauke min ashafa ko kuma uwarta ce.”? Kallona yayi da fad’in “Zakiyi min rashin kunyar da kika saba ne.”
Nace.”Ai gaskiya ce sabida nasan wannan hayaniyar da kazo kana yi min ba tunaninka bane turo ka akayi.”
Hannu ya daga zai kwada min mari na kauce da sauri ya mari iska.

Yana huci yace.”Wai me yasa kika raina ni Sa’ida me kika mayar dani a cikin gidana.”

Cike da takaici nace.”Alhaji kaine kasa kima da mutuncinka duk suka zube a idona kasan Allah a yanzu dai sai dai kawai na kalleka domin kayi min bazata ban ta’ba zaton zan shigo gidanka nayi irin wannan rayuwar ba.”

Yace.” Wannan rayuwar kuma ki rubuta ki ajiye yanzu kika fara ni haka tsarina yake a gidana babu wata macan data isa tace min ga yanda zanyi ‘karya take.

Dariya ya bani na kalleshi yana tsaye a kaina sai daga murya sama yake nace.”Yanzu dai magana ta wuce akan na ‘ki zaman falo aka zuga ka kazo kaci min mutunci to naji na dauka nayi laifi kayi hakuri.”

Shuru yayi yana sauke ajiyar zuciya, Nace.”Ka zauna inaso muyi magana. a watse ya kalleni da fadin”Kin san ba girkin bane ko.”? Nace.”Eh na sani ai ba wata doguwar magana zamuyi ba.

Zama yayi kusa dani yana kallona. Nace.”Kasan me? a ya mutse yace.”Sai kin fada.” Nace.”Ka hana wannan matar zuwa gidan ka ina nufin hajiya Aziza ‘kawar aunty Murja.”

“A kan wane dalili zan hanata zuwa.”? Yayi maganar tare da tsareni da idonsa.

Nace.” Ba alkairi ne yake kawo ta gidan ba tana zuwa ta hana mala’ikun rahama shigowa gidanka sabida haka ka hanata zuwa shi yafi alkairi.

“Ba zan hana ta shigowa gidana ba sai naji dalilin ki.” ajiyar zuciya na saukw idona akansa nace.” *’YAR MADIGO (LESBIAN)* ce.”

Wani irin kallo yake min kafin yace.”Shine me? dan Aziza tana Lesbian sai kike zargin Matata Murja.”?

Cike da karsashi da kwarin gwiwa nace.”Kwarai kuwa dole nayi zarginta saboda tayi abinda zai janyo hakan Hajiya Aziza a sati sai tazo sau uku ko sau hudu sannan idan suka hau sama suka rufe kofa sai yamma suke saukowa.”

Shuru yayi kansa a ‘kasa na cigaba da cewa”Yau tazo gidan lokacin Aunt Murja ta tafi gidan biki ni kuma ina daki ina bacci ta shigo ta same ni ………..Duk abinda ya faru ta kwashe kaf ta fad’a masa.

Wani irin gumi! ne yake karyo masa ya dinga kallona bakinsa na rawa da alama magana yake so yayi amma tsabar rud’u ya hana shi cewa komai.

Nace.”Dan Allah ka fahimci maganata kuma ka yanke hukuncin daya dace wallahi tallahi banyi musu sharri ba.

Da ‘kyar ya iya fadin”Sa’ida a gidan nawa ake aikata wannan kafurcin tsayin shekaru ban sani ba.

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Yau ne Allah yaso kasan abinda yake faruwa saboda haka sai kayi namijin kokari gurin ganin ka kori wannan masifar da ta kunno maka a gida.

Mi’kewa yayi ya kama hanyar fita yana tafiya yana had’a hanya babu shakka al’amarin yayi masifar saka shi cikin rud’u da tashin hankali mai tsanani.

Tana kwance a gado cikin kayan bacci masu fitar da tsaraici ya shiga dakin sama-sama ta amsa sallamarsa domin taji masifar haushin zaman da yayi a dakin Sa’ida.

Ya nemi gefan gado ya zauna yana kallonta a burkice!

Zaune ta mi’ke had’e da ajiye wayar hannunta tace.”Lafiya na ganka ka shigo a burkice wani abun ne ya faru.”?

Ya kalleta da jajayan idanunsa yace.”Murja ashe dama ha’intata kikeyi.”? da sauri tace.”Wace irin magana ce wannan.”? Hannu ya daga mata a kaushashe! yace.” Menene tsakanin ki da wannan matar dake zuwa gurunki.?

Gabanta ne ya fad’i baki na rawa tace.”Wace mata kake magana.”?

Yace.”Hajiya Aziza matar da kuka had’u da ita a fece book.” Ajiyar zuciya ta sauke tace.”Alhaji babu abunda yake tsakanina da Aziza sai mutumci da zumunci.”

Yace.”Ban yarda da maganarki ba Murja kina gayyato min ‘yar iska gida kuna iskanci yaushe kika zama lalatacciya.”?

Cikin firgici tace.”Wai ya kake magana a baibai ne ka fito fili ka fada min abinda kake nufi dani.”

Yace.”Sa’ida ta tabbatar min da cewa” Aziza *’YAR MADIGO (LESBIAN)* ce domin a dazu da tazo bakya nan sai ta nemi Sa’idan akan suyi harkar ita kuma ta’ki amince mata.”

Wani irin kuka ta fashe dashi tana salati da tafa hannaye tace.”Yanzu irin sharrin da yarinyar nan za tayi min kenan.”? Yace.” Ki fada min gaskiyar magana ba kuka nace kiyi min ba shin kema kina aikatawa ko kuwa.?

Hanci ta shaqa a fusace! ta miqe tsaye da fad’in “Wallahi tunda yarinyar nan ta kai ni karshe sai na hukuntata har ni za tayi wa sharri na lesbian lallai sai na nuna mata kuskuranta.

Kafin yayi wani yunkuri har ta bude kofar dakin ta fita ya mike da saurin gaske ya bi bayanta yana kiran sunanta, da gudu ta sauka k’asa kai tsaye dakin Sa’ida ta durfafa.

Shaf na manta bayan fitarsa ban rufe kofa ta ba na kwanta bacci ya daukeni kawai sai jin shaqa nayi a makogwarona tari ya sarqe ni na bude ido ina kakari! kafin na ankara naji mari mai zafi a kumatuna.

” Ni zakiyi wa k’azafi Sa’ida ashe baki da mutunci da ‘ya’yana da mutuncina amma ki zaunar da mijina marufar asirina uban ‘ya’yana kice masa ni ‘Yar Lesbian ce.”

A mutukar galabaice nace.”Ki sakar min wuyana.” tana kumfar baki tace.”Ba zan saki ba sai kin fada min a inda kika gan ni ina lesbian. ”

Nace.”A cikin gidanki na kama ki a dakin ki kina lesbian sai me.”? Ta sake kawo min mari! na rike hannunta da karfin gaske na ture ta na sauko daga gadon ina haki nace.”Idan bakya lesbian din meye naki na tayar da hankali.”

Tayo kaina tana ihu! nace.”Wallahi kika kuskura kika doke ni sai na zubar miki da hakora.”Kuka tasa a daidai lokacin daya shigo dakin take fad’in “Amma wannan yarinya kin cuce ni wallahi sai Allah ya sake min gida kuma zan fita na barshi tunda kinfi bukatar haka.

Nace.” Idan kin tafi kin bar gidanki da ‘ya’yanki kanki kika cuta ba wani ba.

Ta kalleshi tana kuka da fad’in “Alhaji kaga irin abunda nake nuna maka ko? dama nasan sai haka ta faru tunda nasan duk wata mace da zaka aura burinta ta shigo ta rabani da kai shikkenan tunda abin ya kasance a haka ni zan tafi gida domin ba zan zauna ba.”

Tana gama maganarta ta bude kofa ta fita, zuwa yayi ya zauna kusa dani yana goge gumi nace.”Alhaji kada ka bari ta tafi gidansu kaje ka hanata”

Yace.”Sa’ida ki ‘kyaleta taje jikina na bani maganarki akwai alamun gaskiya a ciki taje kawai sai nayi binkice.”

Jikina yayi sanyi da jin abinda ya fada hakika da nasan haka zata faru da ban fada masa ba domin bana so ta sanadiyar al’amarin auransu ya samu matsala nafi bukatar ta shiryu su cigaba da zama mai tsafta a tsakaninsu.

Aunty Murja kwananta biyu a gidansu mahaifinta ya nemeshi da su tattauna……………Kima da darajar dattijon tasa shi janye kudirinsa akanta domin da yayi niyyar datse igiyar auranta sai kuma dattijon ya bashi tausayi ya hakura amma kafin ta dawo gidan sai da yayi mata gargadi akan cewa babu ita babu hajiya Aziza duk sanda ya sake ganin matar a gidansa to ta tabbatar kwanan auranta dashi ya ‘kare.”

Tunda ta dawo gidan ta tsiri gaba dani ko na gaisheta bata amsawa ni kuwa da yake ban iya gaba ba ko na fara ajiyewa nake nai mata magana tsakanina da yaran ta babu wata matsala hakanan tsakanina da mijina ma sai godiyar Allah dan yanzu na fahimci halinsa ‘bangaran auratayya ma yana kokari yanzu dan bana ta’ba bari ya sauka daga kaina sai na biya bukatata yanzu ya saba da jarabata yana kuma kokari akan hakan.

Ranar Lahadi Khalid yazo min gida wai yazo yayi min sallama zai koma Lego’s ni dai tunda ya shigo gidan gabana yake fad’uwa! na kalleshi da fadin.”A maimakon ka kira ni a waya kayi min sallama sai kuma kazo min gida kasan dai bani kadai bace ko.”?

Yana min wani irin kallo yace.”Me kika d’auke ni ne ? bake kadai bace to ina ruwana da kishiyarki ni gurunki nazo muyi sallama ba zuwa nayi na kalli kishiyarki ba.

Nace.”To nagode sai ka tashi ka tafi Allah ya kiyaye hanya.” Murmushi yayi tare da miqewa tsaye…..Sosai naji dadin hakan dan na dauka zaiyi min gardama. Nace”Tsaya anan ina zuwa.” D’akina na bude na shiga na bude drowar domin dauko masa sabulai da turare…..ina d’agowa na hangoshi ta mirror ya shigo dakin….gabana yayi wani irin fad’uwa! sanin da nayi cewa Alhaji Bai fita yana sama dakin Aunty Murja ga Khalid ya shigo masa gida ba tare da sanin sa ba………jikina na rawa na juyo cikin tsawa! nace……

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*56&57*
“Khalid me yasa zaka shigo min daki bayan cewa nayi ka tsaya a falo na fito me yasa kake so ka janyo min matsala a gidan aurena.” ? Ba tare da yace uffan ba ya mayar da kofar ya rufe ya durfafo inda nake tsaye, gabana ya tsananta faduwa cikin rawar baki nace.”Ka juya ka fita falo gani nan kaga maigidan yana nan bai fita ba kada ya shigo ya gan ka wata matsalar ta afku.” Cikin zuciyarsa yace.”Dama ai ni so nake matsalar ta afku. daf dani ya tsaya hucin numfashinsa na sauka a fuskata, kauda kaina nayi tare da matsawa daga kusa dashi. cikin wani irin voice yace.” A yanzu Babu wani abu da yake tsakani na dake sai alkairi ni banzo gidanki da niyyar na kashe miki aure ba.” Na kalleshi da fadin.”Amma dai kasan babu dadi mutumin nan ya shigo ya ganka har gadon baccinsa.” Murmushi yayi yana shafa sajensa yace.”To menene? ai da sauki ma idan ba wani abu ya shigo ya tarar muna aikatawa ba.” Nace.”Kasan yanzu yana da ikon d’aukar mataki akanka ko tunda ka shigo masa gida ba tare da izininsa ba.” ‘Yar dariya yayi idonsa a kaina yace.”A’ina zai gan ni da zai dauki mataki a kaina an jima kadan na bar garin.” Tsaki! naja cikin jin takaicin abinda yake na ratse shi domin fita na bar masa dakin….Kawai naji ya riko hannuna. cikin wani irin shocking na juyo da saurin gaske na fuzge hannuna da fad’in “Kada ka sake idan kuma ka’ki sai ka fuskanci ‘bacin rai.”
Daf dani ya matso yana kokarin magana. Ya shigo dakin. naji gabana yayi wani irin rugugi! da mugun sauri na janye jikina gwiwata a bala’in sanyaye na nemi bakin gado na zauna ina zare ido!

Cikin basarwa yace.”Alhaji barka da wannan lokaci.” Alhaji Nura bai amsa masa ba ya karaso cikin d’akin fuskarsa tamkar hadarin dake daf da zubar da ruwan sama.

“Kai me ya kawo ka gidana? waye kuma ya baka damar shigowa har dakin bacci na.”? A nutse yace.”Afuwa Alhaji nima nasan ban kyauta ba kuma a yanzu ma maganar da mukeyi kenan da ita tana nuna min rashin dacewar abunda na aikata kayi hakuri dama nazo nayi mata sallama ne zan koma gurun sana’ata Lego’s. ”

Yace.”Kada ka kuskura ka kara shigo min cikin gida domin ni ban yarda da kai ba babu ruwana da ‘yan uwantakar dake tsakaninku.”

Cikin mamaki yake kallonsa kafin yace.”Kana nufin zaka iya raba hanta da jini kenan.”? Alhaji Nura yaji tamkar ya soka masa wuka a ma’koshi yace.”Kai ashe baka da kunya ? ka taka sharia ka shigo gidana babu izini na amma kake kalubalanta ta.”

Killer smile yayi yace.”Aa Alhaji naji kana wata magana ne mara ma’ana shiyasa nayi wannan maganar shigowa gidanka kuma babu izini ai na nemi afuwarka.

Mikewa tsaye nayi rai a ‘bace! nace.”Khalid kama hanya ka fita bana bukatar ganinka a gidan aurena.”

Wani irin kallo yayi mata zuciyarsa na wani irin zafi ya lura duk da ya kar’be budurcinta mutumin na sonta yana kuma kishinta bai ta’ba tsammanin cewar za tayi watanni a gidansa ba tare da ya sake ta ba.

Murmushi yayi ya kalleta ya kalli mijin nata yace.”Kuyi hakuri da aikin ‘kuruciya kada kuma ku fassara abinda nayi da wata manufa mara kyau saboda haka ni na barku lafiya.”
Hanyar futa ya kama gabad’ayan mu muka bishi da kallo har ya bude kofar dakin ya fita……Kaina ya juyo yana wani irin numfarfashi da huci! yace.”Ashe dama baki da mutunci da kamun kai Sa’ida.”?

Shuru nayi masa domin nasan nike da laifi. ya cigaba da cewa”Sabida rashin kamun kai da rashin sanin darajar aure ki gayyato tsohon saurayin ki dakin auranki shin me hakan yake nufi.”?

Cikin ‘kokarin kare kaina nace.”Wallahi bani na gayyatoshi ba shigowa yayi.” a fusace! yace.”Rufe min baki munaf*cka idan baki bashi fuska ba ta yaya zai shigo min gida har dakin bacci na”

Kaina na sunkuyar ‘kasa ina addua a cikin zuciyata…..Cikin sigar cin mutunci da wulakanci ya cigaba da zazzaga min bala’i yana fad’ar duk maganar da tazo bakinsa.

Cikin kuka nace.”Ni dai dan Allah kayi hakuri an san ba’a kyauta maka ba amma ka daina zargi na da yaron nan wallahi babu abinda mukayi wanda ya sa’bawa sharia.

“Babu abinda kukayi na shigo na sameku daf da juna kamar zaku rungume junanku.” shuru nayi ban tanka masa ba, ya cigaba da cewa”To wallahi wannan shine na farko kuma shine na karshe duk ranar da yaron nan ya sake shigo min gida a bakin auranki.”

Da sauri na daga kaina ina kallonsa da mamakin maganarsa…..Yace.” Kwarai kuwa ki kalleni da kyau ni ba yaro karami bane da zaku dinga wasa da tunani na na lura har yanzu da akwai soyayyar yaron nan a zuciyarki sabida haka wallahi kuka ci amanata sai na baku mamaki.

Hannu nasa na goge hawayen fuskata nace.”Amma dai kasan ba zaka hana ni zumunci dashi ba ko.”?

“Babu ruwana da wani zumuncin ku idan kun had’u can kuje kuyi amma ban lamunce a shigo min gida ba.” Yana gama maganarsa ya bude dakin a fusace ya fita.

Kwanciya nayi naci kukana na koshi a gaskiya Alhaji Nura bashi da sauki mugun masifaffen mutum ne mara fahimta………Gabadaya dauke min wuta yayi a gidan ya daina shiga sabgata ko nice da girki bama mu’amular arziki fuska a murtuke yake ‘kare kwanakin sa ya bar min dakina babu kyakykyawar mu’amula. sosai na shiga damuwa mai tsanani domin a cikin ‘yan watannin da muke shiri dashi na saba sosai dashi da soyayyarsa tunda duk ranar girkina sai munyi auratayya duk da baya bani had’in kai sosai amma ina gamsuwa dashi……Gabadaya sai na shiga cikin wani irin yanayi na tashin hankali da fargaba gefe guda kuma ga masifaffiyar sha’awar dake nema ta zautar dani.

Yau dai girki na ne kuma nayi alkawarin neman sa a kan hakki na domin ba zan zauna kullum marata na ciwo ba. Koda ya shigo dakin kai tsaye toilet ya nufa yayi uzirinsa ya fito ba tare da ya kalli inda nake zaune ba ya haye gadon yaja bargo ya rufe jikinsa.

Murya na rawa nace.”Ina da magana da kai.” shuru yayi min be tanka ba. Nace.”Ni gaskiya na gaji da irin wannan zaman da mukeyi ina cikin matsatsi da takura ya kamata kayi hakuri da abinda ya faru ka daina fushi mu cigaba da mu’amula kamar yanda muka saba.”

Nan ma uffan bece ba. na matsa jikinsa ina kokarin shiga bargon ya mike a fusace! yace.”Kada ki kuskura ki hana ni bacci Sa’ida idan kuma kin ‘kiji to ranki ne zai ‘baci.”A sanyaye nace.”Bangane ba Alhaji dan na matso kusa da kai sai na hana ka bacci.”

Yace.”Eh bana bukatar wata fitina a yanzu ni bacci zanyi na huta gajiya.” Kai tsaye nace.”Ni kuma gashi ina bukatarka ya za’ayi kenan.”?

Tsaki yaja ya juya min baya. na dauki hannu na dora a bayanshi a harzuke ya ture ni dan har sai da na kusa faduwa a kasan gadon…..Na bishi da kallon mamaki! rufe jikinsa yayi ya gyara kwanciyarsa kawai sai naji wasu zafafan hawaye masu ciwo sun kwace min.

Sauka nayi daga gadon na kwanta kasan kafet tare da takure jikina wata irin gawurtacciya sha’awa ce take taso min na dinga mutsu-mutsu ina takure jikina hawayen bakin ciki da dana sani suna ta ambaliya a fuskata.

Yanda naga rana haka naga dare da asuba ina jin motsinsa ya tashi ya shiga toilet yayi wanka ya fito yayi shirye-shiryensa ba tare daya ko kalli inda nake kwance ba ya kama hanya ya fita daga dakin.

A daddafe na mike na shiga toilet nayi wanka na dauro alwala na fito riga da zani na atamfa nasa a jikina ko mai ban shafa ba nasa hijabi na tayar da sallah……Koda na idar da sallar kasa fita falo nayi sai nayi kwance a kan daddumar ina matse hawaye marata har yanzu ciwo take mun.

Muryar Yusura naji a kaina tana fad’in “Aunty Sa’ida kizo muyi breakfast inji babanmu.”

Bude idona nayi ina kallonta dishi-dishi a idona nace.”Kije gani nan.” Yarinyar ta bude kofa ta fita ba.

Sun dan zauna zaman jiran fitowarta da suka ga bata fito ba sai kawai ya umarcesu da suyi breakfast d’insu…………..Ba tare da damuwar komai ba ya shige ya tafi kasuwa bai ko duba halin da take ciki ba.

Sai kusan sha d’aya da rabi na samu sassaucin abinda yake damuna na mike da mataccan jiki na fita falon……Shuru yaran duk sun tafi makaranta ita kuma tana sama kamar tsuntsuwa, gurin cin abincin na nufa naja kujera na zauna a nutse na had’e tea domin shi kadai nake jin zan iya sawa a cikina ba tare dana sa madara ba na dauki cup din ina kur’ba tare da had’awa da soyayyan dankali da kwai.

Koda na gama karyawa banyi tunanin shiga kicin ba kai tsaye daki na koma na kwanta kan bed wayata na dauka na nemi number Hauwwa ita kadai nake jin zan iya fadawa matsalata.

“Kinga Sa’ida ki rabu da mutumin nan tun kafin ya jefa rayuwarki a matsala wannan ce shawarar da zan baki.” Hauwwa ce ke wannan maganar bayan ta gama sauraran duk jawabin da nayi mata.

Shuru nayi ina nazarin maganarta Tace.”Ni wallahi a rayuwata na tsani maza marasa adalci irinsu Alhaji Nura Sa’ida wallahi bana shakka wannan halayyar tasa itace ta janyo matarsa take lesbian saboda baya tsayawa ya biya mata bukatarta kawai kansa ya sani bukatarsa na biya shikkenan bai damu da halin da zaku shiga ba.

Nace.”Hauwwa nima na fara zargin haka wallahi dan gaskiya idan ya kasance Aunty Murja tana da karfin sha’awa kuma tana da rauni to zata iya jefa kanta cikin matsala amma ni bana fatan nayi wannan harkar Hauwwa zan duba shawarar ki dan gaskiya ina masifar ‘kwaruwa a zamantakewa ta da mutumin nan.”

Tace.”To shikkenan Allah ya za’ba miki abinda yafi alkairi.” na amsa da ameen ya Allah ‘kawata nagode kwarai da gaske.”

Haka rayuwar ta cigaba da tafiya yau da dad’i goge babu ta ‘bangaran maigidan babu dad’i bangaran Aunty Murjar ma haka domin kwata kwata yanxu ni da ita bama shiri tun ranar da ta fahimci cewa na gane abinda takeyi ta sanja taku a gidan bata shiga sabgata sai da ni sa’i da lokaci inayi mata magana idan tayi ra’ayi ta amsa idan ba tayi ba ta share ni………..

Ranar Wata laraba tayi bakuwa da yake a falo suka zauna ina jin hayaniyarsu a dakina a nutse na bude kofa na fito. ganin matar dake zaune a kusa da ita yasa gabana ya yanke ya fadi da sauri nayi niyyar komawa daki sai kuma na fasa domin nasan sun riga sun gan ni! A dake na k’arasa falon na nemu kujera na zauna da fadin.”Aunty Murja bakuwa kikayi ne.”? Yau da mutuminci ta amsa min da “Eh wallahi dama yanzu take cewa zata tafi kuma baku gaisa ba.

Nace.” Allah sarki ina kallonta nace.”Ina wuni ya gida ya yara.”? Ta amsa tana min wani irin kallo kaina na sunkuyar kasa gabana na faduwa ina addua a zuciyata akan Allah yasa bata gane ni ba.

Tace.”Ni kam kamar na san wannan fuskar taki.” na kalleta tare da kokarin kauda fargabata nace.”Allah ko.”? Tace.”Kwarai kuwa kamar kece watanni takwas da suka wuce kikaje asibiti keda wata tsohuwa domun a duba miki virginal d’inki.”

Nace.”Anya kuwa bani bace.” ‘Yar dariya tayi tace.”Kece mana ko ba sunanki Sa’ida ba.”? Nace.”Sunana Sa’ida mana.” Tace.”Sannan kuma kice min bake bace.” shuru nayi mata domin idan nace zanyi magana zan iya fashewa da kuka shikkenan asirina ya tonu.

Aunty Murja tace.” Maryam naji kina maganar wata takwas da suka wuce kuma yanzu auransu da Abban Yusura wata biyar kenan.

Tace.”Nima dai abinda ya bani mamaki kenan lokacin taje akan a dubata ko ta qaru a d’inke ta lokacin dana duba sai na fahimci cewar kamar tayi gardama ne a lokacin da za’a kar’bi budurcinta sai na rubuta mata magunguna. har nake tambayarta ina mijinta a lokacin take cewa dani yayi tafiya shine yace tazo asibiti a dubata duk ina da sheda a rubuce.”

Aunty Murja ta dinga yi min wani irin kallo ni kuma sai wani irin gumi nake zabgawa tamkar wacce tayi gudun famfalaki.!

Mi’kewa nayi jikina a bala’in mace na bude dakina na shiga na fada a saman gado kuka na dinga rafsawa ina kiran sunan Allah.

Aunty Murja wayarta ta dauka da fad’in “Dama neman hanyar da zan hukunta yarinyar nan nake domin nima data rufa min asiri zan rufa mata dan haka yanzu zan kira Abban Yusura a waya yazo kiyi masa bayani da bakin ki.”

Dr Maryam tace.”Aa Murja kada kiyi haka dan Allah wallahi ni ban fadi wannan maganar da wata manufa ba ki rufa mata asiri ta zauna dakinta.”

Murmushin takaici tayi tace.”Maryam wallahi ba zan kyale yarinyar nan ba domin itace tayi sanadiyar da Alhaji ya hana Aziza zuwa gidan nan sannan kuma tayi sanadin zuwana gidanmu nayi kwanaki tsayin shekarun aurena da mijina hakan bata ta’ba faruwa ba sai da ta shigo gidan sannan kuma kice na kyaleta ni dai kawai idan yazo kiyi masa cikakken bayanin da zai gamsu nayi miki alkawarin kyauta ta mussaman.”

Dr Maryam tace.”Ai shikkenan tunda ta kasa rufa miki asiri kema sai ki bankad’a nata.” tace.”Ashe kin fahimce ni.

Aunty Murja ta dauki waya ta kira mijinta tace dashi maza maza yazo gida akwai abinda yake faruwa. jin haka Alhaji Nura ya shigo motarsa ya kamo hanyar gida.

Wani irin tashin hankali ya shiga a lokacin da Dr Maryam ta gama warware masa ‘boyayyan sirrin Sa’ida dake lullu’be! ya cire hularsa ya ajiye a hannun kujera yasa hannu ya sharce gumin goshinsa ido jajawur ya kallesu yace.”A ranar dana kusanci yarinyar nan sai da na gane ba budurwa bace amma sabida ta iya tsari da ‘karya ta kawo min wasu hojjojinta na banza to sabida haka tunda yanzu na gane gaskiya lamari zan dauki mataki a kanta domin ni ba zan lamunci zama da macen da zata ha’ince ni ba.”

Yana gama maganarsa ya mike da saurin gaske ya kama hanyar dakinta, ido suka bishi dashi har ya bude dakin ya shiga.

Maganarsa naji a saman a kaina, a furgice na mike zaune ina kallonsa tunda na ganshi a burkice nasan ya samu labarin abinda yake da akwai.

Yana huci! yace.” Sa’ida an yanka ta tashi yau Allah ya tona asirinki Dr Maryam ta bud’a min dukkanin sirrukan ki saboda haka tunda ke kin kasance ma ha’inciya macuciya kije na sake ki saki uku! sai kiji ki auri yaron da yake bibiyarki har gidan auranki wanda dama shi nake zargin ya lalataki kafin aure na dake.”!
Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un! kawai nake nanatawa a cikin raina yayin da nake jin wani irin mugun ciwon kai da mugun jiri d’akin sai juyawa yake dani a takaice dai ban san sanda ya gama cin mutuncinsa ya fita daga dakin ba.

*708 465 3262: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*58&59*
Na jima ina nanata kalmar innalillahi wa’ina ilahiri raji’un a fili da zucci kafin naji wani k’arfin gwiwa gami da danga a tare dani……mikewa nayi jiki a mace na bude wardrobe na had’a kayana cikin akwati tsaf sai da na kwashe kayan sanyawata da duk abinda nasan ina bukata nasa a akwatin kana na rufe ta da kyar ina tunanin wanda zai dau’kar min.

Hijabi na nasa na d’aga akwatin tare da janyo hannunta da yake mai tayoyi ce sai kawai naja ta na bude dakin na fito kaina a kasa dan ko kadan bana kaunar na hada idona dasu….maganarsa naji a kunnena yana fad’in “Tsaya ki tafi da sakamonki cutar da kikayi min kuma na barki da Allah.”

Tsayawa nayi ba tare dana juya ba zuciyata in banda tafarfasa babu abinda take

Daf dani ya tsaya hannunsa rike da takardar sakin nawa….”Kar’bi ki fice min daga gida bana bukatar sake ganinki shiyasa nayi miki saki uku domin hukuncin daya cancanta dake kenan ”

Hawayen dake kokarin kwace min na danne hannuna na rawa na kar’bi takardar da fad’in “Nagode ina rokon Allah yasa haka shi yafi alkairi.”

“Shine ma alkairi kije ki auri daidai dake amma ni ban kasance mazinaciya ba nasan Allah ba zai jarrabe ni da auran mazin…..Hannu na daga masa da fadin” Kaga ka daina kira na da wannan sunan tunda dai ka datse igiyoyin auranka shikkenan.

Aunty Murja dake zaune akan kujera tace.”Ai gaskiya Abban Yusura kayi kuskure banji dadin sakin wulakancin da kayi mata ba haba ina laifi kayi daya ko biyu.A harzuke yace.”Murja saki uku ne ya dace da wannan macuciyar saboda haka ki daina nadama dan na sake ta.

Juyowa yayi kaina yana magana ban tsaya sauraransa ba da sauri na bude kofar falon na fita ina jan akwatin kaya na.

Duk da babu wata tazara mai tsayi sai da na nemi adaidaita sahu ya sauke ni har kofar gida, dari biyu na bashi naja akwatin kayana na shiga gidan gabana har yanzu bai daina faduwa ba.

Yau Gwaggo towon alkama take sha’awa dan haka sau ta tuka abin ta da miyar bushashshiyar ku’bewa ta idar da sallar isha’i ta janyo kwanukan abincin domun taci nayi sallama a gidan.

Labule ta d’aga da fadin.”Kamar muryar Sa’ida nake ji da daddaran nan.” Nace.”Itace Gwaggo.

Tana kallona tace.”To maraba lale shigo daga ciki nima danshi (ra’ba) ne ya hana ni zaman tsakar gidan kin san kwana biyu an tafka ruwan sama.

Ina kokarin shiga dakin nace.”Eh Kwarai hakane kwana biyu ana ruwa sosai.”

“Amma dai lafiya dai domin na gan ki da akwati Allah dai yasa ba yaji kikayi ba.

A sanyaye na zauna gefan tabarmarta nace.” Ya sake ni Gwaggo.”

Wani irin shocking taji a jikinta da sauri tace.”Sa’ida me kike fad’a”?

hawaye na zuba nace.”Gwaggo ina nufin Alhaji Nura ya sake ni kinga ma shedar nan.” Takardar hannuna na mika mata.

A sanyaye tace.”Yo ni ina nayi karantawa Sa’ida me ya faru mutumin nan yayi miki wulakanci kuma saki nawa yayi miki.”

“Saki uku ne.”? Na fada muryata na rawa, Gwaggo innalillahi wa’ina ilaihi raji’un kawai take nanata wa cikin furgici tace.”Sa’ida anya mutumin nan kuwa yana da hankali saki uku a lokaci guda ke kuwa wane irin laifi kikayi masa.”?

Cikin kokarin danne damuwata nace.” Asiri ne ya tono Alhaji Nura ya gane ‘boyayyan sirrin dake lullu’be shine ya yanke min wannan hukuncin.”

“Sa’ida ta ina zai gane ke ba budurwa bace bayan da farko kinyi masa bayani kuma ya amince.

hawaye na share nace.” Nifa Gwaggo bana zargin kowa da mutuwar aurena sai Khalid.” Da sauri tace.”Tofa! bakya zargin kowa sai Khalid to me yayi miki yaron da tuntuni ya tafi gurin sana’arsa.

Hannu nasa na share fuskata nace.”Gwaggo Khalid yaje gidana kuma har cikin ‘kuryar dakina sai da ya shiga kuma Alhaji ya shigo ya sameshi.

Gwaggo rike baki tayi da fad’in “Ashe dai duk jan kunnan da nayi wa yaron nan be ji ba sai da yaje to me yaje yayi miki.”?

Nace.”Gwaggo ya kike tambayata me yaje yayi min gashinan abu a zahiri Khalid yaje gidana dan ya lalata min aure to bukatarsa ta biya sai ya zuba ruwa a kasa yasha.

Gwaggo ta dinga girgiza kai tana fadin.”Kai amma wannan al’amari beyi dadi ba Khalid kuma bai kyauta duk da khalid ya kasance dan uwanki amma ai bai cancanta yana baligi irin wannan ba ya shiga gidan matan aure ba tare da neman izina ba dik abinda Alhaji Nura yayi masa na hukunci daidai ne tunda shi ya taka sharia.

Nace.”Gwaggo to me yasa kin san gaskiya kike takewa me yasa bakya ganin Laifin Khalid kuma me yasa kike fifitashi akaina.”

Cikin nutsuwa tace.”Sa’ida kada ki fassarani da wata manufa mara kyau ni dake da Khalid dik daya kuke a gurina babu wanda yafi wani hakika kuma naji bakin ciki da takaicin abinda yayi saboda haka an jima idan ya kira ni a wayar daya siya min zan nuna masa ‘bacin raina.”

Shuru nayi ina sha’kar bakin ciki! ta girgiza kanta tana jimanta al’amarin tace.”Wai saki uku a gaskiya wannan mutumin bashi da hankali ko kad’an wallahi naji ciwon abinda yayi.”

Nace.”Gwaggo kiyi min addua kawai Allah yasa haka shi yafi alkairi Allah ya za’ba min miji nagari.”

A sanyaye ta amsa da ameeen ya rabbi. dakin ya sake daukar shuru na ‘yan mintina kafin nace.”Gwaggo kin tuna asibitin da kika rakani a washe garin ranar da Khalid yayi min fyad’e.”?

Kallonta tayi a sanyaye tace.”Sa’ida bana so naji kina wannan maganar wallahi babu dadin ji.” Cike da takaici nace.”Gwaggo har duniya ta nad’e ba zan daina maganar nan ba kuma ba zan fasa neman sakayya gurin Ubangiji ba.”

Babu walwala a tare da ita tace.”To naji ya isa haka magana dai tuntuni ta wuce tayar da ita bashi da amfani yanzu sai ki fuskanci abinda yake gabanki.

Nace.”Magana ai tuntuni na barwa Allah yanzu ma dalili tayi shiyasa na fada miki abinda yake zuciyata.

Shuru tayi ba tai magana ba, nace.”Wannan likitar data duba ni ashe kawar aunty Murja ce.”

Kallona tayi da mamaki a tare da ita, na cigaba da cewa “Itace duk ta warware masa komai shi kuma ya fusata ya yanke min wannan hukuncin kafin na fito daga gidan ba kiji irin zagi da cin mutuncin da Yayi min ba.”

Hawaye ta goge tace.”Ki rabu dashi daga shi har ita likitan Allah zai saka miki kuma duk wanda ya tona asirin wani shima sai Allah ya tona nasa yanzu ni tsorana Allah da Annabi kada maganar ta fita jama’ar gari su dinga yi mana wani irin kallo.” Tana kuka take maganar.

Gabadaya naji zuciyata ta karye zafafan hawaye suka fara zubo min nace.”Gwaggo insha Allahu hakan ba zata kasance ba idan kuwa maganar ta fita to zan tattara kayana na gudu gurin mahaifiyata.”

Kuka takeyi sosai tana kallona had’e da girgiza kanta, Kaina na sunkuyar kasa ina shakar hanci tare da jin tsananin tausayinta a cikin raina.

“Gwaggo ba’kuwa kikayi ne na fito domin d’ibar ruwa naji magana a dakin ki.” Maganar Ummatu ce ta dawo damu nutsuwarmu tana tsaye a bakin kofar dakin hannunta ri’ke da labule.

Ido muka had’a tace.”Au ashe Sa’ida ce.” Nace.”Eh Ummatu Ina wuni ya gida.”?

Ta amsa a sake tana tambayata maigidana….Gwaggo tace.”Rabi wane maigida kike tambaya bayan ya sake ta.

Da sauri tace.”Gwaggo ban gane maganarki ba.” Tace.”Ina nufin Alhaji Nura ya saki Sa”ida saki uku.”

Da sauru tace.”Subahannallahi Sa’ida garin ya haka ta faru me kikayi masa.”?

Gwaggo a d’an hasale tace.”Rabi har kin manta ashe.”? Kallonta tayi jikinta duk yayi sanyi Gwaggo ta cigaba da cewa”Ko wane namiji dai yana kulafucin wannan abu (budurci) to da Alhaji Nura ya tabbatar da cewa Sa’ida bata dashi shine ya yanke shawarar sakin ta.”

Ummatu shuru tayi jikinta duk yayi la’asar Tace.”To amma me yasa tun farko beyi magana ba sai da tayi wattani a gidansa Gwaggo anya wannan ce matsalar.”

Girgiza kanta tayi tace.”Rabi wannan ce matsalar ko kinqi ki kin so sai matsala ta biyu ashe Khalid duk jan kunnansa da nayi akan kada yaje gidan mutumin nan sai da yaje saboda tsabar wuce gona da irin nasa har ‘kuryar daki ya shiga.

Ummatu gabanta na fad’uwa tace.”Gwaggo a yaushe Khalid din yaje gidan bayan yau satin sa uku da tafiya.

Tace.”A ranar da zai tafi yaje da safe kuma Alhaji Nuran ya ritsa shi a dakin baccin sa Rabi wace irin masifa yaron nan yake so ya janyo mana

Ummatu taji ‘kwalla ta cika idonta Itakam ta rasa wace irin masifa ce wannan wane irin kwadayi da kulafuci yaron keyi akan wacce bata dace dashi ba, aranar da Gwaggo take masa fada akan kada ya kuskura yace zaije gidan tana jinsu har ta shiga dakin tasa baki tayi masa gargadi sosai ashe jinsu kawai yake da kunne ya mayar dasu shashashai sai da yaje ya dauko musu magana.

Kai ta kad’a ta bar gurin ba tare da tace komai ba, Gwaggo tace.”Duk kauce-kaucen da za kiyi dole sunan Khalid ya fito a cikin mutuwar auran Sa’ida.”

Koda kawu ya dawo ya sameni a gidan bai kawo komai ba a cikin ransa muka gaisa a nutse ya shiga gurin sa domin cin abinci da hutawa.

Gwaggo bayan ta tabbatar da cewa yaci abinci ya huta sai ta fito tsakar gida tana ‘kwala masa kira, da sauri ya bude kofar gurun nasu ya fito yana fadin”Gwaggo lafiya dai ko? Ina S’ida ina fatan ta tafi gidanta.

Tace.”Sa’ida tana nan ai kuma ta dawo kenan sabida saki ukun da mijin nata ya rattaba mata.”

Kawu wani irin gumi! ne ya jika masa riga baki na rawa yace.”Gwaggo me yasa mutumin nan zaiyi mana haka? me yarinyar nan tayi masa da har zaiyi mata irin wannan hukuncin

Kai tsaye tace “Munafurtar sa akayi Ibrahim me yasa tun farko baka sameshi ka fada masa abinda ya faru ba.

Yace.” Gwaggo ya za’ayi na tonawa yarinyar nan asiri? wane namiji ne kike gani zai ji wannan al’amari ya yarda da auran.”

Tace.”To ai *”GA IRINTA NAN!* An yanka ta tashi domin dai likitar data duba ta a washe garin ranan da al’amarin ya faru To itace ta tabbatar masa da gaskiyar lamarin bayan haka kuma ashe Khalid a ranar da zai tafi sai da yaje gidan saboda kuma wace gona da iri irin nasa har uwar daki ya b ita a takaice ma dai sai da maigidan ya shiga ya same shi Ibrahim ka fad’a min shin Khalid me yake nufi da aikata hakan.”?

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*60&61*
Kawu Iro shuru yayi a gurin tamkar ruwa ya cinyeshi gabadaya al’amarin ya daure masa kai ya rasa ma bakin magana shi kam ya rasa wane irin yaro Allah ya bashi. Gwaggo ta kalleshi da fadin”Ibrahim kayi shuru ka kasa magana.” Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace.”Gwaggo al’amarin ne ya daure min kai shiyasa kikaji nayi shuru na kasa cewa komai wato Khalid yayi hakane domin ya kashe mata aure ta fito daga gidanta shi ya aureta hakane ko ba haka bane.” ? Gwaggo tace.”Ato nima abinda nake zargi kenan…..Ummatu ta karaso gurun da fad’in “Dan Allah Gwaggo kuyi wa al’amarin nan kyakykyawar fahimta kada ku zargeshi da mummunar manufa tunda kun san dai maganar auransa da Jamila tayi nisa to mai zai sanya ya kashe auran Sa’ida wannan magana tuntuni ta mutu domin ya hakura ya kar’bi Jamila a matsayin matar auransa.

Kawu yace.” Rabi ke kika haifi Khalid amma har yanzu baki san halinsa ba yaron mugun Hatsabibi ne.” Cikin bacin rai yayi maganar….Gwaggo tace.”Kada kayi masa baki Ibrahim ka daina kiransa da wannan suna addua za’ayi masa.

Yace.”Gwaggo idan wannan ce manufar Khalid akan Sa’ida to ni mutukar ni na haifeshi ba zan lamunce masa auranta ba Allah zai kawo mata miji daidai da ita ta aura.”

Jin abinda ya fada Yasa Ummatu jin dadi a zuciyarta gurin ta bari tana godewa Allah. Gwaggo jiki a sanyaye tace.” Allah ya kyauta ya za’ba mana abinda yafi alkairi.” amsawa yayi da amin ya kama hanyar fita yana kokarin fito da wayarsa.

Kofar gida ya zauna yana goge gumi hankalinsa a tashe ya nemo number wayar Alhaji Shamsu ya kirashi domin ya sheda masa halin da ake ciki.

Alhaji Shamsu hankalinsa ya tashi jin irin bayanin da Kawu Iron ke masa yace.”Ibrahim na jima ban ji ‘bacin rai irin na yau ba kuma banta’ba tsammanin Alhaji Nura zaiyi mana wannan wulakancin ba shin me yarinyar nan tayi masa da har zaiyi mata saki uku.”?

Kawu ya goge gumi yana dawurwura hakika yana jin nauyi da kunyar fada masa dalilin da ya janyo sakin….Alhaji Shamsu yace.”Ibrahim ka kwantar da hankalinka Alhaji Nura bamu ya tozarta ba kansa ya tozarta kuma abinda kayi wa d’an wani kaima sai anyi wa naka.

Kawu yace.”Kwarai da gaske Alhaji maganarka haka take.” Yace.”Yanzu yanzu zan kirashi a waya dole ya fad’a min dalilin da yasa ya saki yarinyar nan domin hankalina gabadaya ya kasa Kwanciya inata tunani babu shakka ruwa baya tsami banza.

Jiki a mace Kawu yace.”To shikkenan Alhaji duk yanda kukayi dashi sai ka kira wayata ka sanar dani.”

Alhaji Shamsu yace.”Insha Allahu zan kaji daga zarar mun tattauna magana dashi.”
Sallama sukayi kowanne ya kashe wayarsa.

Washe gari da safe Alhaji Shamsu ya zaunar da matarsa kafin ya fada mata abinda yake faruwa sai da yayi mata nasiha mai ratsa jiki sannan ya sheda mata abunda ya faru da ‘yarta.

UmmuHabiba fashewa tayi da kuka tana girgiza kanta take fadin.”Innalillahi wa’ina ilaihi raji’una Alhaji wannan wane irin wulakanci ne? saki uku a lokaci guda akan wane dalili ashe dama mutumin nan auran sha’awa yayi.”

Alhaji Shamsu ganin hankalinta ya tashi tana kuka ya shiga rarrashinta yana bata baki har sai da tayi shuru tana goge fuskarta yace.” Dama yanzu nake tunanin kiransa a waya naji bayani daga bakinsa domin tabbas akwai dalili mai karfi da ya janyo hakan.”

Tace.”Eh ai gwara ka kirasa a wayar yayi mana bayani muji abinda ya janyo wannan cin mutuncin.

Wayarsa ya dauka ya nemo number Alhaji Nuran ya shiga gurin kira.

Yana kokarin fita kasuwa kiran wayar ya sameshi ya fito da ita daga aljihu yana dubawa, ganin number Alhaji Shamsu yasa yaja tsaki! aunty Murja ta kalleshi da fadin”Lafiya dai.”? Yace.”Mahaifin yarinyar nan ne Sa’ida.” shuru tayi bata ce uffan ba har wayar ta katse wani kiran ya sake shigowa.

Tace.”Kayi hakuri ka dauka mana kaji abinda yake tafe dashi a yanzu dai ai babu wata magana tunda saki uku kayi mata.”

Wayar ya daga yasa a kunnensa had’a da sallama…..Alhaji Shamsu ya amsa masa a nutse suka gaisa da juna kafin yace.”Alhaji Nura wane gagarimin laifi yarinyar nan tayi maka kayi mata saki uku a lokaci guda.”?

A tur’bune yace.”Kana so kasan dalili kenan.”? Da sauri yace.”Eh ai sabida inaso nasan dalilin yasa na kira wayarka domin dai nasan babu shakka ruwa baya tsami banza.”

Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace.”Ai Alhaji kune da laifi kuma banta’ba tsammanin zaku munafurce ni ba ashe yarinyar nan sai da ta gama watsewa da lalattatun maza a waje ku rufe min na aureta.

Cike da mamaki yace.”Wace irin magana kake Alhaji Nura ban fahimci inda ka dosa ba yarinyar nan Sa’ida da kima da mutuncinta muka aura maka ita.”

Da sauri yace.” Waye ya fada maka haka? bari ma dai na daina rufe maka magana a ranar dana kusanci yarinyar nan na gane ba budurwa bace fanko ce. lokacin dana turketa ina tuhumarta tana kuka ta kawo min wasu hojojji wanda suka kashe min jiki har na yarda da ita na cigaba da zama da ita, a kwanakin baya yaron da nake zargin shi ya lalata ta yazo har cikin gidana sabida tsabar cin fuska har cikin d’akina na same su nan ma raina ya ‘baci sosai na nuna mata kuskuranta hakuri ta bani ta nuna min babu wata alaqa a tsakaninsu sai gashi jiya Dr Maryam likitan ta ta tabbatar min da gaskiyar magana kuma itama Sa’idar ba tayi musu ba akan abinda ake zarginta dashi al’amari ya fusata ni sosai kuma naji takaicin abinda kukayi min na ha’inci wannan dalilin yasa na yanke alaqar aurena da ita.”

Alhaji Shamsu ji yayi gumi na tsatstsafo masa bakinsa ya bushe qamas da kyar yace.”Alhaji Nura ka dai fad’i wata hujjar amma ba wannan ba yarinyar nan Sa’ida bata san ko wane namiji ba lafiya lau muka aura maka ita kadai kara binkice akan maganarka.”

Alhaji Nura yace.”Alhaji a yanzu dai babu batun tashin-tashina a tsakaninmu tunda dai na yanke alaqar data had’a mu shikkenan magana ta ‘kare dan Allah kada ka ‘kara kiran wayata kazo min da maganar Sa’ida na sake ta saki uku babu ni babu ita.”

A fusace! Yace.”To sai me don ka saketa Alhaji Nura akwai maza a duniya da zasu aureta kuma wallahi ina mai tabbatar maka da cewa sai kayi nadamar abinda ka aikata.”
Yana gama maganarsa ya kashe wayar sam baya bukatar sake jin wata magana daga bakinsa sabida yayi masifar ‘bata masa rai.”

Ummu Habiba kallonsa kawai take ko beyi mata bayani ba ta fahimci komai tunda wayar a hands free take…..Gumin goshinsa ya goge yace.”Saboda kawai yana so ya rabu da yarinya sai yayi mata kazafin zina Habiba kina jin abinda mutumin nan yake fada akan yarinyar nan Sa’ida wai bai sameta da budurci ba to bai samu budurcinta ba me yasa tun farko bai fada ba sai yanzu da tayi watanni a gidansa ni nafi tunanin cewa ya gaji da zama da ita ne shiyasa ya shirya wannan maganar.”

A sanyaye tace.”Ni kaina al’amarin ya daure min kai kuma duk bayanin da yayi maka naji da kunnena dama can ba son Allah da annabi yake mata ba sha’awarta yake.”

Ya dauki hularsa yasa da fad’in “Ai babu komai duk wanda yayi nagari kansa kiyi hakuri kuma ki cigaba dayi wa yarinyarki addua insha Allahu Allah zai za’ba mata abunda yafi alkairi a rayuwarta.

A sanyaye ta amsa da ” Ameeen Alhaji nagode sosai da kulawar ka akan yarinyar nan.” Yace.”Habiba ni na dauki Sa’ida tamkar ni na haifeta saboda ina tausayawa maraicinta ina kuma kwadayin ladan kula da maraya sabida haka kada ki damu zan tsaya tsayin daka akan yarinyar nan.”
Tace.”To shikkenan Alhaji Allah ya shige mana gaba kai kuma abinda kakeyi na alkairi Allah ya baka lada.” ya amsa da ameeen ya Allah yana kokarin fita sai ta mike a nutse tabi bayansa domin taka masa.

Koda ta dawo gidan dakinta ta shiga ta zauna kan kujera babu kuzari a tare da ita ta dauki wayarta number ‘yar tata ta nema ta shiga gurin kira.

Lokacin data kira ina bandaki ita kuma Gwaggo bata iya da waya ta ba kira ta dinga kwala min da fadin na fito ana kiran wayata.

A gugurje na fito daga bandakin na ajiye butar hannuna, wayar ta miko min da fadin.”Kinga har ta katse sai ki duba kiga ko wanene idan Khalid ne kada ki daga ki shareshi kamar yanda nake masa idan ya kira ni.”

Murmushi kawai nayi ba tare da nace mata komai ba na nufi dakin da wayar a hannuna ina dubawa

Ganin number Ummana yasa da sauri na zauna gefan gado na shiga gurin kira da alama wayar tana hannunta domin sau daya tayi ringing ta daga, yanda naji muryarta a sanyaye yasa nima jikina ya mutu a nutse na gaisheta ta amsa tare da fadin.”Ya mukaji da wannan abu.”

Nace.”Alhamdulillahi Umma.” Tace.”Kiyi hakuri kinji ko kowane mutum akwai irin kaddararsa kisa a ranki cewa dukkanin abinda ya faru da rayuwarki kaddara ce insha Allahu wataran sai labari.”

Hawayen da suka zubo min na share murya na rawa nace.”Insha Allahu Umma ki taya ni da addua akan Allah ya za’ba min abinda yafi alkairi.”

Tace.”Sa’ida addua kullum akanta muke Ubangiji Allah ya amsa mana adduo’inmu na alkairi.” cikin sanyin murya na amsa da ameeen Ummana.” Tace.”Ki gaishe min da Gwaggo da kyau.” nace.”To zataji insha Allahu.” Sallama mukayi da juna……Gwaggo ta shigo dakin tana fadin.”Dawa kike waya ne.”? Nace.”Umma Habiba ce tace ma a gaisheki.”

Kallona tayi da fadin.”Ita kuma a ina ta samu labarin abinda yake faruwa.”? Nace.”Watakila ko Kawu ya sanar da mijinta ne.”

Tace.”Eh hakan zata iya yuwu wa Allah dai ya kyauta.” cikin mutuwar jiki na amsa da “ameeen ya Allah.

*BAYAN SATI DAYA*
Na d’an samu nutsuwa hankalina ya dawo jikina sai nayi tunanin kiran Hauwwa a waya domun na sheda mata abinda yake faruwa……….Sosai Hauwwa tayi mamakin al’amarin daga bisa ni tace.” Yanzu dai kinga ne abinda ke da akwai ko? a yanzu dai kin fahimci cewa auran Babban mutum bashi bane tunda gashinan wata shida har anyi an gama ya rattaba miki saki uku wallahi da Khalid kika aura ba zaki fuskanci wannan matsalar ba babban tashin hankalin ma mutumin nan yayi miki sanadin aikin ki.”

Nace.”Ni wallahi a yanzu shine babban abinda yake damuna wata shida bai zama lallai idan na koma aiki su kar’be ni ba……Hauwwa tace ko zasu kar’be ki sai an kai ruwa rana amma babu matsala ni zanyi miki kokari kin san Shugaban makarantar yana zawarcina zanje har ofis d’insa na lalla’ba shi.” Nace.”Yawwa aminiyata nagode kwarai dan Allah kiyi min kokari.” Tace.”Kada ki damu mybe ma gobe idan mun tashi na shigo domin mu tattauna.” Nace.”To shikkenan sai kin shigo Hauwwa nagode Allah ya bar zumunci.” ta amsa da ameeen ya Allah ki gaishe min da Gwaggo.” nace.”Za taji insha Allahu.”

Wayar na kashe ina jin sassauci a cikin zuciyata…..Gwaggo dake kad’i ta kalleni da fad’in.” Naji kina magana komawa gurin aiki Sa’ida ke yanzu sai ki koma cikin maza bayan zargin da ake miki.”?

Nace.”Gwaggo kina so kenan na zauna a gida babu aikin fari bare na baki ko.”? tace.”Oh!o ni nafi so ki samu miji kiyi aure Sa’ida.” Nace.”Gwaggo kada kiyi min maganar aure a yanzu domin dai bashi ne a gabana ba” Tace.”To ai shikkenan idan lokacin auran yazo sai ki hana Allah ikonsa.” shuru nayi mata domun nasan neman magana take…..Ummatu ta daga labulan dakin da waya a hannunta tana fadin.”Gwaggo ga d’an d’akinki ya kira waya wai yana so ku gaisa.'”

Tace.”Ke Rabi raba ni da wannan yaron ki fada masa ni bana bukatar magana dashi a yanzu.” Tace.”Gwaggo me yayi zafi.”? Tace.”Rabi duk irin kulawa da rarrashin da nakewa yaron nan besa yaji maganata ba to ni kam me zaice dani ai na daina wahalar da kaina a kansa.”
Ummatu jikinta a mace ta bar gurin…Gwaggo taja tsaki da fad’in “Kawai kin d’auko wata kod’add’iyar yarinya kin nana masa ya aura yarinya sai kace zabiya tana yawo sai kace takand’a babu kumari babu ‘kira da cika irin na mata.'”

Dariya nasa ina kallonta nace.”Gwaggo kefa naji kina kod’a yarinyar kina cewa sun dace da juna gata kyakkyawa mai kuruciya.”

Tace.”Ai ni banta’ba ‘karewa yarinyar kallo ba sai ranar da ta zo gaishe ni lokacin yana nan be tafi ba ranar nayi azimin litinin yaje ya dauko ta wai tazo tayi min sannu da shan ruwa tsabar haushi ko kayan data kawo min ban duba ba na bawa al’amajirai.”

Nace.”Yanzu dai kina nufin bakya kaunar al’amarin kenan.”? Tace.”Yo Sa’ida me Jarumi zai samu a jikin yarinyar nan jiki a bushe ko’ina babu kumari sai qashi shi kuwa kato dashi tubarkallah ai yana da kyau ya samu ‘koshashshiyar mace yanda zai more kuruciyarsa.

Dariya nayi sosai ina kallonta nace.”Gwaggo wai dan Allah me yasa bakya kunyar fadar magana ne? Tace.”Sa’ida wace kunya kuma ai gaskiya na fad’a.” Nace.”To Allah dai kyauta Gwaggo ni dai shawarar da zan baki ki kauda kanki daga al’amarin nan idan kika ce zaki zuga Khalid ya bijirewa umarnin mahaifiyarsa zaki jefe shi a masifa sannan Ummatu da ‘yan uwanta zasu dinga jin haushinki.”

Tace.”To dama Sa’ida ni ina ruwana yaje ya aureta nasan duk daran dad’ewa sai ya sake aure tinda ni nasan halin fitinarsa wannan siririyar yarinyar ba iyawa za tayi dashi ba.”

Ina dariya nace.”Gwaggo ai ba’a nan take ba sai kiga mace mara qiba amma sai ki sameta da juriya da kuzari ita kuwa mai qibar sai ki sameta da raki da rashin juriya.”

“Ummm! tace ta cigaba da abinda takeyi a jiyar zuciya na sauke a hankali nace.” Gwaggo ni dashi Allah ya za’ba mana abinda yafi alkairi ki tsananta dayi mana addua.” Tace.”Insha Allahu Addua ba zamu bari ba har sai ranar da numfashi ya fita daga gangar jikinmu.”

[3/24, 11:39 AM] +234 703 008 7807: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*66&67*
Gefan zaninta tasa ta share hawaye da fadin.”Ai shikkenan Sa’ida tunda haka zaki ce dole nayi hakuri da hukuncin da kika yankewa kanki amma ni sam bana sha’awar ki da wannan mai ba’kar fuskar.” Kallonta nayi ina mamakin maganarta Gwaggo idan bata son abu komai kyawun sa ta dinga kushe shi kenan amma in banda haka meye laifin Yaya Aminu kyakykyawa ne sosai Khalid din babu abinda zai nuna masa sai haske fata.

Nace.”Gwaggo maganar nan ta wuce don Allah ki daina kuka da damuwa ki cigaba da addua ni da Khalid din Allah ya za’ba mana abunda yafi alkairi Gwaggo duk sonki da na auri Khalid idan Allah bai nufa ba dole ki hakuri kin san komai nufi ne na ubangiji mussaman sha’ani na aure ba’a katsalandan a ciki kawai ki roki Allah alkairi sai kiga ya tabbatar miki.

Tace.”To me kika ji na k’ara cewa? ai magana kuma ta wuce wannan yaro Khalid kuma Allah ya sanya masa dangana.”
Ameeen na amsa ina kokarin mi’kewa tsaye

*Bayan sati biyu*
A tsakanin kwanakin Yaya Aminu yazo guri na mun gaisa sosai kuma yanda yake nuna kulawarsa a kaina yasa na gane cewa lallai ba dole akayi masa ba domin ‘karara yake nuna min so da kauna ga uwar hidimar da yake min sai kace hauka ya kawo min sabuwar waya mai kyau da tsada kudi kuwa duk bayan kwana uku ko hudu zan ga alert dubu ashirin dubu talatin har dubu hamsin turo min yake idan nayi masa magana sai yace shine yayi niyya idan inada bukatar ya ‘kara min wasu sai nayi magana, al’amarin ya dinga bani mamaki mutuka gidan Hauwwa naje domin mu tattauna maganar dan gaskiya ni kudin da yake bani suna bani tsoro ni ba auran kudi nake so nayi dashi ba nafi bukatar idan na aureshi ya rike ni tsakani da Allah mu zauna lafiya…..Koda Hauwwa ta gama jin bayani na sai tayi dariya tana fadin.”Sa’ida kenan ke yanzu saboda rashin wayo da dubara har magana kike masa ya daina baki kudi? to idan ya daina baki wa kike dashi wanda zai baki? komai fa da kika gani yana da lokacinsa saboda haka ki kwantar da hankali Idan kullum zai dinga sa miki million a accont dinki kada kice masa don me kiyi godiya kawai idan baki kar’ba ba wasu can a waje su za su kar’be Yana da kudi to me zaiyi dasu tunda dai shi bashi da nauyin kowa a kansa ke d’in dama ke zai bawa sai mahaifiyarsa da sauran ‘yan uwansa saboda haka ki nutsu ki samu abinda kika samu kafin lokaci ya kure miki.”

Shuru nayi ina ta nazarin maganarta tace.”Ni wallahi nayi miki murnar auransa domin ta ko’ina yayi bashi da makusa saboda haka kawai ki kwantar da hankalin ki ayi al’amarin nan cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Shikkenan Hauwwa Allah yasa hakan shi yafi alkairi.” ta amsa da ameeen tana kokarin mikewa tace.”Bari na kawo mana abinci.” ido kawai na bita dashi ina mamakin son kud’inta Na lura bata da tsinkaye da tunani mutukar akan kudi ne.

Can gidan Alhaji Shamsun kuwa kowa yana cikin farin ciki manya da yaransu amma banda mahaifiyarsa Hajia Mariya tun sanda maigidan ya sheda mata hukuncin da ya yanke take cikin k’unci sam bata so d’anta ya fara da bazawara a ganinta kamar hakan koma baya ne domin kuwa babu abinda d’anta ya rasa na jin dadin rayuwa to ta yaya za’a ce lallai sai ya auri bazawara sai kawai ta yanke shawarar tun karar maigidan da maganar Alhaji Shamsu tunda yaga take taken ta ya bude mata wuta sosai ya nuna mata kuskuranta yace kuma mutukar yana numfashi to sai anyi auran don haka kawai tayi addua domin shine abinda ya cancanta.” Sanin halin mijin nata yasa bata sake tankawa ba duk irin hidimar da akeyi a gidan idone nata su kuma kishiyoyin nata sai suke ganin kamar kawaici da kunya take irin na d’an fari Tsakaninta da Umma Habiba babu wata matsala dan ko a fuska bata nuna mata cewa bata son auran ba, ta bar komai a cikin zuciyarta tana dai kallonsu sai farin ciki da murna sukeyi……..Manya akwati mai sheda cike da manya kaya masu tsada aka kai wa Sa’ida a matsayin kayan lefe Gwaggo da Ummatu da sauran jamaa suka dinga mamaki ko auranta da Alhaji Nura bata samu wannan alkairi ba Gwaggo dai gajiya tayi da duba kayan sabida tsabar yawan su ta bar gurin sai surutai takeyi Ummatu kam sai da ta lissafa iya adadin kayan lefan Atamfa Talatin les Talatin shadda talatin komai dai gashinan kamar hauka don tsakar gidan cika yayi da kayan makota nata shigowa suna gani sai can dare kafa ta dauke a gidan……Koda Kawu Iro ya dawo Gaggo turkeshi tayi da fadin.”Ibrahim wai shin meye sana’ar wannan yaron ne.”? Yace.”Gwaggo wa kike nufi.”? Tace.”Aminu mana.”? Murmushi yayi yace.” Siyar da tufafi ko wane iri shine sana’arsa a ‘kalla yana da rumfuna sama da biyar a kantin kwari kuma akwai wani babban company da suka bude a chana suke sarrafa audiga ai bai fiye zama a gari ba.

Tace.”Koda naji duba kaga irin uban lefen don Allah mutane sai gulma suke shigowa mu ba kudi muke so ba albarkar aure muke bukata.

Murmushi yayi yace.”Gwaggo kenan ai mutane dama ba zaki rabasu da wannan gulmace gulmacen ba to duk dai wanda ya shigo da sunan ganin kayan lefe sai ku nuna masa shine abinda ya dace.”

Tace.”To Allah ya kyauta dai ya rufa asiri.” ya amsa da ameeen ya rabbi tace.”Yanzu sati nawa suka d’iba domin daurin aure.”? Yace.” Kwana bakwai ne rana ita yau kenan.” Tace.”To Allah ya nuna mana. ” ya amsa da ameeen yana kokarin barin gurin tace.” D’azu da safe kuwa Khalid yace yana kan hanya zaizo gobe ko jibi wai zasu tafi america suyi wasa.”

Yace.”Gwaggo Nifa bana son yaron nan da wannan harkar kafurci ne tsagwaronsa.” Tace.”Ibrahim nima bana so to ya zamuyi idan ya kasance anan abincinsa yake.

Yace.”Dole idan yazo na zauna dashi domin bana tsammanin zan barshi ya koma Lego’s din nan bare ya tafi wata uwa duniya america Buga ball da turawa ya haramta.” Tace.”Ai ko bada da turawa ba ma buga ball a ko’ina ne bai halasta ba kamar an tozarta ahalin gidan Annabi ne.” Yace.”Gwaggo ai ba kama bane Gaskiya ne duk wanda ya buga ball kamar yana buga kawunan Shirafa’u Jikokin Annabi Muhammad (SAW) wannan dalilin yasa idan ya dawo zan zauna dashi akan al’amarin.

Tace.”To shikkenan Allah Ubangiji Ya za’ba abinda yafi alkairi.” Ya amsa da ameeen tare da barin gurin

To koda Hauwwa tazo ganin kayan lefen itama sai da tayi mamaki mussaman data ga set din gold har biyu da ‘kirar saudi dana dubai ta dinga mamakin al’amarin tana girgiza kanta ta kalleni da fadin.”Ke dai Sa’ida ‘kashin ki na manyan mutane ne duba dan Allah lefe sai kace na ‘yar gatan budurwa.”

Murmushi nayi kawai nace.”Hauwwa kenan Ni wallahi yanzu duk ba wannan ne a gabana ba burina kawai naga na zauna kalau a dakin aurena dan bana so da kuruciya ta kawai a dinga lissafin min aure ina addua akan Allah yasa anyi kenan.

Tace.”Ki daina wani wasiwasi da zancan zucci insha Allahu baki da matsala da Aminu tinda yana sonki zai kula dake kamar yanda kike bukata.” Wannan kalaman nata suka sanya ni naji sanyi a cikin zuciyata sai kawai muka shiga tattauna yanda al’amuran biki zai kasance.

Ya kama saura kwana uku daurin aure Khalid ya dira a garin ni lokacin ma bana gidan ina gidan Hauwwa tare da masu gyaran jiki.

Kawai naji kira ya shigo waya ta dana duba sai naga number Gwaggo ce amma kuma ina daga wayar naji muryar Ummatu tana fad’in “Sa’ida sai ki zuba ruwa a kasa kisha ga Khalid a kwance yana aman jini.

Gabana ya dinga buguwa nace.”Ummatu ban gane maganarki ba. Tana kuka tace.”Ai dama ba zaki gane ba tunda bukatar ki ta biya ni dai idan ki kayi sanadiyar mutuwar yaro na Allah ya isa.” Kafin nace wani abu ta kashe wayar.

Jiki a mace na kalli Hauwwa dake kallona nace.”Wai Khalid ne ya dawo yake aman jini.” da sauri tace.”Aman jini kuma.”? Murya na rawa nace.”Eh.” Tace.”Sa’ida me ya janyo masa to.”? cike da mamaki nake kallonta Nace.”Haba Hauwwa ya kike tambayata kamar baki san komai ba.”?

Tace.”Ashe dai har yau be hakura ba.”? nace”Gashinan kuwa mybe daya samu labarin daurin aurena al’amarin ya afku.”

Tace.”Kai gaskiya wannan yaron yana nacin sonki haba ai ya dace ace ya hakura kuma tinda dai yanzu kinyi masa nisa gabad’aya ma ke jininki bana ‘kananun yara bane sai ya hakura kawai.”

A sanyaye nace.” Zai hakura ai yaron mugun naci ne dashi bayan abinda yake bukata ya samu a gurina to menene na kulafuci.” Kallona tayi tana neman ‘karin baya ni a maganata, na share maganar ina kokarin mikewa tsaye…..Yarinyar dake sa min salatif a kafata tace.” Aunty ya zaki tashi kuma ki zauna a cigaba da saka salatif din kada yasha iska.”

Ina kokarin sa hijabi na nace.”Mansura bana tsammanin zan zauna zaman ‘kunshi a yanzu zanje na duba halin da d’an uwana yake ciki.”

A sanyaye tace.”To aunty Allah ya bashi lafiya.”Hauwwa ta kalleni da fad’in.” Amma zaki dawo ko.”? Nace.”Watakila zan dawo idan hali yayi.” Tace.”To shikkenan Allah ya sauwake.”

Babu cikakkiyar nutsuwa a tare dani na amsa da ameeen nagode jakata na dauka da sauri na kama hanyar fita.

Yanda naga sun masa rumfa yasa gabana ya tsananta faduwa murya na rawa na kira sunansa yana kwance a kan katifa idonsa a rintse…….Jin muryar ta yasa da sauri ya bude idonsa, saurin sunkuyar da kaina nayi haka kawai naji ina jin nauyi da kunyarsa…. motsa bakinsa yake yana so yayi magana sai ya fasa ya mayar da idonsa ya rufe kawai sai ganin hawaye mukayi yana sauka a kuncinsa…

zuciyata ta karya ina rawar Murya na kalli Gwaggo da tayi firgai-furgai hawaye duk ya bushe a fuskarta nace.”Gwaggo mu tafi asibiti dashi a duba shi sosai ina aman jinin da yayi.”? ina maganar ina bin tsakar gidan da kallo.

Tace.”Sai kawai mu zauna zaman jiran ki ai tuntuni mukaje asibiti suka duba shi suka kuma bashi magani aman jini kuma an wanke domun ke baki isa ayi miki ‘karya ba.

Nace.”Gwaggo me ya kawo wannan maganar ai nima ba ‘karyatawa nayi ba.” Dauke kanta tayi ta cigaba dayi masa firfita da maficin hannunta, tsakin Ummatu naji akaina kafin na juyo ta bar gurin tana surutai.

Girgiza kaina nayi nasa hannu na goge hawayen da suka zubo min…..Tace.”Sa’ida ai kuka yanzu kika fara tunda baki da tausayi sai Allah ya sakawa wanda kika zalinta.

Shuru nai mata na mayar da hankalina kansa har yanzu idonsa a rufe yake murya na rawa na kira sunansa.

Shuru yayi bai amsa min ba, na sake kiran sunansa tare da kama hannunsa……da mugun sauri ya fizge hannunsa ya bude idonsa yana kallona cikin Sha’kakkiyar murya yace.”Bana bukatar ganin ki Aunty Sa’ida I hit you i hit it !! na tsane ki! bana sonki! sai kinga sakamakon abinda kikayi min kije ki auri duk wanda zaki aura ni kuma zan mutu da sonki a cikin raina.” Yana maganar yana tari da riqe kirji! Gwaggo duk ta gigice tana rirrikeshi cikin dauriya na hau katifar sosai ina kokarin rikeshi kamar walkiya ya juyo a zafafe ya hankad’e ni na fad’i a kasan gurin! da hannu yake nuna ni yana so yayi magana amma kuttun bakin ciki ya hanashi kawai sai jini muka gani ya ambulo daga bakinsa.

Ihu! na kurma! a kid’eme na sake hawa katifar na kamo shi gefan hijabi na nasa ina goge masa ina kuka wurjajan na kalleshi da fadin.”Khalid ashe da gaske ne? me yayi zafi Khalid kada ka kashe kanka don Allah kayi ta wakkali ka cigaba da neman za’bin Allah.”

Zafafan hawaye ne suke sauka a kumatunsa hannu na na rawa na dinga goge masa ina kuka da fadin.”Kayi hakuri dan Allah ka barwa Allah lamarin nan Khalid ka daina aman jini kada kasa mu cikin masifa.

Gwaggo da tausayin su ya isheta sai ta mike jiki a sa’bule ta shiga dakinta tana share hawaye da adduar d’auki daga Allah.

Rarrashin sa na cigaba dayi ina shafa kanshi da bayansa gabad’aya ya lafke a jikina sai ajiyar zuciya yake saukewa nauyin sa be dame ni ba ni dai buri na yayi min magana yaja bakinsa yayi shuru idonsa a rufe sai sake sakin jikinsa yake a jikina.

A hankali na kira sunansa. Ya bude idon yana kallona nace.”Kayi hakuri ko.”? tsira min rikitattun idanun nasa yayi nayi tsai ina karanta abinda yake cikinsu…….Babu wata alama data nuna ya dauki nasiha ta…..Hannuna na turmutsa cikin tarin suman kanshi a sanyaye nace.”Khalid komai na rayuwa yana tafiya ne da ikon Allah duk yanda mutum yake son abu idan Allah baya sonsa da abun dole ya hakura shiyasa kaji ina cewa kayi hakuri ka nemi za’bin Allah Ni bana ‘kin ka Khalid idan Allah ya kaddara aurena dakai duk rashin sona dole na hakura don Allah ka kwantar da hankalinka.

‘Kuguna ya zagaye da hannuwansa, kallonsa nayi gabana na faduwa……….”Zaki auri wani ya ‘karasa kwashe min Ni’ima ko.”? yafada cikin sar’kewar murya. gabana na wani irin bugawa nake kallonsa….lumshe idonsa yayi ya sake yin release a jikina…….Bana bukatar wani banza ya ra’bi jikin ki aunty Sa’ida ke kuma gashi kina ta basu goyon baya akan hakan yanzu me kika hango a tare da wannan mutumin da zaki aura ko kudinsa kike so.”?

Ajiyar zuciya na sauke ina kokarin cire shi daga jikina nace.”Khalid me yasa kullum kai baka daukar nasiha ka daina barin shed’an yana tasiri a tare da kai aure nufin Allah ne.

Kansa ya d’ago yana kallona na kauda kaina da sauri! hannu yasa ya juyo da fuskata yana kallona yace.”Idan na tafi amarica na tafi kenan ba zan dawo ba tunda kince na fita daga rayuwarki na fita har abadah zan barki kiyi zaman aure.

Hawaye suka kwace min nace.”Kada ka yanke wannan hukuncin Khalid America ba gurin zama bane kada ka biyewa sharrin zuciya ka jefe mu a cikin masifa.”

Murmushi mai ciwo yayi yace.”Zama na a Najeria babban Jidali ne bana tsammanin zan iya barin ki ki zauna kalau a gidan auranki idan nayi nesa sai kinfi samun kwanciyar hankali.” Sosai nake hawaye ina girgiza masa kai…..Hannu yasa yana goge min hawayen muka kurawa juna ido…..Haka kawai nake jin mugun tausayinsa na ratsa ni Khalid yana masifar sona babu shakka da maganar aurena da Aminu ba tayi nisa ba zan iya hakura na aureshi ko ya samu nutsuwa sai dai kash lokaci kadan ne ya rage a daura min aure bana tsammanin zan iya watsa mijin mahaifiyata ‘kasa a ido…………..”Salamu alaikum.” Sallamar da muka ji itace ta sanya muka dawo nutsuwar mu. Baito ce da Jamila suka shigo gidan Baito sakin baki tayi tana kallon mu tare da tallafe ha’ba, ita kuwa Jamila ido jawur ta wuce gurin Ummatu fuuuuuuu! kamar tashin Iska.

_Nagode kwarai da adduarku masoya ciwon kai da sauqi sai dai dole ku cigaba dayi min uziri har zuwa lokacin da zan warware ina fata da yardar Allah na gama muku littafin nan kafin azimi a yanzu dai ina shan magani wannan pege din ma dauriya ce ganin kun damu da yawa yasa nayi typing din Ina rokon Ubangiji Allah ya ‘kare mu da lafiya wannan zafin da muka shiga Allah kasa mu wuce lafiya NAGODE da Alfarma👏🏻_

*64&65*
Ina fita bakin titi adaidaita sahun Salim taci burki a gabana, dauke kaina nayi ina sake tamke fuskata ya leko da kansa da fadin.”Aunty Sa’ida ina zuwa haka.”? Ba tare dana kalleshi ba nace.”Hotoro na nufa.” Murmushi yayi cike da kulawa yace.”Aikuwa zaki jima baki samu babur ba domin a daidai wannan lokacin munfi dau’kar ‘yan kasuwar kwari da bakin asibiti amma tunda Allah ya had’amu kawai ki shigo na kai ki.

Jin abinda yace yasa na shiga babur din ba tare da nayi masa musu ba, jan babur din yayi da sauri muka bar gurin……Sai da mukayi nisa sosai kira ya shigo wayarsa jin ya ambaci sunan Khalid a maganarsa yasa gabana faduwa, shuru ina sauraran maganar tasu yace.”Okey to ni yanzu ina kan hanya amma idan na samu nutsuwa zan kira ka mu tattauna wata magana.” Daga can bangaran Khalid yace.”Okey to shikkenan nima ai na kusa shigowa garin domin nayi muku sallama zamu tafi amarica wasa.” Salim cike da jin dadi da farin ciki yace kai amma nayi murna da farin ciki abokina Allah ya kara daukaka yasa ka zama zakaran gwajin dafi Allah yasa ka ciyo mana kofi.

Khalid yace.”Ameeen abokina nagode sosai sai na jika.” Salim yace.”Babu damuwa zan kira ka idan na samu nutsuwa.” Sallama sukayi da juna kowane ya kashe wayarsa…..Jikina ne yayi na d’an fahimci wasu maganganun nasu. ta mirror ya kalleni da murmushi a fuskarsa yace.”Aunty Sa’ida kinji Khalid zai zo sallama ko? kullum yana sake samun nasara akan harkokinsa dan Allah ku taya shi da addua.

“Humm! kawai na iya cewa na kautar da kaina ina kallon hanya, to shima Salim din ganin babu fuska sai yaja bakinsa ya rufe ya cigaba da abinda yake gabansa.

Lokacin dana shiga dakin su biyu na samesu a zaune ga dukkanin alamu muhimmiyar magana suke tattaunawa, a nutse naje na zauna kasan kafet tare da risinar da kaina kasa nace.” Alhaji barka da safiya.” cike da nuna kulawa ya amsa da barka dai Sa’ida kin ‘karaso.”? Nace.”Eh wallahi.” Kallonsa nayi kansa a sunkuye yana kallon kasan kafet nace.”Yaya Aminu ina kwana.”? babu yabo babu fallasa ya amsa min.

Dakin yayi shuru na ‘yan mintina. Alhaji yayi gyaran murya tare da kallona, jikina yayi sanyi na sunkuyar da kaina kasa ina addua akan Allah yasa alkairi ne.

“Sa’ida naji uzirin ki a bakin Kawun ki Ibrahim inda yake fada min cewa kina so ki koma gurin aiki hakane ko.”? a sanyaye nace.” Eh hakane Alhaji dan tuntuni komai ya kammala gurin aikin nawa sun kar’bi uzirina sunce babu damuwa zan iya komawa bakin aiki.”

Yace.”To shikkenan Sa’ida amma ban tari hanzarin ki ba ina neman wata alfarma a gurin ki ina fata zan samu.”

Kallonsa nayi ina mamakin maganarsa a duniya akwai abinda mutumin nan zai nema a gurina na kasa yi masa.

Nace.”Alhaji ko wace irin alfarama kake nema a gurina zanyi maka mutukar inada iko da ita.

Yace.”To Alhamdulillahi Sa’ida nagode sosai da kika karrama ni sabida haka dan Allah inaso ki amince na had’aku aure da Yayanki Aminu domun hakika naji ciwo da takaicin abinda Alhaji Nura yayi miki da k’ananun shekarunki ya sake ki.”

Na dinga jin wani irin shocking a jikina gumi duk ya tsatstsafo min banta’ba tsammanin haka daga gurinsa ba shuru nayi bakina ya mutu murus na rasa ma abinda zance.”

Yace.”Sa’ida kinyi shuru ko baki amince ba.”? a sanyaye na dago kaina na kalleshi kafin na mayar dashi kasa nace.”Alhaji na amince mutukar shi Yaya Aminun ya amince zai aure ni da zawarcina.

Murmushi yayi yace.”Alhamdulillahi naji dadi sosai kuma kada ki damu da Aminu yanzu kafin ki shigo muka gama magana dashi ya tabbatar min da cewa ya kar’bi auranki kamar yanda na umarce shi.”

Nace.”To shikkenan Alhaji Allah yasa hakan shi yafi alkairi.” ya amsa da ameeen ya Allah ya d’ora da fad’in “maganar aiki ki bar ta tunda anayi ne domin biyan wasu bukata na yau da gobe na tabbata idan Allah ya kaddara auraki da Aminu baki da matsala tunda Alhamdulillahi Allah ya rufa masa asiri.”

Gumin saman goshina nagoge nace.”To shikkenan Alhaji duk yanda kace hakan za’ayi Allah yasa haka shi yafi alkairi.” ya amsa da ameeen ya Allah.” Umarnin tafiya ya bani na mike a sanyaye na fita daga dakin.

Zaune na sameta a bedroom dinta tana ninke kayan sawarta, zama nayi gefan gado kuka ya kwace min…..a nutse ta juyo tana kallona kuka nake sosai! tace.”Sa’ida ki rufa min asiri na fita kunyar mutumin nan dan Allah kada ki watsa min kasa a ido.”

Cikin rawar murya nace.”Umma anya al’amarin nan zai yiwu kuwa Yaya Aminu saurayi ne ya za’ayi ace za’a had’ashi dani bazawara sai nake ganin kamar tilas akayi masa baya sona.

Girgiza kanta tayi tace.”Sa’ida idan ma tilas akayi masa ai shine ya janyowa kansa me yasa tuntuni baiyi aure ba me ya rasa na rayuwa yana da kudi gida da mota to me yake jira kuma ki daina kiransa saurayi sai dai ki kirashi tuzuru domin ya tashi daga sunan saurayi ya koma matashi kuma baki wuce sa’ar auransa ba ni dai babban burina ki bani had’in kai akan wannan al’amari domin kin san Alhaji ya wuce komai a gurinmu.”

Shuru nayi ina girgiza kaina gabadaya kaina ya kulle na rasa wane irin tunani zanyi idan Allah ya kaddara aurena da yaya Aminu wace irin rayuwa za muyi ni dai ba zan iya d’orar da halinsa ba tunda ba zaune nake dashi ba abinda dai zan iya tunawa shine yana da saukin kai da iya mu’amula sai dai halayen mutum basa fitowa sai zama yayi zama ina tsoron abinda zai faru a rayuwar auranmu domin a yanzu gabadaya auran ya fice min daga rai mussaman idan na tuna irin zaman da nayi a gidan Alhaji Nura gabadaya sai naji auran ya fice min daga raina.

Salim sai da ya koma gida cin abincin rana ya samu damar kiran wayar abokin nasa….Khalid yace.”Wai wace irin magana zaka fada min ne.”?

Salim yace.”Khalid wai auran aunty Sa’ida ya mutu ne.”? Cike da mamaki yace.”Me yasa ka fad’i haka.”? Yace.”Sau tari ina ganinta a unguwa idan zata wani guri a takaice dai yau ma ni na dauketa a babur dina na kaita hotoro kuma mayafinta a kafad’a gaskiya jikina na bani babu aure a tare da ita.

Khalid ya saki sanyayyar ajiyar zuciya yana murmushi yace.”Lallai kace na dawo gida da kwarin gwiwata.” Salim yace .”Wai kai don Allah har yanzu baka hakura da ita ba.”?

Yace.”Salim idan kaga na hakura da aunty Sa’ida to kace bukatata ta biya na aureta amma na rantse maka muddun ina numfashi sai na hanata sunkuni.

Salim yace.”Khalid ka ji tsoron Allah ka nemi za’bin Allah kada kace zaka tsananta akan dukkanin hukuncin da Allah ya zartar.”

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Salim Allah ne ya d’ora min kaunarta kuma kullum idan zan dungura goshina a ‘kasa sai na rokeshi da ya za’ba min abinda yafi alkairi tunda naga har yanzu zuciyata ta kasa hakuri da ita na tabbata a gaba ina tare da nasara zan cigaba da bibibyar rayuwarta har sai sanda Allah ya cika min burina .”

Salim ya dinga girgiza kansa yana mamakin al’amarin a sanyaye yace.”To ai shikkenan tunda kace haka Allah ya za’ba mata dukkanin abinda yafi alkairi.” ya amsa da ameeeen ya Allah.

Suna yin sallama da Salim din ya shiga kiran wayarta lokacin tana tare da mahaifiyarta tana sake kwantar mata da hankali….koda taga kiran nasa daukar wayar tayi ta kashe tana jan tsaki.

Cikin jin ciwon abinda tayi masa ya nemi number Wayar gwaggo ya shiga gurin kira, ta dauki wayar tana dubawa ta gane sunansa da yayi mata serving da *Jarumi* yau dai tayi ra’ayin d’aga wayar domin dama can daurewa take tayi kewarsa.

Tana dagawa ya sauke ajiyar zuciya da fadin.”Har naji sanyi a cikin raina.” Tace.”Khalid ka kyauta akan abinda kayi.” Da sauri yace.”Gwaggo me nayi kuma babu gaisuwa sai ki fara ‘korafi.”? a fusace! tace.”Ka kashewa Sa’ida aure sai ka zuba ruwa a kasa kasha.”

Murmushi yayi had’e da shafa sajensa yace.” Gwaggo ni kada ku d’aura min laifi ta yaya zan kashe mata aure bayan bana gari dama can auran matacce ne.”

Tace.”Kafin ka tafi ai ka shirya kitumurmurar da ta janyo mutuwar auran ashe bakaji maganar da nayi maka ba sai da ka wanke kafa kaje gidan kuma saboda tsabar rashin mutumci ka shiga har dakin baccinsu.”

Yar dariya yayi yace.”Gwaggo cewa tayi nayi mata wani abu dana shiga k’uryar dakinta.”? Tace.”Oh!o ai ko bakayi mata wani abuba tunda mijinta ya shigo ya ganka dole ya zargi wani abu a tsakaninku tunda dama can akwai soyayya.

Ajiyar zuciya ya sauke da fadin.”To ai shikkenan magana ta kare Allah yasa haka shi yafi alkairi.”

Tace.”Dama ai haka zakace tunda haka kake so to kama daina rawar jiki domin babanka yayi rantsuwa akan ba zaka aureta ba.

‘Dif! yayi yana jin wani d’aci a makogwaronsa yace.”Gwaggo akan me? zaiyi rantsuwa? akan me zai hana abinda Allah ya halasta.” Tace.”Ai bani zaka tuhuma ba wayarsa zaka kira ka kai masa k’abali da ba’adi.” Tana kare maganar ta kashe wayar tana fad’in “Ja’iri kawai mara zuciya tamkar yarinyar nan ce mace a duniya ya nace dole sai ya aureta

Khalid ka sa’ke yayi da waya a hannunsa gumi sai tsatstsafo masa yake babu shakka dole yaje gida a kurkusa domun yana jin tsoron ayi masa sakiyar da babu ruwa.

Yamma likis na koma gida Gwaggo ta dinga bina da kallo tana so tayi min magana amma tayi shuru da bakinta sai bayan muyi sallar magariba ne na kalleta da fadin.”Gwaggo kin san abinda yake faruwa kuwa.”?

Girgiza kanta tayi tace.”Ina zan sani bayan naga kamar kina ‘boye min ai shiyasa nayi shuru da bakina na zuba miki ido.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Dama so nake ki samu nutsuwa tukkuna na sheda miki abinda yake faruwa.

Tace.”To ina sauraranki Allah yasa alkairi ne.” a nutse nace.”Alhaji ne ya nemi alfarma akan na auri babban d’ansa Aminu.”

Zuba min ido tayi tana kallona kafin tace.”Sai kika ce masa me.”? a sanyaye nace.”Gwaggo na amince domin ba zan iya jayayya dashi ba mutumin bai cancanci haka daga gurina ba.

Tace.”Ai dole ki fadi haka mana dama ai abinda yake nufi kenan shiyasa yace kije yana neman ki ashe maganar kenan zai kama ya aura miki yaronsa da yake fama da matsala.”

Nace.”Gwaggo wace irin matsala kuma don Allah kiyi wa al’amarin kyakykyawar fahinta.”

Tace.”Sa’ida ni kam bana miki sha’awar auran wannan mutumin sam baku dace ba.” Nace.”Gwaggo saboda me kike ganin bamu dace ba.”

“Haka kawai banyi na’am da al’amarin ba amma tunda har kin amince masa to bani da tacewa sai dai kawai nayi miki fatan alkairi.”

Shuru nayi kaina a kasa ina nazarin maganarta to ko dai Gwaggo ta hango wani nak’asu ne a tarrare da Yaya Aminun yasa take fad’ar wannan magana! Ni dai a zahiri ban ga makusa a tare dashi ba cikakken namiji ne wanda ya tara dukkanin abinda ake bukata sai dai hausawa suna cewa abinda babbah ya hango yaro ko ya hau tudu ba zai hangoshi ba.

Kwana nayi da tunani da zullumin al’amarin da safe da Kawu ya shigo nake fada masa yanda mukayi da Alhajin….Yace.”Sa’ida ina da masaniyar komai domin kafin kije ku tattauna sai da ya kira ni har gida naje na sameshi ya sanar dani komai tabbas naji dadin al’amarin kuma na taya ki murna samun nagartaccen namiji kamar Aminu ina rokon Allah ya tabbatar muku da alkairi. ” A raunane na amsa da “Ameeen ya Allah Kawu.” Ya kalli Gwaggo da fadin.” Baki ce komai ba Gwaggo.” Tana cigaba da abinda yake gabanta tace.”To me zance Ibrahim ai tunda kun riga kun gama yanke hukunci bani da tacewa.

Yace.”Gwaggo kiyi hakuri kiyi wa al’amarin kyakykyawar addua.” Tace.”Ai tun jiya da ta fada min maganar nayi addua Babu komai ka tafi kasuwarka Allah ya bada sa’a.”

Yanda ta fadi maganar zaka gane akwai wani abu a cikin ranta da yake damunta. A sanyaye yace.”To shikkenan Gwaggo sai na dawo.” Tace.”Allah ya tsare ya bada sa’a.” Ya amsa da ameeen yana kokarin fita.

Dago kanta tayi ta kalleni da fadin.”Yanzu Sa’ida abinda kukayi shine daidai anya ba zaku rage son kai ba.”?

Nace.”Gwaggo me kuma mukayi.”? Tace.”Fisabilillahi Sa’ida yaron nan Khalid yana kulafucin ki amma ke sam bakya ta tasa wai shin dan Allah wace irin kiyayya kike masa haka me yasa ba zaki aureshi ba.

Cike da wani irin yanayi nace.”Gwaggo wai don Allah me yasa kike dawo da hannun agogo baya na dauka tuntuni maganar Khalid ta wuce tunda zaiyi aurensa to me yasa zaki dinga tayar da abinda ya wuce.

Gefan zaninta tasa ta goge hawayen fuskarta tace.”Wallahi tausayinsa nake ji Sa’ida ya kwallafa ransa a kanki sai wahalar dashi kuke hakika da ana sanja zuciya da sai na sanja masa zuciyarsa ya daina wahalar da kansa a kanki Jiya nan sai da ya bugo min waya yana cikin damuwa banda maganarki babu abinda yake mai zai sanya ba zakiyi mana kara ba? me zai sanya ba zaki tausayawa dan uwanki ba? Sa’ida duk fa namijin da Ibrahim yake so ki aura ba kamar d’an cikinsa ba zaifi so ki auri Khalid amma sabida baya so yayi miki dole yake rarrashinki da bin abinda kike so ke kuwa mai zai sanya ba zaki kyautata masa ba.

Cikin kuka nace.”Wai shin Gwaggo ya kike so nayi ne? wallahi da mace tana auran maxa biyu a lokaci guda to da na auri Khalid da Yaya Aminu amma yanzu lokaci ya kure dole Khalid ya sake hakuri a karo na biyu tunda na ruga na amince da maganar auran Yaya Aminu duk sai mu barwa Allah abinda ya hukunta.”

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*66&67*
Gefan zaninta tasa ta share hawaye da fadin.”Ai shikkenan Sa’ida tunda haka zaki ce dole nayi hakuri da hukuncin da kika yankewa kanki amma ni sam bana sha’awar ki da wannan mai ba’kar fuskar.” Kallonta nayi ina mamakin maganarta Gwaggo idan bata son abu komai kyawun sa ta dinga kushe shi kenan amma in banda haka meye laifin Yaya Aminu kyakykyawa ne sosai Khalid din babu abinda zai nuna masa sai haske fata.

Nace.”Gwaggo maganar nan ta wuce don Allah ki daina kuka da damuwa ki cigaba da addua ni da Khalid din Allah ya za’ba mana abunda yafi alkairi Gwaggo duk sonki da na auri Khalid idan Allah bai nufa ba dole ki hakuri kin san komai nufi ne na ubangiji mussaman sha’ani na aure ba’a katsalandan a ciki kawai ki roki Allah alkairi sai kiga ya tabbatar miki.

Tace.”To me kika ji na k’ara cewa? ai magana kuma ta wuce wannan yaro Khalid kuma Allah ya sanya masa dangana.”
Ameeen na amsa ina kokarin mi’kewa tsaye

*Bayan sati biyu*
A tsakanin kwanakin Yaya Aminu yazo guri na mun gaisa sosai kuma yanda yake nuna kulawarsa a kaina yasa na gane cewa lallai ba dole akayi masa ba domin ‘karara yake nuna min so da kauna ga uwar hidimar da yake min sai kace hauka ya kawo min sabuwar waya mai kyau da tsada kudi kuwa duk bayan kwana uku ko hudu zan ga alert dubu ashirin dubu talatin har dubu hamsin turo min yake idan nayi masa magana sai yace shine yayi niyya idan inada bukatar ya ‘kara min wasu sai nayi magana, al’amarin ya dinga bani mamaki mutuka gidan Hauwwa naje domin mu tattauna maganar dan gaskiya ni kudin da yake bani suna bani tsoro ni ba auran kudi nake so nayi dashi ba nafi bukatar idan na aureshi ya rike ni tsakani da Allah mu zauna lafiya…..Koda Hauwwa ta gama jin bayani na sai tayi dariya tana fadin.”Sa’ida kenan ke yanzu saboda rashin wayo da dubara har magana kike masa ya daina baki kudi? to idan ya daina baki wa kike dashi wanda zai baki? komai fa da kika gani yana da lokacinsa saboda haka ki kwantar da hankali Idan kullum zai dinga sa miki million a accont dinki kada kice masa don me kiyi godiya kawai idan baki kar’ba ba wasu can a waje su za su kar’be Yana da kudi to me zaiyi dasu tunda dai shi bashi da nauyin kowa a kansa ke d’in dama ke zai bawa sai mahaifiyarsa da sauran ‘yan uwansa saboda haka ki nutsu ki samu abinda kika samu kafin lokaci ya kure miki.”

Shuru nayi ina ta nazarin maganarta tace.”Ni wallahi nayi miki murnar auransa domin ta ko’ina yayi bashi da makusa saboda haka kawai ki kwantar da hankalin ki ayi al’amarin nan cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Shikkenan Hauwwa Allah yasa hakan shi yafi alkairi.” ta amsa da ameeen tana kokarin mikewa tace.”Bari na kawo mana abinci.” ido kawai na bita dashi ina mamakin son kud’inta Na lura bata da tsinkaye da tunani mutukar akan kudi ne.

Can gidan Alhaji Shamsun kuwa kowa yana cikin farin ciki manya da yaransu amma banda mahaifiyarsa Hajia Mariya tun sanda maigidan ya sheda mata hukuncin da ya yanke take cikin k’unci sam bata so d’anta ya fara da bazawara a ganinta kamar hakan koma baya ne domin kuwa babu abinda d’anta ya rasa na jin dadin rayuwa to ta yaya za’a ce lallai sai ya auri bazawara sai kawai ta yanke shawarar tun karar maigidan da maganar Alhaji Shamsu tunda yaga take taken ta ya bude mata wuta sosai ya nuna mata kuskuranta yace kuma mutukar yana numfashi to sai anyi auran don haka kawai tayi addua domin shine abinda ya cancanta.” Sanin halin mijin nata yasa bata sake tankawa ba duk irin hidimar da akeyi a gidan idone nata su kuma kishiyoyin nata sai suke ganin kamar kawaici da kunya take irin na d’an fari Tsakaninta da Umma Habiba babu wata matsala dan ko a fuska bata nuna mata cewa bata son auran ba, ta bar komai a cikin zuciyarta tana dai kallonsu sai farin ciki da murna sukeyi……..Manya akwati mai sheda cike da manya kaya masu tsada aka kai wa Sa’ida a matsayin kayan lefe Gwaggo da Ummatu da sauran jamaa suka dinga mamaki ko auranta da Alhaji Nura bata samu wannan alkairi ba Gwaggo dai gajiya tayi da duba kayan sabida tsabar yawan su ta bar gurin sai surutai takeyi Ummatu kam sai da ta lissafa iya adadin kayan lefan Atamfa Talatin les Talatin shadda talatin komai dai gashinan kamar hauka don tsakar gidan cika yayi da kayan makota nata shigowa suna gani sai can dare kafa ta dauke a gidan……Koda Kawu Iro ya dawo Gaggo turkeshi tayi da fadin.”Ibrahim wai shin meye sana’ar wannan yaron ne.”? Yace.”Gwaggo wa kike nufi.”? Tace.”Aminu mana.”? Murmushi yayi yace.” Siyar da tufafi ko wane iri shine sana’arsa a ‘kalla yana da rumfuna sama da biyar a kantin kwari kuma akwai wani babban company da suka bude a chana suke sarrafa audiga ai bai fiye zama a gari ba.

Tace.”Koda naji duba kaga irin uban lefen don Allah mutane sai gulma suke shigowa mu ba kudi muke so ba albarkar aure muke bukata.

Murmushi yayi yace.”Gwaggo kenan ai mutane dama ba zaki rabasu da wannan gulmace gulmacen ba to duk dai wanda ya shigo da sunan ganin kayan lefe sai ku nuna masa shine abinda ya dace.”

Tace.”To Allah ya kyauta dai ya rufa asiri.” ya amsa da ameeen ya rabbi tace.”Yanzu sati nawa suka d’iba domin daurin aure.”? Yace.” Kwana bakwai ne rana ita yau kenan.” Tace.”To Allah ya nuna mana. ” ya amsa da ameeen yana kokarin barin gurin tace.” D’azu da safe kuwa Khalid yace yana kan hanya zaizo gobe ko jibi wai zasu tafi america suyi wasa.”

Yace.”Gwaggo Nifa bana son yaron nan da wannan harkar kafurci ne tsagwaronsa.” Tace.”Ibrahim nima bana so to ya zamuyi idan ya kasance anan abincinsa yake.

Yace.”Dole idan yazo na zauna dashi domin bana tsammanin zan barshi ya koma Lego’s din nan bare ya tafi wata uwa duniya america Buga ball da turawa ya haramta.” Tace.”Ai ko bada da turawa ba ma buga ball a ko’ina ne bai halasta ba kamar an tozarta ahalin gidan Annabi ne.” Yace.”Gwaggo ai ba kama bane Gaskiya ne duk wanda ya buga ball kamar yana buga kawunan Shirafa’u Jikokin Annabi Muhammad (SAW) wannan dalilin yasa idan ya dawo zan zauna dashi akan al’amarin.

Tace.”To shikkenan Allah Ubangiji Ya za’ba abinda yafi alkairi.” Ya amsa da ameeen tare da barin gurin

To koda Hauwwa tazo ganin kayan lefen itama sai da tayi mamaki mussaman data ga set din gold har biyu da ‘kirar saudi dana dubai ta dinga mamakin al’amarin tana girgiza kanta ta kalleni da fadin.”Ke dai Sa’ida ‘kashin ki na manyan mutane ne duba dan Allah lefe sai kace na ‘yar gatan budurwa.”

Murmushi nayi kawai nace.”Hauwwa kenan Ni wallahi yanzu duk ba wannan ne a gabana ba burina kawai naga na zauna kalau a dakin aurena dan bana so da kuruciya ta kawai a dinga lissafin min aure ina addua akan Allah yasa anyi kenan.

Tace.”Ki daina wani wasiwasi da zancan zucci insha Allahu baki da matsala da Aminu tinda yana sonki zai kula dake kamar yanda kike bukata.” Wannan kalaman nata suka sanya ni naji sanyi a cikin zuciyata sai kawai muka shiga tattauna yanda al’amuran biki zai kasance.

Ya kama saura kwana uku daurin aure Khalid ya dira a garin ni lokacin ma bana gidan ina gidan Hauwwa tare da masu gyaran jiki.

Kawai naji kira ya shigo waya ta dana duba sai naga number Gwaggo ce amma kuma ina daga wayar naji muryar Ummatu tana fad’in “Sa’ida sai ki zuba ruwa a kasa kisha ga Khalid a kwance yana aman jini.

Gabana ya dinga buguwa nace.”Ummatu ban gane maganarki ba. Tana kuka tace.”Ai dama ba zaki gane ba tunda bukatar ki ta biya ni dai idan ki kayi sanadiyar mutuwar yaro na Allah ya isa.” Kafin nace wani abu ta kashe wayar.

Jiki a mace na kalli Hauwwa dake kallona nace.”Wai Khalid ne ya dawo yake aman jini.” da sauri tace.”Aman jini kuma.”? Murya na rawa nace.”Eh.” Tace.”Sa’ida me ya janyo masa to.”? cike da mamaki nake kallonta Nace.”Haba Hauwwa ya kike tambayata kamar baki san komai ba.”?

Tace.”Ashe dai har yau be hakura ba.”? nace”Gashinan kuwa mybe daya samu labarin daurin aurena al’amarin ya afku.”

Tace.”Kai gaskiya wannan yaron yana nacin sonki haba ai ya dace ace ya hakura kuma tinda dai yanzu kinyi masa nisa gabad’aya ma ke jininki bana ‘kananun yara bane sai ya hakura kawai.”

A sanyaye nace.” Zai hakura ai yaron mugun naci ne dashi bayan abinda yake bukata ya samu a gurina to menene na kulafuci.” Kallona tayi tana neman ‘karin baya ni a maganata, na share maganar ina kokarin mikewa tsaye…..Yarinyar dake sa min salatif a kafata tace.” Aunty ya zaki tashi kuma ki zauna a cigaba da saka salatif din kada yasha iska.”

Ina kokarin sa hijabi na nace.”Mansura bana tsammanin zan zauna zaman ‘kunshi a yanzu zanje na duba halin da d’an uwana yake ciki.”

A sanyaye tace.”To aunty Allah ya bashi lafiya.”Hauwwa ta kalleni da fad’in.” Amma zaki dawo ko.”? Nace.”Watakila zan dawo idan hali yayi.” Tace.”To shikkenan Allah ya sauwake.”

Babu cikakkiyar nutsuwa a tare dani na amsa da ameeen nagode jakata na dauka da sauri na kama hanyar fita.

Yanda naga sun masa rumfa yasa gabana ya tsananta faduwa murya na rawa na kira sunansa yana kwance a kan katifa idonsa a rintse…….Jin muryar ta yasa da sauri ya bude idonsa, saurin sunkuyar da kaina nayi haka kawai naji ina jin nauyi da kunyarsa…. motsa bakinsa yake yana so yayi magana sai ya fasa ya mayar da idonsa ya rufe kawai sai ganin hawaye mukayi yana sauka a kuncinsa…

zuciyata ta karya ina rawar Murya na kalli Gwaggo da tayi firgai-furgai hawaye duk ya bushe a fuskarta nace.”Gwaggo mu tafi asibiti dashi a duba shi sosai ina aman jinin da yayi.”? ina maganar ina bin tsakar gidan da kallo.

Tace.”Sai kawai mu zauna zaman jiran ki ai tuntuni mukaje asibiti suka duba shi suka kuma bashi magani aman jini kuma an wanke domun ke baki isa ayi miki ‘karya ba.

Nace.”Gwaggo me ya kawo wannan maganar ai nima ba ‘karyatawa nayi ba.” Dauke kanta tayi ta cigaba dayi masa firfita da maficin hannunta, tsakin Ummatu naji akaina kafin na juyo ta bar gurin tana surutai.

Girgiza kaina nayi nasa hannu na goge hawayen da suka zubo min…..Tace.”Sa’ida ai kuka yanzu kika fara tunda baki da tausayi sai Allah ya sakawa wanda kika zalinta.

Shuru nai mata na mayar da hankalina kansa har yanzu idonsa a rufe yake murya na rawa na kira sunansa.

Shuru yayi bai amsa min ba, na sake kiran sunansa tare da kama hannunsa……da mugun sauri ya fizge hannunsa ya bude idonsa yana kallona cikin Sha’kakkiyar murya yace.”Bana bukatar ganin ki Aunty Sa’ida I hit you i hit it !! na tsane ki! bana sonki! sai kinga sakamakon abinda kikayi min kije ki auri duk wanda zaki aura ni kuma zan mutu da sonki a cikin raina.” Yana maganar yana tari da riqe kirji! Gwaggo duk ta gigice tana rirrikeshi cikin dauriya na hau katifar sosai ina kokarin rikeshi kamar walkiya ya juyo a zafafe ya hankad’e ni na fad’i a kasan gurin! da hannu yake nuna ni yana so yayi magana amma kuttun bakin ciki ya hanashi kawai sai jini muka gani ya ambulo daga bakinsa.

Ihu! na kurma! a kid’eme na sake hawa katifar na kamo shi gefan hijabi na nasa ina goge masa ina kuka wurjajan na kalleshi da fadin.”Khalid ashe da gaske ne? me yayi zafi Khalid kada ka kashe kanka don Allah kayi ta wakkali ka cigaba da neman za’bin Allah.”

Zafafan hawaye ne suke sauka a kumatunsa hannu na na rawa na dinga goge masa ina kuka da fadin.”Kayi hakuri dan Allah ka barwa Allah lamarin nan Khalid ka daina aman jini kada kasa mu cikin masifa.

Gwaggo da tausayin su ya isheta sai ta mike jiki a sa’bule ta shiga dakinta tana share hawaye da adduar d’auki daga Allah.

Rarrashin sa na cigaba dayi ina shafa kanshi da bayansa gabad’aya ya lafke a jikina sai ajiyar zuciya yake saukewa nauyin sa be dame ni ba ni dai buri na yayi min magana yaja bakinsa yayi shuru idonsa a rufe sai sake sakin jikinsa yake a jikina.

A hankali na kira sunansa. Ya bude idon yana kallona nace.”Kayi hakuri ko.”? tsira min rikitattun idanun nasa yayi nayi tsai ina karanta abinda yake cikinsu…….Babu wata alama data nuna ya dauki nasiha ta…..Hannuna na turmutsa cikin tarin suman kanshi a sanyaye nace.”Khalid komai na rayuwa yana tafiya ne da ikon Allah duk yanda mutum yake son abu idan Allah baya sonsa da abun dole ya hakura shiyasa kaji ina cewa kayi hakuri ka nemi za’bin Allah Ni bana ‘kin ka Khalid idan Allah ya kaddara aurena dakai duk rashin sona dole na hakura don Allah ka kwantar da hankalinka.

‘Kuguna ya zagaye da hannuwansa, kallonsa nayi gabana na faduwa……….”Zaki auri wani ya ‘karasa kwashe min Ni’ima ko.”? yafada cikin sar’kewar murya. gabana na wani irin bugawa nake kallonsa….lumshe idonsa yayi ya sake yin release a jikina…….Bana bukatar wani banza ya ra’bi jikin ki aunty Sa’ida ke kuma gashi kina ta basu goyon baya akan hakan yanzu me kika hango a tare da wannan mutumin da zaki aura ko kudinsa kike so.”?

Ajiyar zuciya na sauke ina kokarin cire shi daga jikina nace.”Khalid me yasa kullum kai baka daukar nasiha ka daina barin shed’an yana tasiri a tare da kai aure nufin Allah ne.

Kansa ya d’ago yana kallona na kauda kaina da sauri! hannu yasa ya juyo da fuskata yana kallona yace.”Idan na tafi amarica na tafi kenan ba zan dawo ba tunda kince na fita daga rayuwarki na fita har abadah zan barki kiyi zaman aure.

Hawaye suka kwace min nace.”Kada ka yanke wannan hukuncin Khalid America ba gurin zama bane kada ka biyewa sharrin zuciya ka jefe mu a cikin masifa.”

Murmushi mai ciwo yayi yace.”Zama na a Najeria babban Jidali ne bana tsammanin zan iya barin ki ki zauna kalau a gidan auranki idan nayi nesa sai kinfi samun kwanciyar hankali.” Sosai nake hawaye ina girgiza masa kai…..Hannu yasa yana goge min hawayen muka kurawa juna ido…..Haka kawai nake jin mugun tausayinsa na ratsa ni Khalid yana masifar sona babu shakka da maganar aurena da Aminu ba tayi nisa ba zan iya hakura na aureshi ko ya samu nutsuwa sai dai kash lokaci kadan ne ya rage a daura min aure bana tsammanin zan iya watsa mijin mahaifiyata ‘kasa a ido…………..”Salamu alaikum.” Sallamar da muka ji itace ta sanya muka dawo nutsuwar mu. Baito ce da Jamila suka shigo gidan Baito sakin baki tayi tana kallon mu tare da tallafe ha’ba, ita kuwa Jamila ido jawur ta wuce gurin Ummatu fuuuuuuu! kamar tashin Iska.

_Nagode kwarai da adduarku masoya ciwon kai da sauqi sai dai dole ku cigaba dayi min uziri har zuwa lokacin da zan warware ina fata da yardar Allah na gama muku littafin nan kafin azimi a yanzu dai ina shan magani wannan pege din ma dauriya ce ganin kun damu da yawa yasa nayi typing din Ina rokon Ubangiji Allah ya ‘kare mu da lafiya wannan zafin da muka shiga Allah kasa mu wuce lafiya NAGODE da Alfarma👏🏻_

[3/25, 9:47 PM] +234 906 667 3667: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*68&69*
‘Kokarin cire kansa nake daga kan kirjina yana sake lafewa a cikin jikina har da sa hannu da zagaye ‘kuguna. Baito ta shiga tafa hannuwa tana fad’in ”Iko sai Allah Khalid wane irin iskanci ne wannan ashe dama rashin lafiyar naka na karya ne akaje har gida aka d’aga mana hankali.”?

Ina kokarin magana Gwaggo ta fito daga dakinta ganin Baito a tsaye a kanmu tana surutai yasa tace.”Aa Baito kada daga shigowarki kiyi wa yara kazafi shin me kika shigo kika tarar sunayi da har kike farfad’ar maganar da bata dace ba.” Kallonta tayi cikin kumfar baki tace.”Na shigo na tarar dasu rungume da juna kice kada nayi musu kazafi ki duba fa ki gani har yanzu yana kwance a cinyarta shin me hakan yake nufi.”?

Gwaggo ta juyo tana kallon gurin da muke….babu kuzari a tare dani na dauke kansa daga cinyata na mike na shiga daki raina a masifar bace da abinda Baito tazo tana yi.

Gwaggo tace.”Saboda kawai tana rarrashinsa a matsayinsa na d’an uwanta sai ki fassara al’amarin da wata manufa Baito kada kice zaki watsa min zuria domin ni kaf ahali na babu mai mugun hali.”

Baito na kokarin magana ya daga mata hannu a kasalance yace.”Baito dan Allah a bar wannan maganar ta isa haka babu wani mugun abu da mukeyi da Auntyna kada kiyi mana mummunan fassara.”

‘Kwafa tayi da fadin.”Ai shikkenan Khalid tunda ka mayar dani shashasha naga abu da idona amma ka ‘karyata ni.” Shuru yayi mata ransa duk a dagule ya tsani rashin fahimta irin na kakar tasa. Baito kofar Ummatu ta nufa tana surutai Gwaggo taja tsaki da fadin”Duk wani sharrinku sai dai ya koma kanku.” Baito tana ji bata tanka mata ba saboda ta riga tasan duk masifarta Gwaggo ta dame ta ta shanye.

Kallonsa tayi da fadin.”Khalid ya jikin naka.”? Kansa na kallon kasan katifa yace.”Da sauki Gwaggo wanka nake so nayi ko naji dadin jikina.”

Tace.”To bari na d’ora maka ruwan zafi kayi wankan sai kasha magani ko.”? Yace.”To shikkenan Gwaggo nagode.” Da sauri ta nufi kicin domin ta hura wuta.

Gefan gadon Gwaggo na zauna kawai na tsirawa guri guda ido gabadaya na rikice na rasa wane irin tunani zanyi hakikanin gaskiya lamarin Khalid yayi masifar tsaya min a raina kuma banta’ba tsammanin cewa son da yake min yayi girman haka a cikin zuciyarsa ba aman jini gaskiya na tsorota sosai cikin zuciyata naji ina tausaya masa domin Allah ya jarrabeshi da son abu gashi kuma ga dukkan alamu ba alkairi ne a tare dashi ba da zaiyi hakuri yayi tawakkali ya mayar da al’amuransa gurin Allah sai yayi masa kyakykyawan tukwici amma gabadaya ya kasa hakuri da kaddara gashi yana nema ya janyowa kansa mummunan ciwo.

Hawaye na goge ina girgiza kaina lokaci ya kure maganar aurena da Yaya Aminu tayi nisa saura kankanin lokaci babu yanda za’ayi nazo da wata magana dole mu hakura mu barwa Allah ikonsa amma dole a cikin ‘yan kwanakin da suka rage min na saki jikina da yaron na rarrashe shi ya kwantar da hankalinsa ina ganin idan nayi masa hakan zai dan samu sassauci.

“Kinga Jamila ki daina kuka da damuwa na fada miki mutukar ni na haifi Khalid to ba zai auri wannan tsohuwar guzumar ba duk wani abu da sukeyi daurin gindi suka samu a gurin waccar tsohuwar kuma na lokaci kad’an ne tunda ai saura kwana uku a daura mata aure kinga kuwa Khalid ko yaki ko ya so dole ya hakura da ita.

Jamila ta share hawayen fuskata murya na Rawa tace.” Allah Ummatu ba kiji yanda zuciyata take zafi ba na rasa abinda yake min dadi Yaya Khalid duk kuruciyarsa da wayewarsa ya rasa wacce zai mak’alewa sai sauran maza A makaranta fa kullum cikin bin ofis din malamai take suna aikata masha’a.” Baito tayi karaf tace.”Eh ai gashinan shima tana lalata shi yaro bashi da lafiya ta rungumeshi a kirjinta nayi magana kakar tasu ta daure musu gindi sabida rashin mutunci to wallahi Rabi tun wuri ki tashi tsaye akan d’anki dan mutukar kika zauna kina zuba ido akan duk abinda yake faruwa to zaki d’ora hannu aka sabida tsabar bakin cikin da takaici.”

Ummatu tace.”Baito kiyi shuru kawai da bakin ki ai da Khalid din da ita mai daure masa gindi duk zanyi maganinsu akwai lokacin da zai zo na nuna mata cewa ni nake da hakki akan d’ana sabida nice uwarsa ni na haifeshi nayi wahala dashi babu wacce ta isa tayi min iko akan ikona wallahi akan hakan sai dai duk abinda zai faru ya faru.” Baito tace.”Kamata yayi ma ki cigaba da neman taimako gurin malamai dan dole sai ana sa miki hannu a cikin Al’amuranki idan kina so kiga daidai.” Ummatu ta shiga bin dakinta da kallo tana neman abunda zata d’aga ta siyar…….”Baito yawon malam sai kana da kudi kina dai kallo yanzu bani da katifa a dandayar kasa nake kwanciya sai dai idan samiru na zan siyar.”
Baito tace.”To meye a ciki don kin siyar da Katifa da Samiru ai dama kafin bukata ta biya dole sai ansha wuya sabida haka wannan karon kawai idan munje gidan malam zamu sa ayi musu farraqu ma’ana a rabashi da kakar tasa haihatahaihatan!.” Jamila tace.”Eh Baito abinda zakuyi kenan sannan don Allah nima idan kunje kusa malam yasa masa soyayyata a cikin zuciyarsa.
Baito tace.”Kada ki damu Jamila zan nema miki taimako kuma ki kwantar da hankalinki Khalid kamar ya aure ki ya gama.”
Jamila mirmushin jin dadi tayi da fadin.”Nagode sosai Baito…….Motsin shigowar Gwaggo gurin yasa sukayi shuru da bakinsu Gwaggo tace.”Rabi kina ina ne? ki bude min dakin Khalid zan daukar masa kayan sawa yayi wanka.” Ummatu da sauri ta fito daga dakin tana fadin.”Gwaggo shi ba zai shigo yasa kayan da kansa ba sai kinzo kin daukar masa ni bani da mukkulin dakinsa.

Gwaggo tace.” To da yaya aka samu ma yayi wankan kin san jikinsa babu kwari shiyasa na karbi mukkulin dakin nasa gashi a hannuna kizo ki bude min dakin.

Ummutu ba don ranta yaso ba ta kar’bi Mukkulin ta bude mata dakin, a maimakon tayi tafiyarta sai taja tunga ta tsaya tana kallon Gwaggo na bude wardrobe d’in kayansa tana fad’in ‘Yar karamar riga yace a dauko masa kin san garin akwai zafi.”

Ummatu shuru tayi sai hararar ta take, Gwaggo ta dauko masa shirt da 3qutar tana fadin.”Naga yafi amfani da irin wannan a lokacin zafi.” Nan ma Ummatu uffan ba tace ba.

Gwaggo ta bita da kallo tana nazarinta lokaci guda ta fusata tace.” Rabi da kika ja tunga kika tsaya kina kallona ko gadi na kike yi dan kada nayi masa sata.”

Ummatu da sauri tace.”Aa Gwaggo ni ba haka nake nufi ba.

Gwaggo tace.”Haka ne mana Rabi menene na tsayawa a kaina kina kallona gashi ina miki magana kinyi banza dani.”

Ummatu ganin Gwaggo na nema ta mayar da al’amarin babba yasa da sauri ta bar gurin ba tare da ta sake magana ba, Gwaggo taja tsaki da fadin.”Ke dai naga sanda zakiyi hankali.” fitowa tayi daga dakin ta kulle ta fita daga gurin.

Yana zaune jinge ne da bango (garu) daga shi sai gajeran wando tunda ya fito daga wanka ya zauna a haka ko mai bai shafa ba kawai ya tsira min rikitattun idanunsa, ni kam jikina ne yayi sanyi da kyar na iya masa magana akan yasa kayan da ya cire kafin Gwaggon ta kawo masa wanda yake so.

Girgiza min kansa yayi alamun ba zai sanya ba ya cigaba da hautsina ni da salon kallonsa.

Jiki a mace na mike domin fita daga dakin ina ganin zama na a dakin zai iya haifar da d’an da bashi da ido domin kuwa wani irin masifaffen feelings ne ke taso min……Hannuna ya rike na juyo ina kallonsa tare da kokarin kawar da abinda ke taso min…..A marairaice yace.”Ina zakije kuma? bayan kin san kallonki kad’ai yana sanyawa naji sanyi a cikin zuciyata.

Ba tare da nayi nazarin maganar ba nace.”Khalid ni kuma zaman ka ne a haka bana so sabida ina jin wani iri a tare dani.” ido ya tsira min da munafikin murmushi a fuskarsa yace.”Kina son suffata kenan dama ai na san ni kadai ne namijin da zai iya dake.

Da sauri nace.”Aa ba haka nake nufi ba Khalid ina nufin zaman ka babu riga zai janyo mana matsala kada Gwaggo tayi ba’ki zasu zargi wani abu.

Murmushi kawai yay ya janyo ni na zauna a cinyarsa cike da mamaki nake kallonsa gabana na wani irin bugawa, hannuwansa yasa ya zagaye ‘kuguna ya dora fuskarsa a kirjina a kasalance yace.” Ina mutukar shiga cikin shauki idan na dora fuskata a kirjinki.”

Cikin tashin tsigar jiki na dauke fuskarsa daga kirjina na fara kokarin mikewa daga jikinsa ya wani ru’kun’kume ni yana sakin wani irin nishi!! ture fuskarsa nayi raina a d’an ‘bace nace.”Khalid kada kaga na sakar maka fuska ka dinga kokarin shige gona da iri sake ni don Allah.”

Shuru yayi be tanka min ba ya cigaba da cusa fuskarsa a kirjina! jikina ne ya soma rawa nasa karfi ina tureshi kamar mayen ‘karfe yana mannewa a jikina……’Kwalla ta cika idona ni kam na rasa wace irin masifa ce wannan? hakura nayi na kyaleshi sai goga fuskarsa yake a sassan wuya na yana sake rungumeni a jikinsa…….Koda Gwaggo ta shigo taga abinda yake faruwa salati tasa da fadin.” Wane irin rashin mutunci ne wannan Sa’ida saura kwana uku daurin auranki kuke wannan shashanci.”

Hawaye suka kwace min dama nasan ba zata ga laifinsa ba dole ni zata d’orawa laifi nace.”Gwaggo wallahi ba laifina bane nasa ne kina ganin yanda ya matse ni a jikinsa ko.”

Gwaggo tsawa! ta buga masa murya na rawa tace.”Kai Khalid idan kai romio ne gurin soyayya dole ka hakura da yarinyar nan wannan wace irin masifa ce? wato kuna so ku janyo min abin kunya ko? kuna jin yanda Baito take yar min da habaici tana kokarin d’aid’aita min zuria.”

Hawaye na goge nace.”Gwaggo wane abun kunya kuma? ai abin kunya tuntuni an riga anyi sa.” Tace.”Sa’ida wannan lamari da ya faru idan ban dani dake da khalid din waye ya sani? sai Rabi ita kuma mijinta ya gargad’e akan maganar nasan babu wanda zata fadawa.”

Murmushin takaici nayi ba tare da nace komai ba na yunkura domin sauka daga jikinsa, saki na yayi na mike tsaye, ya zuba min idanunsa da sukayi jajawur!

Gwaggo taja tsaki da fad’in “Kai kam Jarumi ban san inda zaka kai jaraba da fitina ba to ni bana son wannan d’abi’ar taka zan iya zare hannuna daga kanka mutukar kace haka zaka cigaba dayi.

A sar’ke yace.”Gwaggo ki gafarce ni.” Uffan ba tace masa ba ta mika masa kayansa. ganin yana kokarin sa kayan a gabanmu yasa ni da ita muka fita daga dakin.

Fitowa yayi ba tare da ya kalli inda muke zaune ba ya nufi gurinsu…..Har yanzu suna zaune suna sa’ka mugun zare.

Ummatu ta kalleshi da fadin.” Dama jira nake ka shigo domin nayi maganar karshe da kai Ga Baito ka Jamila su zasu zama sheda bayan Ubangijin mu.”

Ji yayi gabansa ya fad’i! A sanyaye ya nemi guri ya zauna yana kallonta sai kawai ta fashe da kuka tasa gefan zaninta tana share hawaye tana kallonsa tace.”Yanzu Khalid abin kunyar da zaka janyowa zuriarmu kenan.”?

Yace.”Ummatu me kuma ya faru.”? Tana kukan tace.”Baka da lafiya kana Fama da kanka Baito ta shigo ta samaku kai da Sa’ida kun rungume junanku shin hakan me yake nufi.”?

Kansa ya sunkuyar kasa domun dai bashi da abin fad’a…..Ta cigaba da cewa.”To wallahi wannan shine na farko kuma shine na ‘karshe Khalid idan ka ‘kara shiga sabgar Sa’ida Allah ya isa ban yafe maka ba.” Da saurin gaske ya kalleta…..Baito tace.” Ba wai zamu raba ka da ‘yar uwarka bane Aa muna gudun mugun halinta shiyasa kaga bama so kana mu’amula da ita idan kana so kayi albarka a rayuwarka to kabi maganar mahaifiyarka.”

Ya dinga jin kansa yana masa wani irin ciwo……Ya kalleta ido jawur yace.”Ummatu Sa’ida ‘yar uwata ce ta jini ta yaya zakiyi min tsakani da ita.”

Tace.”Gaisuwa kawai na amince maka kayi da ita ban yarda ka sake wata mu’amula da ita ba ka cire sonta daga ranka na rabaka da ita har abadah kazo ka rungumi Jamila itace za’bin da nayi maka.”

Gumin goshinsa ya sharce! ya sunkuyar da kansa kasa yana jin wani irin nauyi a kirjinsa……Cikin tsawa! tace.”Saboda kai sakarai ne har ka iya yarda sonta ya janyo maka aman jini to bari kaji idan ka kwanta ka mutu bata da damuwa kuma ba zata fasa auranta ba, saboda haka kayi wa kanka fada ka cire ta daga ranka.

Ya dago kansa yana kallonta a shaqe yace.”Ummatu insha Allahu daga yau nayi miki alkawarin cire Sa’ida daga raina na hakura da ita har abadah mutukar zaki samu farin ciki a cikin zuciyarki.

Murmushin samun nasara tayi tace.”To Allah Ubangiji yayi maka albarka Khalid.” jiki a mace ya amsa da ameeen ya mike ya fita daga dakin.

Mukkuli yasa a dakinsa ya bude ya shiga ya kwanta rigingine yana tunanin rayuwa tabbas dole ya hakura ko yaki ko ya so saboda duk yanda yaso da al’amarin rayuwarsa ya kasance Allah bai so ba dole ya bi maganar mahaifiyarsa mutukar yana so yaga nasara a rayuwarsa amma shi kansa yasan cire auntyn nasa daga cikin rayuwarsa babban jidali ne…..

_Kuyi hakuri da yanayin labarin littafin nan ku cigaba da karantawa a yanda yake insha Allahu a gaba zaku gane inda na dosa NAGODE_

*Littafin na kudi ne….Kada ki siya ki fita dashi…idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing……Idan kika karanta baki biya ba na biki bashi…..Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake… Vip gruop#600 normal gruop#300…account.. 0542382124…Binta umar gtbank….Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/25, 9:47 PM] +234 906 667 3667: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*70&71*
Tunda ya shiga d’akinsa ya kulle bai fito ba sai da yaji kiran sallar magariba ya bude dakin ya fito yana ya mutsa fuskarsa lokacin su Baito sun dade da tafiya sai Ummatu a kicin tana aikin tuqa towon teba. ganin fitowarsa yasa ta bishi da kallo cikin kulawa tace.”Wai dama tun dazu kana cikin dakin.”? Sumar kansa ya shafa a hankali yace.”Eh ina ciki bacci ne ya daukeni.” Ya fadi hakane domin ta kyaleshi da tambaya, tace.” Sai kayi sallah kazo ka irin abincin da kake so nayi maka.
Yana kokarin daukar buta yace.”To shikkenan nagode Ummana.” Bandaki ya shiga ya fito ya tsuguna yana daura alwala ta kalleshi da fadin.”Ya jikin naka.”? Yace.”Da sauki.” Tace.”To Allah ya kara afuwa ina fata dai kaji maganata ta dazu.” Yace.”Kada ki damu Ummatu insha Allahu zan kiyaye.” Taji wani irin dadi a cikin zuciyarta juyawa tayi ta cigaba da aikinta shi kuma ya nufi massalaci.

Tare suka shigo gidan da mahaifinsa. Kawu ya tsaya suna magana da mahaifiyarsa shi kuwa da sauri ya shige gurinsu…..hakan sai duk ya basu mamaki! amma dai duk basu kawo komai ba a cikin ransu….Gwaggo ta cigaba da bawa Kawu Iro Labarin irin halin da Khalid din ya shiga a lokacin da ya samu labarin auran Sa’ida da Aminu…..Kawu Iro ya dinga girgiza kansa yana mamakin al’amarin Gwaggo tace.”Wallahi Ibrahim sosai na tsorata da ganin yaron nan yana aman jini hakika ba karamin son Yarinyar nan yake ba don Allah Ibrahim kayi wani abu kai domin ceto rayuwar yaron nan.

Kawu ya girgiza kai da fadin.”Gwaggo wane abu zanyi akan Al’amarin nan aski yazo gaban goshi dole khalid yayi hakuri bashi da rabo dama aman jini kuma ina ganin kamar shi ya d’orawa kansa tunda bashi da tawakkali.”

Tace.”Ibrahim idan kana nunawa Khalid kiyayya sai naga kamar ba kai ka haifeshi ba ya za’ayi yaron nan ya dorawa kansa ciwo yanda aka yaudareshi ina ganin zai iya yanke jiki ya fadi saboda tashin hankali.

Kawu Murmushi yayi yace.”Gwaggo mu dai har kullum za’bin Allah muke nema saboda haka dukkanin abinda ki kaga yana faruwa daga Allah ne Khalid kuma duk abinda nake nunawa a kansa ‘kauna ce ta janyo haka saboda haka ki daina cewa bana sonsa.

Tace.”To ai shikkenan dama nasan ba zaka ta’ba fahimtar maganata ba Ubangiji Allah ya bashi lafiya.” Ya amsa da ameeen yana kokarin shiga gurinsu.

To har wajan tara da rabi na dare Khalid bai leko inda muke ba Gwaggo hankalinta ya tashi ta kalleni da fadin.”Sa’ida anya kuwa lafiya kinga yaron nan har yanzu bai shigo ba ko dai yana can a kwance a d’aki ciwon nasa ya tashi.

A sanyaye nace.”Kije ki duba ki gani.” Yunkurawa tayi ta mike ta kama hanyar fita tana fad’in.”Ai dole naje na duba shi.

Lokacin data shiga gurin samun sa tayi a kusa da mahaifiyarsa suna hira…….Ganin ta shigo yasa sukayi shuru….Tace.”Khalid ashe lafiyarka lau ina can ina zaman jiran ka ka shigo kaci abinci shuru baka shigo ba nace bari nazo na duba ka.”

Cikin kulawa yace.”Gwaggo ina nan muna hira da Ummatu abinci kuma na riga naci amma ki ajiye min d’umame.”? Jiki a sanyaye tace.”Yau kuma a gurin Uwarka kayi ra’ayin cin abincin.”?

Murmushi yayi bece komai ba Ummatu tana ‘yar dariya tace.”Gwaggo yau yana so ya faranta min rai ne a matsayina na Uwarsa ni kuma sai na samu damar zaunar dashi ina masa nasiha akan rayuwa.

Gwaggo na k’ok’arin juyawa tace.”Eh ai kam kin kyauta Rabi ki cigaba dayi masa nasiha.” Tana gama maganarta ta fita daga gurin jikinta duk a mace babu shakka akwai abinda Surikar tata take shirya mata.

Haka muka kwana ni da Gwaggo cikin tunane tunane mara dad’i da ma’ana……Da safe cikin kayan motsa jiki ya leko dakin a maimakon ya shiga kamar yanda ya saba sai kawai ya dogare a bakin kofa hannunsa rike da labule yace.”Gwaggo kun tashi lafiya.”? Tace.”Lafiya lau Jarumi ya karfin jiki.”? Murmushi yayi yace.”Naji sauki sosai gashinan ma zan fita atisaye.” Tace.”To masha Allah kafin ka fita ka shigo ka karya kummalo tukkuna.

Yace.”Gwaggo a yanzu dai bana bukatar wani abu sai bayan na dawo.” Baki a sake muke kallonsa….ya kalle ni babu yabo babu fallasa yace.”Auntyna kin tashi lafiya.”? Nace.”Lafiya lau ya jikin ka.”? murmushi yayi be amsa min ba ya saki labulen dakin ya bar gurin.

Shuru dakin yayi na minti biyu kafin ta kalleni a sanyaye tace.”Sa’ida Rabi ta kitsawa yaron nan mugun nufi akan mu ko bakya ganin abinda yake sai kace dodanni ya’ki ya zauna a inda muke.”

Nace.”Nima tun jiya na fahimci hakan amma bana so ki tayar da hankalin ki gwaggo ki kyaleta don Allah duk rintsi bata isa ta sanjawa towo suna ba.”

Gwaggo tace.”Aikuwa dole sai na zauna dashi munyi magana idan ma uwarsa ce take zuga shi sai ya fada min.” Murya na rawa take maganar….Tausayi ta bani na girgiza kaina gami da fadin.” Komai dai yayi farko yana da karshe Gwaggo idan kin kwantar da hankalinki Ummatu bata isa ta raba soyayyar dake tsakaninki da Khalid ba.

Hawaye ta share ba tare da tace komai ba ta dauki jug din kunu tana tsiyayawa a kofi….Mikewa nayi na fita domin nayi wanka da wuri nake so na fita gidan Hauwwa domin cigaba da gyaran jikina.

Tsaf na gama shiryawa na zauna ina karyawa in ban da hirar yaron babu abinda take min gabadaya duk ta d’aga hankalinta kan abunda yake ni dai lalla’bata nake yi akan kada bayan fita ta daga gidan ta takali Ummatu da wata rigimar sabida na riga nasan halinta da rashin hakuri ita kuma Ummatu idan ranta ya ‘baci ta mayar da martani suyi ta hayaniya a gida mak’ota na jinsu hakika ina masifar jin takaicin abinda sukeyi.

Mayafi na yafa ina kallonta nace.”To ni zan tafi sai na dawo.” Tace.”To shikkenan nima idan anjima zanje a lalla’be min kaina idan yaso da daddare sai na kunshe fafafuna da lallai.”

Nace.”Hakan nada kyau Amma Gwaggo don Allah ki dauki maganata kada bayan na fita ki takali Ummatu da wata maganar.” Tace.”Kije abinki babu abinda zai faru sai alkairi.” Nace.”To dama haka nake so naji.

Ina fitowa soro kira ya shigo wayata ina dubawa naga angona ne a nutse na daga wayar tare da sata a kunnena cikin nutsuwa muka gaisa yace.”Ki fito gani a waje ki same ni.”

Cike da mamaki nace.”Yaya Aminu ina fata dai lafiya.”? Murmushi yayi a nutse yace.”Lafiya lau sai alkairi.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Gani nan fitowa dama na shirya zuwa gurin gyaran jiki.” Yace.”Okey to ina sauraranki.”

Wayar na kashe da sauri na kama hanyar fita……….Motar Ya Aminu abar kallo ce baga yara ba baga manya ba duk wanda yaga motar yasan za taja kudi masu yawa, yara-yaran dake tafiya makaranta suka dinga tsayawa suna kallon motar wasu har zuwa suke su shafa motar……Khalid da abokansa suka shigo layin jikinsu duk yayi ‘kura da kasa……Faduwar gaba naji lokacin da muka hada ido dashi, da sauri na kauda kaina na nufi motar Yaya Aminu gilashin motar ya sauke fuskarsa a sake yace.”Shigo mota mana….hannu nasa ina kokarin bude motar Khalid ya karaso gurin….kallonsa nayi gabana na faduwa bana so ya zubar min da mutunci a gurin wanda zan aura amma ga mamakina sai naga ya saki fuskarsa cikin nutsuwa ya mika masa hannu da fadin.”Alhaji barka da Asubah.” Yaya Aminu da sauri ya mika masa hannu da fadin.”Barka abokina ya gida ya al’amura.”? Ya amsa da komai “Alhamdulillahi.” Yaya Aminu yace.”To Allah ya taimaka.” Ya amsa da “Ameeen tare da cire hannunsa a nasa ya bar gurin

Yaya Aminu ya kalleni da sauran murmushi a fuskarsa yace.” Amma dai wannan d’an uwanki ne ko.”? Nace.”Khalid ne fa.”? Yar dariya yayi yace.” Ina zan san shi tunda ni d’in ba mazauni bane.”

Nace.”Hakane fa Yaron Kawu Iro ne.” Yace.”Eh shiyasa ai naga kuna d’an kama dashi.” Dariya kawai nayi na bude motar na shiga.

Cikin kulawa yace.”Sa’ida kin san wani abu.”? Kaina na girgiza ina kallonsa yace.”Wallahi tafiya ta kama ni zuwa india zan shigo da wasu kaya an jima nake sa ran tafiya amma bazan dade a can ba kada ki damu za’a daura aure kamar yanda aka tsara za kuma ki tare a gidanki insha Allahu sati biyu kacal zanyi na dawo.”

Rau rau nayi da ido ina kallonsa nace.”Me zai hana idan an d’aura auran na zauna a gida har ka dawo bana so na zauna ni kadai wallahi.

Hankici yasa yana goge min hawaye yace.”Da haka na tsara amma Alhaji yace bai amince da hakan ba ya fiso idan an daura auran ki tare a gidanki idan yaso sai a turo miki wanda zai ta yaki kwana daga gidan mu.”

A sanyaye nace.”To shikkenan Yaya Aminu Allah ya kai ka lafiya ya kuma dawo da kai lafiya.” Ya amsa da ameeen Ya rabbi dole sai kinyi hakuri da yanayin kasuwanci na Sa’ida.”

Nace.”Haba ai babu komai Yaya Aminu Allah ya baka halas d’inka.” Ya amsa da ameeen ya rabbi……”Yanzu muje na ajiye ki a gidan gyaran jikin idan yaso daga can sai na wuce airport. ” Nace.”Tom shikkenan hakan yayi.” Motar ya kunna yaja mukar bar gurin.

Koda na koma gida kasa fad’awa Gwaggo maganar nayi saboda na riga nasan halinta da nanata magana, sai a washe garin ranar ne da Kawu ya shigo yake fada mata halin da ake ciki aikuwa ta dinga surutai tana fad’in “Wannan wane irin d’aid’aitaccen aure ne.” Tsabar bakin ciki da takaici ya hana Kawu cewa komai ya fita daga gidan yana mamakin halin mayafiyar tasa.

Ni kam ai surutan da take sai da ya janyo min ciwon kai kawai na haye gado tare da juya mata baya naci kuka na na koshi ina addua akan Allah yasa kada tayi wa al’amarin baki.

Sai da Khalid ya shigo sannan ta tsahirta da surutan da take ta kalleshi da fadin.” Kai kuma sai yanzu kaga damar shigowa ka gaishe ni? ai na dauka an hana ka ka gaishe ni.”

Yace.”Gwaggo tunda na dawo daga sallar asubahi nake bacci sai yanzu na tashi ina fitowa naji surutan ki keda waye ne.”?

Tace.”Humm! Khalid dole nayi surutu wannan wane irin gantalallan aure ne da za’a d’aura shi babu ango a kusa wato kudi ya fi mutunci ko? duk wanda yaga haka zaice dama kudinsa muka gani muka bashi auran ‘yarmu.”

Yace.”Nifa ban fahimce ki.”? A nutse ta warware masa abinda yake faruwa….Yace.”To ai ba laifi bane don anyi daurin aure babu ango a kusa sau tari hakan na faruwa kuma hakan ba yana nufin cewa aure bai d’auru ba aure ya dauru mutukar an d’aura shi akan tsari da shedu da kuma waliyyai sabida haka don Allah ki daina wannan surutan.”

Gwaggo shuru tayi tana kallonsa mamaki dan’kare a zuciyarta tace.”Khalid kai kake fadar wannan maganar kanka tsaye yaushe Allah yasa maka dangana haka.”?

Murmushi yayi yace.” Tuntuni Allah yasa min dangana Gwaggo ai na barwa Allah komai na hakura da Aunty Sa’ida tunda ba alkari ce a tare dani ba.”

Zaune na mike ina kallonsa sam banji dadin maganarsa ba. kallona yayi na second guda ya dauke kansa agogon hannunsa ya duba da fadin.”Ni zan dan fita gurin abokaina.” Tace.”To shikkenan sai ka dawo.” Ba tare da yace komai ba ya bar gurin.

Kaina na sunkuyar kasa ina mamakin sadudar yaron ikon Allah lokaci guda yayi sanyi ya mikawa Allah lamarin duk tsananin kishi irin na Khalid wai shine yake musabaha da wanda zan aura hakika al’amarin ya bani mamaki mutuka.

To kamar yanda ango ya tsara al’amarin hakane ya kasance kwanasa biyu da tafiya kasar india aka daura auran kuma a ranar na tare a dan’kareran gidana dake Unguwar Jambulo gida gari guda komai na more rayuwa akwai a gidan Yaya Aminu jin dadi dai na duniya na sameshi sai dai fatan zaman lafiya Layuza da Karima ‘kannansa su aka turo domin su taya ni zama kafin ya dawo naji dadin zuwansu sosai dama mun saba dasu tunda ina ziyaryar gidansu sa’i da lokaci, bamu da fargabar komai gidan tunda akwai matakan tsaro a gidan sosai akwai securities masu dagi da karninuka a Estate d’in.

*72&73*
A ranar da Gwaggo tazo gidan sai da ta kusa bani kunya gabansu Layuza sai wasu irin maganganu takeyi akan gidan da kuma maigidan sai da nayi mata jan ido tukkuna tayi shuru da bakinta tana yin sallar azuhur tace ita tafiya za tayi abubuwan kwad’ayi na had’a mata masu yawa nasa direba ya dauketa ya kaita har gida, Gwaggo koda ta koma gidan kasa shuru tayi da bakinta da Kawu Iro ya shigo ta tare shi da maganar wai anya kuwa A harkar kasuwanci Yaya Aminu ya tsaya baya yakan kai wannan uwar dukiya daka gani bata Allah da Annabi bace.” Kawu Iro zaunar da ita yayi ya dinga yi mata nasiha gami da kawo mata misalai Allah yakan arzita bawansa da dukiyar da bai san iya adadinta ba saboda haka ta kwantar da hankalinta duk wani binkice yayi ya kuma tabbatar da cewa mutumin a harkar kasuwanci ya tsaya.” Gwaggo dai shuru tayi da bakinta tana jajanta al’amarin.

Gwaggo kullum za tayi girkin ta da nama taci ta koshi ta ajiyewa mutumin nata idan ya dawo tace masa yazo yaci abinci kai tsaye yake ce mata ba zai ci ba ya gwammace yaci garau-garau din da mahaifiyarsa tayi ko kuma yaci aljihunsa…..Gwaggo tayi tai masa naci shi kuwa yace.”Ba zai ci ba dole take hakuri ta kira almajirai ta raba musu sadaka.

“Khalid kwata-kwata fa ni ban amince maka da wannan tafiyar ba, kai harkar ball din ma gabadaya bana sonka da ita ka hakura ka zauna a gida ka fara kasuwanci shine yafi alkairi a tattare da kai.

Cikin wani irin yanayi na damuwa yake kallon mahaifin nasa yace.” Baba kayi hakuri ka lamunce min tafiyar nan akwai nasara a cikinta.

Kawu Iro yace.”Ai dama duk hanyar shaid’anci zaka samu nasara a tare da ita hanyar Allah da Annabi kuwa kun dinga kawo suka a cikinta to ni dai na gama magana mutukar ni na haifeka ban lamunce maka tafiya wata america ba.

Kawu Iro na gama maganarsa ya bar gurin…..Ya jima a tsugune a gurin yana sa’kawa da kwancewa kafin ya mike kai tsaye gurin Gwaggo ya nufa domin kuwa yana ganin itace kadai zata iya tursasa mahaifinsa ya barshi ya tafi inda yake muradi.

Tana zaune da kwanon farfesun kaji a gabanta gefe ga lemo nan irin na kwali farfesun take sha hankali a kwance Gwaggo har wani qiba tayi saboda ka’bakin arzikin da Sa’ida take kawo mata duk bayan kwana uku ko hud’u……Dakin ya shiga ya zauna yana kallonsa….Sai ta tura masa kwanon farfesun da fadin.”Gashinan ko kayi sha’awa.”

Girgiza kansa yayi yace.”Bana bukata.” Kwanon farfesun ta janye ta cigaba dasha tana tauna tsokar data dahu luguf.

Yace.”Gwaggo Alfarma nake nema a gurun ki.” Tace.”Ai dama tinda naga ka shigo dakina ka zauna nasan da walakin goro a miya.

Sajensa ya shafa yace.”Eh wallahi Gwaggo ke kadai ce zaki umarci Kawu Yayi abinda kike so.”

Tace.”Eh kwarai kuwa ai mahaifinka yana da biyayya duk abinda nace inaso to shima yana so.

Yace.” Yawwa Gwaggo dan Allah kice masa ya barni na koma gurin sana’ata.”

Tace.”To akan me dama zaice ba zaka koma ba.”? Yace.”Kin san kwanaki nayi miki magana kancewa zamuje america muyi wasa to tafiyar ce ta taso dan tun satin da ya wuce oganmu yake kiran waya ta na bashi hakuri kancewa insha Allahu ya tsammaci zuwa na a cikin satin nan to kuma yanzu da nake shedawa Kawun maganar yake cewa shi bai amince ba.

Tana sud’e hannunta tace.”Khalid wace irin ball ce har sai anje america mai zai hana ka ka cigaba da buga abarka a cikin ‘kasar ka nima wallahi sam bana sonka da wannan harkar.

Yace.”Gwaggo kada kice haka mana zuwa na america matakin nasara ne domin kuwa zanje mu fafata da manya manyan ‘yan ball wanda suka shahara sukayi suna duniya tasan dasu.”

Hararasa tayi tace.”Kai kuma shahara kake nema da makiya Allah da Annabi kenan.”? Girgiza kansa yayi da sauri yace.”Aa Gwaggo ai ba kafurai ne kawai ba harda musulmai a ciki kowa yana kokarin ya nuna bajintarsa ne.”

Shuru tayi masa ya matsa kusa da ita gami da rike hannunta yana rarrashinta. Tace.”Shikkenan ka kwantar da hankalin ka zan sameshi muyi magana Allah ya za’ba maka abinda yafi alkairi.”

Cike da farin ciki ya amsa da ameeen Uwargidana.” Harararsa tayi tace.”Ina uwargidanka amma ka daina cin abincina ko da yake ai nasan uwarka ce take zuga ka.” Cikin kulawa ya kalleta da fadin.”Gwaggo babu ruwan Ummatu ni ne dai ba zanci wani abu da ya shafi aunty Sa’ida ba kin san haka tsarina yake ba tun yau ba.

Tace.”In banda abinka kuma wane kishi za kayi bayan komai ya wuce kake cutar kanka.” Yace.”Kinga Gwaggo dan Allah a bar maganar duk nau’in abincin da nake so naci ina da kudin siya ba sai kin tursasa ni naci abincin ki ba.

Tace.”To ai shikkenan tunda haka ka za’ba, mi’kewa yayi yana kallon agogon hannunsa yace.”Ni zan fita gurin abokaina.” Tace.”To sai ka dawo.” Fitowa yayi tare da sa takalmansa ya fita daga gidan.

Kullum ta Allah Yaya Aminu yakan kira waya ta sau biyu ko uku mu jima muna hira dashi al’amarin ya dinga bani mamaki ganin gabadaya baya nuna wani d’oki da zumud’in irin na angwaye idan ya kira waya ta hirar kasuwancinsa kawai yake min babu wata kalma mai dadi irin to so da nuna cewa ina bukatar ki abin ya dinga bani mamaki yana sani a cikin damuwa! a gaskiyar magana lamarin yana min ciwo sabida ni na kasance mace mai son soyayya inaso naga namiji na kula dani da nuna min so……Amma Yaya Aminu sam babu wannan a tare dashi shidai harkokinsa yasa a gaba.

Yau asabar Allah yayi nufin dawowarsa sosai nayi gayu cikin shaddan galila taji uban stone work nayi ado da gold wuya da hannu sai zuba kamshin tururuka nakeyi ni kaina dana tsaya gaban mirror sai da nayi mamakin uban kyawun da nayi……Amma abin mamaki wanda akayi kwalliyar dominsa bai wani kula sosai ba dan bayan na bashi abinci yaci dakinsa ya bude ya shiga ya kwanta, sai nayi tunanin binsa dakin koda na ta’ba kofar sai naji a kulle. jiki a sabule na bar gurin zama nayi kujerar falo abin duniya ya dame ni, ga Layuza da Karima sun tafi sai ya kasance ni kadai a gidan dana gaji da zaman falo mikewa nayi na shige dakina na kwanta kawai sai hawaye suka ‘balle min wannan wane irin ango ne mara kula. sosai naci kuka na na koshi bacci ya dauke ni.

Sai daf da la’asar na tashi a gurguje nayi wanka na fito daure da alwala sai dana kimtsa jikina tukkuna na tsaya kan dadduma na tayar da sallah.

Ina sallama ya shigo dakin daga kai nayi ina kallonsa kamshin turaransa duk ya cika dakin a shirye yake da alama futa zaiyi…..zama yayi gefan gado har na shafa addua na juyo muka hada ido dashi, murmushi yayi min da fadin”Amarya.” ya’ke kawai nayi naje na zauna kusa dashi tare da gaishe shi, ya amsa cikin kulawa ido ya tsira min kafin yace.”Naga idanuwanki sunyi jawur ina fata ba wata matsala bace.”

Daurewa nayi nace.”Babu komai bacci nayi shiyasa idon ya sanja.” Yace.”Okey to ya kike ya zaman kadaici.” Mirmushi kawai nayi ban tanka masa ba.

Ya kalli agogon hannunsa da fadin.”Ni zanje babban gida mu gaisa dasu.” Nace.”To ka gashe min dasu.” Mikewa yayi yana fadin.”Insha Allahu zasuji sa’kon ki.

Bayansa nabi da kallo har ya bude dakin ya fita…..Jingina baya na nayi jikin gadon na shiga tunanin rayuwa.

Sai kusan tara da rabi ya shigo gidan, gani na a zaune a falo ya bashi mamaki yace.”Baki bacci ba.”? A nutse na mike da fadin.”Eh na tsaya ka dawo ne.” Murmushi yayi na kar’bi wayoyinsa ina masa barka da zuwa.

Amsawa yayi ya rike hannuna muka nufi dakinsa.

Da kaina na hada masa ruwan wanka yana ta sa min albarka na fito masa da jallabiya da gajeran wando na ajiye kusa dani…..Daure da towel ya fito sai yayi saurin dauke kansa a maimakon ni naji kunyar ganinsa a haka sai ya kasance shi yake jin kunyata, dan sai naga kamar a tsarge yake tsayawa yayi bakin kofar toilet din da fadin.”Bani kayan nan.” Da sauri na mike da kayan a hannuna na kai masa, kawai sai naga ya koma toilet din ya banko kofar. sakato nayi da baki ina mamaki!
Ina nan tsaye ya fito ya wuce ni ba tare da ya tanka ba, a sabule nabi bayansa falon sai na sameshi zaune a kasan kafet yana duba loptop. zama nayi a hankali nace.”Ba zaka ci abinci ba.”?

Hankalinsa nakan Loptp din yace.”Bari na rage aiki tukkun.” shuru nai kawai na zuba masa ido ina mamakin al’amarinsa.

Kusan rabin awa yana aiki a loptop din kafin ya rufe a nutse ya kalle ni da fad’in “Tashi muje dainng din ki bani abincin.” Mikewa nayi ya biyo bayana.

Tsaf na shirya masa abincin na tura masa gabansa zama nayi ina kallonsa yana cin abincin yana amsa waya

Nace.”Yaya Aminu kayi abu d’aya mana ka ajiye wayar kaci abinci sai hakan yafi.”

Ba tare da ya kalle ni ba ya cigaba da wayarsa…..Ji nayi raina ya ‘baci sai kawai na miqe na bar masa gurin.

Koda ya kammala cin abincinsa zuwa yayi ya dauki loptop dinsa bece min uffan ba ya bude dakinsa ya shige! ni dai mamaki ne ya kusa kasheni a gurin da kyar na iya kai kaina daki na kwanta.

Haka rayuwar mu ta cigaba da tafiya tsayin wata guda da dawowarsa babu wata mu’amula ta aure data ta’ba shiga tsakanina dashi Kullum a dakinsa yake kwana a garkame! gabadaya ma ya daina yarda na ra’bi inda yake dan duk kokarin da nake masa idan ya dawo daga kasuwa sai ya dakatar dani yace naje na huta shima Allah ya bashi lafiya zai iya had’a ruwan wankansa.
Ganin wulakancin yayi yawa yasa na daina shiga dakinsa sai dai idan ya fito mu gaisa ya kama hanya ya fita…….Gashi kamar mara tunani kullum sai ya tura min kudi accont d’ina al’amarin dai sai kace hauka! kuka naci na koshi na yanke shawarar tun kararsa da magana domin dai ni na gaji ba auran kudi nayi ba halastaccan aure nayi irin wanda Allah yake so……Sai da ya fito falon sannan nima na fito daga dakina na sameshi a zaune yana abinda ya saba lissafi da amsa kiran waya cikin zuciyata nace.”Ban ta’ba ganin sahoramin namiji irinka ba. Wayar hannunsa ya kashe ya kalle ni da fadin.”Kina da wata bukata ne.”? a nutse nace.”Eh ina da ita.” Ya zuba min ido da fadin.”Ina sauraranki.” Murya na rawa nace.”Yaya Aminu wai me kake nufi ne.”? Cikin wani irin kallo yace.”Bangane ba.”? Na d’aure fuska tamau! nace.”Shin dutse ka ajiye a gidan ka kome? ko kana da lalura ne.”? Tsira min ido yayi yana kallona na sake cin kunu da fadin.”Tsayi wata d’aya da sati biyu nake cikin gidan nan naci na koshi naci nama nasha madara nasha nono na kwanta a Ac me kake tsammanin zai faru.” ? Dariya yasa yana kallona, sai kawai hawaye suka ‘kwace min. Nace.”Wato saboda kai baka da damuwa ka maisheni mahaukaciya kana min dariya ko to wallahi na gaji ni zan samu mahaifiyarka na fad’a mata halin da ake ciki.” Da sauran dariyar a fuskarsa yace.” Ai ba sabon abu bane a gurinta idan kin fada mata tuna mata kikayi domin tafi kowa sanin matsalata.” Hannu nasa na share hawaye da fadin.”To me yasa kasan kana da matsala ka amince da aurena.”? Jim yayi kafin yace.”Kawai bana so na bijirewa umarnin mahaifina ne.” Cikin takaici nace.”To kawai daga yau ka kira kanka da mace tunda ka fita daga sawun maza wato har wani fad’a kake kana da lalura to zaman me kake a haka da ba zaka nemi magani ba.”? Rai a d’an ‘bace yace.”Ke Sa’ida kada ki fad’a min maganar banza mana.” Nace.”Ai gaskiya ce.” Hannu ya daga min da fad’in “To tunda dai kin damu yau zan jarraba na gani.” Naji wani kuttun bakin ciki ya tokare min a ma’koshi nace.”Wallahi tallahi kudin ka na banza ne tunda har ka sake ka mayar da kanka haka meye amfanin neman kud’in naka kana fama da lalura irin wannan.” Shuru yayi min, na dinga masa surutai ina farfad’ar masa maganar da duk tazo bakina…..A fusace! yace.”Ki tashi ki bani guri idan ba haka ba wallahi ranki zai ‘baci! Mi’kewa nayi na bar gurin raina a mugun ‘bace.!

[3/29, 8:12 AM] +234 706 435 8270: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*74&75*
Koda na koma dakin kasa hakuri nayi raina a bace na dauki wayata number Hauwwa na nema kiranta zanyi na fada mata abinda yake damuna domin hausawa na cewa Abokin kuka shi ake fadawa mutuwa na yarda da Hauwwa mutuniyar kirki ce kuma na tabbatar da cewa ba zata fadawa kowa sirri na ba…… Cikin barkwanci tace.”Amarya Amaryar Alhaji Aminu young millionaire ya kike ya amarcin.”?

‘Karamin tsaki naja ciki ciki nace.”Hauwwa ki daina kira na da amarya domin dai har yanzu ban amsa wannan sunan ba.”

Cike da mamaki! tace.”Kawata bangane ba.” Ajiyar zuciya na sauke nace.”Hauwwa akwai gagarimar matsala kizo don Allah.

A sanyaye tace.”Sa’ida matsala wace iri kuma? mai kika rasa a wannan gidan da har kike kiran matsala.”

Nace.”Hauwwa sai dai kinzo sai mu tattauna maganar domin a waya ba zaki gamsu ba.

A sanyaye tace.”Tom shikkenan idan na taso zan shigo Allah yasa mu dace.” Na amsa da ameeen ya Allah.”

Motsin shigowarsa dakin naji sai nayi saurin rufe idona gabadaya bana son kallon fuskarsa dan wani irin mugun haushinsa nake ji.

Zama yayi a kusa dani yana kiran sunana, shuru nayi ban amsa ba.

Yace.”Nasan idonki biyu ki tashi inaso nayi magana dake.” Sai da na mula tukkuna na tashi ina kauda kaina.

Cikin taushin murya yace.”Ki juyo ki kalle ni ki kuma fahimci maganata.”

A hankali na juyo muka hada ido sai na hango alamun damuwa a fuskarsa.

“Sa’ida nasan na zalince ki dana amince da auranki bayan nasan bani da wani karfi irin na mazantaka bani da wani kwanjin da zan biya miki bukatarki ta aure saboda wannan dalilin. Sa’ida tunda na taso na girma na kai munzali ban ta’ba jin sha’awar wata ‘ya mace ba ban san meye dalili ba mahaifiyata sosai al’amarin ya dameta duk inda taji labarin wani mai magani sai taje ta bada sadaka ta kar’bo min bana mata gardama zan kar’ba nayi amfani dashi amma duk da haka bata sanja zani ba har yanzu jiya i yau bana jin wani sauyi a tare dani kiyi hakuri insha Allahu zan je asibiti domin a duba lafiya.

Nace.” Yaya Aminu mai yasa kasan kana da irin wannan matsalar ka kar’bi aurena.”? Girgiza kansa yayi yace.”Na fada miki dalili na bana so na bijirewa umarnin mahaifina ne.”

Ajiyar zuciya na sauke na koma na kwanta da fadin.”Allah ya sawwa’ke maka.” Ameeen yace tare da mikewa tsaye hanyar fita ya kama na bishi da kallo ina jin wani katon abu ya tokare min a kirji a gaskiya banga dalilin da zai sanya na cigaba da zama dashi da wannan lalurar ba dole ne na nemawa kaina mafita.

Kimanin minti ashirin da fitarsa ya sake shigowa a shirye da shirin fita ya kalle ni a nutse yace.”Ni zan fita.” Ba tare dana kalleshi ba nace.”To Allah ya bada sa’a.” Ya amsa da “ameeen ya Allah.”
Ya juya ya fita daga dakin.

Sai yamma Hauwwa tazo gidan nace.”Amma dai kin biya wani gurin ko.”? Tace.” Wallahi naje asibitin Yurolaji dubiya kwana biyu talakawa sai wuya suke sha suna fitsarin jini dalilin shan kayan lemo na leda da sukayi.”

Cike da mamaki nace.”Wane irin kayan lemo kuma.”? Tace.” Kayan lemo dai irin wanda kika sani Vevi mix Tiara d’an tsami da dai sauransu.

Nace.”Ikon Allah wannan shekaran kuma annobar data afku kenan.”? Tace.”Wallahi kuwa ai al’amarin ma da sauki tunda an fahimta da wuri mutane duk sun tsorata suna kokarin kare kansu da lafiyarsu.

Jiki a mace nace.”Talaka dai ya shiga uku wato ganin azimi yazo yasa aka shigo da wannan muguntar.” Tace.”Shine manufarsu dama jama’a suyi ta sha suna mutuwa.

Nace.”To Insha Allahu sai Allah ya kare al’ummarsa duk mai nufin talaka da sharri zai koma kansa

Dariya tayi tace.”Na lura al’amarin ya firgita ki Sa’ida.” Nace.”Sosai kuwa fitsarin jini fa.” Tace.”Wallahi kuwa sai ma kinga yanda suke shan wahala sai karin jini ake musu idan abun yazo da karar kwana har mutuwa ake.

Girgiza kaina kurrum nayi ina jajanta al’amarin.

Ta kalle ni a nutse tace.”To Sa’ida gani nazo kuma ni banga wata damuwa a tare dake ba na dai ga kinyi kyau kinyi qiba da haske alamun kina cikin kwanciyar hankali.”

Kallonta nayi nace.”Hauwwa a jikina ina jin nayi rama sabida damuwa amma kice nayi qiba.”

Murmushi tayi tace.”Kin san Allah ni banga wata rama da kikayi ba.'”

Nace.”Okey mybe dan kin kwana biyu baki gan ni ba ne.” Tace.”To zata iya kasancewa hakane.

Shuru dakin yayi na minti biyu na kalleta da fadin.” Hauwwa kin san me.”? ta girgiza kanta tana kallona. Nace.”Yau tsayin wata guda da kwanaki a gidan aurena babu wata mu’amular aure data shiga tsakanina da Yaya Aminu.

“Bangane ba.”? Tafada tana kallona da mamaki a tare da ita.

Murmushin takaici nayi nace.” Abinda dai yake faruwa kenan Hauwwa Yaya Aminu yaki yarda mu had’a shimfida hannuna wannan bai ta’ba rikewa ba, dazu na sameshi da maganar sabida inaso ya fada min a wane matsayi nake a gidansa, Budar bakinsa sai cewa yayi shi yana da lalura wai tun da yake bai ta’ba sha’awar wata a mace ba amma wai zai nemi magani.

Hauwwa zuba min ido kawai tayi tana kallona. sai kawai naji zuciyata ta karye hawaye na kokarin kufce min.

Tace.”Sa’ida wannan karon kuma da wannan masifar Allah ya jarrabe ki.” Girgiza kaina nayi nasa hannu na goge hawayen da suka zubo min nace.”Hauwwa ina da karfin sha’awa ni kaina nasan da hakan amma Allah yana jarrabata ta da sakarkarun maza har gwara Alhaji Nura yana min kokari amma shi wannan d’an tahilikin kamar dutse haka ya mayar dani bama ya min kallon matar auransa kallon kanwa yake min.

Hauwwa ta dinga girgiza kanta ita kanta al’amarin ya daure mata kai Tace.”Allah sarki dama hausawa suka ce dan adam tara yake bai cika goma ba wato shi kuma Alhaji Aminu irin tashi kaddarar kenan, ki duba kiga yanda Allah yayi masa arziki amma kuma ya jarrabeshi da rashin karfi da kuzari irin na maza.

“Shine ai nake fada masa cewa kudin sa na banza da wofi ne tunda ba zai nemi magani ba to wa yake tarawa kudin tunda dai shi bashi da d’a ko jika.”

Tace.”Kwarai hakane maganarki Sa’ida dole dake dashi ku dage da neman magani domin dai kema zama bai kama ki ba mutukar kina bukatar zama dashi to dole ki taimaka masa gurin neman magani.

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Hauwwa ai dole ne kodan nima na samu biyan bukatata amma ko da wasa bana so aurena ya mutu ta wannan dalilin.

Tace.”To kinga kuwa dole ne ki taimaka masa amma ga shawara itama ina gani zata taimaka miki.”

Nace.”To ina sauraranki.” Tace.”Ai kina da k’ananun kaya ko.”? Jim nayi kafin nace.”Ina dasu amma basu da yawa.” Tace.”Ki dinga amfani dasu idan yana gidan kisa ki zauna a inda yake ina ganin idan kika gwada hakan za’a samu wani cigaba

Murmushin takaici nayi nace.”Hauwwa ana miki wata magana kina wata mutumin nan fa na fada miki bashi da lafiya baya sha’awa to me zai bashi sha’awa a jikina.”

Murmushi tayi tace.”Ki dai gwada ki gani watakila a dace idan ma baki da masu fitar da tsaraici to insha Allahu gobe zan shiga kasuwa na siyo miki.

Murmushi kawai nayi ina kallonta tace.”Allah da gaske nake da kaina zan shiga kasuwa na siyo miki masu fitina domin bana so kan wannan matsalar ki fita daga gidan auranki.”

Nace.”Shikkenan Hauwwa zan gwada na gani nagode sosai da shawarwarin ki Allah ya kara mana zumunci.” Ta amsa da ameeeen ya rabbi.

Bayan tafiyar Hauwwa na jima ina tunani akan maganarta zanyi kokarin yin amfani da shawararta ko Allah zai sa a dace.

Kicin na shiga nayi masa abinci har kala uku na gyara daining din tsaf kana naje nayi wanka na shirya cikin kananun kaya riga mai gidan nono da madauri a wuya gabadaya baya na a bude yake rigar ta matse a jikina kuma iya cibiya ta tsaya breast dina kuwa tsabar matsewar da sukayi dik sunyo waje ta saman rigar.

Karamin siket nasa iya gwiwa shima ya matse min jikina tsam! kwankwanso na ya fito sosai gashin kaina na gyara na daureshi guri guda.

Turaruka masu sanyin kamshi nasa a jikina na fito falo na zauna ina sauraran shigowarsa.

Shida da rabi ya kira waya ta yake fada min yau zai dan jima bai shigo ba kada naji shuru ya tsaya wani uziri ne.

Jikina ne yayi sanyi nace.”Shikkenan Allah ya dawo dakai lafiya.” Cike da kulawa ya amsa da ameeen.” Kashe wayar nayi na ajiye ina jan tsaki.

Sai kusan goma da rabi ya shigo zaune a falon ya same ni.

Na mike da sauri ina masa barka da zuwa…..Wani irin kallo ya shiga bina dashi, sai naji dadi ganin tarkona ya kamashi.

Wayoyin hannunsa na kar’ba ya bini da kallo da alama da akwai magana a bakinsa, Juyawa nayi ina wata irin tafiya dik domin na dauke masa hankali.

Yazo yasa key ya bude dakin a sanyaye yace.”Shigo mana.” da murmushi a tare dani nace.”Yau ana bukatata kenan.

Uffan bece min ba ya shiga dakin kai tsaye toilet ya nufa, sai na ajiye masa wayoyin nasa kan bedside na zauna zaman jiran fitowarsa.

Koda ya fito daga toilet din be kalli inda nake ba ya wuce wardrobe dinshi yana kauda kansa! al’amarin sai ya bani da dariya da gaske dai Yaya Aminu kunya ta yake ji ikon Allah sai kallo.

Jallabiya yasa ya juyo yana kallona babu yabo babu fallasa yace.”Muje ki bani abinci yau nasha zurga zurga.”

Mikewa nayi da fad’in “Amma dai kaje asibitin ko.”? Girgiza kansa yayi da fadin.” Aa ban samu zuwa ba sabida uzurirrikan da sukayi min yawa.

Shuru nayi masa tsabar takaici na fita daga dakin ya biyo baya na.

Muna zaune gurin cin abincin yana ci yana bani labarai na kasuwancin sa. Ni dai umm kawai nake cewa daga karshe nace.”Yaya Aminu ina zaka kai kudi naga baka da magana sai ta kud’i kai kenan yawo kasa-kasa neman kud’i shine al’amarin yake bani mamaki.”

Murmushi yayi yace.”Sa’ida ina neman kudi ne saboda kaina da kuma Iyalina da ‘yan uwana da kuma mabukata wannan shine dalilin da yasa ki kiga ina neman kudi babu dare babu rana.”

Kallonsa nayi nace.”Yaya Aminu lafiyarka fa.”? Yace.”Sa’ida Allah ne ke bada lafiya kuma kullum cikin rokonsa nake.”

Nace.”Eh duk da haka Allah yace tashi na taimake ka me yasa dazu bayan mun gama magana da kai akan zakaje asibiti ba kaje ba Yaya Aminu mai yasa kafin daukar harkokin kasuwancin ka da mutunci.”?

Shuru yayi min yana tsakurar abincin gabansa…..”Kayi hakuri idan maganata ta ‘bata maka rai amma ni dai kasan ba zan zauna da kai a haka ba ko.”?

Kallona yayi da ‘batacciyar fuska nace.”Ba wai ina nufin mu rabu ba ina nufin idan ka’ki neman magani to ni zan nema maka sai ka bani hadin kai.”

Yace.” Babu damuwa Allah yasa a dace.” Na amsa da “ameeen ya Allah.”

To koda ya gama cin abincin nasa falo ya koma ya zauna kasan kafet ya fara dube dube a loptop kamar yanda ya saba, zama nayi kusa dashi jikina na ta’ba nashi.

A hankali ya dago kansa ya kalleni, nai masa wani irin kallo ta tare da rike hannunsa.

Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya rufe loptop din ya rike hannuna muka mike tare, kai tsaye dakinsa muka nufa yana ta murza tafin hannuna dake cikin nashi.

Hasken dakin ya kashe ya rungumo ni jikinsa yana shashshafa ni a hankali yace.”Wannan kwalliyar tayi miki kyau Sa’ida.”

Nace.” Allah ko.”? Fuskata ya dago da fadin “Sosai kuwa.” Lumshe idona nayi ina jin wani irin feeling na taso min.

Gadon muka zube ni dashi jikinmu sai rawa yake al’amarin ya dinga bani mamaki ganin yanda dik ya d’imauce yana rawar jiki sai abubuwan da yake so yake yi gabadaya ya gama ya mutsa ni ya masifar tayar min da sha’awa rungumeshi nayi ina sakin nishi hade sa shiwa Hauwwa albarka domin ganin itace ta bani shawara mai amfani.

Mun kai kusan rabin awa muna shafe-shafe gabadaya na kai makura gabana ya jike da ruwa muguwar sha’awa ta rufe min ido jiki na kyarma na hau kanshi ina kokarin sa’bule masa gajeran wandonsa.

Kwanciya yayi ya lafke kamar matacce cikin kulafuci da zumudi na cire gajeran wandon ina shirin ganin JARUMA ta a tsaye sai kawai na ganta a kwance a cure a guri guda motsin kirki ya kasa yi sai shashsheka yake yana matsa mazaunai na…….Hannu nasa kan Jarumar ya zabura da sauri ya matse jikinsa……Wasu zafafan hawaye suka kwace min murya na rawa na kira sunansa…..Amsawa yayi kamar zai fashe da kuka. Nace.”Yaya Aminu ya zakayi dani ina cikin wani hali.”

Mikewa zaune yayi ya rungume ni kam – kam! jikinsa sai kyarma yake yace.” Sa’ida na fada miki matsalata ki ka matsanta kin gani dai da idonki bani da wani kuzari bani da wani K’wanjin da zan iya yi miki wani abun.” Yanda yake maganar yana rawar murya yasa ni fashe da wani irin kuka na rungumeshi tsam a jikina cikin jin tausayinsa nace.”Yaya Aminu hakika Allah ya jarrabe mu da babbar jarraba Yanzu ni da kai ya zamuyi.”?
Fuskarsa ya d’ora a kafadata a hankali yace.” Sa’ida Allah zai mana magani zan nemi magani da yardar Allah za’a dace.” Kuka kawai nake tsabar fargaba da damuwa ya hana ni magana sai uban hawaye kawai nake zubarwa……

*Littafin na kudi ne….Kada ki siya ki fita dashi…idan kika ganshi a gruops kada kiyi sharing……Idan kika karanta baki biya ba na biki bashi…..Idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake… Vip gruop#600 normal gruop#300…account.. 0542382124…Binta umar gtbank….Idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan numbers*
*07084653262*
*08089965176*
*BINTA UMAR ABBALE*
[3/29, 8:12 AM] +234 706 435 8270: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*76&78*
Na jima a kwance a jikinshi ina mur’kususun wahala shi kuma yana kara rikita min jikina sai shasshafa ni yake yana mutsika min breast wai shi duk a kokarinsa na ganin ya biya min bukata ta wanda ni kuma nake sake jin wata gawurtacciyar fitina na yawo a sassan jikina a galabaice nayi yun’kurin sauka daga gadon ya rike ni a sanyaye yace.”Kiyi hakuri na taimaka miki da dabaru.” Kaina na girgiza masa a sarqe nace.”Yaya Aminu kyaleni wannan abin da kake min ba mafita bace ba zan ta’ba samun biyan bukatata ba sai ma tashin hankalin da zan shiga saboda haka kawai ka kyaleni.” Sakar min jiki yayi na sauka daga gadon ina kuka na kama hanya toilet….koda na fito samunsa nayi a zaune a gefan gado ya zuba uban tagumi yana kallon kasan gurin..

Inda yake na nufa ina lalubi kayana nasa a jikina hanyar fita daga dakin na kama ba tare dana tanka masa ba.

Koda na koma dakina na jima a kwance kafin bacci mara dadi ya dauke ni……. Koda nayi sallar asubahi ban koma ba kicin na shiga na shirya mana abin kari wanka nayi na shirya tsaf na nufi dakinsa.

Bugu guda nayi yazo ya bude ya shirya tsaf sai kamshi yake da kwarjini da kamala a tare dashi….babu cikakkiyar walwala muka gaisa daga ni harshi….Nace.”Amma zaka karya kafin ka fita ko.”? Yana duba agogon dake daure a hannunsa yace.”Ina da muhimin uzuri amma muje ki hada min abin karin.

Juyawa nayi ba tare da nace komai ba ya biyo bayana.

Tea na had’a masa yace kada kisa min madara Nascafe ya isa.” Nace.”Tom tsaf na hada masa duk abinda yake bukata na tura gabansa.

Yana break din yana amsa waya jamaa sai kiransa suke ni abin har mamaki yake bani. kallonsa nayi nace.”Dan Allah ka ajiye wayar nan ka karya a nutse kada ka kware kayi wa kanka uziri mana.

Ajiye wayar yayi yana murmushi yace.”Na ajiye gimbiya.” Shuru kawai nai ina kallonsa wayar nata ringing yaki dauka a nutse nace.”Ina so ka bar ni naje gurin Gwaggo mu gaisa.”

Jim yayi kafin yace.”Okey ai naga a shirye kike ko.”?

Nace.”Eh a shirye nake.” Yace.”Okey tom jeki dauko mayafi sai na ajiye ki idan na dawo da yamma sai na shigo na dauke ki amma kuma ko zaki fara zuwa can hotoro ku gaisa dasu.”

Nace.”Aa so nake na ware rana kowa ne gida naje musu na yini.” Yace.”Okey hakan yayi.” Mikewa yayi hade da daukar key da wayoyinsa na mike da sauri na nufi dakina domin dauko mayafi.

Bakin kofar gidan yayi parking ya kalle ni da fadin.”Idan nazo daukar ki zamu gaisa da Gwaggon.” Nace.”Tom shikkenan Allah ya tsare ya bada sa’a.” Ya amsa da ameeen.”

Kokarin bude motar nake ya juyo da fuskata ga mamakina sai kawai baga ya dora bakinsa a kan nawa ya manna min kiss akan labbana. tsigar jikina ta tashi ido na tsira masa ina kallonsa yace.”Ki kara hakuri kinji ko insha Allah Allah zai mana magani.

Wani irin tausayinsa ya rufe ni nace.”Babu komai Yaya Aminu Allah ya baka lafiya.” Yana kokarin kunna motar ya amsa da ameeeen matata nagode.”

Ajiyar zuciya na sauke bayan wuce warsa daga gurin na tsallaka a nutse nufin gidan.

Yana zaune a bakin rijiya da wando 3qutar a jikinsa ko arzikin vest babu a jikinsa, koda nayi arba da faffad’an kirjinsa mai cike da yalwar gashi sai naji duk rashin kuzari a jikina, cikin sark’ewar murya nai sallama, yayi gaggawar dago kansa muka had’a ido, kauda kaina nayi da sauri gabana na wani irin faduwa….Babu yabo babu fallasa ya amsa da fadin.”Sannu Gimbiya.” da sauri na kalleshi Yaya Aminu ya kira ni da Gimbiya shima ya kira ni da Gimbiya shin me hakan yake nufi……Muryar Gwaggo ce ta katse min tunani….”Wannan kamshin turaran daga ina yake fitowa.” Da sauri na juya muka hada ido da ita a lokacin da take kokarin fitowa daga dakinta.

Ganina a tsaye yasa tace.”Haba koda naji ashe matar manya ce Sa’ida ke kike tafe da sanyin safiyar nan.”? Ajiyar zuciya na sauke na karasa cikin gidan sosai ina fadin.”Gwaggo nice nazo gaishe ki ko bakya maraba da zuwa na.”

Tana kokarin gyara tabarma tace.”Wace ni ai zuwanki alkairi ne dama jiya sai da nayi mafarkin ki ina cewa zanzo har gidanki na dubaki.”

Murmushi nayi nace.”Gwaggo ki dauke tabarmar mu shiga daki.” Na fadi hakane sabida bana so na zauna a tsakar gidan sabida shi

Tace.”Ai dakin ne da zafi kin san fuskar rana ce duk da kasancewa yanzu gari ya waye amma zafi a dakin shiyasa nayi shimfida a waje to amma tunda kin fiso mu shiga dakin to sai mu shiga.”

Takalma na na cire na daga labulan dakin na shiga na zauna gefan gadonta ita kuma ta biyo baya na hannunta rike da redion ta.

Zama tayi kan shimfid’arta cike da kulawa tace.”Ina fata dai lafiya Sa’ida wannan zuwan naki na sassafiya yasa nasha jinin jikina.

Murmushi nayi a nutse nace.”Gwaggo lafiya sumul kawai nazo gaisheki ne.” Cike da jin dadi tace.”To har naji dadi a raina da kika ce haka me kike so na girka miki wanda zaki ci.”

Cike da mamaki nace.”Gwaggo daga zuwa kuma sai maganar abinci.” Tace.”Eh ai gwara ki za’bi abinda kike so sai nasa almajiri yayi cefane.

Nace.”To shikkenan kiyi min danwanke.” Tace.”Keda bakya cin danwake kuma yau shi kike sha’awa ko dai an samu karuwa ne.”?

Girgiza kaina nayi ina gyara yanayin fuskata nace.”Aa gwaggo ba’a samu ba kawai dai ina sha’awarsa ne.”

Tace.”To Allah ya kawo mai albarka Danwaken da miyar taushe kike so ko kuma da man gyda da yaji.”?

Nace.”Gwaggo kiyi min me miyar taushe amma miyar manja.'” Tace.”Tom shikkenan bari naje da kaina nayo cefane.” Nace.”Gwaggo ashe har yanzu kina zuwa yawon cefane baki daina ba.

Tana kokarin yafa mayafinta tace.”To Sa’ida da raina da lafiya ta mai zai gagare ni ai duk sanda Rabi ta ‘bata min rai yafa mayafi nake naje nayi cefane na na dafa duk abinda nake so daga nau’in abincin da kike aiko min dashi.

Nace.”Haba shiyasa naga kinyi shar dake kinyi ki’ba.” Dariya tasa tana kallona tace.”Eh haka Uwale ke fad’a wai nayi k’iba.”

Gyara fuskata nayi nace.”Gwaggo ashe har yanzu kina tare da Uwale baki rabu da ita ba.

Taja ta tsaya tana kallona ido da ido tace.”Eh ina tare da ita muddun rai jiya ma anan ta wuni muna hira sannan duk alkairin da kike aiko min dashi biyu nake rabawa na dauki daya ta dauki daya.”

Mamaki kawai yasa na bita da kallo gabadaya na garara magana.

Takalmanta na danqo tasa a kafarta ta kama hanyar fita tana surutai ni dai bin ta kawai nayi da kallo ina mamakin al’amarinta sai kace ciki guda suka fito da Uwale taki rabuwa da ita.

Maganarta naji ta dawo gidan ta shigo tana fad’in “Kinga Jarumi ma ya huttashe ni yace na dawo gida zai siyo min kayan miyan.”

Nace.”To babu laifi hakan. shigowa dakin tayi tana fadin.”Kinga kuma sai bayan ya tafi na manta bance masa ya siyo d’anyan naman da za’a sa a miyar ba.”

Nace.”Gwaggo ko ba’a sa naman miya ba babu laifi ai Allah ya hore miki iya girki nasan miyar za tayi dadi ko babu maggi.”

Dariya ta kyalkyale da ita tana kallona tace.”Yo dama yaushe zaki had’a mutanan da dana yanzu ai dama iya girki sai mutumin da na yanzu sam babu abinda suka iya sai fele’ke da iyayi.”

Nace.”Hakane kam amma gaskiya Gwaggo ni bani da matsala na dauki darasi a gurinki.”

Redio ta dauka tana murd’awa tace”Aikuwa kin taimaki kanki.”

Dakin ne yayi shuru ina duba waya ta ita kuma tana aikin murda redio kamar yanda ta saba…..Dagowa nayi na kalleta ina dawurwura akan maganar dake bakina.

“Gwaggo wata muhimmiyar magana nake so na fada miki amma don Allah ki fahimce ni bana so ki d’aga min murya har makota suji sirri na.”

Redion hannunta ta ajiye cikin kulawa ta kalle ni da fadin.”Haba ai dama nasan akwai wani abu da kike tafe dashi tabbas jikina sai da ya bani hakan to ina sauraranki.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Gwaggo baki yi k’arya ba dalilin daya kawo ni gidan nan mai karfi ne.” tayi shuru tana kallona, Nace.”Gwaggo ina cikin matsala a gidan aure na babu kwanciyar hankali domin kuwa bana samun biyan bukatata ta aure shine nace bari nazo na sheda miki halin da ake ciki ko zaki taimaka tunda kina da ‘yan uwa wanda suke ‘kauye watakila zasu taimaka mana da magani.”

Tace.”Sa’ida magana kike a rufe nifa bangane maganarki ba, bakya samun biyan bukata ta aure shin bukata wace iri.”?

Sunkuyar da kaina kasa nayi nace.”Gwaggo Yaya Aminu bashi da lafiyar gaba yana fama da rashin karfi da kuzari baya iya ta’buka komai tsayin wata daya da satika wata mu’amula ta aure bata ta’ba shiga tsakanina dashi ba, shine nace ko zaki taimaka min da neman magani.

Ido kawai ta zuba min tana kallona fuskarta gabadaya ta nuna alamun bacin rai.

“Yanzu dama Aminun bashi da lafiya amma akayi rufa-rufa aka daura miki aure dashi? shin wannan wane irin zalinci ne? wato dan an ganki marainiya sai a zalince ki yanzu ina amfanin aure babu wannan mu’amula ai aure bai cika ba saboda haka wannan auran sam bashi da amfani.”
Cikin d’aga murya take maganar….Fuska na ‘bata nace.”Gwaggo tun kafin fa na fada miki matsalata sai da na fada miki abinda bana so me zai sanya ki dinga daga murya ba zaki tsaya ki fahimce ni ba.”

Hannu ta daga min a fusace! Tace.”Kinga Sa’ida mutukar akan wannan matsalar ce ba zan tsaya na saurare ki ba wannan ai cuta ce da zalinci to bari Ibarahim din yazo yanda sukayi qula-qular su suka daura auran to sai sun warwareshi mutukar ina numfashi.

Kuka nasa ina kallonta nace.”Kashe min aure zakiyi akan wannan matsalar.”? Tace.”To meye amfaninsa tunda babu biyan bukata.” Nace.”To ai bake kike zaune da mara lafiyar ba nice kuma ni banzo nan domin ki kashe min aure ba taimakona nazo kiyi amma kina nema ki sanja magana.

Tana kokarin magana ya daga labulan dakin hannunsa rike da ledoji da kayan miya masu yawa.

Ganin yanayin da muke ciki yasa ya sha jinin jikinsa a nutse yace.”Aunt Sa’ida Allah dai yasa bake kika sata ‘bacin rai ba.”

Kauda kaina nayi daga barin kallonsa nace.”Ni babu ruwana Khalid kamar ka mance halinta na saurin fusata.”

Ya kalleta da fadin”Gwaggo ga cefanan kayan miyan nayi miki.” Tace.”To Jarumi nagode wallahi sai na manta bance ka siyo nama ba.

Yace.”Kada ki damu na siyo gashinan a ledar sa daban.” Tace.”Allah ya kara bud’a maka Jarumi Allah yasa ka zama zakaran gwajin dafi akan dukkanin harkokinka.” Ya amsa da ameeen Gwaggo.”

Kallona yayi da fadin.”Aunty Sa’ida gobe idan Allah ya kaimu zan koma legos bayan sati biyu kuma zamu tafi kasar america da ‘Yan uwana inaso kiyi min addua.

A nutse nace.”Khalid Allah yasa kaje lafiya ka kuma dawo lafiya Allah ya baka nasara a rayuwarka.” Ya amsa da ameeen Ya Allah auntyna.” labulan dakin ya saki ya bar bakin kofar.
Ta juyo da hankalinta kaina da fadin.”To tunda kince zan kashe miki aure me kike so ayi yanzu.”?

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min_*

_Na lura dai idan ban cigaba da littafin nan ba za’a samu masu zuwa inda nake😃 nayi magana ya kai sau nawa wasu sun kasa fahimta wasu ma gani suke ‘karya nake to na samu gilashi tunda naci kud’i ai dole a hanani nutsuwa Allah ya bamu rai da lafiya nagode sosai da k’auna da kuma kyawawan adduoinku zamu cigaba da littafi da yardar mai duka🥰_

*79&80*
Ajiyar zuciya na sauke cikin tararrabi nace.”Gwaggo kije can k’auye ki samo wa Yaya Aminu magani shine manufar zuwana gurinki.” Kauda kanta tayi tace.”Sa’ida meye nawa a cikin wannan sha’ani haka kawai zan dauki kafa na tafi k’auye samo wa mijinki maganin ka’rfin maza ai dama hausawa suna cewa duk wanda ya sayi rariya yasan zata zubda ruwa ai GA IRINTA NAN garin son zuciyarki da kwad’ayin ki kin guji d’an uwanki yaro mai jini a jika kin auri mara lafiya saboda haka idan kin damu kuma kina so ki cigaba da zama da mijinki sai ki wanke k’afarki ki tafi k’auyen da kanki ki nemo masa maganin karfi ni kam babu inda zani.” Ta kare maganar tana kokarin mikewa, kallo kawai na bita dashi zuciyata na wani irin tafarfasa kafin na ankara hawaye masu mugun zafi sun kufce min, maganganunta na dinga ji kasa- kasa a tsakar gidan “Haka kawai za’a sani zuwa k’auye akan wane dalili? ba zanje ba to kaji.”!! Murya na rawa nace.” Wato Gwaggo ke baki da sirri ko kin fita kina surutai a tsakar gida kina so ki fallasa sirrina ko.”?

“Oh o! ni ba nufi na kenan ba Sa’ida maganar dai nake jajantawa.” Cikin kuka nace.”Ni dai maganar ta isa haka tunda dai ba zaki taimaka min ba sai kija bakin ki kiyi shuru.”

‘Kasa-‘kasa tace.”Eh ba zan taimaka ba kije da kanki ki nemawa mijinki magani ehe.” Khalid ne ya shigo gidan a lokacin da take maganar, Yace.”Surutan me kike ke kadai ina aunty Sa’idan.”?

“Tana daki surutai kuwa dole nayi domin kamawa tayi.” Ganin yanda ta fadi maganar da bacin rai yasa yace.”Me ya faru gwaggo dan Allah ki dinga samawa kanki lafiya.”

Tana wanke kayan miya tace.”Khalid al’amarin ne ai da bakin ciki wallahi shiyasa na kasa hakuri.”

Yace.”To koma dai menene sai ki barwa Allah kiyi addua akan Al’amarin.”

“Oh!o ni babu wata addua da zanyi ai ita ta janyowa kanta.” Shuru yayi yana kallonta ta bude baki zata cigaba da magana na fito daga dakin ido jajur nace.” Gwaggo idan kika fada masa sirri na zanyi miki Allah ya isa.”

Gabadaya ita dashi suka juyo suna kallona. baki ta ri’ke tace.”Sa’ida ni zaki wa Allah ya isa.”?

Kafin nayi magana ya magantu cikin bacin rai yace.”Wai aunty Sa’ida me yake faruwa ne da har kike wannan maganar Ni bare ne da har kike gudun naji sirrin ki.”

Share shi nayi na nufi hanyar fita raina a masifar ‘bace! hanya ya tare yana watsa min wani irin kallo yace.”Ba zaki tsaya ki huta ba zaki tafi gashinan Gwaggo na kokarin dora miki girki.

Murya na rawa nace.”Khalid bani hanya na wuce na tafi.” Girgiza min kai yayi yace.”Ba zaki tafi ba sai naji Abinda yake damunki.”

“Khalid ko kaji babu abinda zaka iya yi min.” Karaf Gwaggo tace.”Aikuwa shi yake da abinyi.” Kallonta nayi raina a ‘bace nace.”Me kike nufi.”? kanta ta sunkuyar ta cigaba da abinda take.

Tsaki naja k’asa-kasa na juya da niyar fita, da sauri ya tare ni da gangar jikinsa saurin janyewa nayi tsigar jikina na tashi wani irin kallo nai masa “Bani hanya na wuce.” Kansa ya girgiza min babu walwala a tare dashi ya rike hannu na.

Gabadaya jikina ya mutu ya jani muka zauna kan tabarma…..shuru na minti biyar Yace.”Gwaggo fada min matsalar auntyna ko ina da magani.

Tace.”Bari naje na kai markade na dawo tukkuna.” Mikewa yayi ya kar’bi kayan miyan da fadin.”Bari na samu yaro a waje na bashi ya kai miki.”

Tace.”To yawwa hakan yayi.” da sauri ya fita ita kuma ta dauki tukunyar nama tana wankewa……”Gwaggo kada ki fadawa yaron nan abinda ya shafe ni kinga bai kamata ba.

Shuru tayi min ta cigaba da aikace aikacen ta…..Murya na rawa nace “Gwaggo kina jina ko.”

“Sa’ida shin baki ji abinda ya fada ba? yace watakila yana da taimakon da zaiyi miki babu laifi idan yaji matsalarki.”

“Ni dai na fada miki kada ki fada mas……shigowarsa gidan ta katse maganata ya zauna kusa dani da fadin.” Gwaggo ina sauraranki.

Kallonsa tayi tace.”Khalid Sa’ida tazo akan na taimaka mata naje k’auye na samowa mijinta maganin ‘karfin maza wai bashi da lafiya.”

Sunkuyar da kaina kasa nayi kaina sai sarawa yake nayi da nasanin zuwana gurin Gwaggo da wannan maganar……….Cikin wata kasalalliyar murya yace.”Aunty ne hakane maganar Gwaggo.”?

Kasa dago kai nayi na kalleshi ballantana na bashi amsa kunyar duniya ta ishe ni.

Murmushi yayi wanda ya tsaya iya le’bansa yace.”Auntyna ya haka ta faru kuma ashe kallon kitse ki kai wa rogo shin ya sunan wannan auran naki tunda babu biyan bukata ta aure.”?

Jarumta da dauriya na aro na dago kaina tare da ‘bata fuska nace. “Kaga Khalid wannan magana bata shafeka ba ba naso na sake jin kayi wata magana akai.”

Hannu ya tusa a tarin sumar kanshi yana wani irin murmushi kasa kasa yace.”Magana ta shafe ni tunda har ta shafe ki ko kin manta abinda yayi Khalid shi yayi Sa’ida.”?

Shuru nayi masa tare da dauke kaina.

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Kin san me.”? shuru nai masa yace.” Kina jina ko.”? ba tare da na kalleshi ba nace.”Kunne ne ke ji.”

“Okey inaso kiyi min bayanin yanayin mijin naki akwai wani mai maganin hausa a Lego’s da zan had’a ku dashi.

Da sauri na dago kaina ina kallonsa…..da murmushi a fuskarsa ya daga min gira domin so ya tabbatar min da maganarsa…….. Kaina na sunkuyar kasa Nace.” Ina ganin ba sai kaji wani abu ba kawai ka bani number mai maganin.”

Girgiza kansa yayi idonsa kuri a kaina yace.”Bashi da waya mai maganin abinda yasa kuma kikaga nayi magana wani abokinmu da yake fama da rashin lafiya irin ta mijinki ya samu lafiya dalilin zuwa gurin mai maganin.

Shuru nayi ina nazari yace.”Ko dai baki yarda dani ba aunty Sa’ida ni yanzu babu wani abu da yayi saura a tsakaninmu sai zumunci ina tausaya miki rayuwar aure babu biyan bukata.”

Zuciyata ce naji ta karye nace.”Khalid ya zanyi kaddara ce a haka.” cikin sigar bugun ciki yace.”Kina nufin wancan alhajin ma haka yake bai da lafiya.

Kamar wata shashasha na d’aga masa kaina a raunane nace.”To gwanda shi akan Yaya Aminun amma duk tafiyarsu daya.

Khalid ya danne ‘bacin ransa yace”Okey shi Alhaji Nuran kina gamsuwa dashi kenan.”? Ba tare dana kalleshi ba nace.”Babu laifi.”

Shuru yayi yana yaqi da zuciyarsa…….”Yanzu kin yarda dani zaki min baya nin matsalar mijinki ko kuwa.”?

“Khalid idan zaka taimaka mana zan fada maka.” yayi mata wani irin kallo da fadin.” Zan taimaka muku saboda haka ke nake sauraro meye matsalarsa.”?

“Bashi da lafiya gabadaya tunda mukayi aure bai ta’ba biya min bukatata ba.” shuru yayi na minti biyu da ‘kyar yace.”Kina nufin gabanshi baya tashi kome? ko kuma sha’awa ne baya yi.”?

Shuru nayi kunya ta hanani magana….Yace.”Aunty Sa’ida ke nake saurare.” Da kyar nace.”Khalid Yaya Aminu abun yayi masa yawa baya sha’awa sannan kuma gabanshi ‘karami ne irin na yara baya mi’kewa.”

Sunkuyar da kansa yayi yana ‘boye dariyar dake kokarin kufce masa amma inaa sai da ta su’bce ta futo fili ya dinga yi yana kallona ni kuwa kamar shashasha na dinga kallonsa gabana na wani irin faduwa.

Gwaggo ta fito daga kicin hannunta ri’ke da ludayi tace”Jarumi wannan wace irin dariya ce haka.”?

Da kyar ya gimtse dariyar yace.”Gwaggo je ki cigaba da aikin ki.” kicin din ta koma tana fadin.”To Allah ya kyauta dai.

“Juyowa yayi yana kallona da murmushi a fuskarsa, rai a ‘bace nace.” Ashe baka da mutunci ko ? ka mayar dani sakarai na fada maka sirri na kana dariya.”

Fuskarsa ya gyara yace.”Auntyna naso na gimtse dariyar amma sai da fita okey mu bar wannan maganar muyi mai amfani ko.”

Tsaki naja tare da kauda kaina gefe…..Yace.”Ki kwantar da hankalin ki insha Allah idan na isa Lego’s zan samu me maganin mu tattauna dashi mybe ma idan zan sake zuwa nazo muku da magani Allah yasa a dace amin.”

Shuru nai masa ban tanka masa ba ya karaci surutan sa ya mike cike da wani irin nishadi ya kama hanya ya fita daga gidan domin sallama da abokanansa.

Gwaggo aikace aikacen ta kawai takeyi taki cewa dani komai haushin hakan yasa na mike ina gyara mayafi na sai Uwale ta rangwada sallama a gidan, ganina ya sanya ta washe baki da fadin.”Aa amarya ce a gidan.” Gwaggo ta fito daga kicin da fadin.”Aikuwa dai Uwale kece da hantsi.”

Tana kokarin zama kan tabarma tace.”Wallahi kuwa ai ‘kauyen daburau zan tafi yanzu kwana biyu basir ne ya tayarwa Ayuba shine zanje na samo masa magani acan.

Gwaggo tace.”Aikuwa gwanda da kika shigo domin dama koda baki shigo ba nayi niyyar zuwa gidanki da wata magana.”

“Gwaggo ni zan tafi.”? Kallona tayi da fadin.” Aa ki koma ki zauna mana tunda neman taimako kika zo ga Uwale zataje kauyen daburau sai ki bata sautu.”

Ji nayi kamar na kwada mata mari saboda takaici da bakin cikin abinda take takalmana nake kokarin sanyawa sai kawai ta fashe da kuka da fadin.”Wannan yarinya kina nema ki sanya zuciyata ta buga ko wato ba zaki ji maganata ba zaki tafi wacan uban abincin waye zai ci.”

Uwale ta sassauta fuska da fadin.”Haba Sa’ida kada ki tafi mana ki zauna mu tattauna magana naji matsalarki.”

Ajiyar zuciya na sauke na cire takalmi na na zauna tare da fadin.”Ni ba zakiji komai daga bakina ba ita data fara fada miki maganar ta karasa fada miki.”

Uwale ta kalleta da fadin.”Gwaggo me yake faruwa ne.”? Da saurin gaske ta shiga fada mata abunda yake faruwa

Uwale tayi murmushi tare da fadin.”Yo ai Sa’ida wannan matsalar ba sabuwa bace mu da muke yawo gidajen masu magani mu muke ganin abubuwa wannan matsalar itace ke damun wasu mazan kuma idan anyi katari da magani mai kyau sai kiga an dace saboda haka ki kwantar da hankalinki yanzu ki bada sadaka sai nayi sauri na tashi na tafi insha Allahu kafin la’asar na dawo.

Shuru nayi ina nazarin maganarta…..Gwaggo ta fusata! da fadin.”Ke duk wanda zai taimaka miki sai kin zarge shi ki saki zuciyarki ki bada sadakar magani tunda dai ke kikaji kika gani sai ki daura d’amarar neman magani.”

“Uwale dan Allah kada naji maganar nan a wani guri.” hankalina a kanta nayi maganar .

Gabad’ayansu suka rike baki Uwale cikin jin haushi tace”Sa’ida munaf*cka kika mayar dani kome.”?

Da sauri nace”Aa ni ba haka nake nufi ba halinki na sani idan labari yayi miki dadi sai ki manta ki fadi abinda bai kamata kowa yaji ba.”

Cikin takaici Gwaggo tace.”Uwale tashi kiyi tafiyarki ina dalilin wannan abu yarinya ta dinga kokarin cin fuskarki a banza a wofi.”

Da sauri nace.”Gwaggo kinga don Allah ki tsame kanki daga cikin maganar nan tunda dai ke kinqi taimakawa ai sai kija bakin ki kiyi shuru ki kyale wanda zasuyi.

Tsaki taja ta bar gurin.

Handbag d’ina na bude na dauko kudi dubu dubu guda biyar na bata da fadin “Uwale ga sadaka Allah ubangiji yasa a dace.” Hannu tasa ta ‘karba da fadin.”ameeen ameeen.” Na mika mata dubu daya da fadin.”Ga wannan sai ki kara kudin mota.” tasa hannu ta kar’ba da fadin.”To nagode a na tashi na tafi kada naje na samu layi a gurin.”

Nace.”To shikkenan Allah yasa a dace.”Takalmanta tasa tana amsawa ta leqa kicin a gurguje tayi sallama da Gwaggo ta fita daga gidan.

Mikewa nayi jiki a sanyaye naje na kwanta gadon gwaggo ina tunanin wautar dana tafka sai yanzu da na zauna nayi tunani da nazari na gane manufar Khalid wato ya bugi cikina yaji dukkanin sirri na yana min dariya idan banda tsabar iskanci a ina zai samo maganin da yake magana gabadaya kaina ya daure tunani na ya ta’allaqa gurin ganin na samu mafita akan abinda yake damuna shiyasa na saki jikina dashi na fada masa abinda ke damuna dariyar da yake itace ta tabbatar min da cewa kawai tsabar iskanci ne babu wani taimako da zaiyi mana.

Kwanciya na gyara a kan gadon ina addua akan Allah yasa dai a dace da magani idan hakan ta faru itama Uwale dole a samu kyauta ta mussaman ayi mata mutukar ta kasance wacce tayi sanadiyar samuwar abinda muke bukata.

Motsin shigowarta naji dakin nayi saurin rufe idona “Sa’ida kinyi bacci ne.”? Shuru nayi mata sai naji tana cewa” Allah sarki watakila tayi bacci oh! ko wane bawa dai da irin jarrabawarsa a rayuwa.” Fita tayi daga dakin na bude idona ina kallon bakin kofar da tunanin maganarta ashe tasan kaddara ce amma idan rigimar ta tashi sai ta mayar da laifin kaina.

Jin ana kiran sallah yasa na sauko daga gadon fita nayi domin daura alwala lokacin har ta kammala aikinta tana kashe wuta.

Kallonta banyi ba na shiga bandaki na fito ina daura alwala tace.”Ai na shiga dakin naga kina bacci.”

“Umm.” abinda nace kenan na cigaba da abinda nake tace.”Idan kinyi sallar ai sai kici abinci ko gashinan na kammala.” Ina kokarin mikewa nace.”Nifa Gwaggo ba cin abinci ne ya kawo ni gidan nan ba zaman da kika ga nayi ina jiran Uwale ta dawo na kar’bi magani nayi tafiyata.” Ina gama maganata na bar gurin ba tare dana saurari abinda za tace ba.

Ina zaune akan dadduma ta shigo dakin, na kauda da kaina da fadin.”Gwaggo na tashi a hannunki nayi wayo a hannunki kiyi min aure amma ace ba zaki rufe sirri na ba shin wannan wace irin rayuwa ce Shikkenan tunda abin naki ya zama haka dukkanin matsala ta zan dinga tunkarar mahaifiyata da ita nasan tunda ita ta haife ni zata rufa min asiri kuma ta taimake ni.”

Uffan ba tace dani ba ta hau kan dadduma ta tayar da sallah, koda ta idar da sallar sai da taja carbi kafin ta ajiye ta mike ta fita.

Kwanonin abincin ta shigo dasu dakin ta ajiye daidai lokacin Ya shigo dakin ya tsaya daga bakin kofa da fadin.”Gwaggo Ummatu bata dawo bane.”?

Tace.”Khalid yaushe Rabi zata dawo gidan nan ka manta ‘Yar gidan yayarta ce ta haihu ko bata fada maka ba.”?

Kansa ya sosa yace.”Wallahi ranar da akayi haihuwar ma ta fada min na manta ne gabad’aya okey ina tsammanin yanzu idan naci abinci zanje can Dalan nayi sallama dasu.”

Tace.”To hakan yayi daidai sai ka shigo kaci abincin.” Yace.”Bari tukkuna na watsa ruwa zafi akeyi wallahi.” Tace.”Ai dama kai ko babu zafi a gari baka gajiya da kuzawa kanka ruwa.

Dariya kawai yayi ya bar gurin.

Kallona tayi da fadin.”Sa’ida kin gama cin mutuncin.”? A hasale nace.”Gwaggo wane irin cin mutumci gaskiya ce na fada miki tunda dai kin kasa rufa min asiri zan koma gurin uwar data haife ni.”

Kuka ta fashe dashi tana nuna kirjinta tace.”Ni kike fadawa wannan maganar.”? dauke kaina nayi na ‘bata rai sosai! ta cigaba da share hawaye tana fadin.”Ai shikkenan tunda fahimtar da kikayi min kenan babu komai akwai Allah.”

“Gwaggo laifin me nayi miki da zaki had’a ni da Allah nifa wallahi Uwale nake jira ta dawo na bar muku gidanku.”!

Baki ta rike tana kallona a tsorace! nace.” Eh ba zan zauna a gidan da ake nuna min wariya ba a zahiri kina nunawa kin fi son Khalid dani.”

Hawaye ta share ta saisaita kanta a nutse tace.”Sa’ida maganar nan ta wuce kada kisa jinina ya hau dake da Khalid duk daya kuke a gurina saboda haka kiyi hakuri ki daina wannan maganar dazu ma raina ne ya ‘baci shiyasa kikaji ina surutai amma tunda bakya so na daina Allah yasa a dace da magani mai kyau.”

Uffan bance mata ba ta cigaba da maganganunta nace.”Gwaggo bafa zanci abincin nan ba ki daina wani damuwa a koshe nake.”

Ta dinga kallona tana girgiza kanta dauke kaina nayi dan ko kadan bata bani tausayi ba saboda halinta.

Shigowa yayi ya ganta cikin damuwa…..”Gwaggo menene naga kamar kinyi kuka idonki yayi jawur.”
Kallonsa nayi na ganshi daga shi sai short Neckar ko arzikin singlet babu a jikinsa, gabadaya hankalina ya tashi na sunkuyar da kaina kasa gabana na bugawa.

Dakin ya shigo sosai ya zauna kusa dani ina jin kamshin sabulun da yayi wanka wani masifaffen feeling’s ya dinga taso min.

“Aunty Sa’ida me ya faru.”? ba tare dana kalleshi ba nace.” Gaka gata ka tambaye ta mana.” Murmushi yayi yace.”Gwaggo menene.”?

Ajiyar zuciya ta sauke tace.”Khalid wai ba za taci abincin nan ba shine nake mamaki.” Ya kalle ni da fadin.”Akan wane dalili.”? Tsaki naja na mike na fita na bar musu dakin. ita dashi gabadaya suka bini da kallo.

Tsakar gida na zauna ina duba waya ta ina jinsu suna magana ‘kasa-‘kasa sam bai dame ni ba babban burina naji sallamar Uwale da magani a hannunta.

To sai daf da magariba Uwale ta dawo a jigace hannunta rike da wani katon buhu cike da itacen magani da saiwowi.

Gwaggo ta gyara mata tabarma tana mata sannu…..Tace.”Gwaggo bani ruwa nasha yau nasha bakar wuya kafin na samu ganin mai daburau.”

Gwaggo da sauri ta mike ta ciko kofi da ruwan randa ta bata tasha sosai ta ajiye kofin tana sauke numfashi…..Sai da hankalinta ya dawo tukkuna nayi mata sannu ta amsa da yawwa Sa’ida ai tafiya tayi kyau sosai tunda anyi dace an samo magani gashinan cikun buhu.

Nace.”To Alhamdulillahi Nagode sosai sai kiyi min bayanin maganin.” Tana kwance buhun tace.”Ai dama yanzu zanyi miki bayanin yanda zakuyi amfani dashi.”

Tsaf ta zazzage itacen maganin da wasu gari a daure a leda da saiwa ta shiga yi min bayani nace.”To insha Allahu zanyi kokarin bin ka’ida. Tace.”Kuma mai maganin yace.”Bayan sati biyu a koma masa da bayanin yanda mara lafiyar yaji a jikinsa.” Nace.”To shikkenan Uwale insha Allah zanzo har gidanki da bayanin.” Ta shiga mayar da maganin cikin buhu tana cigaba da magana da ‘kawar ta.

Gwaggo ta mike da fadin.”Bari na kawo miki abinci nasan dai kinsha yunwa acan.” Tace.”Aikuwa dai dama kin san babu masu siyar da abinci da kyar na samu mai awara na siya na toshe wata kafar.”

Tace.”Ai dama dubara akeyi idan mutum zashi irin wannan guri sai yayi abincinsa ya zuba a fulas ya tafi dashi maganin yunwa.” Tace.”Wallahi kuwa ai na dauka ba zan dade ba shiyasa ban tafi da abinci ba sai kuma naje na tarar da layi jamaa kowa lalura ta ishe shi.”
Gwaggo dake kicin tace.”Ai fa abinda ake ta fama dashi kenan Ubangiji Allah yayi mana magani.” Gabadaya muka amsa da ”Ameeen Ya Allah.”
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*81&82*
Gwaggo abinci mai yawa ta had’awa Uwale tasa mata miya da nama sosai ta ajiye mata a gabanta ta dauki kofin silban gabanta ta debo mata ruwa a randa ta ajiye mata tare da zama kusa da ita. Uwale tace.”Sannu da aiki Gwaggo nagode sosai da hidima.” Gwaggo tace.”Haba Uwale ai babu komai an riga an zama d’aya muma mun gode sosai da taimakon ki muna rokon Allah yasa kwaliya ta biya kudin sabulu.” Uwale na kokarin kai lomar abinci bakinta tace.”Insha Allahu za’a dace domin mutane da yawa sun sheda kyawun maganin mai daburau shiyasa jama’a keta rububin zuwa gurinsa kar’bar magani.”

Gwaggo tana kokarin magana Ummatu ta shigo gidan kafafunta fururu! gabadaya muka bita da kallo gani na a zaune yasa ta washe baki da fadin.”Aa ashe amarya ce a gidan.”? babu yabo babu fallasa na gaisheta ina satar kallon jikinta. ta kalli su gwaggo da fadin.”Sannunku da gida.” Uwale ce kawai ta amsa Gwaggo a dakile tace.”Yanzu Rabi ki fita tun farar safiya sai ana kiran magariba zaki dawo.”? Shan kunu tayi da fadin.”Gwaggo kafin na fita sai da na sheda miki cewa Hamara’u ce ta haihu ‘yar dan uwana kuma mune iyaye dole muje da wurwuri muyi mata ayyuka.” Gwaggo tace.”Wane ayyuka Rabi ke dai kin biya yawon da kika saba dubi kafafunki.”? Ummatu tabi kafafunta da kallo na minti biyu girgiza kanta tayi ta bar gurin…….aikuwa suka dasa gulmarta ita da Uwale sai magana suke kasa – kasa nace.”Kuna dai rage mata zunubi duk inda taje ita da Allah ku dai babu ruwanku da wannan surutan da kuke gwara ku tashi kuyi alwala dan lokacin sallah yayi.

Uwale tana kokarin mikewa take fadin.”Gaskiyarki Sa’ida Allah dai ya yafe mana amma a zahirin gaskiya abinda Rabi takeyi a gidan nan dole ne a taka mata burki.”

Shuru nayi ban tanka ba suka mike tare da daukar butoci domin daura alwala.

Uwale sai da tayi sallar isha’i tukkuna ta tayi mana sallama ta tafi bayan ta sake jadadda min yanda za’ayi amfani da maganin data kar’bo.

Karfe takwas da rabi Yaya Aminu ya kira waya ta yace mani gashinan a waje na fito domin nayi masa jagora cikin gidan.

Na kalleta tana fama da redio a hannunta nace.”Gwaggo Yaya Aminu yazo yana so ya shigo ku gaisa.” Redion ta ajiye da fadin.”To ai babu komai ya shigo mana.” Mikewa nayi domin naje na shigo dashi.

Ina kokarin fita Kawu ya shigo zubewa nayi gwiwa a kasa ina gaisheshi cike da kulawa ya amsa yana ta farin ciki yace.”Sa’ida ashe anan kika yini yanzu yanzu mijin naki yake sheda min.”

Nace.”Eh wallahi Kawu tun safe ina nan yace nazo na gaishe ku lokacin kuma da nazo kai ka fita dama inata addua Allah yasa kafin na tafi ka dawo mu gaisa.”

Yace.”Aikuwa ya kyauta sosai kuma naji dadin ganinku keda mijinki kicin koshin lafiya ina rokon Allah ya dawwamar miki da zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan auranki.”

A sanyaye na amsa da ameeen ya Allah Kawu.” Yace.”Kiyi maza kije ki shigo dashi yace yana so ya gaisa da Gwaggo.” Nace.”To Kawu.” Hanya ya bani na wuce shi kuma ya karasa bakin kofar dakin mahaifiyarsa.

Gwaggo cikin girma da mutunci suka gaisa da Yaya Aminu kamar ba itace mai zagin sa da ganin aibun sa ba sai wasa take masa tana masa adduar fatan alkairi. Yaya Aminu da yake mutum ne mai saurin sabo ya saki jikinsa sosai suka dinga hira har ta zuba masa abinci ya zage ciki yana ci harda cire hula ita kuwa sai tsokanarsa take wai kada dai garin santi ya manta hularsa….Cikin wannan halin Khalid ya daga labulan dakin, ganin mu cikin raha da annushuwa yasa ya kirne fuskarsa kamar baya so ya miqa masa hannu da fadin”Barka da dare Alhaji.” Yaya Aminu da sauri ya amsa da “Barka dai abokina ya kake ya al’amura.”
Babu wani sakewa ya amsa da “Alhamdulillahi.” Labulan dakin ya saki zai bar gurin Gwaggo da sauri tace.”Jarumi ka shigo kaci abinci mana.” Yana kokarin barin gurin yace.”Sai an jima yanzu inada uziri.” Gwaggo kasa’ke tayi tana tunani yanayin yanda yayi maganar a cunkushe ya nuna mata lallai akwai abinda yake damunsa.

Yaya Aminu sai da ya cika cikinsa tsaf da abinci Gwaggo yasha ruwa babu wani kyankyami ya goge bakinsa da hankici ya kalleta a tsanake yace.”Uwargida ran gida nagode sosai yau naci abincin tsofaffi wanda na jima banci irinsa ba.

Gwaggo na dariya tace.”To masha Allah ai haka nake so naji kana kira na da uwargida domin dama so nake na kar’be gidan gabadaya.'”

Dariya yayi ya sunkuyar da kansa minti biyu a tsakani ya kalleta da fadin.”Gwaggo insha Allahu sha biyar ga azimi zaki je umara k’asa mai tsarki inaso kiyi min addua akan wasu bukatuna.”

Gwaggo ta kalleshi cikin farin ciki da kuma tausayi tace.”Aminu Allah ya yaye maka damuwarka nagode sosai daka za’be ni a matsayin me maka addua nagode da wannan karamcin.

Na kalleshi a sanyaye nace.”Yaya Aminu Gwaggo ta gode sosai Allah ya saka da alkairi.” Ya amsa da ameeen ai babu komai Sa’ida insha Allahu tare dani dake zamuje mu dawo.” Nace.”To Allah ya yarda Allah kuma ya amsa adduarmu.

Yaya Aminu mikewa yayi bayan ya duba agogon hannunsa ya kalleta da fadin.”Gwaggo mu zamu tafi sai kinji kira ko.”? Ta mike da sauri tana fadin.”To shikkenan Allah ya kaimu lokacin nagode.

Mayafi na na gyara na fito na same su a tsakar gida suna magana har Ummatu ta fito daga gurinta ya dauko kudi masu yawa ya bawa kowacce Ummatu bakinta ya kasa rufuwa sai juya kudin take a hannunta tana zabga godiya, Khalid kuwa na bakin rijiya a zaune yana gyaran fuskarsa uffan bece ba sai da muka zo fita Yaya Aminu ya tsaya yana masa magana Da kyar yace.”A sauka lafiya.” Tsabar bacin ran abinda yake yasa na watsa masa harara tare da jan tsaki nabi bayan mijina da sauri Gwaggo har soro ta rako mu tana mana fatan alkairi da godiyar abin alkairi.

Koda ta koma cikin gidan Khalid rufe ta yayi da masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, Gwaggo dai tasan akan abinda yasa yake bala’i da ta gaji da bashi hakuri sai kawai ta shiga daki ta barshi a gurin………Bayan ya gama gyaran fuskar zuwa yayi ya tsaya bakin kofar dakin da fadin.”Sabida kawai ya biya miki umara sai wani rawar jiki kike masa harda bashi abinci da kawo shi daki har nawa umarar take to ni insha Allahu aikin hajji zan kai ki wata shekarar wannan shashashan mutumin kudinsa na banza ne tunda ba’a hanyar halak ya samesu ba.

Gwaggo tace.”Aa Khalid bana san sharri da kazafi Yaron nan Aminu dukiyarsa ta halas ce.” a zabure! yace.”Waye ya fada miki haka? kina zaune a gida kike masa sheda duk ‘yan kasuwar nan macuta ne mutsiyata kawai.” Gwaggo baki ta rike tana kallonsa mamaki fal a zuciyarta.

Khalid ya cigaba da masifa da fadin.”Shashashan namiji hotiho kawai kullum yana yawo cikin galla-gallan shadda da hula a saman a kansa amma gidansa hoto ne Allah ya tsinewa wannan auran.”!

Gwaggo gumi ya dinga tsatstsafo mata ita kam wannan masifa ta isheta wallahi ta dauka yaron tuntuni ya hakura ashe bai hakura ba….Khalid bai saurara dayi wa Gwaggo rashin kunya ba sai da ubansa ya fito tukkuna ya bar gurin yana huci!! koda Kawu ya tambaye ta abinda yake faruwa kasa fada masa tayi ta dinga Kare Khalid din tana fadin.”Aa ni ba wani laifin yayi min ba muna mayar da magana ne.” Kawu yace.”Amma nake jiyo shi yana daga murya kamar wanda yake magana da sa’arsa.”

Murmushi tayi cikin kokarin bagarar da maganar tace.”Ibrahim kasan Halin Khalid wani lokacin baya abu cikin kintsi amma ni babu wani abu da yayi min na bacin rai.”

Kawu girgiza kansa kawai yayi domin yasan kawai ta fadi maganar ne domin ta kare yaron amma babu shakka akwai abinda yake faruwa. Yace.”To Allah ya sawake shi kuma wannan yaro da ya biya miki umara Allah yayi masa albarka ya sake daukaka darajarsa.” cikin farin ciki ta amsa da ameeen ya rabbi.

Khalid kuwa haka ya kwana da yunwa tsabar bakin ciki da takaici bai ta’ba tsammanin Gwaggo fuska biyu gare ta ba sai yau ashe duk goyon bayan da take nuna masa na gaibu ne tunda gashi yazo ya tarar tana hira da abokin adawarsa a daki har da bashi abinci…….da wannan takaicin ya kwanta ya kuma tashi dashi, a gurguje yayi shirinsa ya fito da jakar kayansa yana kokarin kulle dakinsa kira ya shigo wayarsa…..Oga Labaran ne ya daga wayar suka gaisa cikin mutumci kafin yace.”Gani nan na fito Oga kada ka damu.” Daga daya bangaran oga labaran yace.”To Alhamdulillahi Allah ya kawoka lafiya ” ya amsa da ameeen tare da kashe wayar.

Bakin kicin ya nufa inda mahaifiyarsa take ya tsuguna har kasa suka gaisa tace.”Khalid har ka fito kenan.” Yana duba agogon dake daure a hannunsa yace “Eh Wallahi Ummana inaso na sauka da wuri ne.” Tace.”To ka tsaya ka karya kummalo mana.” Ya mike da fadin.”Umma kiyi hakuri zan samu wani abu a mota nasa a cikina kiyi min fatan alkairi.” Ummatu tace “To shikkenan Khalid Allah ya kiyaye hanya ya baku nasara akan abinda kasa a gaba.””

Ya amsa da ameeen Ummatu nagode sosai inaso ki cigaba dayi min irin wannan adduar har karshen numfashina.” Tace.”Insha Allahu Khalid zan cigaba dayi maka kyawawan addua mutukar ina numfashi a duniya.” Khalid ya saki fuskarsa sosai yana mata godiya yaji dadi matuka da suka rabu lafiya ba tare da yayi mata wani abu na bacin rai ba. koda ya fito babban tsakar gidan Mahaifinsa ya samu a tsaye a bakin kofar dakin Gwaggo suna magana, hannu ya mika masa sukayi musabaha da juna Kawu yace.”Har ka fito kenan.”? Yace.”Eh wallahi da wuri nake so na sauka. Yace.”To Allah ya tsare sai ka kiyaye da abinda na fada maka Khalid kada kaje kasar waje ka hadu da arna ka watsar da addininka ka kula da sallah da salati da istigifari.” Yace.”Insha Allahu zan kula.” Gwaggo ta fito daga dakin tana kallonsa duk tayi kalar tausayi

Kauda kansa yayi yana jin tausayinta kadan a ransa da kyar yace.”Gwaggo ni na tafi.” Murya na rawa tace.”Khalid Allah ya tsare dan Allah ka buga kwallo a hankali kada su karya ka kasan kafuran nan basa kaunar musulunmi da gayya ma zasu jefar da kai ka karye.”

Duk d’aurewar da yake sai da yayi dariya ya kalleta tana goge hawaye yace.”Idan sun karya ni ai ai sai na dawo gida kiyi jinyyata.”
Girgiza kanta tayi tace “Bana fatan haka Khalid na fiso kaje ka dawo lafiya.” Yana kokarin magana kira ya shigo wayarsa Salmanu ne sai yayi sauri ya daga wayar tare da sawa a kunnensa hanyar fita ya nufa yana amsa wayar hade da jan jakar kayansa….Gwaggo da Kawu suka bishi da kallo tare da bin shi da kyawawan addua gami da fatan alkairi.
[
******
Tun bayan kwanaki uku da suka wuce Yaya Aminu ya daina amfani da maganin gurin Uwale da farko dai kamar gaske duk sanda zan kawo masa maganin zai kar’ba yasha yana ya mutsa fuskarsa sannan idan dare yayi yakan kar’bi na shafawar wanda aka had’a da manshanu ya shafa a gabanshi wani lokacin ma ni yake sawa ina shafa masa maganin a gurin….amma kuma yanzu ban san abinda yasa ba duk sanda zanyi masa maganar maganin sai rai na da nasa ya ‘baci! gabad’aya hankalina ya tashi da abinda yake yi na rashin arziki.

Samun sa nayi a kwance a dakinsa na zauna kusa dashi, ya kalleni da fadin.”Sa’ida kina da damuwa ne.”? Girgiza kaina nayi raina a k’untace nace.”Yaya Aminu shifa magani ko wane iri ne hakuri yake bukata babu yanda za’ayi ace daga fara shan maganin ka kwana uku kaga aikinsa a jikin ka dan Allah kayi hakuri ka daure ka cigaba da shan maganin nan.”

Shuru yayi be tanka ba na kalleshi da fadin .”Yaya Aminu magana fa nake dan Allah dan Annabi kada ka bani kunya ka bani hadin kai gurin amfani da maganin nan.”

Ido a rufe yace.”Sa’ida bafa zan sake shan maganin nan ba domun kashe min jiki yake wai shin baki ga yanda na koma bane kullum ina kwance a gida ina bacci sai kace malalaci wannan wane irin banzan magani ne.”?

Murya na rawa nace.”Ai ko wane magani da irinsa watakila aiki yake a jikinka shiyasa yake kashe maka jiki kuma shi na shafawar kamar yana aiki ko.”?

Shuru yayi min. na mike a nutse na dauko ‘yar k’aramar robar maganin na zauna kusa dashi hannu na dora a jikinsa da fadin.”Dan Allah ka bari na shafa maka kaga jiya da daddare ba’a shafa ba kuma mai maganin yace kada a tsallake ko wace rana kwana bakwai za’ayi ana shafa maganin.

A fusace! ya mike zaune da fadin.”Shin wai me maganin nan Ubanki ne ko kuma Kawun ki.”!? Sakin baki nayi ina kallonsa gabana na wani irin faduwa.” fuska a tur’bune ya cigaba da cewa”Haba kin dame ni akan abinda yake cutar dani dole ne? idan kin damu kiji ki samo wani maganin amma bazan ‘kara amfani da wannan ba domin baya amfana min komai sai wahala.”

Murya na rawa nace.”Yaya Aminu abun har ya kai da zagi kuma.” Komawa yayi ya kwanta yana jan tsaki! hawaye suka zubo min kawai na zuba masa ido ina kallonsa takaici da bakin ciki kamar su kashe ni.
Bacci ne ya dauke shi na mike jiki a sanyaye na fita daga dakin ina tunanin ta inda zan ‘bullowa al’amarin.

Sai bayan hudu na yamma ya fito tsaf dashi sai kamshi yake fuskarsa babu walwala ya tsaya a kaina yana magana. ”Yanzu idan banda lalaci da tasirin wannan maganin da kika kawo mai zai sanya ni kwanciya a gida nayi ta bacci har la’asar ban fita ba bayan akwai jama’ar dake jira na a waje.”

Hannu na daga masa babu walwala a tare dani nace.”Yaya Aminu ni dai yanzu ba wata magana nake nema ba kaje kawai Allah ya bada sa’a magani kuma zan zubar dashi tunda baka bukata.”

Yace.”Hakan shi yafi alkairi domin ba zanyi amfani da abinda zai cutar dani ba.” shuru nayi masa. ya kalli agogon hannunsa da fadin.”Ni na fita.” kasa-kasa nace.”Allah ya bada sa’a.” Ya amsa da ameeen tare dayin gaba.

Bayan kwana goma da faruwar al’amarin sai ga Uwale tazo tunda na ganta ita kadai nasan akwai abinda ke tafe da ita bayan mun gaisa na kawo mata abinci taci ta koshi sai ta kalle ni a tsanake tace.”Sa’ida shuru ina ta tsammanin zuwanki domin naji abinda yake faruwa shuru baki zo ba shine nace to idan zan koma gurin me maganin na shigo na tambayeki halin da ake ciki.

Jim nayi na minti biyu kafin nace.”Uwale magani yayi kyau sosai.” Yanda na fadi maganar cikin inda-inda yasa ta kalle ni da fadin.”Anya kuwa Sa’ida.”? zuciyata ce ta karye dama neman wanda zai rarrashe ni nake ina kuka nace.”Uwale mutumin nan yaki bani had’in kai tunda yayi amfani da maganin nan na kwana uku ya daina amfani dashi karshe ma sai ya kasance a duk sanda zanyi masa magana akan maganin sai munyi fada wannan dalilin yasa gabadaya na tattara maganin na zubar dasu.”

Uwale ta dinga girgiza kanta tana mamakin al’amarin tace”Anya Sa’ida wannan mijin naki zai amince ku rufawa kanku asiri kuwa? wace irin rayuwa ce wannan ace namiji babu lafiya amma ba zai sha magani ba wane irin hali yake so ki shiga.”?

Hawaye na share nace.”Uwale wai cewa yayi maganin yana kashe masa jiki yayi ta sashi bacci.” Uwale tace”To idan banda abinsa ai haka ake so alamun maganin yana tasiri a jikinsa.”
Nace”To wallahi babu yanda banyi dashi ba ya’ki sha sai fad’a yake wai maganin cutar dashi yake.”

Tsaki taja tace.”To ai shikkenan kansa yayi wa ke yanzu wace shawara kika yankewa kanki.”? Hawaye na zuba nace “Uwale wace shawara zan cigaba da hakuri kawai.” Girgiza kanta tayi tace.”Aa ba za’ayi haka ba Sa’ida ai yana da magabata saboda haka kije ki samu iyayensa da maganar idan kika ce zaki cigaba da hakuri to zaki cutar da kanki saboda haka kije ki shedawa mahaifiyarsa halin da ake ciki.” Ajiyar zuciya na sauke nace.”Shikkenan Uwale zanyi kokarin zuwa insha Allahu amma don Allah kada naji maganar nan a bakin kowa Uwale ni bana so sirri na ya fita ko’ina.”

Tace.”Haba kada ki damu Sa’ida babu wanda zaiji maganar nan.” Mikewa nayi na shiga daki na dauko mata kudi, ta kar’ba tana ta godiya direba nasa ya dauketa a mota domin ya kaita inda ta nufa.
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*82&83*
Bayan tafiyar Uwale na jima a zaune ina nazari akan shawararta tabbas dole manya su shiga cikin al’amarin tunda duk iya bakin k’okari nayi akan kada maganar ta fita waje wani yaji ya’ki bani had’in kai ni naso ace daga ni sai shi muka kashe matsalarmu amma rashin fahimtarsa yasa ya mayar da al’amarin wani iri mutukar kuwa nace zan cigaba da zama dashi a haka to rayuwata tana cikin garari tunda ni Allah ya hallice ni cikin masu tsabanin bukata wannan dalilin ya sanya kawai na yanke shawarar tunkarar iyayensa da maganar sai dai kuma ban san ya za’ayi na iya fad’a musu maganar ba……..”Kawai idan kinje gidan ki samu mahaifiyarki ki sheda mata halin da kike ciki a gidan auranki.” zuciyata ce ke tunasar dani abinda ya dace, ajiyar zuciya na sauke na amince da shawarar Uwale da kuma shawarar da zuciyata ta bani akan al’amarin.

Bai dawo gidan ba sai bayan tara na dare koda ya dawo din bayan yayi wanka falo ya fito ya zauna yana abinda ya saba lissafi da amsa kiran waya duk yabi ya wani murtuke fuskarsa dan kada nayi masa maganar magani. sai kawai na tashi na bar masa falon na shiga dakina nayi wanka na kimtsa na kwanta kan gado ina tunanin yanayi na rayuwa bacci ne ya dauke ni na dinga wani mummunan mafarkin da ya sani tashi a firgice ina takure jiki na bedlamp na kunna ina wulkita idona a dakin gani nake kamar yaron yana dakin ya ‘buya a wani gurin a sanyaye na sauko daga gadon na shiga duba bayan labule gani nake kamar ya ‘boya a wani gurin.

Jiki a mace na shiga toilet na wanke jikina na fito na zauna gefan gado tare da zabga tagumi! yanayin yanda mukayi mu’amula da yaron a cikin mafarkin tamkar a zahiri shine al’amarin yayi masifar gigita ni gabadaya nipples dina sun mi’ke sun dame bu da kyaikyayi ga wani irin ruwa dake fita daga jikina. zazzafar ajiyar zuciya na sauke na koma na kwanta tare da rungume filo rintse idona nayi ina sake tunano yanda yaron yake sarrafa ni a mafarkin babu abinda yafi gigita ni sai girman joystick d’inshi sosai ta cika min mara ta cif-cif! yanda kuma yake buguna yana sucking d’in breast d’ina shi ya dinga sanya ni sakin ihu ina rungumeshi da kiran sunansa, ina daf da samun gamsuwa mafarkin ya katse….”Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un ! Astagafirullah ya Allah.” abinda nake ta nanatawa kenan ina birgima a gadon masifaffen feelings na taso min.

Ganin ina neman mutuwa ne yasa na mike a jigace na nufi dakin Yaya Aminu duk da nasan ba wani abun zan samu ba ina ganin dai ko rungume ni yayi ya tatta’ba ni zan samu saukin wani abun.

A bude kofar take na shiga tare da mayar da kofar na rufe, yana kwance a gadonsa yana bacci hankalinsa a kwance.

Ajiyar zuciya na sauke na karasa a hankali na kwanta a kusa dashi tare da dora kaina a kirjinsa……Ajiyar zuciya dai na sake saukewa a hankali na shiga kiran sunansa, shuru be amsa ba sai kawai na shiga shashshafa sassan jikinsa gabana na fad’uwa na fara ko’karin sa hannuna a cikin wandonsa.

A firgice ya tashi zaune ya wani ture ni na matsa gefe guda.

Bedlamp ya kunna yana kallona hade da matsawa baya….na kalleshi da idanuwa na da suka k’ankance saboda fitinar dake damuna.

“Yaya Aminu ina cikin wani yanayi ka taimak………Hannu ya daga min tun kafin na karasa yace.” Sa’ida wane irin taimako zanyi miki kamar baki san komai ba me yake damun ki ne.”?

Murya na rawa nace.”Sha’awa ce ta taso min cikin dare Yaya Aminu mara ta ciwo take na rasa yanda zanyi dan Allah kayi wani abu.”

Kansa ya dafe yana cijar lips d’inshi. jikinsa na matsa na dora hannuna a cinyarsa da sauri ya ture ni yana hararata yace.”Kada ki janyo wa kanki ‘bacin rai Sa’ida ni ba zan iya aikata miki komai ba a yanzu ki rabu dani nayi bacci.”

Raina ne ya soma ‘baci nace.”Haba Yaya Aminu ya kake wannan maganar kamar ba namiji ba kayi min dabaru dan Allah na samu satisfaction ko yaya ne.”

“Sa’ida idan nayi miki dabaru kin samu gamsuwa ni kuma fa? zaki barni cikin halin damuwa kiyi hakuri nima ina bukatar naji dadi amma babu hali shiyasa gabadaya na ajiye maganar aure a gabana saboda lalura ta ina ganin zan iya kare rayuwata a haka saboda haka ki cigaba da hakuri insha Allahu komai yana da karshe.”
Yana gama maganarsa ya mike ya shiga toilet ya barni da baki a sake ina binsa da kallo.

Ya jima a ciki kafin ya fito ya kalle ni da fadin.”Ashe baki je kin kwanta ba kina zaune.”? Ba tare da nace masa komai ba na sauko daga gadon na kama hanya na fita daga dakin zuciyata tamkar zata fashe sabida tsabar takaici da bakin ciki.

Ruf da ciki nayi kan gado na dinga rizgar kuka ina rokon Allah ya kawo min dauki!! jaraba sai k’ara nunnukuwa takeyi al’amarin da ya gigita ni mutuka ba tare da nayi tunanin abinda ka iya zuwa ya dawo ba na dauki waya ta na kunna number Khalid na lalabo na shiga gurin kira………….Muryar wani naji ta doki kunnena da sauri na cire wayar ina dubawa tabbas number sa ce to ya akayi wayarsa taje hannun wani.

“Da wa nake magana ne.”? Mutumin yayi magana. a sanyaye nace.” Sunana Sa’ida daga kano inaso nayi magana da Khalid.

Yace.”Eh naga sunanki akan wayar sai dai kiyi hakuri fa Domin Khalid baya kasar nan sun tafi wasa kasar america.”

Jiki a mace nace.”Dan Allah babu yanda za’ayi ka bani number da yake amfani da ita a can din………Yace.”Zan iya baki mana sai dai ko na baki number be zama lallai ki samu amsa akan lokaci ba saboda kullum yana busy. ” Nace.”Babu matsala ka bani number.”

Yace.”Okey bari na miki text. ” ajiyar zuciya na sauke da fadin.”Nagode sosai. wayar na kashe ina dan jin sauki a cikin zuciyata.

Number ya tura min nayi sauri nayi serving agogo na duba karfe goma sha biyu da minti arba’in inaso na kira shi amma kuma ban san me zan ce dashi ba.

Gwada kiran wayar nayi cikin ikon Allah ta shiga sai dai har ta karaci ringing ta katse bai dauka ba, text na tura masa na sheda masa cewa nice nake kira ya dauka.

Lokacin suna dakin hutu shida abokansa domun basu jima da fitowa daga filin wasa ba, koda ya duba text din sai kawai ya share yaki kiran ta akan wane dalili zata kirasa da daddare ta tayar masa da hankali ta hanashi gudanar da abinda ke gabansa wayar ya ajiye kan drowar ya shiga toilet daidai lokacin dana sake kiran wayar tayi ta ringing babu wanda ya daga a cikin jama’ar dake dakin kowa harkar gabansa yake…..sai bayan ya fito daga toilet din yana tsane jikinsa da towel Salmanu yace.”Khalid an kira wayarka kana wanka kuma da alama daga gida Najeria ne.”

Yace.”Salmanu rabu da ita don Allah aunty Sa’ida ce me za tayi min da daddare salon ta jaza min masifa ta kuma hanani gabadatar da uzurina.”

Salmanu yace.”Amma nayi mamaki fa to me zata ce maka bayan tana gidan auranta.” Yace.”Nima abinda na gani kenan.”

Salmanu yayi jim yana nazari yace.”Baka kuma tunanin ko wata matsalar ce ta faru a gida ka kira ta kaji ko menene.”? Girgiza kansa yayi yace.”Aa ba zan kira ta ba Salmanu idan wata matsalar ce Babana zai kira ni ya fad’a min tunda yana da number ta.” Salmanu yace.”To shikkenan Allah yasa alkairi ne.” Yana kokari sanya short nickar a jikinsa ya amsa da “Ameeen Ya Allah.”

Jikina a mace na ajiye wayar na kwanta rigingine idona na kallon rufin dakin hawaye kawai yake zuba a fuskata duk yanda naso da na samu bacci a daran abin ya gagara yanda naga rana haka naga dare na tashi da wata irin kasala da mutuwar jiki! da kyar na shirya break fast na samu nayi wanka na kimtsa jikina na fito falo na zauna ina jiran fitowarsa.

A shirye ya fito da shirin fita kamar yanda ya saba babu yabo babu fallasa muka gaisa da juna na mike na nufi gurin cin abincin ya biyo bayana.

Haka mukayi zaman kurame a gurin babu wanda yayi magana da dan uwansa tun bayan gaisuwar data shiga tsakanin mu.

Kallonsa nayi yana goge bakinsa da tissue nace.”Yaya Aminu ina so ka ajiye ni a hotoro mu gaisa da mutan gida.”

Jim yayi na minti biyu kafin yace.”Ina fatan a kimtse kike.”? nace.”Eh mayafi na kawai zan dauko.” ya mike da fadin.”Okey to kiyi sauri ki fito ki same ni a bakin mota.”

Da sauri na mike da fadin.”To shikkenan.” hanyar fita ya kama ni kuma da sauri na shiga dakina domin dauko mayafi na.

Ko a motar ma haka mukayi zaman kurame sai jefi-jefi muke magana da juna waya kuwa ban san iya adadin nawa ya amsa ba duk wayoyinsa a lokaci guda sai a kira sai ya gama da wannan sai ya dauki wannan.

A tsaitsaye ya shiga gidan suka gaisa da mutanan gidan ya wuce ya tafi kasuwa, ni kuwa ko wane daki sai da nabi daya bayan daya muka gaisa sai dai na jima a dakin mahaifiyarsa muna hira sama-sama kafin na fito.

Ummu Habiba ta kalle ni da fadin.”Ina fatan dai kuna zaune lafiya babu wata matsala.” ?

Shuru nayi ina wasa sa hannuwana. tace.”Sa’ida idan da akwai matsala ki fada min baki da wacce ta kaini a duniya.

A raunane nace.”Hakane Umma sanin hakan ne ma yasa nazo gurin ki domin na sheda miki abinda yake faruwa.”

Zama ta gyara tana kallona a nutse tace.”To ina sauraranki.” Na jima kaina a sunkuye kafin nace.”Ummu ashe Yaya Aminu bashi da lafiya.”?

Tace.”Bangane ba idan Aminu bashi da lafiya ai zaki fi kowa sani ya za’ayi kuma ni da nake gefe guda ki tambaye ni.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Ummu ki fahimci maganata mana Yaya Aminu a zahiri lafiyayye ne amma a bad’ini nakasashshe ne.”!

Ta dinga kallona tana neman karin baya ni. Murya na rawa nace.”Ummu ranar wanka ba’a boyan cibi kamar yanda kika fada hakane bani da wanda zan kaiwa matsalata ya saurare ni sai ke da kika haife ni To inaso na sanar miki da cewa tsayin watannin aurena da Yaya Aminu wata mu’amular aure bata ta’ba shiga tsakani na dashi ba gabadaya bashi da kuzari bashi da girma irin na maza haka nake zaman hakuri har aka kawo wannan lokacin da na kasa hakuri nazo na sheda muku koda taimakon da zakuyi a matsayin ku na iyayenmu tunda nima nayi iyakacin bakin kokari na akan matsalar.”

Ido ta tsira min tana girgiza kanta daka ganin yanayin ta al’amarin ya bata mamaki! “Sa’ida yanzu tsayin wata hudu da kwanakin auranku babu wata mu’amula ashe.”?

Kaina na daga mata hawaye na kokarin kwace min.” Tace.”Amma al’amarin ya bani mamaki mutuka kuma babu kama ko kad’an to shin me yake damun wannan yaron haka.”?

Nace.”Wallahi nima ban sani ba gashi baya son shan magani dan har zuwa nayi gidan Gwaggo Uwale taje can kauyen daburau ta samo masa magani amma sau uku kacal yasha yace a zubar dashi ba zai kara amfani dashi ba.”

Ummu Habiba tace.”Ai to hakan ba zata yiwu ba dole ya nemi magani domun rayuwa ba zata ta’ba tafiya a hakaba wace macace zata zauna dashi a haka babu shakka dole yau mahaifinsa yasan halin da ake ciki domin yasan matakin da zai dauka.

Nace.”Ummu ni wallahi da Ya bani hadin kai a gida babu wanda zaiji ko ya gani tunda dai wannan maganar ta sirri ce be kamata a fad’a ba amma duk kokari na akan hakan be samu ba gabadaya ma yanda na fahimce shi matsalar bata damunsa.”

Ummu tayi shuru tana nazari kafin tace.”Ko shiyasa ya’ki aure ne saboda yasan bashi da lafiya.” Nace.”To ina jin dai hakane manufarsa.” tace.”To ai shikkenan Allah yayi mana magani kuma naji dadi da baki rufe maganar ba kika fito kika fad’a domin a san matakin dauka saboda haka kada ki damu insha yau idan Alhaji ya dawo zan isar masa da maganar.” Ajiyar zuciya na sauke da fadi.”To shikkenan Umma Allah yayi mana magani.” ta amsa da “Ameeen Ya Allah.”

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*84&85*
Koda Alhaji Shamsu ya samu labarin abinda yake faruwa sai ya rasa bakin magana yayi shuru yana mamakin al’amarin da kyar ya iya d’aga kansa ya kalli inda nake zaune kaina a kasa yace.”Sa’ida ina neman gafara a gurinki a bisa wannan al’amari da ya faru wallahi dana san yaron nan yana da matsala da ban tilasta ki auransa ba ni duk abinda yake faruwa ban sani ba bani da labari shi bai fada min ba kuma mahaifiyarsa ma haka saboda haka kiyi hakuri da wannan al’amari nasan anyi miki laifi amma mutukar al’amarin nan ya zama da akwai cutuwa a ciki to zan sanya Aminu ya sawwake miki sai kiyi auran da hankalin ki zai kwanta.”

Umma Habiba ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye tace.”A’a Alhaji ba za’ayi gaggawar yanke hukuncin rabuwa ba kamata yayi shi Aminun ya nemi magani domin a duniya babu cutar da bata da magani amma kada kace zaka raba auran.”

Yace.”Habiba yaron nan ya bani mamaki mutuka wato ashe yasan yana da dauke da lalura irin wannan amma bai ta’ba zama tare dani munyi maganar ba to Habiba ta yaya za’ayi rayuwar aure babu wannan mu’amular akwai cutuwa a ciki dole a raba auran.

Murya na rawa nace.”Aa Alhaji ka dai kira shi kayi masa magana ya mayar da hankalinsa gurin neman lafiyarsa nima bana so a kashe min aurena ina tausaya masa halin da yake ciki.

Kallona yayi yana girgiza kansa yace.”Sa’ida hakika ke ‘yar halak ce kuma hakika ke din matar rufin asiri ce duk namijin da yayi dace da samun mace kamar ki ya samu jin dadin duniya ina rokon Allah yayi miki albarka ya azurtaki da ‘ya’ya masu albarka kuma insha Allahu kamar yanda kika bukata cewa ba kya so a raba auranki da Aminu to bazan raba ba amma dole duk inda magani yake yaje ya nema kuma yatsa tsayin daka gurin amfani dashi.”

Umma Habiba tace.”Eh dama hakan shine maslaha a tsakaninsu Ubangiji Allah ya bashi lafiya kamar ko wane da namiji.” Cikin alhini da damuwa ya amsa da ameeen ya Allah.”

Tunda na shiga motar naga fuskarsa kamar hadari nasha jinin jikina, a sanyaye nace.”Yaya Aminu ya kasuwa da Jama’a.”? Shuru yayi min a zafafe yaja motar muka bar gurin.
Sunkuyar da kaina nayi gabana na fad’uwa! wato saboda mahaifinsa yayi masa fad’an gaskiya yake jin haushi na akan gaskiya ni ina ganin idan da mutunci ban cancanci wannan sakamakon daga gurinsa ba tunda duk abinda nake saboda da lafiyarsa nake babu laifi domin iyayensa sun san halin da yake ciki.

A haka muka isa gida kamar kurame! yana gama parking ya bude motar da sauri ya fita barni a ciki….Na jima ina mamakin al’amarin kafin na fito da sanyayyan jiki nabi bayanshi.

Kasa shiga dakina nayi na yanke shawarar bin sa dakinsa, tsaye na sameshi da towel a jikinsa wanka zai shiga sai kawai ya daga min hannu a fusace yace.”Ki fita ki bani guri bana bukatar ganin ki a dakina tunda dai ke kin kasance mace mara sirri.”

A sanyaye nace.”Yaya Aminu kada kayi min mummunar fahimta dan Allah ka tsaya ka fahimce ni.”

“Sa’ida babu wata fahimta da zanyi miki nagode da abinda kikayi min.”

Rai a ‘bace nace.” Yaya Aminu laifi ne dan mahaifinka yasan lalurarka kada fa ka manta shine silar samuwar ka a duniya me yasa kake ‘bacin rai akan yaji matsalarka.”

“Ki rufe min baki munufaka kawai tunda nake ban ta’ba samun sa’bani da mahaifina ba sai ta dalilin ki dama bani nace ina sonki ba tilas ta min akayi idan kika takura min zan iya sawak’e miki babu lallai babu dole.”

Wani irin gumi ne ya shiga yanko min na dinga kallonsa ina mamakin furucinsa ashe dama alkairi yana zama sharri! ban ta’ba tsammanin shima yana da mugun hali ba sai yau.

“Yaya Aminu na fahimci kai baka san abinda ya dace ba kuma kana da son kanka da yawa a wannan rayuwar da kake ciki duk kudin ka da kima da mu’kamin ka wace macace kake tsammanin zata zauna da kai da mugun halinka da lalurarka to gaskiya ni na gaji da wannan masifar taka nima zaman hakuri nake idan rabuwar itace alkairi meye a ciki.”

“Kada dai kice zaki zage ni ranki zai mummunan baci yanzu yanzu.” Cikin fushi yayi maganar, hawaye na share na juya da sauri na fita daga dakin ba’kin ciki kamar ya dagargaza min zuciyata.

Yau kusan kwana goma kenan baya yi min magana ko gaishe shi nayi baya amsawa abinci kuwa idan na ajiye haka nake dauke abuna daga ya dawo daga kasuwa zai shiga daki ya kulle kansa sai dai kuma na fahimci yana shan magani amma na asibiti ne sabida nagansu akan drowar d’akin shi.

Gajiya nayi da zaman gabar na sameshi a d’akinsa yana shirya kudi a cikin akwati na samu kujera na zauna a nutse nace.”Yaya Aminu barka da asubah.”

Shuru yayi min bai amsa ba, nace.”Kayi hakuri dan Allah babu kyau gaba gashi Azimi zamu shiga idan muka cigaba da irin wannan zaman to ibadar mu za tayi rauni Allah da mala’iku zasuyi fushi damu saboda haka naji ni mai laifi ce a gurina kayi hakuri ka yafe min.”

Kallona yayi babu sassauci a tare dashi yace.”Wallahi kada ki kuskura ki sake fita da sirrin gidana ban amince kowa sake jin matsala ta ba cikin kuwa harda iyayen da suka haife ni bana bukatar suji idan zaki zauna dani a haka ki zauna idan ba zaki zauna ba ga hanya nan a bude.”
Hak’ika
Bai ta’ba ‘bata min rai irin yau ba sai kawai na mike tsaye rai a bace nace.”To sai me? babu d’a babu jika zaman me zanyi dole ne? kabar ganin kana da kud’i to ni ba sune a gabana ba kwanciyar hankali ce a gabana kudin ka na banza ne domin basa gabana zan tafi inda nafi wayo sai ka biyo ni da takarda sai me? idan mun rabu kanka kayi wa.” Ina k’are maganata na juya da sauri zan fita daga dakin. tare hanya yayi fuska a tur’bu ne yace.”Ni kike d’agawa murya Sa’ida.”? Murya na rawa nace.”Yaya Aminu duk abinda nayi maka kaina ka janyo mai yasa ba zaka tsaya mu fahimci juna ba? me yasa ba zaka tsaya mu kashe matsalar mu ba duk fa abinda nake saboda da kai nake amma saboda gadara! ka dinga fad’a min dik maganar da ranka yake so to shikkenan na hakura da zama da kai babu lallai babu dole a rayuwar aure.”
Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Ke da kan ki kikayi wa mahaifina al’kawari cewa zaki cigaba da zama dani da lalura ta me yasa kuma yanzu kike wannan maganar.” Dauke kaina nayi nace.”Ai kai ne naji kana wata magana wacce bata dace ba shiyasa na nuna maka cewar idan mun rabu d’in bawai zan tagayyara bane watakila ma Allah yayi min kyakykyawan sakamako.” Yace.”To duk dai magana ta wuce magani dai naje asibiti sun bani gashi can ma ina kan amfani dashi insha Allahu za’a a dace kiyi hakuri raina ne ya ‘baci.”
Ajiyar zuciya na sauke tare da ratse shi na wuce na barshi a tsaye a gurin gabadaya al’amarinsa ya fice min daga rai.

Saura kwana uku a dauki Azimi Yaya Aminu ya k’are shan maganin asibitin da yake amfani dashi ganin bashi da niyyar komawa asibitin sai na yanke shawarar yi masa magana sai kawai yace dani ranar litinin zai koma asibitin nace.”To amma dai kana gananin sauyi ko.”? shuru yayi min sai da na sake magana yace.”Ni babu wani sauyi da nake gani kullum jiya i yau.” Wani k’aton abu ya tokare min a kirji Nace.”To ai sai kayi musu bayani idan kaje ko kuma kawai kayi na hausa shine daidai.” girgiza kansa yayi yace.”Aa ni duk magungunan hausan nan ban yarda dasu ba zan dai cigaba da neman maganin asibitin.” Fita nayi daga dakin ba tare da na sake masa magana ba Yaya Aminu mugun d’an taurin kai ne wannan lalurar tashi dole sai an hada da maganin gargajiya sam na bature ba zaiyi ba amma ya’ki amincewa.

Kwanciya nayi da waya ta a hannuna cikin rashin zuciya na sake nemo number yaron so kawai nake naji muryarsa ko naji sanyi a cikin raina haka kawai kwana biyu yaron ya tsaya min a raina yanzu gabad’aya hankalina na kansa ina ganin a gurinsa kad’ai zan iya samun abinda nake bukata.

Wayar ce ta katse bai dauka sai na rubuta masa text hade da magiyar ya daga waya ta……Ina kokarin sake kiransa sai ya kira, hannuna na karkarwa na daga wayar tare da sata a kunnena murya na rawa na kira sunansa.

A dakile yace.”Ya akayi ne matar manya kwana biyu kina ta kiran waya ban amsa ba wai shin ma a ina kika samu number na.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Khalid ni kake wulakantawa ko.”? Girgiza kansa yayi yace.”Haba dai big aunty ai ke kinfi karfin wulakanci a gurina lokacin da kike kiran waya ina busy ne shiyasa ya kike ya maigidanki ina fatan kuna lafiya.”?

A sanyaye nace.”Kowa lafiya Khalid.” Yace.”To Alhamdulillah ina fata dai lafiya ko.”? shuru nayi ina nazari akan maganar dake raina.

“Auntyna ke nake saurare fa.” A sanyaye nace.”Khalid ina alkawarin mu.”? kai tsaye yace.”Wane alkawari kuma.”? shuru nayi na minti biyu kafin nace.”Maganar magani mana ina so ka bani number mai maganin zamuyi magana dashi tunda naji kace maganinsa yana da kyau.”

‘Yar dariya yayi yace.”Auntyna ni da bana najeria ina zan samu number wani mai magani kina nufin har yanzu a cikin matsala kike.”?

Kwanciya na gyara a gadon nace.”Eh har yanzu a cikin matsalar muke muna ta maganin asibiti amma ya’ki yi.”

Shuru yayi na minti biyu kafin yace.”Aunty Sa’ida wannan sokon mijin naki ki rabu dashi ba namiji bane mace sunan shi zaman me kike a gidanshi kina k’waruwa.” Kawai sai na tsinci kaina da fad’in.”Khalid kana so ayi ta lissafa min aure ko? ko kuma kai zaka aure ni.”?

Miskilin murmushi yayi yace.”Aa ai ni kinfi karfina aunt ‘Kashin ki bana yara bane na manya ne ni ba zan aure ki amma nasan kina rabuwa da wannan shashashan zaki samu wanda zai auranki.”

Shuru nayi ina nazarin maganarsa nasan magana yake fada min cikin magana amma ni yanzu idan Allah ya kaddara rabuwa ta da Yaya Aminu me zan kuma ci da auran irinsu Alhaji Nura babu dadi Shima Yaya Aminun babu dadi sai takaici da bakin ciki yaro k’arami zan aura na more rayuwata.

“Auntyna zan kashe waya ina da uziri.” maganarshi ta katse min tunanin da nake na sauke masa wata zazzafar ajiyar zuciya a kunnansa……..a kid’ime! yace.”Wai me yake damunki ne magana d’aya biyu sai ki sauke ajiyar zuciya da nishi! ko mijin naki yana kusa dake ne.”?

Murmushin takaici nayi nace.”Kaga bana son rashin kunya Khalid.” Ta’be bakinsa yayi yace.”To shikkenan ni zan kashe waya ta.” Da sauri nace.”Kada ka kashe muyi hira ka d’ebe min kewa.” Al’amarin ya dinga bashi mamaki da al’ajabi yau auntynsa ce ke muradin jin muryarsa lallai ta gane mahimancin sa.

“Babu kyau abinda za muyi a yanzu ni dake idan muka tsananta zamu shiga fushin ubangiji nasan kin sani amma kuma saboda tsabar son zuciya kina take gaskiya to ni na tuba nabi Allah da manzo ba zaki sani na sa’bawa Allah ba.”

Kafin nayi wata magana ya kashe wayarsa, zaune na miqe ina duba wayar kamar me neman wani abu gabad’aya jikina yayi sanyi da al’amarin na kuma san abinda nake aikatawa haramun ne amma son zuciya da sharrin shed’an na nema yasa na kauce hanya. hawaye masu zafi na share ina girgiza kaina tabbas ba kowa ne ya janyo min wannan bala’in ba sai Yaya Aminu da ina samun biyan bukatata a gurinsa nasan da babu abinda zan nema a gurin yaron ballanatana ya fada min maganar da zuciyata zata yi zafi. ko da yake duk abinda ya fada gaskiya ne babu karya nice idona ya rufe na kasa gane daidai da rashin daidai…….
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*86&87*
A daran na jima ina mur’kususu da birgima a gadon kafin wani wahalallan bacci ya d’auke ni mai cike da mafarkai barkatai marasa dadi dasa damuwa, ban tashi da wuri ba saboda yanayin yanda jikina ya saki kasala da rashin kuzari duk sun dabaibaye ni wanka nayi na dauro alwala na fito sai da nayi sallah tukkuna a gurguje na shirya jikina na fita falon nasan yanzu watakila ya shirya domin fita kasuwa gashi ban shirya komai ba.

Ina kokarin shiga dakin nasa ya fito cikin shirin fita gefe na matsa ina d’an satar kallonsa Yaya Aminu cikakken namiji ne a zahiri duk mace zata so ace tana da miji kamarsa wannan lalurar tasa itace kawai tayi masa cikas amma duk inda ake neman cikakken namiji Yaya Aminu ya kai ya cika.

Kallona yayi yana gyara agogon hannunsa yace.”Ina fata dai lafiya ko.”? A kasalance na kalleshi da fadin.”Lafiya lau me ka gani kake wannan tambayar.” yana kokarin zuwa gurin cin abinci yace.”Naga idanuwanki sunyi jawur ne.”
Murmushin takaici nayi nace.”Rashin bacci ne.” tsayuwa yayi yana kallona da fadin.”Me yasa bakya samun bacci.” Girgiza kaina kawai nayi nace.”Mu bar maganar domin tayar da ita zai janyo mana bacin rai.” Jim yayi na minti biyu kafin yace.”To Allah ya kyauta zo ki had’a min abinci zan fita.”

“Wallahi yanzu zan shiga kicin din yau na makara.” Wani irin kallo yayi min. na sunkuyar da kaina a kasa nace.” Kayi hakuri dan Allah ka zauna yanzu sai nayi maka indomee da ‘kwai.”
Yace.”Tunda kike dani kin ta’ba ganin naci indomee.”? girgiza kaina nayi yace.”To kada ki wahalar da kanki tunda kin fiso naci abincin kasuwa shikkenan.”

Nace.”Yaya Aminu tunda ka aure ni yau ne kawai aka ta’ba samun matsala kada kaji haushi kayi min uziri mana.” Yace.”Nayi miki uziri gobe ma ki sake bari na na fita da yunwa.” yana gama maganarsa ya wuce ya barni a gurin. har ya fita ban dauke kaina daga bakin kofar ba mamaki sosai nake da al’amarinsa sam bai da wani uziri idan ba nasa ba bashi da adalci ko kad’an duk hidimar da nake masa rana d’aya nayi kuskure sai yaji haushi ya fad’a min bakar magana. cikin bacin rai na wuce kicin ina addua a zuciya akan Allah ya kawo min sauki.

*GIDAN ALHAJI NURA*
Yau watan Azimi kwanansa biyar dukkanin musulman duniya kowa na kokarin tsarkake zuciyarsa domin yayi ingatacciyar ibadah masu dubara da wayo kullum da carbi a hannunsu bakinsu a rufe suna istigifari da salatin Annabi Muhammad (saw) A daidai wannan lokacin ne kuma Aunty Murja da ita da ‘Kawarta Hajiya Aziza suka bud’e shafi na iskanci iri-iri tunda aka fara azimi ko daya ba suyi ba kullum suna daki manne da juna suna iskancin da suka saba kazantacciyar rayuwa kawai suke yi a gidan lokacin shi kuma Alhaji Nura al’amura sunyi masa yawa yana ta hada-hada a kasuwa saboda zuwan bikin sallah sai sauke kaya suke idan ya fita tun asubah baya dawowa sai yamma likis wannan damar ita Hajiya Aziza ta samu ta tare a gidansa suke she’ke ayarsu.

Hajiya Aziza tunda ta kyalla ido taga nonowa a kirjin Yusura hankalinta ya tashi Yusura Yarinya ce mai garin jiki sosai ga jikinta luwai luwai gata da mazaunai kamar wata babbar mace duka shekarunta goma sha uku amma komai na mata ya bayyana a cikinta. Hajiya Aziza ta kafawa yarinyar Tarko sosai take janta a jikinta ta dinga yi mata siye-siyen kayan kwalliya dana ci Ita kuwa Aunty Murja sam bata kawo komai a ranta ba tana ganin ai yanda suke da Azizar ba zata ha’ince ta ba………..Aunty Murja ta shirya ta tafi duba mahaifinta da bashi da lafiya dama ranar asabar ne ranar da za’a kai Azimi na goma gidan ya kasance daga Hajiya Aziza sai Yusura da dan Uwanta Yasir dama shi baya zaman falo mutukar yana gidan to yana dakinsa yana kallo ko wasan lodo……. Hajiya Aziza ta lumshe idonta tana tauna le’banta a kasalance ta kalli yarinyar da fadin.”Baby tashi muje sama kiyi min tausa na gaji.”
Yarinyar tace.”Mommy Azimin yau yana baki wahala ne.”? lumshe idonta tayi da fadin.”Ke dai bari babyna Azimin yau yana wajiga ni ina jin tamkar na karya.” Tace.”Aa Mommy kiyi hakuri kada ki karya dan Allah.”

Murmushi tayi tace.”To ba zan karya ba tashi muje kiyi min tausa.” Yarinyar ta mike da romot a hannunta ta kashe tv din da suke kallo Hannunta ta ri’ke suka hau saman a tare.

Suna shiga dakin ta murza key ta cire shi yarinyar bata kawo komai a ranta ba suka nufi gadon a tare…….Hajiya Aziza kayan jikinta ta cire tas ta bar pant amma har breziya ta cire manya nonowanta da suka zube suka dinga sheqi da daukar ido

A tsorace tace.”Mommy kisa rigar ki babu kyau bude tsaraici ga Azimi a bakin ki.” Girgiza kanta tayi tana mata wani irin kallo tace.”Baby zafi nake ji shiyasa na tube kayana.

Murya a sanyaye tace.”Mommy babu zafi a dakin tunda da akwai Ac.” shuru kawai tayi mata ta ja hannunta suka zauna a gadon…..Kwanciya tayi ta bude kafafunta tana shafa kan nononta tace.”Baby yi maza ki matsa min jikina kinji ko.”

A tsorace tasa hannu a jikinta ta soma matsa mata, ta dinga sakin nishi tana mulmula nipples d’inta Ita dai yarinyar kallonta kawai take gabanta na faduwa……Hannunta ta zura cikin pant d’inta tana k’wa’kula! a gigice ta janyo yarinyar ta fada saman ta rigarta take kokarin cire mata sai ta fashe da kuka tana fadin.”Mommy meye haka ki daina dan Allah babu kyau….Wanda yayi nisa baya jin kira Hajiya Aziza zigidir tayi wa Yusura sannan itama ta cire pant din da yayi saura a jikinta kawai tasa hannunta a gaban yarinyar tana wasa dashi tana kuma shan nononta

Wata irin miqa yarinyar ta dinga yi tana fadin.”Wayyo Mommy ki bari dan Allah kada ki kashe ni babu kyau abinda kike yi.” Hajiya Aziza k’in daina wa tayi ta dinga tusa harshen ta cikin ramin yarinyar tana yi wa gurin wani irin tsotso yarinyar gigicewa tayi idanuwanta sukayi jajawur ta dinga ihu! cinyoyinta suna karkarwa Mommy kawai take kira tana lasar bakinta……Hajiya Aziza sai da ta gigita yarinyar sannan hankalinta ya kwanta ta cire bakinta a gurin a gigice ta mike zaune ta rungumeta tana shashshek’a tace”Mommy dad’i abinda kikayi min nagode.” Hajiya Aziza dama haka take so sai tayi murmushi tana wasa da nononta tace.”Baby haka nake so dama kiji dad’i babyna nima bari na kwanta kiyi min.” Sai kawai ta kwanta kan gadon ta wargaje kafafunta hannu tasa a gurin tana wasa dashi tace.”Baby zoki sha min.” Ba tare da ‘bata lokaci ba yarinyar ta kafa kanta a gurin ta shiga tsotsa kamar dai wacce ta saba da harkar.

Hajiya Aziza ihu! take tana gurnani tare da mutsika nonowanta wani irin ruwa take zubarwa yarinyar na shanyewa sai tsotsa take tana tusa harshenta a ciki……sun jima suna kazantaciyyar rayuwa kafin su bari sukayi wanka a tare suka sauko k’asa domin cin abinci.

Tun daga wannan rana Yusura ta lalace kullum idan Hajiya Aziza tazo gidansu taga sun hau sama da mahaifiyarta sai kishi ya cika mata zuciya ta shiga daki tayi ta kuka tana sa yatsanta a cikin virginal d’inta tana kwa’kula da kanta take biyawa kanta bukata a duk sanda jarabar ta taso yanzu a makaranta ma sam babu abinda take fahimta kullum idan taje suna karkashin kujeru ita da wata ‘kawarta suna aikin ta’ba nonon juna.

Sha biyar ga watan ramadan muka nufi kasar saudia domin yin umara kamar yanda yayi alk’awari Gwaggo ganinta a gaban ka’aba sai kawai ta fashe da kukan farin ciki ta daga hannu sama ta dinga addua tana hawaye da kyar na rarrasheta tayi shuru abin ya zame mata jiki duk sanda za muje dakin Allah sai tayi kuka sai dai kawai idan ta nayi na kyale ta da kanta take bari.

Kwanan mu goma a can muka dawo gida cike da farin cikin samun ‘yan uwa da abokanan arziki lafiya……….To ko da muka dawo d’in tsananta addua nayi a cikin kwanakin da suka rage kafin watan ya fita na roki Allah sosai akan ya za’ba min abinda yafi alkairi a rayuwa ta….Bangaran Yaya Aminu kuwa tunda ya dawo bai zauna ba da asubah yake fita kuma baya dawowa sai can dare ni dai banta’ba ganin mutum mai son kudin tsiya kamarsa ba kwata-kwata baya bawa rayuwarsa hutu.

Ashirin da bakwai ga watan Ramadan Mahaifin Aunty Murja ya rasu hankali a tashe ta nufi gidansu tana kuka na fitar hankali………Yusura kuwa ko a jikinta dama irin wannan damar take so ta samu sai ta fito falo ta zauna tana jiran zuwan abokiyar shed’ancin nasu……………….Hajiya Aziza ta iso gidan cikin shiga ta alfarama kamar yanda ta saba Yusura a guje taje ta rungume ta sai ta fashe da kuka tana fadin.”Mommyna nayi kewar ki naji dadi yau da muka dai zamu zauna a gidan Mommy bata nan mahaifinta ya mutu ta tafi tana kuka.”

Hajiya Aziza ta dago fuskarta ta sumbuce ta da fadin.” Nima nayi missing d’inki baby naji dadin kasancewa dake muje sama na jiyar dake dadin duniya.” Yusura dariya tayi tana jin dadi ta rike hannunta suka hau saman a tare….

*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*91*
‘Yan uwan Aunty Murja hankalinsu ya tashi sosai a lokacin data shiga gidan da takardar sakin a hannunta babbar yarsu mai suna Hajiya Mairo ta rufe ta da fad’a sosai ta inda take shiga ba tanan take fita ba tace lallai akwai babban dalilin da ya sanya mijin nata ya yanke mata irin wannan hukuncin. Aunty Murja na share hawaye tace.”Wallahi Hajiya ni ban san komai ba kawai yazo ya rufe ni da fad’a daga karshe ya bani takardar saki uku tare da fadin albarkar haihuwa ce tasa ba zaiyi sharia dani ba saboda haka kada na kuskura koma gidansa.”
Hajiya Mairo tace.”Kin dai janyo mana abin kunya Murja Allah yasa ba zargin da jama’ar gari suke miki ba ya samu labari ba ko kuma ya gani da idonsa.”

Murja na kuka tace.”Haba Mairo wace irin magana ce wannan? wane kuma zargi jama’ar gari suke min babu sata ballantana maita.”

Hajiya Mairo tace.”Kinga Murja maganar ta isa haka yanzu zan kira Saminu a waya yazo ya kira Mijin naki domin muji dalilin da yasa ya sake ki.”

Murja gabanta ya tsananta faduwa sai taja bakinta tayi shuru tana zazzare ido.

Alhaji Saminu ya shigo gidan Hajiya Mairo duk ta zayyane masa abinda yake faruwa hankali a tashe ya fito da wayarsa ya nemo number wayar Alhaji Nura domin ya kirashi su tattauna.”

Kiran duniya Alhaji Nura yana gani yaki dauka Alhaji Saminu jiki a sanyaye ya kashe wayarsa yana kallon ‘yan uwan nasa yace.”Da alama mutumin nan a fusace yake kuna dai ji na kira wayarsa yafi sau biyar bai daga ba babu shakka ruwa baya tsami banza.'”

Hajiya Mairo tace.” Gaskiya ne maganarka Yanda Alhaji Nura yake ganin kima da mutuncin mu babban abu ne zai sanya yaki dauk’ar wayarka.”

Alhaji Saminu ya kalli Murja da tayi tsuru-tsuru jikinta dik yayi sanyi yace.”Hakika Murja kin cutar da kanki duk da ban san abinda ya hadaki da mijinki ba amma jikina na bani cewa kece mara gaskiya insha Allahu ba zanyi zuciya ba zanje har kasuwa na sameshi domin mu tattauna maganar.

Tace.”Dan Allah kada kaje masa da wata magana kawai ka rabu dashi tunda ko kaje gurinsa ba gyara auran za’ayi ba tunda saki uku yayi min saboda haka kawai ka kyaleshi kawai wanda ya zalinci wani Allah zai saka masa.” Yanda ta fadi maganar zaka dauka tana da gaskiya. gabad’ayansu sai jikinsu yayi sanyi da maganarta.

*BAYAN KWANA BIYU*
Murja ta dinga kiran wayar Hajiya Aziza tana gani taki d’auka sai al’amarin ya dinga bata mamaki dama tana so ta kira ta ne domin ta fada mata cewa auranta ya mutu text ta tura mata cewa tazo gidansu ta same ta tunda an share zaman makoki.

Hajiya Aziza ta bata amsa da cewa ita yanzu tana Abuja sai dai idan ta dawo.” Murja jikinta ya mutu ganin irin wulakancin da aminiyarta ta take mata.

Shiryawa tayi ta nufi can gidan mahaifiyar Tsohon mijin nata domin ta duba ‘ya’yanta….Koda ta shiga gidan lokacin Yusura tana bakin gate tana aiki sai ta ‘bata fuska ciki-ciki ta amsa sallamar ta dauke kanta.

Tace.”Yusura kina gani na amma kin dauke kanki me yake faruwa ne.”? Yarinyar ta share hawaye masu zafi tace.”Mommy bana son kallon fuskarki kin cuce ni.” Da gudu ta ruga cikin gidan.

Murja gwiwarta tayi sanyi salo-salo tabi bayanta, Hajiya Dayyiba tana zaune a falo Yusura ta zube a jikinta tana gurshe’ken kuka.!

Da sauri ta dago ta tana fadin.”Yusura lafiya menene? kafin ta rufe bakinta Murja ta shigo da sallama a bakinta.

Hajiya da kyar ta amsa sallamar ta dauke kanta…..Murja babu kuzari ta zauna kan kujera a sanyaye tace.”Hajiya sannu ina wuni ya gida da yara.”?

Ba tare da ta kalleta ba ta amsa. tace”Me ya kawo ki gidan nan.”? Murja baki na rawa tace.”Nazo ganin yara na ne.”

Hajiya Dayyiba tayi mata wani irin kallo rai a ‘bace tace.”Tur da uwa irinki Murja Allah ya shirye ki idan zaki shiryu.”

Murja tace.”Hajiya me nayi da zaki dinga la’antata kada fa ki manta kema kin haifa.”

Tace.”Eh na haifa amma bana fata zuria ta ta dauki irin munanan halayen ki Murja munyi nadamar hada zuria dake .”

Murja fashewa tayi da kuka baki na rawa tace.”Hajiya nifa har yanzu ban san meye laifi na ba sai zagi na kuke kuna aibata ni uwa uba anzo anyi min saki uku sakin wulakancin ”

Hajiya Dayyiba tace.”To meye amfanin zama dake Murja? ai kin zama annoba tunda kika aikata abinda Allah ya haramta saboda tsabar son zuciya ki haifi ‘ya a cikin ki amma ki lalata ta sabida bakya jin tsoron Allah da Annabi.”

Sunkuyar da kanta tayi kunyar duniya ta isheta tace.”Ni fa Hajiya ban fahimci inda maganarki ta dosa ba na haifi yarinya a ciki na kuma ta yaya zan lalata ta.”?

Hajiya Dayyiba tace.”Kinga Murja ki tashi sawun ki a likkafa ki fice min daga gida bama bukar ki wa’innan yaran kuma da ana canza uwa to da sai mun sanja musu wata a madadin ki.”

Murja ranta ya ‘baci sosai tace.”Hajiya zan tafi dama ai ba zama nazo ba tunda babu wata alaka a tsakaninmu sai ta haihuwa naji dadi sosai da baku isa ku sanja musu uwa ba dole dai nice uwarsu ko kun so ko kunqi ba zaku sanjawa towo suna ba.

Hajiya Dayyiba tace.” To naji maganarki mara kunya kawai wacce bata tsoron Allah ki tashi ki tafi tunda kinyi abinda ya kawo ki.” Mi’kewa tayi ta kalli Yusuran tace.”Wato har dake a gurin shirya min makirci ko dan ubanki me nayi miki da har ake kira na da suna fasiqa.”

Sunkuyar da kanta tayi a sanyaye tace.”Mommy me yasa idan Mommy Aziza tazo gidanmu kuke hawa sama ku kulle kofa ku dade baku sauko ba ranar da Babanki ya rasu data zo gidan bakya nan shine tace nazo nayi mata tausa da muka hau saman sai ta rufe kofa ta tu’be min kaya na ta………..Kuka ne yaci k’arfinta ta kwanta kan cinyar kakarta tana girgiza kanta.

Murja zaman da’baro tayi a gurin wani irin gumi mai zafi ya shiga yanko mata bakinta sai rawa yake tana so tayi magana tsabar rud’ani ya hanata sai girgiza kanta take kafin wasu zafafan hawaye su shiga karakaina akan f*ckarta.

Cikin takaici da bakin ciki Hajiya Dayyiba tace.”Kukan banza da wofi kike yi ai dama duk wanda ya bijirewa Allah sai ya gani a ‘kwaryar cin abincinsa ke a tunanin ki abinda kuke aikatawa da k’awarki babu wanda zai fahimta to bari kiji idan kowa bai ganku ba Ubangijinku yana ganin ku kuma shine ya tanadi irin zabar da zaiyi muku a ranar lahira sabida haka tun wuri ki tuba ki nemi gafarar Allah akan abinda kika aikata.”

Tana kuka na fitar hankali ta dinga kiran Innalillahi wa’ina ilahi raji’un! Aziza ta cuce ni ta lalata min ‘Yata na shiga uku na lalace.”! Kuka take sosai tana sa bakin zani tana fyace majina sai wani irin gumi takeyi…….Yasir ne ya shigo da kayan Islamiyya a jikinsa ko da yaga Mahaifiyarsa tasa cikin halin damuwa bai nuna damuwarsa ba sai ma ya dauke kansa yana k’okarin wuce ta sai ta janyo hannunsu ta rungumeshi sosai a jikinta tana kuka da fad’in “Yasir ku gafarce ni dan Allah nayi muku laifi kada ku ‘kullace ni kuyi min aikin gafara.” Tana kuka ta janyo Yusuran ta rungume ta a jikinta sai hakuri take basu tana fyace majina.
Hajiya Dayyiba sunkuyar da kanta tayi tana kokarin mayar da hawayen idonta wannan wace irin kaddara ce? ko da yake dama duk wanda ya kaucewa dokokin ubangiji dole ya f*ckancin Fushin Allah ita kam ta rasa da wane ma’auni zata auna al’amarin bahaushe yana cewa son zuciya ‘bacin ta. Allah kasa mufi karfin zuciyoyinmu ameeen.

Murja kasa hakuri tayi ta sake neman number wayar Hajiya Aziza domin ta nuna mata cewa ta fashe ta gane abinda yasa ta gudu daga gari saboda abun kunyar data tafka…..

Kamar ko da yaushe Hajiya Aziza taqi daga wayar Murja ta fusata! kawai sai ta shiga WhatsApp d’inta ta duba taga tana onile voice note tayi mata na rashin mutunci muryarta sai rawa take tace.”Wallahi banta’ba tsammanin za kiyi min haka ba Aziza ashe babu amana yanzu ki rasa wacce zaki lalata sai ‘yar cikina me zaki samu a jikinta me kika rasa a duniya wannan abun kunya dame yayi kama.”

Hajiya Aziza a fusace! tace.”Kinga Murja wannan shouting din ya isa Aa ya kike wannan maganar ne? yanzu ke har kin manta yaran da kika lalatawa rayuwa? ashe laifi ne don nayi sha’awar Yusura na kawar da kwadayi na a kanta meye a ciki? Sauran yaran da muke lalatawa ashe ba iyaye ne suka haife su ba.” A fusace! tace.”Kinga Aziza ki daina wannan maganar don na lura kina so ki kare kanki ne yanzu ke ba zaki iya kawar da kanki akan yarinyar ba sai ki dinga yi min wata maganar banza su yaran da muke mu’amula dasu ai ba dole mukayi musu ba sune suke kawo kansu da kansu kuma kudi ake basu sai me kuma.”?

Aziza taja tsaki da fadin.”To tunda kin kasa fahimta ta ni zan kashe waya ta domin ina da uziri.” Rai a ‘bace tace.” Yar iska mutsiyaciya macuciya insha Allahu sai kinyi mutuwar wulakanci.”

Hajiya Aziza ta fashe da dariya da fadin.” Ni dake za muyi mutuwar kaskanci wallahi ‘yar iska kawai dole ne ki girbi abinda kika shuka.” tana gama maganarta tayi blocking din number ta taja tsaki!

Murja shuru tayi da waya a hannu abin duniya yayi mata yawa sai kawai ta fashe da kuka tana girgiza kanta yanzu wai ya za tayi ne? babu aure babu yara ga ‘yan uwa da dangi sun juya mata baya jama’ar gari suna mata wani irin kallo wace irin rayuwa za tayi ne.? Gefan zanin ta tasa ta goge hawaye tana kiran sunan Allah a zuciyarta.

****
Tun ranar da mukayi sa’insa dashi bai ‘kara yi min magana ba Na lura Yaya Aminu d’an gaba ne ban san me yasa ba laifi kadan sai yayi fushi yayi kwana da kwanaki bai kula ni ba, to wannan karon na gaji kullum cikin tashin hankali babu kwanciyar hankali ta aure sai bacin rai da damuwa ina ganin tun kafin dare yayi min na yanke wa kaina hukunci…………Da yake tunda mukayi haka dashi ya sanja lokacin dawowa gida sai can dare yake shigowa kuma kafin na tashi ya fita yau dai na zauna a falo dole ya dawo akan idona domin ba zan kwanta ba sai naji matsayina a gurinsa.

Sai goma da arba’in da biyar ya shigo gidan Ganina a zaune a falo yasa yayi kici kici da fuska ya kauda kansa hade da kama hanyar dakinsa…….”Yaya Aminu sannu da zuwa.” Ko kallona beyi ba ya cigaba da kokarin bude d’akinsa.

Sai da na bari ya shiga dakin tukkuna na mike nabi bayansa.

Yana kokarin cire rigarsa na tsaya a gabansa fuskata a mugun hade……Rai a bace yace.”Lafiya zaki zo ki sani a gaba.”? Tsaki naja nace.”Ina so naji matsayi na ne? ina so nasan zaman me nake a gidanka.”

Shuru yayi min ya cire rigar tare da ratse ni zai wuce da sauri na tari gabansa na bude baki kenan zanyi magana ya gaura min mari!

Dafe kunci na nayi ina kallonsa idanuwa sunyi jajawur! Yace.”Baki san haushin ki nake ji ba ko.”? Jikina na kyarma nace.”Kana jin haushina kamar yanda nake jin haushinka wallahi na tsanake bana kaunar kallon wannan bakar fuskar taka.”

Murmushi yayi yace.”Duk na gane akan abinda yasa kike min rashin kunya kina so ki tunzura zuciya na sake ki ko.”? shuru nayi ina kallonsa ya cigaba da cewa.”To ba zan sake ki ba sai kin wahala a hannuna tunda ke baki da mutunci.”

Hawaye na share nace.”Komai abinka idan zamana ya kare da kai dole ka sake ni ai ba’a dole na gaji da zama da kai babu lafiya gashi baka san mutunci ba.”

Ture ni yayi na fadi a gurin ya shige toliet din yana fadin.”Hukunci saki a hannuna yake zanga wanda ya isa ya sani na sake ki.”

Cikin mutuwar jiki na mike na fita daga dakin……Gefan gado na zauna ina kuka na dauki waya ta number Umma Habiba na nemo gabadaya na manta da dare burina kawai na samu wanda zai rarrashe ni Yaya Aminu so yake yasa zuciyata tayi bundiga.”

Umma Habiba na kokarin kashe wayarta taga kira gabanta na faduwa ta daga………”Innalillahi wa’ina ilahi raji’un! wannan kalmar ta fad’a hankali a tashe tace.”Sa’ida ya isa ki daina kuka haka kiyi shuru kiyi min bayanin abinda ya faru shin fada kukayi da mijin naki.”?

Cikin shaqewar murya tace.”Umma na gaji da wannan masifar na gaji wallahi So nake ku raba ni da wannan wahala Yaya Aminu yana azabtar dani zuciyata daf take data buga saboda abubuwan da take had’iya.”

Alhaji Shamsu ya miqa hannunsa da fadin.”Bani wayar.” Jiki a mace ta mika masa wayar yasa a kunnensa a nutse yace.”Sa’ida yi shuru kinji ko ki daina kuka haka ya isa duk naji k’orafin ki kuma duk abinda kika ce Aminu yayi miki ba zanyi musu ba domin ba’a shaidar mutumin yau wannan auran dama ni tuntuni ya fice min daga raina saboda wannan gagarimar matsalar ba zan zama mara adalci ba insha Allahu ni zan tsaya miki akan hakkin ki Aminu zai sake ki kamar yanda kika bukata Allah yasa haka shi yafi alkairi.”

Jikina ne kuma yayi sanyi sai tausayin mutumin ya lullu’be ni a sanyaye nace.”Alhaji wallahi ba laifi na bane nayi dukkanin bakin kokari na al’amarin yaci tura Yaya Aminu yaki fahimtata kullum babu nutsuwa da kwanciyar hankali shiyasa kawai na yanke wannan shawarar domin ina ganin kamar itace maslaha.”

Yace.”Kwarai kuwa Wannan shine Maslaha kuma kinyi tunani mai kyau Sa’ida ba zaki kashe kan ki akan bukatar wani ba tabbas kinyi hakuri kuma kinyi namijin kokari akan al’amarin auranki duk wanda zai budi baki ya fadi laifin ki to yaso kansa domin ita gaskiya duk inda take sai ta tona kanta saboda haka kada ki damu kinji ko gobe da safe kizo gida da kayan ki.” A sanyaye nace.”Tom shikkenan Alhaji nagode sosai Allah yasa haka shi yafi alkairi” Cike da kulawa ya amsa da “Ameeen ya Allah.” Kwanciyar rigingine nayi ina kallon rufin dakin…….”Yanzu idan na rabu da auran Yaya Aminu wane irin namiji zan aura? Shin Sa’ida anya kuwa zaki samu nasarar auran wanda zuciyarki take hasashe.”? Zuciyata ce take min wannan zancan…..Idona na rintse gabana ya shiga bugawa! kawai sai na tsinci kaina da addua akan Allah yasa Khalid ya dawo da soyayyarsa a gare ni……..
[5/14, 11:48 AM] NAFEE Alwasa: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*

*_Ha’kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*

*92*
Da wannan tunanin bacci mai nauyi ya d’auke ni da asubah sai da na fara wanka tukkuna na dauro alwala na fito na tayar da sallah bayan na idar na jima ina rokon Allah ya kawo min mafita a rayuwa amma a zahirin gaskiya auran Yaya Aminu ya fice min daga raina. jikina na shirya na nemi guri na kwanta ina jiran gari ya waye sosai na fita daga gidan.

Waya ta dake kan bedside na dauka na kunna time na duba shida da rabi na safe, ajiyar zuciya na sauke ina jin wani irin zazzafan feelings na taso min wani irin so nake wa yaron bana tunanin zan iya auran wani idan bashi din ba tunda yanzu na gane cewa shine daidai rayuwa ta, na jima ina shawarwari da zuciyata kafin na yanke shawarar kiran wayar shi muryarshi kawai nake so naji ko zan samu sassaucin abinda ke damuna a zuciyata……Number shi ta kasar waje bata shiga sai na kira number shi ta Asali cikin ikon Allah kuwa tana fara ringing ya daga.
Ajiyar zuciya na sauke hade da kiran sunansa. cikin alamun bacci ya amsa da wacece.”? saboda bacci ne a idonsa sam be duba wayar ba.

Gabana na faduwa nace.”Khalid nice fa.” Jin muryarta yasa ya bude idonsa tare da gyara kwanciyarsa a kasalance yace.”Aunty Sa’ida kin tashi lafiya.”? Cikin kasala nace.”Lafiya Khalid bacci kake na tashe ka ko.”? k’aramar ajiyar zuciya ya sauke yace.”Eh wallahi tunda nayi sallar asubah na kwanta baccin ya dauke ni kiran wayar ki ya tashe ni.” Cikin taushin murya nace.”Kayi hakuri don Allah.” Murmushi ya saki yace.”Auntyna ai ke bakya laifi ina fata dai lafiya ko.”? shuru nayi ina dawurwura.

Yace.”Kinyi shuru Aunty Sa’ida ke nake saurare.” Cikin mutuwar jiki nace.”Khalid na kasa nutsuwa saboda tunaninka yaushe zaka dawo gida ne.”?

Jim yayi na minti biyu yace.”Gobe ko jibi zan zo gida insha Allahu kada ku damu ina cikin koshin lafiya da nasarori masu yawa.”

Nace.”Alhamdulillah dama haka ake so ai duk na samu labarin irin daukakar da ka samu Khalid na taya ka murna ina rokon Allah ya tsare gabanka da bayanka.” Ya amsa da ameeen Auntyna nagode sosai.”

Shiru mukayi kowa yana sake-sake a zuciyarsa……Murya kasa-kasa yace.”Aunty ya labarin maigidan ki ina fata dai komai yayi normal.”

Murmushin takaici nayi nace.”Yana nan Khalid ai mun rabu da juna.” Kawai na tsinci kaina da fada masa haka.

Yace.”Ai gwara hakan yafi amfani tunda zaman da kike a gidansa na cutar da kai ne Allah ya za’ba miki abinda yafi alkairi.”

Cikin jin dadin maganarsa na amsa da “Ameeen ya Allah nagode k’anina.” Yace.” Yanzu kina ina hotoro ko gidan Gwaggo.”? Nace.” Ina can hotoro amma dai zan dawo gidan Gwaggo idan an kwana biyu.” Yace.”To shikkenan idan na sauka a gari zan kira wayarki.” Cikin farin ciki nace.”To shikkenan Allah ya kawo ka lafiya.” Ya amsa da ameeen ya Allah .” Kashe wayarsa yayi ya barni da tawa a hannu sai murmushin jin dadi nake a zuciyata nace da alama ba zan sha wahala da yaron ba tunda har yanzu akwai kaunata a cikin zuciyarsa………Kaina na dago sai muka hada ido dashi yana tsaye a bakin kofar shigowa fuskarsa a mugun ‘bace! Gabana na faduwa na mike zaune ina kallonsa, cikin wani irin taku ya karaso inda nake sai na sunkuyar da kaina kasa ina addua a cikin zuciyata ha’ki’kanin gaskiya Yaya Aminu ya zame min mijin jaraba bala’in tsoron masifarsa nake.

“Da wane namiji kike waya.”? maganarsa ta daki kunnena. kai a sunkuye nace.”Khalid ne.”? Waye Khalid.”? ya fada cikin sigar zargi Dauriya na aro na kalleshi da fadin.” Yaya Aminu Khalid din ne baka sani ba.”? A zafafe ya daga min hannu da fad’in.”Kada ki mayar dani shashasha mana kina waya da wani d’an iskan kice Khalid ne.” Nace.”To ai sai ka duba wayar ka gani ni bana munafurci mutukar nasan nayi abu to zan fad’a.” Wayar hannuna ya fizge yana dubawa yake fadin.”Na lura dake baki da mutunci da sanin ya kamata ba to zan sanya ido sosai a kanki domin ba zan lamunci ki zubar min da mutunci ba.”
Murmushin takaici nayi nace.”Wane irin mutunci kuma? Yaya Aminu ai kai zaka siyawa kanka mutunci ni wallahi daidai da ‘kwayar zarrah bana ganin mutuncin ka.” Ido ya tsira min nasan mamakin maganata yake dauke kaina nayi ina sake tamke fuskata ‘kwafa yayi cikin bacin rai yace.”Saboda kin kasa samun abinda kike so daga guri na shine kike bibiyar mazan waje ko.” ? Da sauri na kalleshi idanuwa na sun tara ruwa nace.”Sharrin da za kayi min kenan.”? Cikin sigar rashin mutunci yace.” Ke baki isa ayi miki sharri ba gaskiya ce wannan kada kiyi tsammanin ban san dalilin da yasa tsohon mijinki ya sake ki ba kada kuma kiyi tunanin cewa ba san irin iskancin da kike da maza a gurin aikin ki ba nasan komai nayi binkice sosai a kanki kafin na amince a d’aura min aure dake wannan dalilin ne yasa naqi mayar da hankali gurin shan magani domin kuwa banga amfanin had’a zuria dake ba.”

Wasu irin hawaye ne suka kwace min kallonsa kawai nake bakina na rawa na kasa magana tsabar mamaki da al’ajabi.

Yace.” Tunda na gane abinda kike so to ba zanyi ba sai na galabaitar dake tukkuna zaki san wanda kike wa rashin kunya.”

Hanya ya kama zai fita nace.”Tsaya ka saurare ni.” Tsayawa yayi yana watsa min kallon banza Nasa hannu na goge hawayen fuskata nace.”Yaya Aminu nagode da irin sakayyar da kayi min inaso na sanar maka da cewa shi Ubangiji baya bacci kuma shine alkalin kowa na rantse da girman zatin sa ba zan yafe maka k’azafin da kayi min ba.”

Tsaki yaja ya bude kofa zai fita nace.” Kuma zan cigaba da rokon sa akan ya raba ni da kai tunda kai ka kasance azzalimi mara tsoron Allah.” Da sauri ya dawo inda nake yana huci! yace.” Idan kika sake magana a gurin nan sai na baki mamaki wallahi.” shuru nayi ina kallonsa hawaye na sauka a saman fuskata ko a mafarki ban ta’ba tsammanin mutumin zaiyi min haka ba.
Sosai ya tsaya a kaina yaci min mutumci iya son ransa ya kad’a kansa ya fita yana fad’in zai ga wanda ya isa yasa shi ya sake ni.
Hakika na tsorata da al’amarin mutuka saboda haka yana fita na tashi da sauri na harhad’a kaya na a kwati na dauka da sauri na kama hanyar hotoro ina addua akan Allah ya bani rinjaye a kansa.
Kici’bus nayi dashi a lokacin da nake kokarin shiga gidan shi kuma yana fitowa fuskarsa kawai na kalla gabana ya fadi da sauri na dauke kaina nayi gaggawar jan akwatin kaya na domin barin gurin.

Ido jawur ya tare min hanya “Sa’ida ni zakiyi wa haka ko.”? Yanda ya fadi maganar a kufule shi ya nuna min cewar a cikin bacin rai yake.

Cikin jarumta nace.” Me nayi maka.”? Da kyar ya hadiyi wani yawu mai d’acin gaske yace.”Me yasa kika kasa hakuri kika fad’awa mahaifina tsakaninmu.”

Dauke kaina nayi nace.”Saboda na gaji da zama da kai ina bukatar rabuwa da kai shiyasa na shedawa mahaifinka domin hausawa suna cewa ta inda aka hau ta nan ake sauka.”

Zazzafar ajiyar zuciya ya sauke yace.”To bukatar ki ta biya Alhaji ya tursasa ni na sake ki ba dan raina yaso ba.”

Wani irin sanyi naji a zuciyata nace.”Alhamdulillahi Allah nagode maka nasan yanzu dai ka gazgata cewa Allah na kowa ne ba naka bane kai kad’ai.”

Shuru yayi yana kallona idanunsa sunyi jawur…..Ratse shi nayi zan wuce ya rike hannuna yana marairaice fuska yace.”Don Allah kiyi hakuri ki dawo mu zauna ina son ki sosai zan nemi magani a duk inda yake.”

Murmushin takaici nayi nace.” Yaya Aminu kenan ai da wannan matsalar ce kad’ai da kai to da da sauki amma bari na fada maka cewa kai duk macan da ka aura to ba zaka ta’ba zaman lafiya da ita ba saboda halayenka.”

Cikin sanyin murya yace.”Wane irin halaye ne dani Sa’ida duk fa wasu abubuwa da nake miki kece kika janyo amma bana miki mugunta.

Girgiza kaina kawai nayi na ja akwatin kayana na barshi a gurin…….Jiki a mugun mace ya bude motarsa ya shiga yana mamakin yanda al’amarin ya sauya a yanda yaga mahaifin nasa na son auran bai ta’ba tsammanin zai yanke musu irin wannan hukuncin ba, sai bayan ya rubuta sakin ne yaji wani masifar kaunarta a cikin zuciyarsa shi kansa yasan yayi babban rashi duk da bai cika cikakken namiji ba amma yasan yarinyar zata zame masa garkuwa ko babu komai jamaa zasu dinga yi masa kallon cikakken mutum tunda yana da iyali shin yanzu wace mace zai aura da lalurarsa ta zauna dashi a haka a gaskiya abun da kamar wuya.

*****
Sati na biyu a gidan Alhaji hankali ya kwanta sosai kullum ina tare da mahaifiyata tana kwantar min da hankali akan irin kaddarar rayuwa ta………….Gwaggo kuwa data samu labarin mutuwar auran sam bata nuna damuwa da alhini ba koda tazo gidan Alhajin ma cewa tayi Allah yasa haka shi yafi alkairi Kawu Iro ne kawai ya nuna damuwarsa tamkar ya zubar da hawaye saboda damuwa rayuwar yarinyar ce take bashi tausayi har yanzu Allah bai bata nagartaccen namiji ba……Kasa hakuri nayi da zata tafi nace.”Gwaggo kwanaki da mukayi waya da Khalid yace zai zo gida ko.”
Tace.”Eh ai yazo yau kwanansa goma sha biyu da zuwa sai da kullum baya zama jama’a sun takura masa sun mayar mana da kofar gida sansani su cika mana kunne da ihu! bayan ‘yan maula wanda suke dako mana sammako da sassafe ya basu kudi dangin Rabi ma suyi ta damunsa da bani-bani.”

Dariya ce ta kwace min ina yi nace.”Haba Gwaggo sai kace tsohowar redio daga tambaya kin saki baki sai zuba kike kamar kanya.”

Tsaki taja ta kalli Umma Habiba da fadin.”Habiba ki duba magana ta da kyau akwai gaskiya a ciki wallahi tunda yaron nan ya dawo jama’a sun’ki barinsa ya huta wai daga jin labarin yaci kofin gold da miliyoyin kudi da motoci shine fa aketa cika mana kofar gida ni kaina idan na fito matasan layi kamar zasuyi min sujjada saboda tsabar kwadayi.

Umma Habiba na murmushi tace.”Gwaggo ai arziki ne amma dai suma abinda suke bai dace ba haba ai sa barshi ya huta tukkuna.

Tace.”Wallahi kuwa ai abin da takaici sai kinga yanda Dangin uwarsa suke tururuwar zuwa gidan kamar marasa hankali.”

Nace.”Gwaggo ki kyalesu don Allah babu ruwanki saboda nasan halinki da shiga sabgar da bata shafe ki ba.”

Tace.”Oh! o dama ni ina ruwa na abun ne dai yake ban haushi.” Umma Habiba tace.”To Allah dai ya kyauta shi kuma Allah ya kara masa daukaka ya kareshi daga sharri masu sharri.” Gabadaya muka amsa da “ameeen ya Allah.”

Tace.”Sa’ida ki tashi ki shirya mu tafi gida.” Umma Habiba sunkuyar da kanta tayi domin ba taso Gwaggon taga kamar dasa hannunta a gurin zaman Sa’idan a gidan.

Nace.”Gwaggo kije kawai insha Allahu gobe ko jibi zan biyo bayan ki.”

Tsaki taja tace.”In banda rashin zuciya irin naki namiji ya sake ki amma ki zauna musu a gida kamar wacce ta rasa gurin zama to idan sha’awar gidan bulo da bulo kike ki kwantar da hankalin Khalid yana nan yana shirye-shiryen ruguje gidan ya sanja mana gini na zamani.”

Umma Habiba tace.”Haba Gwaggo ai Sa’ida bata da inda ya kai gidan ubanta komai lalacewarsa nan ne tushenta sabida haka don Allah ki daina wannan maganar.”

Ta’be bakinta tayi tace.”To ai nima abinda na gani kenan gashi ke da kika haife ta kin kasa tsawatar mata ta dawo inda take da gado.”

Umma Habiba tace.”Kiyi hakuri dan Allah Sa’ida ki tashi ki had’a kayan ki ku tafi.” Ajiyar zuciya kawai na sauke na mike domin shirya kayana Gwaggo farin ciki yasa ta zauna kan kujera tana jan Umma Habiba da hira duk Rabi ta Khalid ce Umma Habiba murmushi kawai take dama ba tun yau ba tasan matar da jarabar son jikoki komai nata na Sa’ida da Khalid ne….
: *93*
A bakin kofar gidan adaidaita sahu ta ajiye mu ganin tarin mutane a kofar gidan yasa gabana ya yanke ya fadi kallonta nayi ina kokarin magana tace.”Ai kada kiyi mamakin ganin jama’a a kofar gidan dama ai na fad’a miki haka suke damun mutane watakila ai Khalid din ya dawo tunda ga motarsa can a tsallaken hanya”. ajiyar zuciya na sauke nace.”Wallahi Gwaggo ba kiji yanda gabana ya fadi ba ganin mutane a kofar gidan ya tuna min da mutuwar mahaifina.” Girgiza kanta kawai tayi ba tare da tace komai ba ta fita daga babur din tana gyara lullu’binta fitowa nayi ina kokarin daukar akwatin kaya na dake can baya da sauri wasu matasa suka karaso gurin suna fadin.”Gwaggo sannu da zuwa unguwa kika je.”? Tace.”Eh naje hotoro ne.” Sannu da zuwa sukayi mata kafin daya daga cikinsu ya dauko min akwatina sai sannu da hanya suke mana, idona ne ya sauka kan motar tasa dake can gefe a ajiye na dan tsaya ina kallon motar da mamakin k’ayatuwar ta duk irin tarin motocin Yaya Aminu banta’ba ganin shi da irinta ba da alama dai motar sabuwa ce kuma ba tayi yawa a gari ba, ajiyar zuciya na sauke cikin zuciyata nace.”Lallai Khalid ya samu duniya lokaci guda ya tara dukiya da jama’a gashi ya zama super star kowa sai ji yake dashi……… Hayaniya ce ta cika gidan Gwaggo ta kalleni da fadin.”Kin gani ko ai kullum gidan nan a cike yake dangin Rabi maza da mata harda masu aure suzo suci na rana dana dare saboda tsabar rashin tunani uwar tasu Baito tana kallonsu ba zata ha nasu ba.

Nace.”Gwaggo dan Allah kiyi abinda yake gabanki kada ki shiga sabgarsu rai yazo yana b’aci.”! Tace.”Aikuwa sai na shiga na fito dashi watakila yana ciki sun tasa shi a gaba ko abinci basa bari yaci a nutse.”

Kafin nayi magana ta tura kofar gurin ta shige sai surutai take, ni dai sakin bakina nayi kawai ina bin ta da kallo na rasa yaushe Gwaggo zata daina shiga abinda be shafe ta ba.

“Eh ai dama wannan dalilin ne yasa ta kashe auranta taji yaro yayi kudi ya zama attajiri duniya tasan dashi shine ta kashe auranta domun ta aureshi to mutukar ni na haifi Khalid ba zan bari ya aureta ba taje can ta auri daidai da ita.” Maganar Ummatu ce ta daki kunnan gwaggo sai tayi lamfo ta cigaba da saurarar tattaunar da sukeyi Baito tace.” Ai ba zama zakiyi ki saki baki ba domin dai kin san wannan kakar tashi idan ta gindaya masa abu baya tsallakewa kiyi musu farraqu gabadaya yaji ya tsaneta dakinta ma ya daina shiga idan ba haka kikayi ba to babu shakka zata iya sanya shi ya auri ‘yar iskar yarinyar nan mai kashin tsiya.”
Ummatu tace.”Ai yanzu bana fargaba tunda ina da kudin da zan zubewa ko wane irin malami yayi min taimako insha Allahu gobe ko jibi da wurwuri zan fito muje gurin taimakon.” Baito tace.”Yawwa to hakan shine dubara mai kyau.”

Gwaggo kuwa gabad’aya gwiwarta ce tayi sanyi kalau ruwan hawaye ya taru a idonta wannan wace irin rayuwa ce Rabi da mahaifiyarta suka jefa kansu Hakikanin gaskiya Ibrahim beyi sa’ar mace ba hannu tasa tana goge hawaye ta juya da niyyar barin gurin shi kuma ya shigo dama lokacin da muka shiga gidan yana bandaki yana wanka…..Ganinta babu kuzari ga hawaye a idonta yasa gabad’aya ya shiga damuwa kafard’arta ya rike yana tambayarta Gwaggo tsabar tausayin kanta yasa ta fashe da kuka tana girgiza kanta, rungumeta yayi a jikinsa suka fito daga gurin…..Ni dai ina daki naji shashshekar kukanta da sauri na fito gabana na faduwa nasan dama ba zasu kwashe lafiya da Ummatu ba, ganinta rungume a jikinsa yasa da sauri na karasa inda suke amma ban kalleshi ba saboda yanayin yanda yake babu kaya a jikinsa sai wando iya gwiwa gashin kirjinsa ya jike jagab da ruwa fatarshi tayi wani irin haske sai kyalli takeyi sosai ya k’ara girma gabadaya jikinsa ya bud’e ya zama k’aton gaske, gabana ya dinga faduwa ina korar shed’an a zuciyata nake tambayarsa abinda yake faruwa.

Shima ba tare da yayi min cikakken kallo ba ya bani amsa da fadin.”Ban san dalili ba kawai na fito daga wanka na ganta tana kuka.”

Nace.”Ya za’ayi kace baka san dalili ba bayan daga ‘kofar ku ta fito.” ‘Bata rai yayi yace.”Zanyi miki karya ne.”? Nace.” Aa ka wuce kayi karya ai tunda ka girma amma tilas kasan abinda ya faru kawai kana ‘boyewa ne.” Yace.”Kina nufin Ummatu tayi mata wani abu kenan.”? Nace.”Ko Ummatu ba tayi mata ba wasu daga cikin gurin zasu iya yi mata. Kallonta yayi da fadin.”Gwaggo me sukayi miki.”? Tana numfarfashi tace.”Babu komai.” Kai ya girgiza da fadin.”Akawai dalili Gwaggo ki fad’a min waye ya ta’ba min ke na dauki mataki.”

Kallonsa tayi sai kawai zuciyarta ta karye hawaye suka dinga sharara a fuskarta ga jikinta sai karkarwa yake ya dauki zafi sosai.

Hankalina da nashi ya tashi jiki na rawa muka rirri’keta muka shiga da ita dakin muka zaunar da ita kan shimfid’arta……Hawaye na share na kalleta da fadin. “Kinga irin abinda nake gudu ko? shiyasa kafin ki shiga gurin nan sai da na hana ki amma kinqi Khalid dai ba yaro bane ballanatana kice dole sai kin taso shi a gaba yazo yaci abinci gashinan kin shiga sun tayar miki da hankali.”

Ya kalleni da bacin rai a fuskarsa yace.”Kada ki yanke hukunci sai kinyi binkice tukkuna.” Nace.”Babu wani binkice da zanyi gaskiya na fad’a matar nan tsohuwa ce ya kamata a dinga yi mata uziri a gidan nan kuma duk abinda take saboda kai takeyi me zai sanya a dinga kokarin kasheta da bakin ciki.”

A zafafe yace.”To ya isa haka bana bukatar k’ananun magana idan Gwaggo tayi min abu dama can ta saba babu ruwan ki zaman Gwaggo da Ummatu tuntuni haka suke abunsu kowa yana da laifi a cikinsu.”

Nace.”Ai a matsayin ta na uwar masu gida ya kamata ace ana rangwanta mata da wasu abubuwan me yasa ba’ayi mata adalaci.”

Yace.”Okey yanzu dai idan na fahimta kina so ki zagi Ummatu ko wani nata ko.”? Murmushi nayi nace.”Wannan ba halina bane da zan zagi Ummatu da tuntuni na zageta a matsayin uwa take a gurina amma kuma duk inda gaskiya take dole ne a fad’e ta.

“Yace.” To kada ki sake sanya bakin ki akan abinda ya shafi zamantakewar Gwaggo da Ummatu mutukar kin dauketa a matsayin uwarki Bana son mu samu sa’bani dake ta wannan dalilin domin ina ganin kima da mutuncin mahaifiyata…….Bude baki nayi zanyi magana ta daga min hannu a sanyaye tace. “Sa’ida kyaleshi tunda ya nuna yafi son uwarsa dani ka tashi kaje ka sallami jama’ar dake jiranka a waje.

Kallonta yayi yana sassauta fuska yace.” Gwaggo keda Ummatu babu wacce tafi wata a cikin zuciyata domin kun taka muhimiyyar rawa a rayuwa a yanzu dai babu wata mace a gabana bayan keda mahaifiyata saboda haka kada kiyi wa maganata mummunar fahimta.

Tace.”To naji ka tashi kaje kawai Allah yayi mana maganin masifa.” Mi’kewa yayi nai saurin kauda kaina daga kallonsa shafefen cikinsa da yayi guru-guru shi yayi masifar daukar hankali tamkar wanda baya cin abinci ciki a shafe sai ‘kananun gashin da ya dan kwanta a gurin! Kauda kaina nayi har ya suka gama maganarsu ya fita daga dakin Na juyo na kalleta da fadin.” Gwaggo wai don Allah me ya saki kuka ne.”? Sai kawai ta shiga girgiza kanta alamun abun na bata mamaki Tace.” Sa’ida tun kafin na karasa shiga gurin naji muryoyinsu suna shirya mana mugun abu dani dake Suna cewa kin kashe auranki ne domin ki aureshi saboda kinga yayi kudi sannan ni kuma sai sun raba tsakanina dashi zasuje gurin malamin su yayi mana farraqu domin kada na bashi umarin auranki.”
Cikin wani irin mamaki nake kallonta nace.”Au Gwaggo abinda suke tunani kenan.”? Tace.”Eh mana kunnuwa ne suka ji ba karya nayi musu ba.” Sunkuyar da kaina nayi ina mamakin bindiddigi irin na mutane………”Sa’ida mutukar na isa da Khalid sai ya aure ki sai naga ‘karshen kiyayyar da Rabi take nuna miki kuma bayan haka sai na kuntuka mata bakin ciki babu boka babu malam sai nasa Ibrahim yayi mata kishiya zata gane bata da wayo.”

“Gwaggo ki kyaleta don Allah duk sharrin ta zai koma kanta ni wallahi bana son ‘kananun magana kowa yana fama da kashi a gindinsa amma yana hango na wani mutuwar aure ba akaina aka fara ba kuma ba za’a kare a kaina ba aure tsakanina da Khalid kuma idan Allah ya kaddara babu wanda ya isa ya hana.”

Tace.”Ki kwantar da hankali insha Allahu wannan karon sai bukatata ta biya akan ku.”

Bayan sallar magariba Ummatu ta shigo dakin da abinci a jere akan tire…..Nice na iya amsa sallamar ta Gwaggo kuwa kallon mamaki kawai take mata .

Kallona tayi da fad’in.”Sa’ida yaushe kika zo ne.”? Nace.” Wajejan la’asar ne.” Tace.”Ayya lokacin ina tare da baki.” shuru nai mata ta Ajiye tire din abincin da fadin.”Gwaggo yau dai na gama miki abinci da wuri kuma abinda kike so nayi miki.”

Da sauri tace.”Rabi ki kwashe kayan abincin ki bana bukata.” Cike da mamaki tace.”Me yasa Gwaggo ko wani abu ne ya faru.”?

Gwaggo kauda kanta tayi ta cigaba da gyara goron ta Tace.”Haba Gwaggo lafiya lau fa muke zaune da juna me yasa duk sanda ki kaga Sa’ida sai ki sauya min fuska ko dai zuga ki take yi.”
Da sauri na kalleta ina mamakin maganarta Gwaggo tace.”Kada ki zarge ta babu ruwanta Rabi ni sharrin ki nake guda insha Allahu Ubangiji Allah zai sanjawa Ibrahim da mata tagari.”

Ummatu fashewa tayi da kuka tana kallona tace.”Amma Sa’ida kin cika shaid’ainiya wallahi wato daga zuwanki har kin zugata wai me na tsare miki ne.”?

Nace.”Ummatu dan Allah idan zaki fadi magana ki dinga taunawa ni ina ruwana da zaman ku dama ai kun saba don Allah ki daina zargina babu ruwana.”

Tace.”Shiyasa ai gashinan duk inda kika je sai an koro ki saboda mugun hali na gado waye zaiyi sha’awar had’a zuria dake.” Gwaggo tace.”Rabi kin kyauta nagode ki cigaba da zagi na kina aibata zuria ta zan nuna miki ikona idan uban farraqu zakiyi kije kiyi kada ki fasa ni Ramatu naci dubu sai ceto.”

Ummatu ta dinga kuka tana fadin.”Ni kam na shiga uku a gidan nan nagode Allah tunda Allah ya rufawa yaro na asiri zan umarce shi ya siya min gida na fita daga wannan masifar.” Cikin jin rashin dadin maganarta nace.”Don Allah Ummatu kada ki dauki al’amarin da zafi ki zauna ku fahimci juna.”

A fusace! tace.”Rufa min baki munaf*ckar banza da wofi insha Allahu sai Nayi maganinki.” Tana gama maganarta ta fice daga dakin a fusace!!!

Gwaggo tace.”Rabu da kafura borin kunya takeyi domin tasan naji duk irin makircin da suke shiryawa to duk kaidi da sharrinsu zai koma kansu gafalallu marasa tsoron Allah.”
Ajiyar zuciya na sauke nace.”Allah dai ya kyauta.” Ta amsa da ameeen tana gyara redion ta.

Koda Kawu ya dawo ya gan ni a gidan sai ya nuna farin cikinsa ya zauna muka jima muna hira yana ta kwantar min da hankalina da addua akan Allah ya musanya min da alkairi.”

Yana kokarin mikewa Gwaggo tace ya koma ya zauna tana so tayi magana dashi.

Nace.”Don Allah Gwaggo ki kyaleshi yaje ya huta.” Tace.”Aa Sa’ida ai ba zan kwana da maganar nan ba sai na fada masa yasan abinda yake faruwa.”

Kawu Iro ya koma ya zauna jikinsa duk yayi sanyi……Gwaggo ta shiga zayyane masa duk abinda ya faru da irin cin mutuncin da matarsa ta shigo har daki tayi mana.

Kawu ransa yayi masifar ‘baci gumi kawai yake shi kam ya rasa wane mataki zai dauka akan Matar tashi kwata-kwata bata ganin darajar mahaifiyarsa…..Gwaggo tace.”Ibrahim naga hankalin ka ya tashi to ka kwantar da hankalinka a yanzu abu daya za kayi wa Rabi ta shiga hankalinta shine ka ‘kara aure ni dana haife ka na baka umarnin ka fara neman aure bazawara ko budurwa duk wacce kake bukata ni zan shige maka gaba.

Yace.”Gwaggo naji dadin wannan maganar taki kuma insha Allahu zan fara duba macan da ta dace dani wacce zata kula min dake ita kuma Rabi Allah ya shiryeta.” Ta amsa da ameeen ya rabbi sannan kuma inaso ka kafa mata takunkumi ma’ana ka hana ta fita zuwa ko’ina saboda idan ta fita din yawace – yawace take na malamai da bokaye.” Yace.”Insha Allahu yau zata ga b’acin raina zan nuna mata cewa ta za’bi daya aure ko zaman gidansu.” Gwaggo tace.”Yawwa haka za kayi mata jan ido amma ka kula fa kada kayi abinda bai dace ba.” Yace.”Insha Allahu Gwaggo.” Sallama yayi mana ya fita daga dakin.
Gwaggo tace.”Haba jama’a Rabi ta zame mana annoba babu abinda zai sanya ta dawo nutsuwarta sai kishiya zata san ni takewa rashin kunya.” Nace.”Gwaggo ki bar maganar haka tunda dai kin fada masa shikkenan Allah yasa karshen matsalar ce tazo.” amsawa tayi da ameeen tana kokarin janyo kwanonin abincin dake gabanta.

Tare muka ci abincin muna hira sai bayan an gama *taskar labarai* na gyara mata shimfid’a tace.”Sa’ida ai ba zan kwanta ba sai naga shigowar Yaron nan.”

Nace.”Gwaggo don Allahi kiyi kwanciyarki har yaushe zaki zauna zaman jiran shigowarsa tun dazu kike gyangyadi fa.”

“Aa Sa’ida ki bari dai na zauna na jira shi na riga na saba sai ya shigo nake kwanciya.” Nace.”To ai shikkenan ni zan kwanta sai da safe.” Tace.”Allah ya tashe mu lafiya.” amsawa nayi da ameeen na gyara kwanciya ta kan gadon k’arfen ta…….
*94*
Hayaniyar sa naji a saman kaina a furgice na bud’e idona ina kallonsa yana tsaye a kaina yana surutai Gwaggo sai magana take masa amma yaki yayi shuru, zaune na mike na dauki hula ta nasa kallonsa nayi da mamaki a tare dani nace.”Lafiya kake min hayaniya da masifa a kaina bacci fa nake yi.”

Cikin hayaniyar yace.”Ni ina ruwana da baccin ki ina dai fad’a miki cewa ki kama kanki a gidan nan domin ba zan lamunci ki dinga cin mutuncin mahaifiyata ba saboda kawai kina da daurin gindi gurin masu gidan idan abin yayi tsanani zan d’auketa na sauya mata gurin zama tunda zuwan ki gidan ya zama annoba.”

Bakina ne ya mutu kawai na dinga kallonsa ina mamakin rashin kunyar da yake min har yaushe yayi girman da zai dinga buga min tsawa ko dan yaga Allah ya rufa masa asiri ya samu duniya.

Gwaggo tace.”Khalid ka kyauta abinda kake wato ka shiga can gurin uwarka ta fada maka karya da gaskiya shine kazo zaka d’aga mana hankali ko to shikkenan mun gode ka fice min daga dakina.”

Ba tare da ya bata hakuri ba ya buge rigarsa ya fita daga dakin, Gwaggo ta fashe da kuka da fadin.”Sa’ida na rasa yanda zanyi da Rabi ta hanani sakat kullum babu kwanciyar hankali to idan Allah ya kaimu gobe zan tafi k’yauye naje na huta da wannan jarabar.”

“Gwaggo idan kina so ki zauna lafiya a gidan nan to ki fita daga hurumin Ummatu babu ruwanki da duk abinda za tayi ki zuba mata ido duniya ce tafi bagaruwa jima kullum sai na fada miki hakan amma kin kasa fahimta gashinan ai Yaron da kika k’wallafa ranki a kansa ya shigo yaci miki mutunci saboda ita.”

Hawaye ta share tace.” Ki kyale ni dashi ai zan nuna masa fushina zai san wanda yake wa tsawa Allah ya kaimu da safe zamu tafi can k’yauye mu bar musu gidan.

Nace.”Eh hakan ma hukunci ne amma ki nemi shawarar Kawu kafin muyi tafiyar.” Tace.”To shikkenan haka za’ayi ki koma ki kwanta ki cigaba da baccin ki.”

Saukowa nayi daga gadon na dauki buta na fita domin kama ruwa.

Ina fitowa daga bandakin naji muryar Kawu na tashi sama-sama da alama fada yake mata can naji muryarta tana kuka tana bashi hakuri kafin naji maganar Khalid din yana cewa”Baba don Allah maganar nan ta mutu haka wallahi bana son abinda zai daga muku hankali kuma ni ban fifita Uwata akan Gwaggo ba kowa da matsayinsa a zuciyata sannan Aunty Sa’ida ‘yar uwata ce amma bana son irin abinda takeyi a gidan nan mutukar tana nan to Gwaggo da Ummatu sun dinga samun sa’bani kenan shiyasa kawai na yanke shawarar siya mata gida domin a samu zaman lafiya.”

Kawu Iro yace.”Ban amince da wannan tsarin ba Rabi zata cigaba da zama da Mahaifiyata a cikin gidan nan Sa’ida kuma dole ta zauna a gidan domin bata da inda ya wuce nan din.

Yace.”To shikkenan Baba insha Allahu cikin satin nan za a fara aikin gidan idan yaso ita Gwaggon sai a fitar mata da sabuwar kofa ta waje ina ganin kamar hakan shine maslaha.”
Yace.”Duk yanda za kayi kayi amma ban amince Rabi taje wani gurin ta zauna ba.”

Girgiza kaina nayi na bar gurin ina addua akan Allah yasa hakan shi yafi alkairi watakila idan aka raba musu gidan za’a samu zaman lafiya.

Washe gari da Kawu ya shigo Gwaggo take fada masa cewa zamuje can ‘kauye mu kwana biyu.” Sai ya nuna farin cikinsa sosai harda bada sautun gaisuwa ga abokanan arziki.” Sallama yayi mana ya tafi kasuwa.

Khalid yana can yana bacci hayaniyar matasa ta cika kofar gidan wai jiransa suke ya fito su gaisa dashi yayi musu hasafin da ya saba Khalid be watsar da abokanansa ba cikinsu yake zama suyi hira da labarin wassanin k’wallon kafa.

Salim ne ya shigo cikin gidan ya tsaya a bakin kofar dakin Gwaggo suna gaisawa d’an leko da kansa yayi yace.”Kamar aunty Sa’ida ko.” Gwaggo tace.”Eh itace gatanan yau kimanin sati biyar da mutuwar auranta.” Ji nayi tamkar na kwad’a mata mari saboda takaici wani lokacin idan ta aikata wani abun sai kaji tamkar zuciyarka ta buga.

Yace.”Ayya! sannu auntynmu Allah yasa haka shi yafi alkairi Allah kuma ya zaba miki miji nagari.” a zuciyata na amsa Yace.”Gwaggo Khalid yana nan ko? domin naga motarshi a waje.”
Tace.”Eh yana nan ka shiga ka duba watakila ko bacci yake dan ban ji motsinsa ba.”

Yace.”To shikkenan bari na shiga na duba shi.” Salim ne ya tashe shi daga baccin da yake Ya kalleshi da fadin.”Salim wato ba zaku barni na huta ba ko.”?

Yace.”Khalid zaka huta idan lokaci yayi yanzu dai dole kayi hakuri tunda ka tara jama’a gasu Rossy Rabs can a waje suna jiran ka da alama ka manta alkawarin da kayi musu nayin wasa tare dasu.”

Yace.”Wallahi na manta gabad’aya jiya ban kwanta da wuri ba shine dalili bari nayi wanka na karya sai mu fita.” Salim yace.”Okey to bari na fita na fada musu cewa su jiraka ga kanan fitowa.”

Yace.”Okey nagode abokina.” Tare suka fito Salim ya fita shi kuma ya nufi dakin Gwaggo da brush a hannunsa.

Sallama yayi tare da daga labulan dakin Ganinta zaune a bakin gado da rigar bacci a jikinta yasa da sauri ya kauda kansa, Gwaggo kuwa kauda kanta tayi tana ‘bata fuska nice na amsa masa sallamar ciki-ciki.

Yace.”Gwaggo kun tashi lafiya.”? shuru tayi masa yayi jim! yana dan tunani murmushi yayi da ya tuna akan abinda yasa ta juya masa ‘keya shi ya manta ma da sun samu sa’bani jiya…….”Gwaggo ku bani man goge baki mana.”
Da sauri tace.”Bani dashi ni bana san ro’ko a rayuwata duk kudi’n ka amma kazo kana ro’kon abu kaje kayi asuwaki mana.”

Yace.” Sai na fita an jima zan shiga sahad na siya ina da asuwaki ko nayi ina had’awa da brush kawai idan zaki bani ki bani.”

Tace.”Ni bani dashi sai dai ko Sa’ida.” Nace.”Nima bani dashi.” kallona yayi na minti biyu kafin ya saki labulan dakin ya bar gurin.

Gurin mahaifiyarsa ya samu man goge bakin Ummatu da kanta ta had’a masa ruwan wankan ta kai masa har bandaki sai lalla’bashi takeyi shi kam godiya yake mata yana jin dadin irin kulawar da take masa Gwaggo da Sa’ida na d’aki suna jin duk abinda yake faruwa a tsakaninsu……Gwaggo kishi ya cika mata zuciya sai surutai takeyi nace.”Gwaggo don Allah kiyi hakuri ki kai zuciyarki nesa babu ruwanki da duk abinda yake tsakaninta da d’anta Ita uwarsa ce ke kuma kakarsa kowa da akwai matsayinsa.” ‘Kwafa tayi ta girgiza kanta ba tare da ta sake magana ba ta dauki redio ta kama tashar redio *kano Am* ta ware vollom aikuwa wakar *Aminu Ala* mai taken *Share hawaye uwa ma bada mama share hawaye ki daina kuka Ummi Ummina* ta karad’e gidan da sauri ta sanja tasha ta mayar da ita *Freedom redio* lokacin su kuma sun saka wakar *Zumunci yana kara kusanci* Murmushi tayi ta k’aro murya sosai ta ajiye redion. Na dinga kallonta ina mamakin al’amarinta Gwaggo duk da ta tsufa bata da kyau! irinsu ne suke hana kishiyoyi zama da habaice-habaice babu boka babu malam za’a kori kishiya.

A shirye ya fito da shirin fita sai kawai ya ganta a tsaye a bakin kofar dakin nashi.

Cikin kulawa yace.”Umma ina fatan lafiya dai.” Tace.”Khalid inaso nayi magana da kai.” Yace.”To ina sauraranki.” Tace.”Khalid tunda dai Allah yayi maka yanda kake so a duniya kafi karfin komai na rayuwa a yanzu me ya kamata kayi.”?

Shuru yayi yana kallonta ta cigaba da cewa “Tunda ka dawo gida ban ta’ba ji kayi maganar Jamila ba alhalin kasan da akwai alkawarin aure a tsakaninka da ita kada ka watsa min kasa a ido kasa ma’kiya suyi min dariya Khalid.”

Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Umma bana so kina sa damuwa a ranki idan maganar auran Jamila ne babu damuwa dama ai tuntuni na amince da auranta sai a fara shirye shirye nan da wata uku sai a daura aure insha Allah.”

Farin ciki kamar ya kasheta tace.”Amma naji dadin wannan al’amarin Khalid Allah yayi maka albarka ya kara d’aukaka darajarka.”

Ya amsa da ameeen Umma nagode da addua kwarai.” Tace.” Naga kayi shirin fita baka karya ba bana so kana zama da yunwa.”

Goshinsa ya murza yace.”Umma bana sha’awar shan tea kwana biyu kunu nake so wallahi shiyasa ban nemi wani abu a gurin ki ba.” Tace.”Ayya ai daka fad’a min tunda da akwai gasara sai na dama maka kunun.” Yace.”Kin san jiya dani dake duka bamu da nutsuwa shiyasa.”

Tace.”Eh hakane to ko zaka zauna na dama maka kunun.” Girgiza kansa yayi yana duba tsadaddan agogon dake daure a hannunsa Yace.”Tun dazu mutane ke jira na a waje zan fita na saurari uzirinsu.” Tace.”To shikkenan me kake bukata na girka maka.”?

Yace.”Umma duk abinda kika girka min zanci.” Tace.”To ina maka fatan alkairi yaro na Allah ya baka nasara a rayuwarka.” Ya amsa da ameeen ya Allah.” Yana fita tayi murmushi tare da girgiza kai tace.”Cikin ruwan sanyi zan k’wace yaro na daga hannun ma’kiya na dakinta ta shiga ta dauki wayarta tana so tayiwa Jamila albishir da cewa auranta da Khalid ya kusa zuwa.

Kasa fita yayi sai da ya leqa dakin Gwaggon kamshin turaransa ya cika mana hanci satar kallonsa na dinga yi ta ‘kasan idona yayi kyau har ya gaji yana sanye da k’ananun kaya kanshi sanye da f-cap sajensa ya kwanta a fuskarsa ba’ki sosai sai kyalli yake………Ganinsu suna cin d’umame na towo da jug din kunu da kosai a gabansu yasa ya cire Booth din dake kafarsa ya shiga dakin ya zauna kusa dani lokaci k’ankani na rikice feelings mai zafi ya taso min gabad’aya k’amshin dake tashi a jikinsa ya gigita ni.”

“Gwaggo zan sha kunun nima.” a shagwabe ya fadi maganar.” Uffan ba tace masa ba ta cigaba da kur’bar kunun ta tana had’awa da kosai…….Hannu ya miqa yana kokarin kar’bar kofin hannunta tayi saurin janyewa tana harararsa. murmushi yayi ya dauki kosai d’aya yasa a bakinsa ya juyo yana kallona. saurin kauda kaina nayi daga kansa……Matsowa yayi kusa dani sosai yasa hannu cikin d’umamen towon dake gabana ya gutsira yasa a bakinsa. kallonsa nayi ya d’aga min gira da fad’in .”Ko kada nasa miki albarka.” Hannuna na tsame daga cikin kwanon towon nace.”Na koshi ai ka cinye ragowar.” girgiza kansa yayi da fadin.”Ni nafi karfin naci ragowar wani ko kin manta da hakan.”? Jim! nayi ina kallonsa da nazarin maganarsa ya ‘kura min ido da fad’in.”Ina fatan kin gane inda maganata ta dosa .” ? Murmushin takaici kawai nayi na kauda kaina ina mamakin tsagerancin sa.

Gwaggo tace.”Yau dai za muyi balaguro zamuje mu huta mu barwa masu gida gidansu su sakata su wahala.”

Yace.”Gwaggo wace irin magana ce wannan.”? share shi tayi ta cigaba da abinda take. Kallona yayi da fad’in.” Ina zakuje.”? Ba tare dana kalleshi ba nace.” Nima ban sani ba.” shuru yayi na minti biyu kafin yace.”Gwaggo kiyi hakuri kada kuje ko’ina nayi alkawarin raba muku gida keda Ummatu kowa kofar sa daban.”

Tace.”Ai baka burge ni ba na d’auka zaka gina mata k’aton gida ta shiga ta zauna tunda naji tana alfahari da kai cewa kayi kudi zaka share mata hawaye.”

Dariya yasa yana kallonta yace.”Gwaggo ina kudin suke ni talaka ne kuma almajiri mai nema wai mai yasa mutane suke zuzuta magana ne.”

Tace.”Aa kada ka butulcewa Allah mana Khalid kana da kudi tunda kullum cikin kyautarsu kake.” Yace.”Tom Allah ya ‘kara bud’a min hanyar samu.” a zuciyarta ta amsa da “Ameeen.”

Yace.”Gwaggo yanzu ba zaki bani kunun nasha ba.” Girgiza kanta tayi da fadin.”Kaje uwarka ta baka.” Ya rike bakinsa yana mamakin maganarta. Ni kam mi’kewa nayi na fita tsakar gida domin wanke hannuna. abun mamaki ina dawowa na tarar dashi da kofi cike da kunu yana sha. cikin zuciyata nace ” dama duk cika baki ne ba zata iya kauda kanta a kansa ba.

Waya ta na d’auka ina dubawa nan naga text din Yaya Aminu yana bani hakuri akan abinda ya faru wai zai zo da daddare yayi min bayani akan irin cigaban da ya samu domin yaje gurin wani mai magani dake wani k’yauye ya samo magani kuma yayi dace maganin ya kar’be shi.” Murmushin takaici nayi cikin zuciyata nace.”Allah ya kyauta bana tsammanin zan tsaya na saurari mutumin nan sabida har yanzu ban mance irin wahalar da nasha a hannunsa ba..

*95*
Idar da sallah ta kenan kira ya shigo waya ta, a nutse na mika hannu na dauki wayar dake gefe na Yaya Aminu ne ya kira ajiye wayar nayi domin ko na dauka ban san abinda zan ce dashi ba gabadaya yanzu bana bukatar wata alaka ta sake had’a ni dashi. wani kiran ne ya sake shigowa Gwaggo ta kalle ni da fadin.” Sa’ida kina ji ana kiran wayarki ko.”? Kallonta nayi da fadin.”Yaya Aminu ne.” Jim tayi na minti biyu kafin tace.”To ki daga mana ai gaisuwa baya nufin wani abu.” Wayar na dauka tare da sata a kunnena a nutse nace.”Salamu alaikum.” Ajiyar zuciyarsa naji kafin ya amsa da “Wa’alaikissalam ranki ya dade barka da dare.”

Cike da mamakin yanda yake kwantar min da kai na amsa da fadin.”Barka dai Yaya Aminu ya gida da harkoki.” ?

Cikin jin dadi ya amsa da “Alhamdulillahi komai lafiya amma ina bukatar ganin ki yanzu domin ina tsaye a kofar gidanku .”

Nace.”Sai dai kayi hakuri wallahi domin yanzu ina da uziri.” Shuru yayi da alama maganata ba tayi masa dadi ba, Yace.”Sa’ida alkairi ne ya kawo ni gurin ki don Allah ki fito ki bani aron lokacin ki.”
Shuru nayi ina jinsa yana ta magiya da karyar da kai. nace.”Shikkenan ganinan zuwa.” godiya yayi min kafin ya kashe wayar.

Kallonta nayi tana jan carbi nace.”Gwaggo zan dan leqa gurinsa domin naji abinda yake tafe dashi.”

Tace.”To shikkenan Allah yasa alkairi ne.” Cikin zuciyata na amsa da ameeen hijabi na nasa na nufi kofar gidan.

Yana tsaye jikin motarsa idonsa kuri a kofar gidan a nutse na karasa inda yake babu sukuni a tare dani na gaishe shi, ya amsa cikin sakin fuska yana bina da wani irin kallo.

Nace.”Yaya Aminu kai nake saurare.” Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace.”Sa’ida Allah ya bani lafiya yanzu garau nake daidai da kowane jarumin namiji wannan shine albishir din da nazo miki dashi.”

Kallonsa nayi babu walwala a fuskata nace.”Allah sarki amma na taya ka murna Yaya Aminu Allah ya kiyaye gaba.”

Ya amsa da ameeen nagode matata.” murmushin mamaki nayi wai matata………”Sa’ida kina jina ko.” kallonsa nayi da fadin.”Ina jinka .” Yace.”Inaso kiyi hakuri ki dawo d’akin ki tunda dai ba kiyi iddah ba.”

Murmushi nayi nace.”Yaya Aminu a yanzu dai babu wannan maganar a tsakaninmu bana bukatar sake zaman aure dakai a halin yanzu kayi hakuri idan maganata ta ‘bata maka rai.”

Gabad’aya yanayin sa ne ya sauya ya koma wani irin cikin rarrashi yace.”Sa’ida don Allah kada muyi haka dake ki dubi lamarin nan da idon rahama wallahi yanzu zan iya dauke miki dukkanin bukatunki.”

Ina kokarin bashi amsa wata mota tayi parking a gabanmu ni dashi duk muka bi motar da kallo wannan dai ba motar Khalid bace.

Alhaji Nura ne ya fito daga motar cikin manya kaya kansa sanye da hula damanga hannunsa rike da key na mota ya karaso inda muke tsaye.

Kauda kaina nayi gabana na wani irin faduwa. hannu ya mikawa Yaya Aminu sukayi musabaha. Yaya Aminu yayi bala’in shan kunnu domin dai jikinsa na bashi wani abu.”

Yana wani Muzurai ya kalleni da fadin.”Gimbiya inaso nayi magana dake.” Kallonsa nayi fuska a cukune nace.”Alhaji wace irin magana ce wannan ina tare da mijina kake so kayi magana dani”

Hularsa ya tura k’eya yana murza fatar goshinsa yace.”Mijinki wane iri bayan ya sake ki kada kiyi tsammanin bana bibiyar Lamuranki.”

Kaina na sunkuyar kasa ina mamakin al’amarin……Muryar Yaya Aminu naji a fusace! yace.”Alhaji wa kake da suna.? Kada ka kuskura ka shiga gonar da bata ka ba domin a halin yanzu Sa’ida matata ce saboda haka duk sanda ka sake zuwa inda take da niyyar zawarcin ta to zamu tsaya gaban hukuma dani kai.”

Alhaji Nura ya kalleshi sheqeqe! yace.”Aminu kayi shuru ka daina wata fuff*cka ka bari mazaje suyi magana anan gurin kai ka san kanka nima nasan kaina saboda haka dama tsautsayi da kaddara ne yasa har na saketa ka aura yanzu kuma na dawo zan mayar da ita dakinta dan haka kai zan jawa kunne ba kai zaka ja min kunne ba.”

Hannu na daga musu murya na rawa nace.”Ni dai yanzu dik cikin ku babu wani wanda zan komawa auransa dan haka fad’a da cece kuce bai kamace ku ba kuyi hakuri kowa Allah ya bashi daidai dashi.”

Gabad’ayansu suka zuba min ido suna kallona nace.”Ni zan shiga gida sai an jima.” Yaya Aminu sarkin zuciya a fusace! ya bude mota ya shiga da gudu ya bar gurin…..

Shi kuma da sauri ya tare ni “Haba Sa’ida don Allah kada ki tafi ki tsaya mu fahimci juna mana wallahi nayi nadama na gane kece matar rufin asiri na.”

Kallonsa nayi a sanyaye nace.”Ni dai yanzu bani da wata magana da kai Alhaji nasan dai kasan babu kyau neman aure a cikin iddah saboda haka ko na ‘kare iddah bana tsammanin zan komawa auranka.”

Da sauri yace.”Idan saboda Murja kike wannan maganar tuntuni na saketa saboda na gane cewa ita din ba matar rufin asiri bace kece matar arziki Sa’ida shiyasa lokacin dana samun labarin mutuwar auranki raina yayi fari tas saboda nasan Allah ne ya amsa addua ta akan ki.”

Murmushi nayi nace.”Amma naji dadi sosai daka gane gaskiya akan abinda nake fad’a maka dama irin wannan ranar nake so tazo sai dai ina so na tabbatar maka da cewa ni ba zan komawa auranka ba kayi hakuri kaje ka sasanta da matarka.”

A marairace yace.”Babu maganar sasanci a tsakani na da Murja domin shaidaniya ce ina nadamar auranta.”

Ta’be baki nayi nace.”To Allah ya kyauta zan shiga gida a gaishe da yara.” Da sauri ya sake tare min hanya cikin faduwar gabana nake kallonsa.

Yana kokarin magana motar Khalid ta shigo layin…..A hankali motar take tafiya saboda yanda matasa da yara suka kewaye ta hayaniya gabadaya ta cika gurin da kyar suka bashi guri yayi parking ai yana fitowa suka rufu a kansa hannu kawai yake d’aga musu Salmanu da Salim suka bud’a masa hanya ya wuce duk da haka sai da aka samu wa’inda suka bi bayansu.

Kallo guda yayi mana ya kauda kansa sai da suka karasa bakin kofar gidan ya tsaya suka d’anyi magana da abokansa kafin ya shige su kuma suka bar kofar gidan.

Ajiyar zuciya na sauke gabad’aya jikina yayi sanyi da al’amarin yaron………Muryarsa naji yana fadin.”Sa’ida wannan yaron nan ne ko.”? A sanyaye nace.”Eh.” Yace.” Duk da ban kasance ma’abocin kallon k’wallon ‘kafa ba na samu labarin dau’ka’kar da Allah yayi masa kuma ashe shine ya zama Gwarzon shekara ko.”?

Nace.”Eh shine kam.” Yace.”Masha Allah gaskiya na taya shi murna amma yayi aure kuwa.”? Girgiza kaina nayi nace.”Beyi ba har yanzu.”

Yanayinsa ne ya sauya yace.”Don Allah kada kice zaki aureshi domin ke yanzu kin wuce tsaran auransa.”

Da mamaki a fuskata na kalleshi da fadin.”Ashe dama mace tana wuce sa’ar auran Namiji.”?

Shuru yayi yana kallona. Nace.” Idan Allah ya kaddara aurena da yaron babu mahalukin da ya isa ya hana ayi saboda haka kai dai kawai kayi addua akan al’amarin.” Ba tare da na tsaya na saurari maganarsa ba nayi saurin barin gurin.

Tunda na shiga soron gidan nake jin sautin muryarsa na tashi sama-sama da alama shi da Gwaggo ne domin itama naji muryarta………” Ni wallahi ban ta’ba ganin mara hankalin mace irinta ba me za tayi da wannan shashashan mutumin da har zata fita tana magana dashi.” Wannan maganar kunnuwa suka ji “Mara hankali.” sunan da ya kira ni dashi ya masifar ‘bata min rai.

Muryarta naji tana fad’in “Ai kasan halinta ba’a bata shawara ta dauka ni ai cewa tayi dani Aminu ne ashe bashi bane Alhaji Nura to idan gidansa take so ta koma sai ta d’aura niyya.”

Yana kokarin magana na kasara gurin. tsaki yaja da sauri ya bar gurin yana wani irin huci! Kallo na bishi dashi ina mamakin sa.

Magana take kokarin yi na daga mata hannu da fadin.”Gwaggo don Allah bar maganar nan raina a ‘bace yake a halin yanzu.”

Da sauri tace.”Ai dole kiyi bacin rai tunda ke ba zaki dinga fad’ar gaskiya ba.

Murya na rawa nace.”Wai ke Gwaggo dan Allah duk abinda Khalid yayi daidai ne a gurin ki kina jifa yana kirana da shashasha mara hankali sa’ar sa ce ni kome.”?

Shuru tayi min nace.”To idan baki masa magana ba wallahi ransa zai ‘baci dan ba zan kyaleshi ba.” Tace.” Ai gaskiya ya fad’a me kike kufalaci a gurin Alhaji Nura bayan kin san irin zaman da kikayi dashi a baya.”

Nace.” Ni dai kawai addua zaki min bana son k’ananun magana ki nema min alkairi a gurin Allah.”

Tace.”To Allah ya za’ba miki abinda yafi alkairi.” amsawa nayi da ameeen Na shiga d’akin raina duk a ‘bace Gwaggo duk cika bakinta akan Yaron na banza ne zaiyi mata laifi ta gama surutai da cin alwashi a kansa amma daga zarar yazo shikkenan sai ta manta. tayi tai masa rawar jiki tamkar wanda ya sammace ta.

Khalid da asubar fari ya fita motsa jiki can filin wasa na Sharad’a Har muka gama shirye-shiryen mu muka had’a tsaraba muka tafi k’auyen D’ambatta bai dawo gidan ba……Ummatu kuwa yini tayi cikin walwala da farin ciki danginta suka cika gidan suna d’orawa da saukewa.

Sosai ranshi ya ‘baci da ya dawo ya tarar da basa nan wayarsa ya dauko ya lalubi number ta ya shiga gurin kira.

Ina kallon kiran nashi naqu d’aga wa domin yayi masifar bani haushi jiya da daddare ya kira ya kai sau hudu ban daga ba ya hakura da kiran. Kwanciya na gyara kan gadon bunun Baba Ladidi ina jiyo hirarsu a tsakar gidan Gwaggo ta samu ‘yan uwa sai fara’a da farin ciki takeyi su kuma sun ke waye ta kowanne da kwanon abincinsa suna farin ciki da zuwanta garin nasu na gado.

“Sa’ida wai Gwaggo tace ki fito kici abinci.” muryar Jikar Baba Ladadi naji a kunnena.

Ba tare dana tashi zaune ba nace.”Kice gani nan zuwa.” Yarinyar ta juya da sauri ta fita.

Zaune na mike ina gyara dankwalina ya sake kiran wayar……Dauka nayi a hasale nace.”Wai menene.”? Ajiyar zuciya ya sauke yace.”Ki had’ani da Gwaggo za muyi magana.”

“Okey.” abinda nace kenan na kashe wayar gabadaya na ajiyeta. fita nayi tsakar gidan na samesu suna hira sai raha suke a tsakaninsu.

A takaice dai sai da waya ta tayi kwana hudu a kashe sannan na kunna ina sane nayi masa haka saboda na kuntukawa zuciyarsa.

Text messages d’insa ne suka shigo har uku ko wanne sai da na bud’e na karanta dukkaninsu ba’kar magana ce dan zagi na ne kawai beyi ba ya kira ni da shashasha ya kai sau nawa har da fadin Ban san inda yake min ciwo ba. tsabar bakin ciki da takaici ya sani zubar da hawaye…..nasa hannu na goge da fadin.'”Yaron nan ya gama raina min hankali Allah ka cire min jarabar sonsa a zuciyata.

Aikin gidan ake gadan-gadan domin k’wararrun ma’aikata ya d’auko suka ruguje gidan abinka da tsohon gini irin nada sosai aka samu fili ba tare da ‘bata lokaci ba ma’aikata suka fitar da Foundation na zamani aka shiga aikin gidan babu kama hannun yaro…….. cikin sati biyu anyi an gama sai abinda ba’a rasa ba gida yayi kyau mutuka ya haske layin Khalid ya kashe kudi sosai gurin aikin gidan Kofar Gwaggo daban Kofar Ummatu daban komai iri daya ya sa musu set na gado da kujeru da sauran abubuwan bukata Ummatu ta dawo amarya gwaggo ma haka. Ummatu ta dinga jin haushin hakan ‘yan uwanta na zugata dan kakarsa Baito kishin Gwaggo take sosai ta turkeshi da masifa akan lallai itama sai ya gyara mata gidanta ya sanja mata kayan daki.” Yace.”Shikkenan ta bari idan an kwana biyu zaiyi mata. Hankalinta ne ya kwanta jin abinda yace.

Muna can bamu san abinda ke faruwa ba domin tuntuni ya daina kiran waya ta tunda ba dauka nake ba, kwanan mu ashirin da biyar muka fara shirye-shiryen tafiya.
Tsarabar da mutan kauyen suka had’a mana har taso tayi yawa nace.”Baba Ladidi a wace mota zaku kaimu gida da wannan uban kayan.” Tace.”Ai ba za’a rasa a kori kura ba yanzu idan na fita zan shiga gidan Dije mijinta a kori kura yake ja sai ta fada masa cewa gobe zai dauki kaya ya kai birni.” Gwaggo tace.”To hakan yayi Allah ya kaimu goben.” Ta amsa da ameeen ya Allah.

Da daddare ina shirye-shiryen kwanciya ya kira wayar cikin mamaki na dauka ina dubawa ina so naji muryarsa amma kuma ina gudun ya ‘bata min rai da ba’kar maganarsa.

Daga wayar nayi a nutse nayi sallama. ya amsa a cunkushe da fad’in.” Yaushe zaku dawo gida.”? “Gobe idan Allah ya kaimu.” Yace.”Okey to kada ku biyo motar haya zan zo na dauke ku domin nima inaso na gaisa da dangi na kuma nuna musu matar da zan aura.”

Nace.”Okey to sai kazo din.” da sauri na kashe wayar gabana na wani irin fad’uwa! Zai zo ya nuna musu matar da zai aura lallai Khalid wato yana so ya kuntukawa rayuwata tunda ya gane inda na dosa a kansa.

Da kyar bacci ya dauke ni na tashi sukuku don da kyar ma na karya nayi wanka na kimtsa jikina jama’ar garin sai shigowa sallama sukeyi…….Gwaggo kuwa sai share hawaye take sam bata so ta tafi ta bar ‘yan uwanta.

Kiran wayarsa ya tabbatar min da cewa ya shigo garin….da kyar nace.”Idan ka tambayi gidan Malam mai doki kazo gidan ai babu wuyar kwatance.” Yana kokarin magana na datse wayar ina jan tsaki!

Ransa ya ‘baci da abinda tayi masa ya ajiye wayar ya cigaba da tafiya da motar a hankali a hankali yana taka busassun kararen ice.

Jamila dake gefensa a zaune tace.” Ya Khalid baka ta’ba zuwa bane naji kana tambayar kwatancen gidan.”?

Ba tare da ya kalleta ba yace.”Tun ina yaro k’arami rabo na da garin kinga kuwa dole kaina ya juye.”

Tace.”Eh gaskiya ne kuma amma garin ya burgeni wallahi idan mukayi aure zamu dinga zuwa akai akai muna shan iska.” Murmushi kawai yayi ya cigaba da juya sitiyarin motar.

Da kyar suka samu gidan yara yaran k’auyen suka cika bakin motar suna shafawa.

Gwaggo da kanta ta fito domin tar’bar sa sai dai ganinsa tare da Jamila yasa fara’ar fuskarta tayi rauni kadaran kadahan ta amsa gaisuwarta ta jagorance su shiga cikin gidan.

Tsakar gidan akayi musu shimfid’a jama’a maza da mata suka shiga turereniyar zuwa gaisuwa……..Ya fito da kudi ya dinda basu yana Jin dadin yanda suke masa addua da fatan alkairi.

Duk abinda ke faruwa ina daki a kwance ina jinsu inaso na fito domin nayi tozali dashi ina jin takaicin na had’a idona da yarinyar.

Baba Larai ta kalli Jamila da fadin” Wato shine kika biyo shi saboda kada na riqeshi na hanashi tafiya ko to komai dai abinki nice Uwargidansa domin itama Gwaggon baya na take bi saboda haka duk ado da kwalliyar ki baki kama kafafuna ba.”

Jamila ta dinga Dariya tana ‘boye fuskarta ina jinsa yana tare mata da fadin.” Ni me zanyi daku duk kun tsufa mussaman ke Baba Ladidi jikin ki duk jijiya da kai duk furfura babu abinda zaki burgeni dashi.” Baba Ladidi ta riqe baki tana fadin.”Wato wulakanci zakayi min kenan to ai da tsohuwar zuma ake magani kuma dame matar taka tafi ni itama ai bata da wani kumarin kirki dubeta kamar ka busheta tafad’i.”

Gwaggo ta ta’be baki da fad’in “Aikuwa haka yaji ya gani sai yaje yayi ta fama watakila kuma a gaba za tayi qiba.” Jamila shuru tayi jikinta duk yayi sanyi gabadaya taji wani irin tsanar Gwaggo a cikin ranta.

Sai da zamu tafi tukkuna na fito daga d’akin Uffan bance musu ba na kama hanyar fita Baba Ladidi tace.”Ke kuma ta bizaro babu sallama kinyi gaba na lura da akwai abinda ke damunki domin tun jiya kike nukufurci.”

Kallonta nayi da fadin.”Baba Ladidi sau dubu kike so nayi miki sallama ne.” Tace.”Ai wannan salamar daban take da sauran wacce mukayi.” Nace.”To shikkenan mu zamu tafi sai an kwana biyu.” Tace.”To Allah ya sadamu da alkairi muna jiran tsammani Allah ya kawo miki miji nagari muzo musha biki.”
A zucci na amsa da ameeen nayi saurin ficewa daga gidan….

*96*
Jikin motar suka same ni a jingine kauda kaina nayi har suka karaso gurin ‘yan uwa da abokanan arziki sun kewaye motar sai bankwana suke mana Gwaggo sai hawaye take sharewa Baba Ladidi na taya ta nace.”Dan Allah sallamar ta isa haka Gwaggo shigo mota mu tafi idan kuma baki gaji da zama a garin ba sai ki koma ki zauna mu dai tafiya zamuyi.” Baba Ladidi tace.”Rufe min baki ja’ira kawai dama ai ke na lura kamar dole akayi miki kika zauna damu komai abinki garin Dambatta shine tushen ki.”

Yanda take masifa tana tada jijiyar wuya abin ya bani dariya gaban motar na bude na zauna da fadin.”To ni dai na shiga mota Allah ya kaddara saduwarmu.” Jamila tayi kicin-kicin da fuska ganin na zauna mata a mazauni ni kuwa ina sane nayi hakan domin da ita dashi dik neman rigima nake dasu.

Gwaggo da kyar ‘yan uwa suka barta ta shiga motar Shi kuma ya tsaya yana sallamarsu sosai yayi musu rabon kudi tamkar wanda bai san ciwonsa ba.

Kokarin bude motar yake ya ganta a tsaye tasha kunu yace.”Jamila shiga mota mu tafi mana.”

A marairace tace.”Yaya Khalid ai ta zauna min a mazaunina.”

Cikin motar ya duba ya ga yanda na wani ‘kame a zaune kaina na dauke ina sake cin magani……Wani irin kwarjini tayi masa ya kalleta da fadin.”Ki bata guri ta zauna mana.”

Ko kallonsa banyi ba, Gwaggo tace.”Jarumi wai tsayuwar me kukeyi ne kai da ita.”?

Yace.”Gwaggo gata nan tayi mata fin karfi ta zauna mata a gurinta.”

Gwaggo tace.”Aa ban gane ba wane irin fin karfi kuma.”?

Yace.”Gwaggo kamata yayi ace Matata itace a kusa dani to ita kuma aunty Sa’ida saboda neman fad’a ta zauna mata a guri.”

Gwaggo rai a bace tace.”Au motar daga gidansu tazo da ita kenan? ashe har an daura auran naku babu labari to ai shikkenan ke Sa’ida fito mata daga gurin zama sai muje mu samu motar haya inace dai duk mota mota ce kuma zamuje gida kalau.”

Kokarin fitowa take daga motar yayi sauri mayar da ita da fadin.” Yi hakuri ki zauna.” Gwaggo taja tsaki da fadin.” Yo idan ba tsiya ba ya za’ayi tace lallai sai ta zauna a kusa da kai inace da ita da Sa’idar duk daya suke.”

Girgiza kansa yayi yace.”Aa ba daya suke ba wannan auntyna ce ita kuma wannan wife d’ina.”

Tace.”Kai kasan wani Wife ka shiga mota mu tafi kawai.” Juyawa yayi ya kalleta duk jikinta yayi sanyi yace.”Yi hakuri ki shiga ki zauna kusa da kishiyarki Gwaggo muje gida.”

Rai a bace tasa hannu zata bude motar yayi saurin bude mata yana rarrashinta hakan yasa taji sassauci a cikin zuciyarta.

Sai da ya tabbatar ta zauna sosai sannan ya rufe motar ya bud’e mazauninsa ya zauna da bisimillah a bakinsa………..A hankali na sauke ajiyar zuciya a cikin raina dama babban burina na kuntatawa yarinyar naji dadi sosai da ranta ya ‘baci.

Shuru motar babu mai magana sai dai shi jefe-jefi yana amsa waya tinda ya zauna nake satar kallonsa gabad’aya yaron ya gama tafiya da imani na yau yayi ado cikin manya kaya riga tazarce ta shadda kanshi da hula irin ta kanawa yayi wani kwarjini da kamala babu wanda zai ce bashi da iyali saboda yanda Allah yayi masa suttura ta kowane bangare.

Kasuwar ‘yan kaba yayi parking gilashin motar ya sauke yayi magana da daya daga cikin masu siyar da kayan miya yace.”Yana son kayan miya masu kyau.” Motar ya bude ya fita sukayi magana ya bashi kudin yana tsaye yasa masa komai buhu a bayan motar motar ya kunna muka bar gurun.

Gwaggo tace.”Kai kuma me za kayi da uban kayan miya haka.”? Yace.”Gwaggo ke na siya wa kina min miyar ki mai dadi.”

Murmushi tayi tace.”Aikuwa nagode za kuwa kasha miya.” Yace.”Tom nagode Gwaggo yanzu idan mun isa gida zan tura kasuwar Janguza a siyo kaji da zabi ko.”

Tace.”Aa sai dai ka bari a kwana biyu tukkuna domin mutanan Dambatta sun bamu kaji masu yawa motar tsarabar mu nasan ta isa gida tunda tun safe direban ya tashi.”

Yace.”Tom mungode kwarai.” shuru motar babu wanda ya sake magana ringing din waya ta ya katse shurun…….Alhaji Nura ne saboda mugun haushin yaron yasa na daga wayar murya ta na gyara yanda za tayi dadi na fara magana a hankali-hankali wanda duk ‘kwa’kwar mutum ba yanda za’ayi ya ji.

“Eh wallahi nayi tafiya ne zuwa kauye amma yanzu gamu a kan hanya okey kada ka damu Alhaji kasan komai nufin Allah ne.” Shuru nayi ina sauraran kalaman da yake min mirmushi nayi ina sake yin k’asa da murya nace.” Haba dai yaushe zan wahalar da kai kazo d’auka na ka huta kawai tunda yanzu gani tare da direba.”

Wani irin cin birki motar tayi! Gwaggo da take gyangyadi ta bude ido da sauri tana salati.

Kallonsa nayi sai huci! yake yana zufa(gumi) “Fitar min a mota.”! abinda ya fada kenan idonsa yayi jajawur!! Gwaggo tace.” Lafiya me yake faruwa ne.”?

Bai saurareta ba ya bude min mota kokarin tura ni waje yake sai kyarmar jiki yake.

“Khalid wai meye haka bana son wulakanci fa.”

”Kin san Allah sai kin fitar min a mota tunda dai ni ba direban ki bane.”

Shuru nai ina kallonsa nace.”Idan na fita a mota a nan gurin wace motar ce zata d’auke ni.” ?

“Ke kika sani malama ki fita tun kafin nayi miki rashin mutunci wallahi.”

Dariya nayi ina kallonsa kawai naji ya angiza ni waje nayi saurin dafe motar raina yayi masifar ‘baci!

Gwaggo kuka tasa da fadin.”To tunda ka kore ta a motar ka nima ka bude min mota na fita mara mutunci kawai.”

Ko kallonta beyi ba ya figi motar da karfi suka bar gurin……Sakin baki nayi ina kallon hanyar da suka wuce ikon Allah kenan mirmushin takaici nayi na girgixa kaina. waya ta na dauka number Alhaji Nura na laluba kiransa nayi akan yazo ya dauke ni na bashi kwatancen gurin.

Ranar da ake ‘kwallara wa itace ta dame ni na samu inuwa na zauna ina mamakin rashin mutumin yaron nasan kishi ne ya rufe masa ido har yasa ya yi min wannan rashin mutuncin.

“Mara mutunci kawai wato har kayi arziki da zaka dinga wulakanta ‘yan uwanka to shikkenan zamu isa gidan Wallahi sai na samu Ubanka duk na sheda masa abinda kake yi ni mai zanyi da Rabi da Uwarta ai sun cutar dani tunda suka had’a ka aure da wannan afiruwar yarinyar da ido sai kace na tsaka nasan itace ta zuga ka ka kori ‘yar uwarka a motar ka.

Jamila ta fashe da kuka da fadin.” Wallahi Gwaggo babu ruwa na ni ban san abinda ya had’a su ba kawai naji suna mayar da magana a tsakaninsu.

A fusace! tace.” Rufe min baki munaf*cka kawai ai duk sharrin ku sai dai ya koma kanku masu mugun hali kawai.” Jamila kuka kawai take tana shar’be majina…….Yana jinsu yayi musu shuru abinda ya dameshi shi ya dameshi wai kamar shi zata kira shi da direba abin yayi masa zafi mutuka. wani irin tsanarta yake ji a zuciyarsa ita da bazawarin nata.

Koda suka isa gidan Gwaggo taga yanda ya sauya bai burgeta ba zaginsa kawai take tana cin mutuncinsa sosai tayi masa tatas sannan tace ita bai burgeta ba tunda arzikinsa ya zama na izgilanci.

Tana shiga gidan taga kayan tsarabar su jibgi guda a kicin ajiyar zuciya ta sauke ta shiga dakinta ta zauna tana bin ko’ina da kallo sam hakan be burgeta ba hankalinta na kan Sa’ida hawaye suka shararo mata tace.”Allah kayi min maganin Rabi da Uwarta Baito.

Ya jima a motar a zaune kafin ya fito ya shiga gidan…….Dakin Gwaggon ya nufa ya sameta tana kuka duk ta rasa yanda za tayi.

Da hannu ta nuna masa kofa da fad’in.”Ka fita bana son ganin ka aini duk mutumin da zai tozarta Sa’ida to babu ni babu shi har abadah kuma wannan gyaran gidan da kayi sam baka burge ni ba gwara zamana a Danbatta akan na zauna a karkashin inuwarka.”

Juyawa yayi ya fita daga gidan….yana kokarin shiga motar shi mahaifiyarsa ta kirashi babu yanda ya iya haka yaje ya sameta itama ta rufe shi da fad’a dan Jamila tana kuka wurjajan ta shiga gidan.

Tace.”Wato kana fifita Sa’ida akan matar da zaka aura ko? kada fa ka manta Jamila ‘yar dan uwana ce kuma matsayi biyu take dashi a gurinka mai zai sanya a hada baki da kai aci mutuncin ta.

Rashin abin cewa yasa kawai ya bata hakuri Amma ranshi ya baci da abinda Jamilan tayi masa dole yaja mata kunne mutukar tana bukatar zaman lafiya dashi.

Yana fitowa ya shiga motar da sauri hanyar Dambatta ya nufa gabad’aya nadama ta baibayeshi sai tunanin halin da take ciki yake.

Alhaji Nura na isa da motarshi shima ya isa gurin Kusan a tare suka fito daga motar…….Kallon kallon aka shiga yi Khalid zuciyarsa ta sake yin duhu yana ji tamkar yaje ya sha’ke masa wuya ya huta da ganin fuskarsa .

Da sauri ya karasa inda take tsugune…..”Ki tashi ki shiga mota mu tafi” Mik’ewa nayi na ratse shi zan bar gurin.

Hannuna ya ri’ke da sauri na juyo rai a ‘bace nace.”Sakar min hannu ko kuma ranka ya ‘baci yanzu.”

“Me zaki min na ‘bacin rai ki burge shi.”? Ido jawur nake kallonsa yana wani irin huci! yace.” Babu wani abu na ‘bacin rai da zakiyi min ki burgeshi tunda nasan dake dashi na riga na gama yi muku illah a rayuwarku so duk wani abu da zakiyi min ba zan damu ba.”

Hannuna na fizge da sauri nayi nufin barin gurin. sai yayi gaggawar kamo ‘kuguna ya had’a bayana da ‘kirjinsa ri’ke ni yayi sosai a jikinsa.

Alhaji Nura ya rintse idonsa yana jin wani irin d’aci a ma’kogwaronsa. wani irin kishin yaron ne ya taso masa.

Kokarin kwace jikina nake yana sake matse ni hankalina ya tashi gashi motoci na wuce wa a kan titi.

“Khalid bana son iskanci ka sake ni ko bakaji ba.”

Sake rike ni yayi ya tsirawa abokin gamayyarsa ido………Alhaji Nura jiki a sanyaye ya karaso gurin da fad’in.” Kai Yaro ba sai kayi haka ba sannan zaka nunawa duniya cewa kai din mara tarbiya ne.”

Sosai yaji ciwon maganarsa sai ya share cikin sigar ‘kunsa bakin ciki yace.”Ashe kai sai yanzu ka san bani da kunya ai na dauka ta fad’a maka cewa ita d’in saura nace sai da naci na rage ka samu so kaga k’arshen rashin kunya kenan.”

Alhaji Nura ya goge gumi da hankicin rai a ‘bace yace.” Ta fad’a min yanda al’amura suka faru ai dama shaid’ani ne kuma don kayi mata fyad’e a farko hakan ba zai hanani auranta ba tunda ina mata sahihiyar k’auna.”

Tsaki yaja yace.”Kaga malam kaja motar ka kayi gaba wallahi ba zata shiga motarka ba na fada maka magana guda.

Alhaji Nura yace.”Kai kada fa kayi min rashin kunya anan gurin ka sake ta idan ba hakaba yanzu na had’a ka da hukuma.”

A fusace! yace.”Idan uwar hukuma zaka had’ani da ita a shirye nake da kai dasu Mtsww.” Ya ‘kare maganar yana jan tsaki.

Kallona yayi idonsa sunyi jawur! yace.”Sa’ida kina kallon yaron nan yana kokarin zagina ko.” sunkuyar da kaina nayi gabadaya na rasa yanda zanyi Yaron ya galabaitar dani gurin rikon tsaurin da yayi min ga wani irin tausayin Alhaji Nura da ya rufe ni.

“Khalid ka sakar min jiki dan iska mara mutunci kawai.” A zafafe ya juyo dani muka kalli juna gani nayi fuskarsa ta rikid’e….”Ni ne dan iska.”? K’asan makoshi yayi maganar……Kirjinsa na kaiwa duka…ya had’e ni da kirjinsa sosai ya matseni gabansa na fad’uwa nawa ma haka. Ina kokarin kwace wa yayi gaggawar tallafo fuskata bakina ya kama da nasa ya ri’ke da kyau wani irin sha yake wa bakina jikina da nasa sai karkarwa yake.

Alhaji Nura rintse idonsa yayi jikin motarsa ya dukufa hawayen takaici da bakin ciki naso ya kufce masa.

Kafafuna ne sukayi sanyi na dinga kokarin faduwa a gurin kawai ya tallafe ni daukar yara yayi min ya nufi motarsa zaunar dani yayi ban san inda kaina yake ba sai lokacin daya kunna motar tukkuna na dawo nutsuwata can na hango Alhaji Nura jingine a motarsa kamar ya d’ora hannu aka yayi ta kurma ihu!

Wasu zafafan hawaye ne suka kwace min na kalleshi yana driving hankalinsa kwance…………Hannu na kai da niyyar kwad’a masa mari yayi gaggawar ri’kewa motar tayi tangal-tangal ta sauka daga kan titin da hannu d’aya ya tsayar da ita ya juyo yana kallona da fadin.” Mari na zakiyi.”? hawaye na share nace.”Shaid’anin banza da wofi kawai .”

Sakar min hannu yayi yana murmushi yace.”Kema ai shaid’aniyar ce.” Ya kunna motar yana kokarin tafiya na rike sitiyarin da fad’in “Sauke ni ko kuma na haddasa mana accident.”

Shuru yayi yana kallona ina huci nace.”Gwara min Alhaji Nura akan ka mara mutunci wai kai kayi arziki da kudi da mota shine zaka tozarta ni ko.”

Dariya yasa ya mayar dani shashasha! “Ni har yanzu banyi arzikin da zanyi izgalanci da wulakanci ba laifi kika aikata min na hukunta ki daidai da abinda kikayi mi.”

Sitiyarin motar na hau murd’awa motar ta dinga gargada tana cijewa, hankali a tashe yace.” Dan Allah kiyi hakuri kada ki kashe mu lokacin mu beyi ba tukkuna ina bukatar nayi doguwar rayuwa kafin na mutu.”

Cigaba nayi da murd’a sitiyarin motar na wani irin abu cikin tashin hankali ya cire key din ri’ke ni yayi ya matse tsam a jikinsa sai kyarma yake yana had’a gumi! hakuri yake bani akan abinda yayi min.

Jikina ne ya mutu nayi lakwam a jikinsa gabad’aya ya kashe min jiki da yanda yake min magana kasa-kasa yana marmatsa min sassan jiki.

*97*
Sai da nayi ya’ki da zuciyata sannan na kwace kaina daga hannunsa kallonsa nayi idanuwansa sunyi jawur! sai wani irin kallo yake min yana cizan lips d’inshi harararsa nayi tare da jan tsaki kaina na dauke tare da gyara mayafi na da ya sauka kasan kafad’ata.

Ina ji yana saki wani irin nishi kafin ya kira sunana can kasan ma’koshinsa.

Kallonsa nayi fuskata a ‘bace. Yace.” Ina jin feelings ya za’ayi.”? Cikin fad’uwar gaba nace.”Ba zaka kunna mota mu tafi ba ko.”? Kafin yayi magana motar Alhaji Nura tazo ta wuce fuuuuu! gabad’ayanmu muka bi motar da kallo.

Kanshi ya shafa yana wani killer smile yasa key a motar ya tasheta muka bar gurin.

Takaici da b’acin ran abinda yayi ya sanya na dinga tsaki Allah-Allah nake mu isa gida na huce bacin rai na.

Ya kalle ni da fadin.”Auntyna amma kin dan samu sassauci ko.”?

A wulakance na kalleshi ya kanne idonsa guda yana kallona da munafikin murmushi a fuskarsa.

Kauda kaina nayi daga kanshi ya dora hannunsa akan nawa da sauri na fizge hannu rai a ‘bace nace.”Khalid wallahi idan baka daina ta’ba min jiki ba zaka sha mamakin abinda zanyi maka.”

Ba tare da ya damu ba yace.”Me zaki min.”? shuru nai ya cigaba da cewa.” Naga kamar kina so ne shiyasa nake so na rage min zafi okey tunda bakya bukata shikkenan.”

Tsabar b’acin rai bai bari nace masa komai ba kawai na kauda kaina ina kallon hanya a haka muka isa gida babu wanda ya sake kula d’an uwansa.

Zaune a tsakar gida na same ta ita da Uwale suna raba tsaraba ganin shigowata yasa ta sauke ajiyar zuciya tana godewa Allah cikin mutuwar jiki na shiga daki na kwanta kan sabon gadonta rufe idona nayi ina tunanin abinda ya faru a tsakanina dashi.

Koda ya shigo gidan Gwaggo kin kallonsa tayi ta cigaba da abinda take yi Uwale ce kawai tayi masa magana, cikin jin haushi yace.”Gwaggo sai ki daina zagi na gata nan na kawo miki babu abinda ya sameta.”

Uffan ba tace masa ba cikin b’acin rai ya juya zai fita tace.”Kasa a kwashe wannan kayan da ka siya akan hanya domin na raba kashi biyu na aikawa da uwarka nata ta dawo min dashi ban san abinda take nufi ba.”

Shuru yayi yana kallon kayan shi kam ya rasa me yake da mun Ummatu kishi take da Gwaggo ko meye dalili oho.

Yana fita kofar Ummatun ya shiga nan ya same su suna ta hayaniya sai zagin Gwaggo suke da zuriar ta.

Tsabar ‘bacin rai ya hana shi shiga dakin ya tsaya a bakin kofa yana tambayarta kai tsaye tace.” Bata bukata yanda ya raba musu gida to ya raba musu cefane saboda haka idan yana bukatar albarka a rayuwarsa to itama yaje yayi mata siyayya ita kadai ba tare da wani ba.

Dakinsa ya bude ya kwanta abin duniya ya taru yayi masa yawa masifar Gwaggo da Ummatu sai masifaffiyar sha’awar da take damunsa birgima kawai yake kan gadon yana rungume filo ji yake tamkar yaje ya turmushe ta ya biyawa kansa bukata babu wacce yake muradi sai ita lips d’inshi yake ciza yana turje-turje a gadon a haka Jamila ta shiga dakin ta sameshi.

Ganin yana juye-juye yasa da sauri taje ta zauna kusa dashi tana tambayarsa.

Jajayen idanuwansa ya tsira mata yana kallonta sama da ‘kasa.

“Yaya Khalid me yake damun ka.”? Hannunta ya janyo ta fad’a jikinsa rikon tsauri yayi mata ya dinga mutsika ta nonowanta yake luguda ita kuma sai kokarin kwace wa take tana so tayi kuka a sarqe yace.” Ki barni na samu sassauci.”

“Yaya Khalid ka bari don Allah.” tafad’a tana kwace jikinta Ture ta yayi ta kusa faduwa. wuyan rigarta ta gyara sai zare ido take.

Da hannu ya nuna mata kofa da fadin.”Tashi ki fita tunda baki da amfani.” Jiki a mace take kallonsa ya sake buga mata tsawa da fadin.” Ba dake nake ba.” Simi-simi ta mike tsaye hanyar fita ta nufa ya bita da wani wulakantaccen kallo kwata – kwata yarinyar ba tayi masa ba bata da ‘kira da zubi irin na mata saboda zai rage zafi da ita take masa hauka shiyasa yaji gabadaya abin ya fice daga ranshi.

Saukowa yayi daga gadon ya dauki jallabiyarsa yasa gabanshi ya dan fito ta saman rigar bai gama kwanciya ba.

Daga bakin kofa ya tsaya yana magana da mahaifiyar tashi….Tace.”A’a bani da lemon tsami sai dai idan siyo maka za’ayi.”

Ba tare da yayi magana ba ya kama hanya ya fita kofar Gwaggo ya shiga, lokacin ina tsugune bakin famfo ina daura alwalar la’asar tsayawa yayi yana kallonta hankalinsa yayi masifar tashi ganinta da daurin kirji jikinta ko’ina a cike babu rama, ya dinga wani irin nishi jikinsa sai kyarma yake.

Ina mikewa na ganshi tsoro ya bani matu’ka kallon sama da kasa nayi masa na ganshi duk a firgice! Dauke kaina nayi na wuce na barshi a gurin.

Jin sawun tafiyarsa a baya na yasa da sauri na shige dakin yaron tsoro yake bani.

Zuwa yayi ya kwanta rashe-rashe kan gadon Gwaggo ta bishi da kallon mamaki carbin hannunta ta cigaba da ja tana nazarin sa.

So nake na shirya jikina amma saboda tsabar kallon k’urrulan da yake min yasa gabad’aya duk na rasa yanda zanyi.

Kayan na d’auka na fita dasu wani karamin daki na shiga na shirya jikina na fito.

Har yanzu yana kwance a gadon sai juye-juye yake dadduma na shinfida na tayar da sallah ba tare na kalli inda yake ba.

“Kai kuma lafiya kazo kayi min kayi rashe-rashe akan gado.”? shuru yayi mata idonsa a rufe sai shafa marar sa yake.

” Khalid kana jina ko.”? Jajayen idanunsa ya bude yana kallonta. Gwaggo ba yarinya bace ta gane abinda ke damunsa.

“Gwaggo bani da lafiya.” Can kasan ma’koshi yayi maganar.

Ba tare da nuna kulawa ba tace.” Me yake damunka.”? Shuru yayi mata. Tace.”Tom tunda ba zaka fada ba ka tashi ka fita ka bani guri.

A sanyaye yace.”Gwaggo aure nake so marata ciwo take.” shuru tayi tana kallonsa.

Ya mike zaune yana kallonta tace.”To ai kana da matar a hannu ba sai kawai a daura auran ba.”

Shuru yayi ya kasa magana sai cizan lips d’inshi yake……Mikewa tayi ta fita daga dakin….juyowa yayi yana kallona na watsa masa harara kasa-kasa nace.”Fitinanne kawai.” ashe yaji abinda nace sai kawai na ganshi a gabana.

Da sauri naja baya da fadin.”Meye haka.” ? “Wane suna naji kina kira na dashi.”? tsaki naja tare da kokarin barin gurin.

Hannuna ya janyo nayi zaman d’abaro a jikinsa da sauri ya cusa hannuwansa cikin hijabin jikina Brest d’ina ya kama da duk hannuwansa yana wasa dashi.

A tsorace na fizge jikina gabana na wani irin fad’uwa nace.” Wato Kai baka da mutunci ko.” Mikewa tsaye yayi nayi saurin kaucewa danne ni yayi ya had’e da bango (garu) gabana ya dinga duka! “Ki taimaka min auntyna.” a shaqe yayi maganar.

Ihu! ne kawai ban kurma ba idanuwa na duk sunyo waje…..”Khalid matsa daga jikina kada Gwaggo ta shigo ta same mu a haka.”

Kai ya girgiza da fadin.”Ki bani bakin ki nasha shi nake muradi.

Hawayen bakin ciki suka kufce min ni kam Allah ya had’ani da jaraba.

Motsin shigowar Gwaggo mukaji da sauri ya matsa daga jikina ta shigo dakin ganin mu daf da juna cikin alamun rashin gaskiya yasa tayi kasaqe tana bin mu da wani irin kallo…….Yun’kurin barin gurin yayi kawai ya fad’i kasan kafet…..tsakanin ni da ita ban san wanda ya riga wani zuwa inda yake ba.

“Khalid menene? me yake damun ka.”? Gwaggo ce ke masa wannan tambayar ni kuwa hannunsa kawai na rike sai zare ido nake a kanshi.

Zaune ya miqe da fadin.” Cikina ne ke ciwo sai rashin kwarin jiki Gwaggo bacin ranki ne ya janyo min shiga damuwa.”

Hannunta na rawa ta dauki d’an karamin kofin data shigo dashi dakin tasa masa a bakinsa da fadin.”Ga magani na had’a maka kasha zakaji sassauci.”

Hannunsa ya d’ora akan nata ya shanye ruwan lemon tsamin tas sai wani irin gumi yake jikinsa na wani irin rawa.

Ya kai kimanin rabin awa a dakin kafin ya samu sassauci yace wanka zaiyi Gwaggo da kanta ta had’a masa ruwan wanka ya shiga yayi ya daura alwala ya nufi massalaci.

Gwaggo kuwa ta kudurci wani abu a zuciyarta tana ganin shine maslaha ga rayuwar jikokin nata.
*****
Bayan sati hudu Khalid yayi tafiya zuwa kasar chadi inda k’ungiyar *Manchester* na kasar suka gayyace shi wasa a babban filin wasan su dake kasar….Tafiyarsa kasar Chadi tasa hankalina ya kwanta na sake a gidan ina sabgogina wanda ada bana iya sakewa ina yi saboda yanda yake takurawa rayuwata.

Ranar wata Alhamis muna zaune nida Gwaggo muna hira tace.”Sa’ida ni kuwa me zai hana ki rabu da zawarawan nan dake bibiyar ki.”

Nace.”Me yasa kika ce haka Gwaggo.”? a nutse tace.”Kwanakin baya da muna magana da Babanku Ibrahim akan lamarin auranki sai yake cewa da zaki amince da auran Khalid da yaji dadi yana ganin kamar idan kin auri yaron matsalar ki tazo karshe to nima hankali na yafi kwanciya da ki auri dan uwanki domin kwata-kwata bana sha’awar ki koma gidan Aminu ko Alhaji Nura domin gidan jiya zaki koma.

Shuru nayi na minti biyu kafin nace.”Gwaggo yanda yaron nan yake nunawa kamar yafi k’arfi na bana so azo ayi abu rayuka suna ‘baci kin san dai Ummatu bata k’aunata ko.”

Tace.”Sa’ida Rabi bata isa ta hana abinda Allah ya hukunta ba ki kwantar da hankalin ki kuma khalid karya yake yace yafi karfin ki shin ko baki ga yarinyar da zai aura bane? kin fita komai na mata saboda haka ni yanxu amincewarki kawai nake bukata.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Shikkenan Gwaggo Allah ya za’ba abinda yafi alkairi.” Cike da jin dadi ta amsa da ameeen insha Allahu dake dashi zakuyi farin cikin wannan al’amarin.
Cikin zuciyata na amsa da “Allah yasa haka.”

To bayan ya dawo gida da kwana biyu Gwaggo ta kirashi domin ta sheda masa halin da ake ciki……….Shuru yayi bayan ya gama sauraranta tace.”Jarumi kayi shuru ko ba zaka aureta ba.”?

Babu wata alamar farin ciki a tare dashi yace.”Gwaggo don Allah ku bar maganar nan ni bana da ra’ayin auran bazawara a halin yanzu.”

Gwaggo taji kamar ya soka mata wuka a makoshi murya na rawa tace.”Abinda za kace kenan.”? shuru yayi yana duba wayarsa.

Wulakantaccen kallo nayi masa nace.”Khalid ba fa kaine autan maza a duniya ba kada ka dauka rasa mijin aure nayi A’a duk wannan abinda ake ina bin umarnin iyayena ne bani da wata damuwa idan baka aureni ba sai me? akwai dubban mazan da suka fika komai a duniya.”

Ba tare da ya kalle ni ba yace.”An san da haka me yasa aka zo ana min magiya da ‘yar murya kije ki auri maza dubu bai dami Khalidu ba.”

Hawayen bakin ciki suka ciko idona nace.” Kana cewa ba zaka auri bazawara ba tun farko wane shegen ne ya lalata min rayuwa .”?

Kallona yayi yana huci! yace.”Ni kike zagi.”? a harzuke! nace.”Eh na zage ka ko zaka rama ne.”?

Gwaggo ganin al’amarin yayi zafi sai ta shiga tsakani rai a bace tace.”Ka tashi ka tafi tunda ba zaka bi umarnina ba babu komai.”

Mi’kewa yayi ba tare da wata damuwa ba ya fice daga dakin……Takaici da bakin ciki suka taru sukayi min yawa. kwanciya nayi kasan kafet hawaye masu zafi suka dinga zuba a saman fuskata.

*98*
“Ki daina kuka kina damun kanki komai abinsa sai ya had’aku ku biyu ya aura mutukar yana kaunar zaman lafiyarsa.”

Zaune na mike ina kallonta da sauran hawayen a idona nace.”Gwaggo don Allah ku rabu da yaron nan tunda baya so babu dole a cikin al’amarin nan insha Allahu Allah zai kawo min miji daidai da rayuwata na aura.”

Girgiza kanta tayi tace.”Sa’ida insha Allahu baki da miji sai Khalid na gaji da wannan al’amarin shima tsiya ce kawai amma yana sonki yana so ya ‘bata mana rai ne saboda haka kada ki damu Khalid ko yana so ko baya so sai ya had’aku ku biyu ya aura.”

Ina kokarin magana Kawu ya shigo dakin ya shirya cikin manya kaya da alama fita za’ayi hankalinsa a kaina suka gaisa da Gwaggo

A sanyaye na gaishe na sunkuyar da kaina ina wasa da yatsun hannuna…..Cikin rashin jin dadi yace.”Sa’ida ina fatan lafiya naga idonki yayi jawur wani abu ya faru ne.”?

Hawaye ne suka zubo min nasa hannu na goge ina girgiza kaina.

Gwaggo tace.”Ya zaki girgiza kai bayan akwai dalili.” Kallonsa tayi da fadin.” Yanzu nan Jarumi ya fita bayan ya gama rashin arziki na zaunar dashi na sheda masa hukuncin da muka yanke kai tsaye yace shi ba zai aureta ba shine abin yayi mata ciwo take kuka.”

Kawu Ransa ya ‘baci yace.”To tunda haka ya za’ba shikkenan itama Jamilan ba zai aureta ba sai yaje ya nemi wata.” yana gama maganarsa ya bar gurin cikin bacin rai.

Gwaggo tace.”Hakan shine hukunci dama ai ba kowa ne yake zuga shi ba sai uwarsa da ‘yan uwanta to itama Jamilan sai dai ta hakura yaje ya nemi auran a wani wajen.”

Ummatu tana share hawaye ta d’aga labulan dakin tace”Gwaggo wallahi ni bani na hana yaron nan auran ‘yar uwarsa ba ku daina daukar alhakina.”

Gwaggo tace.”To idan bake bace wacece Rabi aini babu abinda zance dake tunda dai bakya so ya yaron ki ya auri Sa’ida to itama Jamila sai ta ha’kura haka shi yafi alkairi.”

Hawaye ta share da fad’in “Ni dai kiyi masa magana ya janye maganar yi min kishiya meye laifina a cikin al’amarin da har za’ayi min kishiya.”

Gwaggo murmushi tayi tace.”Ai ba zan hana abinda Allah ya halasta ba Rabi ke kin kasa tursasa d’anki ni kuma sai kizo ki sani na tauyewa d’ana rayuwa idan mata uku zai aura ba zan hana shi ya more rayuwarsa ba.”

Ummatu hankalinta yayi masifar tashi tana kuka ta koma sashenta, zama tayi tana tunanin mafita babu shakka dole ta zauna da yaron akan al’amarin dan tana ji tana gani ba zata bari ayi mata kishiya ba.

Sai can dare ya dawo gidan yana kokarin bude dakinsa ta fito daga daki ya kalleta da mamaki a tare dashi yace.”Umma baki bacci ba.’?

Tace.”Eh na zauna zaman jiran shigowarka.”

Yace.”To Allah yasa lafiya.” Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace.”Khalid babanka duk ya sheda min abinda yake faruwa ashe sun yanke maka hukuncin auran Sa’ida ban sani ba.”

Yace.”Eh nima dazu Gwaggo ke sheda min sai dai na nuna mata cewa bana ra’ayin hakan.”

Tace.”Ka aureta na baka Umarnin hakan.” Wani sanyi yaji ya sauka a zuciyarsa dama abinda yake so yaji kenan daga gurinta.

Ya nuna kamar baya murna da al’amarin yace.”Umma kina ganin babu matsala ba naso keda ita ku dinga samun matsala tunda jininku bai had’u ba.”

Tace.”Babu matsala mutukar zaka nuna mata cewa ni mai muhimmanci ce to zamu zauna lafiya.”

Yace.”Umma ba zan iya had’a ki da kowa ba saboda ke mahaifiyata ce babu wata ‘ya mace da zan aura ta wulakanta min ke sabida haka ki kwantar da hankalin insha Allah ba zan bari ki wulakanta ba.”

Murmushin jin dadi tayi tace.”To nagode yaron kirki bari na kawo maka abinci.” Yace.”To nagode Ummana.” kicin ta nufa shi kuma yana murmushin jin dadi ya bud’e dakinsa ya shiga cike da nishadi ya cire kayan jikinsa domin ya watsa ruwa.

Washe gari da safe kafin ma mahaifinsa ya tare shi da maganar shi ya rigashi bayan sun gaisa yake sheda masa da cewa ya amince zai had’asu su biyun ya aura.

Yace.” Hakan shine yafi maka alkairi da zaman lafiya saboda haka sai ka fara shirye-shirye domin ba zamu ja dogon lokaci ba.”

Yace.”Insha Allahu komai za’ayi komai cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.” Kawu barin sa yayi a tsugune a gurin ya shige daki……Mikewa yayi ya nufi kofar Gwaggo domin su gaisa.

Kawu ya kalleta da fadin.” Kin Umarci Yaron nan da ya amince da bukatarmu ko.”? shuru tayi tana kallonsa yace.”To ki sani hakan da kikayi ba zai hana ni na ‘kara aure ba domin tuntuni mun riga mun gama daidaitawa da matar da zan aura dan haka sai ki shiga nutsuwarki.” Ummatu baki a sake take kallonsa har ya gama abinda yake ya fita daga dakin……Jiki a masifar sanyaye ta nemi guri ta kwanta tana sak’awa da kwancewa tunda take bata ta’ba tsammanin Mijinta zai iya yi mata kishiya ba, hawaye masu zafin gaske suka dinga sauka a fuskatarta.

Khalid yana can dakin Gwaggo yana neman magana lokacin daya shiga dakin tana bandaki wayarta ya hango kan gado yaje ya dauka yana mata binkice duk number da ba tayi masa ba sai da ya goge sai tsaki yake ja yana girgiza kai…….Cikin wannan yanayin ta shiga dakin ta sameshi.

Hannu ta mike ba tare da tayi masa magana ba. ya harari hannun tsaki yaja ya cigaba da abinda yake da wayar.

Da karfi ta fizge wayar daga hannunsa ta fad’i gurin dake tayi wawar faduwa a take komai yayi pieces a gurin.

Gwaggo tace.”Subahanallahi wai me yake damun ku ne sai kuyi ta fad’a sai kace tsofaffin karnuka a haka zakuyi auran.”

Ba tare da yace komai ba ya mike zai fita daga dakin da sauri na wafci wayarsa dake aljihun gaban rigarsa ban tsaya jiran komai ba na buga ta da bango.” Gabad’aya ta watse a gurin.

Ido jawur yake kallona “Kin san kudin wayar nan kuwa zaki buga min ita da bango(garu)

Hannu na daga masa da fadin.” Kaga ban bukaci sanin kudin wayarka ba kawai ka daina shiga sabga ta meye zaka daukar min waya kana duba min.”

Rai a ‘bace yace.”Dole nayi bunkice a wayarki saboda nasan baki da gaskiya ina so ki daina hurd’a da kowane namiji mutukar kina bukatar ki zauna lafiya.”

“Ko an daura min aure da kai baka isa ka hana ni mu’amula da wanda ya cancanta ba namiji ko mace so saboda haka wannan abin bashi ne mafita ba.”

Girgiza kansa ya kalleta da fadin .”Gwaggo kina jina da ita ko.” ? Tace.” Khalid kaine mai laifi ina ruwanka da wayarta ai sai ka bari a daura auran in yaso sai ka fara kafa mata doka da ordar.”

Yace.”Okey kema abinda zaki ce kenan? auran nan fa tilas akayi min.” Tace.” Kaga ba cewa nayi ka ‘bata min rai ba kazo kayi tafiyarka inda zakaje aure tilas akayi maka kuma idan ka kwantar da hankalin ka zai zame maka alkairi.”

Tsugunawa yayi ya kwashi sim card dinshi ya fice daga dakin yana wani irin huci! tsaki naja raina a bace na zauna ina gyara wayata dake tarwatse a gurun.

Tace.”Sa’ida don Allah ku sanyawa zuciyarku ruwan sanyi kece babba ki daina biye masa kuna shashanci na fiso idan kunyi aure ku zauna lafiya ku samu zuria masu albarka.”

Cikin rawar murya nace.”Gwaggo ya kike so nayi ne yaron nan fa ya raina ni kullum nunawa yake kamar shi yake gaba dani sam baya mutunta ni gashi ko wace irin magana idan ya tashi ya fad’a min babu abinda ya dameshi.

Tace.”Hakuri zakiyi dashi Namiji ne koda babu alakar aure a tsakaninku dole ya dinga nuna miki iko da gadara duk da kin girmeshi to ballanatana kuma yanzu da zaki zauna a k’ar’kashinsa dole kiyi masa ladabi da biyayya.”

Girgiza kaina kawai nayi ina tunanin yanda zama na zai kasance da yaron mutukar zai dinga nuna mun gadara da iko to babu shakka zamu kasance cikin fad’a da rashin zaman lafiya.

*BAYAN SATI UKU*
Al’amura suna cigaba da tafiya cikin nutsuwa da kwanciyar hankali Ginin gidan da Khalid yake yayi nisa saura abinda ba’a rasa ba……Har yanzu babu cikakkiyar jituwa a tsakaninsa da Sa’ida ba dai sa fad’a sai dai da kyar suke kula junansu watarana ma haka zasu kwana su yini ba suyi magana da juna ba duk da cewar suna ganin junansu.

Jamila kuwa damuwa mai tsanani ta shiga a lokacin data samun labarin abinda yake faruwa taci kukanta ta k’oshi ta hakura Baito da Ummatu kuwa ai basu hakura ba sai yawon malamai suke wai lallai sai al’amarin auran ya ruguje sun kasa gane cewa komai nufin Allah ne.

Khalid lokacin da ya tashi had’a kayan aure komai iri d’aya ya siya sam bai bambamta tsakanin Sa’ida da Jamila ba abinda yayi wa budurwa shi yayi wa bazawara al’amarin da ya janyo cece kuce a can ‘bangaran Ummatu kowa na fad’in albarkacin bakinsa Jamila kuwa yini tayi tana kuka ta dauka ai tunda ita budurwa ce zai bambamta da bazawara sai taga akasin haka…..K’awayen ta suka zugata akan tayi masa butsu ta nuna bata yarda ba…….Aikuwa ranta ne ya ‘baci ta gwammace bata kira wayarsa ba dan masifa ya balbaleta da ita yace haka yayi niyya idan bata son kayan taje ta bayar shi babu wata mace data isa da sanja masa tsari. kashe wayarsa yayi ya bar ta cikin bacin rai.

Ummatu ma ranta ya baci mutuka amma saboda samun kwanciyar hankalinta a gidan yasa bata nuna bakin cikinta ba yanzu lalla’ba mijin nata take kada yayi mata kishiya shiyasa take masa ladabi da biyayya duk Umarnin sa bata tsallakewa.

Khalid a can Goran dutse bayan reka ya gina katafaran gida na gani na fad’a masoyansa suka cika da murna da farin ciki suna masa fatan alkairi.

Sati guda ana saukar al’kur’ani a gidan kafin a kulleshi aka cigaba da gudanar da shagalin biki…..Gidan Gwaggo cika yayi da mutanan kauyen Dambatta duk sun zo domin nuna farin cikinsu…..Bangaran Ummatu ma hidima take sosai ita da danginta.

Sa’ida tare suke gabatar da komai da Aminiyarta Hauwwa duk wani gyaran jiki tayi abinta sai dai kallo d’aya za kayi mata ka fahimci cewa kamar bata maraba da auran abubuwa da yawa sun tsaya mata a ranta tana tunanin irin zaman da za tayi da yaron kullum yana mata rashin mutunci da nuna cewa ita ba komai bace a gurinshi amma sam Jamila bata firgitata sabida ta san bata isa ta nuna mata komai ba.

Ana ya gobe daurin Aure Yaya Aminu yayi sallama da ita Kin fita tayi Gwaggo tace.”Kije babu kyau wulakanci ai yanzu kuma duk wani mai naci a kanki dole ya hakura tunda gobe idan Allah ya nufa zaki zama matar wani saboda haka kije kiji abinda yake tafe dashi.”

Hauwwa tace.”Nima dai haka na gani ai babu wata matsala.” Nace .” To shikkenan tashi ki raka ni muje.” Tace.” To shikkenan.

Yana jingine jikin motarsa kansa a kasa a nutse muka ‘karasa kusa dashi…….Cike da damuwa ya dago kanshi na sunkuyar da kaina ina jin dan tausayinsa a cikin raina.

“Yaya Aminu ina wuni ina fatan kuna lafiya ya kasuwa.” Cikin alhini da damuwa ya amsa da fadin.”Amarya ya shirye-shirye.”? nace.”Alhamdulillhi.” Hauwwa ta gaishe ya amsa yana dan ‘kallonta.

Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yace.”Sa’ida a lokacin da komai na rayuwata yayi min sauki a lokacin ne kikayi nisa da rayuwata ina cikin wani hali na tsananin damuwa naso ace nayi doguwar rayuwa dake sai gashi Allah ya raba tsakaninmu na samu labarin daurin auranki gobe hankalina ya tashi mutuka daga baya nayi hakuri ba barwa Allah wannan dalilin yasa nace bari nazo nayi miki fatan alkairi Allah yasa haka shi yafi alkairi a rayuwarmu…
*99*
Cikin nutsuwa nace.”Nagode Yaya Aminu ina maka fatan alkairi a rayuwarka insha Allah Ubangiji zai mu sanya maka da mace tagari wacce ta fini komai da komai na rayuwa.” Girgiza kansa yayi cikin wani irin yanayi yace.”Bana tsammanin zan samu kwatankwacin mace kamar ki ni kaina nasan nayi babban rashi a rayuwata.

Murmushi nayi nace.”Kada ka cire tsammani insha Allahu za’a dace.” Murmushi yayi yana girgiza kanshi. hannu yasa a cikin aljihu key ya fito dashi ya miqa min da fadin.” Ga wannan sannan za kiga sak’o na insha Allah.”

Key din na kar’ba ina dubawa “Yaya Aminu wannan fa.”? Yace.” Mota ce na baki kyauta.” shuru nayi ina kallonsa yace.”Gata can acan tsallaken.” da sauri na kalli gefan mota ce ta gani ta fad’a. Hauwwa na zubawa ido da fadin.” Ki taya ni gani Hauwwa.” Murmushi tayi tace.”Kyautar manya kenan Alhaji Mungode kwarai Allah ya kara suttura.” Da fara’a a fuskarsa ya amsa da ameeen ya Allah.

Kallonsa nayi cikin damuwa nace.”Yaya Aminu anya kuwa wannan motar ba tafi karfina ba kuwa.” ? Yana dariya yace.”Kece kika fi karfin mota a gurina idan kuma zaki iya tuka jirgin sama sai na siya miki.”

Hauwwa tasa dariya tana kallona. kaina na sunkuyar gabad’aya al’amarin ya daure min kai.

Yace.”To ni zan tafi Allah ya sanya alkairi yasa gidan zaman ki ne.”

Kaina na dago nace.”Yaya Aminu nagode nagode sosai nima zanyi maka kyauta ina fatan zaka kar’ba hannu biyu.”

Yace.”Duk abinda ya fito daga gurinki ina bukatarsa.

Hauwwa na kalla tana tsaye tana murmushi nace.”Wannan aminiyata ce bani da kamar ta ina fatan idan na baka amanarta zaka riqe da kyau.”

Zuba mata ido yayi yana murmushi yace.”Kai amma nagode da wannan kyautar Nayi miki alkawarin riqe amanar k’awarki.” Murmushi nayi na kalleta da fadin.”Hawwa ga amanar Yayana nan.”

Kallona kawai take tana mamakin hukuncin dana yanke mata. murmushi nayi na kalleshi da fadin.”Ya Aminu bani wayarka nasa maka number ta.” da sauri ya bani nasa masa number.

Ya kalleta da fadin.”To amanata sai na kira ko.” murmushi kawai tayi ta sunkuyar da kanta…..Yana kokarin shiga motarsa Khalid yayi parking din tashi.

Gabana ne ya fad’i! haka kawai nake jin tsoron masifar yaron.

Da sauri nace “Yaya Aminu ka gaishe da mutan gidan nagode sosai yace.” Zasuji da kyau sai na shigo daurin aure gobe.”

Nace.”To Allah ya kaimu.” Hauwwa ta matsa daga jikin motar yaja ganin Khalid din ya fito daga motarsa yasa ya sauke glass yana masa magana. Khalid sama-sama ya amsa yana d’aga masa hannu. da sauri nace.”Hauwwa mu shiga gida.” saboda ina jin tsoro kada ya wulakanta ni a gabanta.

Gabana ya tara na tsaya ina kallonsa. Sassauta fuskarsa yayi suka gaisa da Hauwwa ta shige cikin gidan ni kam tare ni yayi da gangar jikinsa ya matse ni a bango murde hannuna yayi ya kwace key din.

Yana wani irin huci yace.”Wannan key din na menene.”? Cikin faduwar gabana nace.” Yaya Aminu ne ya kawo min mota a matsayin gift

Wani irin kallo yake min kafin yace.”Ke kika nuna masa kina bukatar mota.”?

Harara na watsa masa da fadin.”Wace irin magana ce wannan haka kawai sai nace ya siya min mota shine yayi niyya.”

Yace.”Okey to kada kisa a ranki zaki shiga motar nan zan bashi key d’insa bana bukata kuma wallahi idan bai fita daga sabgarki ba zaku sha mamaki na dake dashi.”

Cikin galabaita nace.”To naji matsa min hanya na shiga gida.”

K’ara matseni yayi yana bin fuskata da kallo, idanuwana suka ciko da ruwa fitinar yaron nan har tsoro take bani.”

“Me zan samu ne.”? maganarsa ta dawo dani hayyacina kallonsa nayi idanuwansa sun k’ankance.

” Ba zaka bani hanya ba ko anya kuwa kana so auran nan yayi albarka kuwa.”?

“Saboda me kika fadi haka.”? ajiyar zuciya na sauke nace.” Me yasa kake lalube ni a duk sanda ka samu dama wannan ba so bane sha’awa ce.”

Fuskata ya tallafo yana kokarin had’a bakina da nasa fizgewa nayi da karfi na buge shi. zan bar gurin yayi gaggawa riko hannuna.

Wani irin numfashi yake saukewa ya matseni tsam-tsam a kirjinsa wasu irin maganganu yake fada min a kunne tsabar shiga rud’ani yasa sam ban fahimci komai ba sai da ya gama lugwigwita min jiki sannan ya sake ni….Hawaye na goge na tureshi da karfi na shiga gidan da saurin gaske.

*RANAR DAURIN AURE*
Cikin nufin Allah Khalid ya angwace da mata biyu wanda suka kasance ‘yan uwansa na jini ranar daurin auran Gwaggo sai da tayi kuka saboda tsabar farin ciki babban burin ta ya cika ta had’a aure a tsakanin jikokinta guda biyu hakika tayi farin ciki da zuwan ranar.

‘Bangaran Umma Habiba ma tayi nata taron daidai gwargwado sannan tayi zama na mussaman da amaryar tayi mata nasiha mai ratsa jiki ta kuma koya mata dabaru na zaman aure da kishiya daga karshe tayi mata fatan alkairi da samun zuria masu albarka.

‘Bangaran Ummatu kuwa abin babu dadi da albarka dan babu wanda yake fadin alkairi sai sharri sun zaunar da Jamila sai hud’ubar banza suke mata ita kuma mara wayo ta zauna tana sauraransu sannan suka dirka mata maganin mata suna ganin kamar hakan dubara ce.

Ko wacce tana ‘bangaran ta Sa’ida taji dadin hakan dama kwata-kwata bata bukatar abinda zai had’a ta da yarinyar kowa ya zauna a mazauninsa hakan yafi alkari.

Sai wajan d’aya na dare ya shigo gidan a mutukar gajiye abokansa ne suka riqeshi suna ta celebration na murnar auransa.

Kai tsaye part d’inta ya nufa gajiya ba zata hana shi abinda yayi niyya ba.

Lokacin da ya shigo dakin na jima dayin bacci motsinsa naji Lokacin da ya fito daga toilet zaune na mike ina kallonsa ya fito da towel ra taye a wuyanshi gaban mirror ya tsaya ya goge jikinshi turare ya fesa ya bude wardrobe jallabiya yasa ya juyo yana kallona…..dauke kaina nayi tare da mike kafafuna a gadon.

“Kije ki dauro alwala muyi nafila.” Ba tare da nace masa komai ba na nufi toilet din. fita yayi daga dakin ya nufi gurin Jamila domin ya dubata

Bacci ya sameta tana yi ba tare da ya tasheta ya fita daga dakin tare da ja mata kofa.

Da hijabi a jikina ya same ni ganin ya tsaya akan dadduma yasa na mike na tsaya a bayansa, raka’a biyu muka gabatar ya daga hannuwa sama nima nayi irin yanda yayi muka jima a haka yana addua yana shafawa na shafa a fuskata mikewa nayi na koma gadon na zauna.

Kallona yayi babu walwala a tare dashi yace.”Kinci abinci ko .”? Yanda yake ‘bata rai nima haka ciki ciki nace .” Eh naci.” ba tare da yace wani abuba ya kashe fitilar dakin. Gadon ya k’araso ya cire jallabiyar jikinsa kwanciya yayi yana kallon baya na.

Ba tare da na cire hijab din ba na kwanta tare da juya masa baya……..”Sa’ida.” sunana ya kira na amsa da Na’am. “Ki bani kulawa tunda dai ke bazawara ce nasan kema a bukace kike ko ba haka bane.”?

Shuru nayi masa ya matso kusa dani tare da ratsa hannunsa a ‘kuguna ajiyar zuciya muka sauke a tare…………..” Khalid.” ‘kasa-‘kasa na kira sunansa. bai amsa ba sai ya mutsa min jiki yake. hannunsa na rike wanda yake ta kokarin sashi a cikin hijab din jikina. “Ba dakina ya kamata ka fara kwana ba ka tashi kaje gurin Jamila itace budurwa ina ganin itace daidai da fitinarka.”

Wata irin runguma yayi min yana kyarmar jiki yace .” Aa Jamila ba zata iya ba kece daidai dani shiyasa ban tunkare ta ba duk da ta kasance budurwa ke nake sha’awa.

Tsigar jikina ce ta tashi shuru nayi gabadaya jikina ya mutu juyo dani yayi ya dora saman jikinsa hijab din ya cire yasa fuskarsa tsakanin kirjina wani irin nishi ya dinga saukewa yana goga fuskarsa a gurin kanshi na tallafo ido jajawur yake kallona a sarqe nace.”Me kake bukata nayi maka.” Cikin sarqewar murya yace.”Ke nake bukata gabad’ayan ki ki taimaka min.”

Murmushi nayi tare da risinar da idona a nashi. ya tallafo mazaunaina yana matsawa…..Rigar jikina na cire d’imaucewa yayi ya kaiwa Nonowan raruma! d’aya tasa masa a baki ta tallafe kanshi sosai bashi nonon take tamkar wacce take shayar da d’anta.

Wani irin tsotso yake wa Brest din yana jan nipples d’in d’ayan ita kuma sai shafa kanshi take tana bashi zafafan kesses din da suka zautar dashi.

Wani irin yanayi suka shiga mai wuyar fassarawa ita dashi duk sun d’imauce sun kai ‘karshe babu wani abu da yayi saura a jikinsu sai fatar jikinsu haka suka manne wa junansu suna numfarfashi Sa’ida ita ta dinga sarrafa shi tana taimaka masa duk domin jin dad’in su tana kuka yana kuka saboda tsabar feelings sai buga sambatu sukeyi raba dare sukayi suna abu d’aya style kuwa sunyi ya kai biyar gaskiya sun jiyar da junansu dad’i tare sukayi wankan tsarki suka sanja kaya masu tsabta suka kwanta tare da rungume junansu.
*ASUBAH TA GARI AMARYA DA ANGO*
*100*
Washe gari da safe tana kicin tana shirya musu breakfast ya shiga kicin din ya sameta. daga bakin kofa ya tsaya yana mata wani irin kallo na kurulla…….Juyowa nayi muka had’a ido dashi kallon da yake min yasa gabadaya jikina ya mutu a hankali nace.”Ka tashi lafiya.”? Ba tare da ya amsa ba ya shigo kicin din. jin sa a daf dani yasa na d’an matsa baya ya sake matsowa yana bin kirjina da kallo da yake rigar bacci mai k’aramin hannu ce a jikina ta kuma kwanta a jikina sosai lumshe idonsa yayi ya d’ora fuskarsa a gurin, a tare muka sauke ajiyar zuciya ya shiga goga fuskarsa yana sumbatar gurin gabad’aya rikice wa nayi tallafo kanshi nayi ina kallonsa nace.”Ka bari na kammala mana break ko.”

Girgiza kansa yayi cikin shawagaba yace.”Umhum! ni dai muje dak’i.” Dariya ya bani na juya had’e da fadin “Khalid kenan.” wuka na ina kokarin yanka albasa ya rungumeni ta baya yana wasa da hannuwansa a jikina.

A rikice nace.”Don Allah ka bari kada kasa na yanke hannu.” shuru yayi min ya cigaba da wasa da Brest d’in sai tsotsar cikin kunnuwana yake……..Gigicewa nayi jiki na rawa na juyo na rungumeshi tsam-tsam! dama haka yake so sai kawai ya sunkuya ya sa’ba ta a kafad’a suka manta da komai suka shiga biyan bukatarsu.

Sa’ida dai duk zulamarta Khalid sai da ya kaita karshe dan da kuka da magiya suka rabu da kyar ya saurara mata ta shiga toilet jikinta duk yayi wani irin tsami.

A gurguje ta nufi kicin din taji kauri ya cika mata hanci tuntuni ruwan tea din data d’ora a gas ya k’one tukunyar tayi jajawur sai hayaki take.

Da sauri ta kashe gas din ta fita da kicin din saboda hayaki da kaurin da ya cika kicin din

Yana zaune a bakin gado yana waya kansa ya dago ya kalleta a lokacin data shiga dakin, da hannu ya nuna mata cinyarsa wai taje ta zauna. murmushi kawai tayi ta tsaya jikin mirror tana jiran ya gama wayar.

Kashe wayar yayi yana kallonta a hankali yace.”Ya akayi ne Madam.”?

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Khalid kaga fitinar ka ta kusa haddasa mana gobara a gida ko.”?

Cike da mamaki yace.”Me ya faru.” ? tace.”Kazo ka rikita ni na d’ora ruwan tea a wuta ya kone tukunyar tayi jawur.'”

D’an murmushi yayi yace.”Jiya hakuri kawai nayi na kyaleki kikayi bacci shiyasa na tashi a bukace.”

Girgiza kaina nayi nace.”To yanzu dai sai ka tashi ka shirya ka shiga gurin Jamila ka dubata idan yaso idan kun gaisa da juna sai munyi break fast din.”

‘Bata rai yayi yace.”Kina nufin ke zaki nuna min abinda ya dace nayi.”?

Ganin yanda ya ‘bata rai yasa nace.”Aa ni wacece kawai na tuna maka ne.”

Tsaki yaja ya mike tsaye yana kallona yace.”Kada ki sake min magana akan mu’amulata da Jamila babu ruwanki.”

Cike da mamaki nake kallonsa hanyar toilet ya nufa yana ‘kananun magana.

Girgiza kaina nayi na fita daga dakin ina mamakin al’amarin Allah dai yasa yaron nan ya zama adalin namiji.

‘Bangaran Jamila kuwa da bacin rai ta tashi daga bacci ta zauna taci kukanta ta koshi kafin tayi wanka ta shirya jikinta ta fito falo ta zauna ranta a masifar b’ace a ganinta ita ya cancanta ya fara kwana a dakinta tunda itace budurwa amma saboda rashin adalci yana can ya tare a gindin bazawara sosai al’amarin ya ‘bata mata rai da duk wani masoyinta tana kuka ta kira wayar Ummatu ta sheda mata abinda akayi mata Ummatu rarrashinta tayi tace tayi hakuri insha Allahu idan yazo gidan za taji dalilin da yasa yayi mata haka a matsayinta na budurwa.

Babu cikakkiyar walwala a tare dashi ya shiga gurin nata.

Dauke kanta tayi daga kanshi, ya samu kujera ya zauna yana kallonta da jiran gaisuwarta.

Jamila shareshi tayi ta cigaba da share hawaye daga karshe ma mikewa tayi ta shige bedroom ta barshi a zaune a gurin.

Rai a ‘bace ya bita dakin nan ya sameta sai gursheken kuka take, a kanta ya tsaya hannunsa guda cikin aljihun trouser din dake jikinsa yace.”Ke kuma me akayi miki kike wa mutane kuka da sassafe.”?

Ido jage-jage da hawaye ta kalleshi da fadin.” Yaya Khalid ban ta’ba tsammanin baka da adalci ba sai yau yanzu ace haka shine daidai a gurinka tun jiya nake gidan nan amma baka shigo ba sai yanzu kuma kamata yayi ka fara kwana a gurina tunda nice budurwa.”

“Wannan shine dalilin da yasa baki amsa sallamata ba baki kuma gaisheni ba.”?

Shuru tayi tana cigaba da sheshshekar kukanta. Kansa ya girgiza rai a bace ya kama hanyar fita daga dakin, da sauri ta dago kanta tana kallon bayansa mamaki takeyi wato ba zai ma tsaya ya rarrasheta ba ya kad’a kansa ya fita. wasu zafafan hawayen masu zafi suka kwace mata kwanciya tayi tana kuka tana tunanin mafita.

Tsaf na kammala break fast muka zauna a daining din tare amma babu magana ya wani ci kunu sai shan qamshi yake jefi jefi yana amsa waya. ganin haka yasa nima na shareshi koda na gama mikewa nayi na shiga daki na kwanta bacci ne a idona saboda jiya da kyar ya barmu muka rintsa.

” Haba Khalid wannan wane irin rashin adalaci ne saboda rashin tunani ka tsallake budurwa mai mamora ka tafi gurin bazawara ragowar maza biyu wannan ai cutar da kai ne a gaskiya ba muji dadin wannan al’amarin ba.

A nutse yace.”Baito waye ya kawo muku wannan gulmar.”? da sauri tace.” yarinya ce ta kira waya tana kuka ta sheda mana wulakancin da kayi mata ashe tunda aka kaita dakinta baka dubata ba sai yanzu Haba Khalid Jamila fa ‘yar uwarka ce.”

Murmushin takaici yayi yace.”Baito dan Allah ku rage surutu da ‘kananun magana ni komai na rayuwata yana tafiya ne kan tsari Sa’ida da ita aka fara daura min aure dole dakinta zan fara shiga babu ruwana da budurwa ko bazawara ina bin tsarin addinin musulunci ne.”

Ummatu tace.”Duk da haka dai ka nunawa duniya cewa kafi son Sa’ida ai shikkenan tunda haka ka za’bawa rayuwarka.

A nutse yace.” Ummatu don Allah ku kwantar da hankalin ku tsakanin Sa’ida Jamila babu wacce tafi wata a gurina duk daya suke tunda dukkaninsu zumunci ne mai karfi a tsakanin mu bayan haka ga babban al’amarin da ya ratsa tsakanin mu to ina ganin a halin yanzu duk wasu surutai da ‘kanunan magana basu dace ba babban burina shine Allah ya bani ikon rike jagorancin daya bani inaso ku taya ni da addua akan haka.

Jikinsu ne yayi sanyi Baito tace.”Addua kam muna yi sai dai muqara akan wata amma dai duk da haka sai ka jajurce ka zama namijin duniya duba da cewa ita Uwargidan naka uwar mata ce ta fika wayo da dubara sannan ta girme ka ta kuma girmi Jamila dole ne ta wani gefan ta cutar daku shiyasa hankalinmu ya kasa kwanciya.

‘Bata rai yayi yace.”Baito kada ki sake cewa Sa’ida ta girme ni bana so.” Baki ta riqe tana kallonsa tace.”To ai ko ba’a fad’a ba ido ba mudu ba yasan kima dama dai don ka kwallafa ranka akanta ne amma ai ba sa’ar auranka bace.”

Mi’kewa yayi ya dauki wayoyinsa da key ya fita ya basu guri yaji mugun haushin maganar Kakar tashi a ganinsa yanzu maganar girma da shekaru ta kare tunda shine yake gaba da ita a k’arkashinsa take tilas ya kar’be shekarunta ita ta kar’bi nasa.

Gurin Gwaggo ya nufa ya sameta a bakin murhu tana ta dahuwar kaza a cikin madaidaiciyar tukunya………Cikin rashin jin dadi yace.”Gwaggo duk Gas din gidan nan ba zaki amfani dashi ba sai ki kunna ice duba don Allah sai hayaki ne yake tashi a gidan idanuwanki na ruwa wai shin ma me kike girkawa.”

Tace.”Ai ka bari mu gaisa kafin ka kalubance ni.” Guri ya nema ya zauna ta karkad’e tabarma ta shinfida kusa dashi tana kallonsa…..Murmushin jin dadi tayi tace.”Ango mijin Sa’ida da Jamila Jarumi D’an gidan Rabi da Ibarahim Jikan Lawali da Ramatu.”

Dariya yasa yana kallonta itama tana dariyar tace.”Wallahi jiya da kyar nayi bacci saboda tsabar farin ciki ina fatan kun wayi gari lafiya da kai da iyalin naka.”?

Yace.”Lafiya lau Alhamdulillhi.” Tace.”To masha Allah ai naji dadin zuwanka dama ina ta tunanin wanda zai kaiwa Sa’ida dawur kazarta.”

Yace.”Ai ni nan da kika gani sai can dare zan koma gidan……Tace.”Don Allah komai dare kazo ka tafi mata abin ba ita kad’ai zai amfana ba harda kai.”

Yace.”Gwaggo wace irin kaza ce wannan da za’a dauka idan tana so ita tayi farfesun mana.” Tace.”Ni dai ba doguwar magana na nema da kai ba kawai kace to.”

Yace.”To naji ita Jamila ba zaki bata kazar ba.” Girgiza kanta tayi tace.”Kowa kansa ya sani ita wa yasan irin gyaran da iyayenta sukayi mata.” Sai da ta fadi maganar sai ya fahimci inda ta dosa Dariya ya dinga kyalkyalawa yana fad’in.”Gaskiya nima ban yarda ba sai kin bani maganin kar’fi ai nima jikan ki ne me yasa ba zaki gyara ni domun mataye na suji ni garau ba.”

Mifici tasa tana dukansa da fadin.” Tashi ka tafi harkokin ka bana son rashin ta ido ai kai tuntuni nasan da cewar Jarumi ne koda za’a tara maka mata dubu sai ka iya dasu.”

Khalid ya dinga kyalkyala dariya yana girgiza k’anshi Yana masifar kaunar kakarshi saboda yanda take kaunarsa da damuwa da al’amuransa yasan babu wani abu da zaiyi mata ya biya ta akan irin abinda take masa na aikairi yanda yake jin Gwaggo a cikin ranshi baya jin iyayensa Gwaggo nada kima da daraja a gurinsa.

Ina cikin bedroom d’ina ina gyare-gyare naji motsi a falo da sauri na ajiye abayar dake hannuna na bude kofar dakin na fita.

Ido hudu mukayi da ita tana tsaye a tsakiyar falon ita da wasu ‘yan mata guda biyu da alama dai ‘kawayenta ne…….Babu walwala a fuskata nace.”Ku zauna mana kun tsaya a tsaye sai kalle-kalle kukeyi ko kun ajiye wani abu ne.”?

Wani irin kallo tayi min kafin tace.”Kinga mu ba zama ne ya kawo mu ba me zamu zauna muyi miki.”?

Tsayuwa na gyara ina kallonsu nace.”Okey to me ya kawo ku.”? Daya daga cikin k’awayen nata tace.”Munzo muyi miki warning ne.”?

Da mamaki a tare dani nace.”Warning kamar yaya.”? Dayar tace.”Kema ai kin sani aikin banza aikin wofi mutum da girmansa sai zuciyar yara in banda ma abin d’a namiji mai zai ci dake bazawara ragowar mutun biyu.”

Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafowa a jikina kawai na zuba musu ido suna ta surutu da fadin duk maganar da tazo bakinsu.

Jamila tace.”Suwaiba ku kyaleta naga kamar jikinta yayi sanyi tayi nadamar abinda ta aikata ku muje kawai da alama bata da abin fad’a.

Juyawa sukayi zasu fita da sauri na janyo rigarta dan har sai da wuyan ya yage wawan! mari na kwad’a mata a kumatu.!

Dafe kumatun tayi tana kallona hawaye kuwa tuni sun wanke mata fuska.

A wulakance na kalleta da fad’in.”Wallahi ki shiga hankalin ki dani ni zaki shigowa daki ki zaga harda gayyato wasu shashashan k’awayen ki me suka isa su tare miki.”

Suwaiba tayi tsagal tace.”Aikuwa mun isa mu tare mata aikin banza kawai mugu……Kafin ta ‘karasa ta bata nata marin wanda taga gilmawar taurari a cikinsa.

Murya na rawa tace.”Kika mare ni.”? a fusace! Nace.” Idan baku fice min daga guri ba wayar redio zan dauko naci ubanku shashashan yara marasa tarbiya.”

Jamila na kuka take fadin.” Za kiga abinda zai faru wallahi sai na fanshe marin da kikayi min muguwa azzalima kawai.”

Tsawa! mai razanarwa na buga mata da fadin.” Ba zaki rufe min wannan ru’babben bakin naki ba ko.”? shuru tayi tana kallona nace.” Alkairi zan gani da yardar Allah duk wani sharrin ki dana iyayenki zai koma kanku.”

Girgiza kanta tayi cikin kunar zuciya ta kama hanyar fita simi-simi suka rufa mata baya ko wacce jikinta yayi sanyi da abinda nayi musu…..Raina a bace na koma cikin dakina na cigaba da abinda nake.

Kimanin awa guda da faruwar al’amarin ya kira waya ta, ina d’aga wa ya fara masifa ” Me Jamila tayi miki zaki mareta ita da ‘kawayenta Nifa bana son mugunta da neman fitina.”

Sassauta murya nayi nace.”Kaga ka tsaya ka saurare ni don Allah bana so ka sake tunzura min zuciya.

A dakile yace.” To na saurara sai kiyi min bayanin abinda ya faru.”

Ajiyar zuciya na sauke cikin nutsuwa na zayyane masa dukkanin abinda ya faru a tsakanin mu.

“Me yasa ba zaki bari na dawo ki fad’a min ba? me yasa zaki dauki mataki a hannunki? ashe ke kike da kanki baki dana gaba dake ko.”?

Raina ne ya ‘baci da maganarsa Nace.” Khalid kana nufin hukunci na beyi daidai ba kenan.”?

‘Kwarai kuwa baiyi daidai ba kinyi zalinci saboda kin san kinfi k’arfinta shine zaki zage karfi a kanta ki fasa mata baki da hanci.”

Tsaki mai karfi naja nace.”Tunda nafi karfinta idan ka dawo gidan sai ka rama mata.” kashe waya ta nayi ba tare dana saurari abinda yake fad’a ba.

Be shigo gidan ba sai wajan sha d’aya da rabi na dare lokacin ma ni na jima da yin bacci ya jima a gurin Jamila yana lalla’bata da bata hakuri akan abinda Sa’ida tayi mata sai da ya sata dariya sannan yayi mata sallama ya nufi Side din Uwargidan nashi…

*101*
Motsin shigowarsa dakin ne ya farkar dani na miqe zaune ina kallonsa ya a jiye lodojin dake hannunsa, ba tare da yace min komai ba ya nufi toilet kamar na tashi na bishi domin nasan wanka zaiyi na had’a masa ruwa sai wata zuciyar ta kwa’be ina jin tsoron iskancin yaron domin na lura da cewa idan yaga ina masa rawar jiki yafi wulakanci.

Ina zaune ina tunanin rayuwa ya fito daga bandakin daure da towel da karami a hannunsa yana goge jikinsa.

A nutse nace.”Sannu da zuwa.” Yana tafiya zuwa mirror ya amsa ba tare da ya kalleni ba.

Komawa nayi na kwanta tare da juya bayana, boxer yasa a jikinsa ya had’a da vest wacce ta matse shi kaina yazo ya tsaya yana min magana cikin gadara da Iko.

Zaune na mike ina kallonsa “Ki tashi ki bani abinci.” Cikin jin haushi nace “Ka duba daining da akwai komai.”

A fusace! yace.”Kina nufin ni zanyi hidima da kaina kenan.”

Nace.”Kaga Khalid bana neman fitina cikin daran nan don Allah idan za kayi min magana ka daina d’aga min murya kana buga min tsawa ba sai kayi haka ba za’a san kai maigida ne.”

“Anyi miki tsawar ko zaki mayar da martani ne.”? Cike da mamaki na dinga kallonsa sai wani huci yake yana kumfar baki Nace.” Akan na mari Jamila ka tsaya a kaina kake kokarin zagi na.”

“Eh akan hakane me yasa ba zaki jira na dawo ba ki fad’a min na dauki hukunci da hannu na ko kuma zaman kanki kike.”?

Murmushin takaici nayi da fadin.” Naga kaji zafin abin abinda za’ayi yanzu kawai ka rama mata marin sai ka huce haushin ka.”

Tsaki mai karfi yaja yace.”Wannan shine na farko kuma shine na karshe wallahi mutukar kika sake fitar da hannu kika daki yarinyar nan sai na hukunta ki dake da ita dukkaninku Amanar ku a hannuna take.”

Kwanciya kawai nayi na kyaleshi yana surutai “Kin raina min mahaifiya sam bakya ganin kima da mutuncin dangi na kina maganar duk sharrin su zai koma kansu me sukayi miki na sharri da har kike fad’in wannan maganar.”?

Kaina ne naji yana wani irin ciwo nace.”Don darajar Allah ka matsa daga kaina wannan masifar taka ta haddasa min ciwon kai Khalid bana son damuwa naji na amsa laifina shikkenan ko.”?

Gurin ya bari yana cigaba da k’ananun maganganu cikin zuciyata nace.” Tunda Allah ya riga ya had’a ni zama da mutum mara hakuri dole na dauki kaddara.

Can cikin bacci na na jishi a naniqe a jikina yana kokarin cire min rigar bacci.

Haushi ya turnuke ni Khalid bai da kunya ko kad’an ya gama cin mutuncin na amma yazo yana lalube ni.

Hannunsa na d’auke na matsa can karshen gado…..Janyo ni yayi ya matse a kirjinsa yana wani irin nishi……..”Auntyna kiyi min taimako irin na jiya kinji ko.”

Shuru nayi masa ina jinsa yana magana kasa-kasa sai kokarin cire min riga yake ina hana shi.

Murya na rawa yace.”Kina so nasa miki karfi ko.”? Uffan bance masa ba, ya mike zaune bedlamp ya kunna haske ya gauraye dakin. mikewa zaune nayi ina kallonsa gabadaya kammaninsa sun sanja idanuwansa sunyi jajawur.!

“Ba zaki amince min ba ko.”? Yafada yana bina da wani mayataccan kallo.

Babu fara’a a fuskata nace.” Ka tafi gurin Jamila tayi maka ni ina bukatar hutu a halin yanzu.”

Rai a bace yace.” Ba zanje ba kuma wallahi ba zaki huta ba kin janyowa kanki fushi na sai na kwana a kanki.”

Cike da mamaki nake kallonsa wai sai ya kwana a kaina ko ayu ma ai yana sauka ya huta……..Bedlamp din ya kashe kafin nayi wani yunk’uri ya turmushe ni ‘karfi yasa min gabad’aya ya galabaitar dani saduda nayi na sakar masa jiki yayi abinda yake so amma shi yake kid’an sa yake rawar sa duk sonsa da nayi masa wassani qi nayi duk ya wani susuce yana kama hannuna yana d’orawa kan joystick d’inshi ina cirewa gabad’aya naqi nayi masa abinda yake so.

Jin haushin hakan yasa ya zage k’arfi a kaina ya dinga bugu na tamkar wanda Allah ya aiko shi da k’yar ya bar mu muka rintsa a daran.

Washe gari da safe a murtuke ya tashi gaisuwa ce kawai ta had’a mu ya shirya tsaf domin fita…..Kamar kada nayi masa magana sai da na daure nace.” Zaka fita ba kayi break fast ba.

Yana gyara agogon dake daure a hannunsa yace.” Ba zanyi ba.”

“Kamar yaya ba za kayi ba.”? Hannu ya d’aga min da fadin.” Bana bukatar doguwar magana tunda nace ba zanyi ba sai a kyale ni ko.”

Nace.”To an kyale ka Cikin ka ne ba na wani ba.” bai tanka min ba ya kama hanyar fita, kallo na bishi dashi mai mugun hali kawai. cikin zuciyata nayi wannan maganar.

Ya jima a gurin Jamila kafin ya nufi gurin taron da zasu gabatar na ‘yan kungiyarsu ta Kano pillars taro ne mai muhimmanci wanda ya had’a manya ‘yan siyasa hatta da maigirma Governor zai hallaci taron saboda mahimmacinsa……..Wani wasan za’a buga a kasar Italy Khalid Lawali tare da Ahamad Musa sune zasu jagoranci kungiyar tasu wannan dalilin ne yasa mai girma governor ya zauna dasu da shuwagabbaninsu domin tattauna yanda al’amura zasu tafi cikin tsari.

Khalid da Ahamad sunyi alkawarin cewa zasu tsaya tsayin daka suyi wasa cikin kyau da tsari kuma insha Allahu zasu ‘kara kankaro martaba da kima na Jahar Kano…..Wannan bayanin nasu ya faranta ran duk wanda yake zaune a gurin a take manyan masu kudi da ‘yan siyasar dake gurin suka soma yi musu kyautuka na mussaman.

Bai dawo gida ba sai gefin magariba Security dinshi ne ya bude masa mota ya fito takardun dake hannunsa ya miqa masa ya umarci shi da ya biyo bayansa. Motar ya rufe da sauri yabi bayansa da takardun a hannunsa.

A bakin kofar falo ya tsaya yaron nashi ya karaso inda yake ya kar’bi takardun tare da sallamar shi, har yayi nisa ya kira sunansa……..”Chinedu.” da sauri ya amsa tare da dawowa da baya. key din motarsa ya mika masa da fadin.” Ka bude mota za kaga wani abu a daure a leda ka dauko min yanzu.”

Da sauri ya karbi key din ya tafi. Shaf ya manta da sakon Gwaggo sai yanzu ya tuna dashi mybe ma abin ya lalace tunda ya kwana.

Tsayuwa yayi bakin kofar falon yana kallona, a nutse nace.”Ka dawo.” Shuru yayi min idonsa kuri a kaina dama ina sane nayi shigar k’ananun kaya na tamke fuskata had’e da fadin.” Ka shigo mana ka tsaya a bakin kofa.”

Ajiyar zuciya ya sauke a miskile yace.”Babu oyoyo kenan.” Kallonsa nayi ina mamakin rashin kunyarsa sai yayi abu ya nuna kamar beyi ba saboda biyan bukatarsa.

Gajiya yayi da tsayuwar ya karaso inda nake fulas din hannunsa ya ajiye min a gabana da fadin”Ga sa’kon ki inji Gwaggo tun jiya ta bani na kawo miki na manta sai yanzu na tuna.”

Daukar fulas din nayi ina dubawa, dahuwar ta soma lalacewa amma dai idan aka gyara za’a iya ci saboda nasan muhimmancin abin yasa da sauri na shiga kicin domin gyarawa.

Zaune a falo na sameshi yana ta waya cikin zuciyata nace waya dai waya sam baya gajiya ko da yake dole hakan ta kasance dashi saboda yanayin sana’arsa.

Cikin dakina na zauna naci kazar a nutse kadan na rage ina sanya ran kafin na kwanta na cinye sauran.

Sai da nayi sallar isha’i na fito falon lokacin ya jima da fita zama nayi kan kujera da carbi karami a hannuna………….Sai da nayi zaman awa biyu da rabi ya dawo. kusa dani ya zauna naji yana kamshi turare ba irin wanda na san shi dashi ba turaran irin nawa ne da nake amfani dashi……..Raina ne ya ‘baci kishi ya sanya na dauke kaina daga kanshi.

“Wai me yasa kullum sai nace ki bani abinci ne.”? Kallonsa nayi rai a bace nace.” Kamar yaya? inace dazu kafin ka fita sai da nayi maka bisimillah kace baka bukata to me zai sanya na damu kaina da lallai sai kaci abinci.”

“To yanzu ina bukata.” cikin sassauci ya fadi maganar….a nutse na miqe na nufi gurin cin abincin baya na ya biyo yaja kujera ya zauna yana aikin latsa waya.

Ina had’a masa abincin na bar gurin domin bana so na zauna rai yazo yana ‘baci.

Shirin kwanciya nayi cikin rigar bacci iya cinya pant kawai nasa ban sa breziya ba tattare gashin kaina nayi na had’e guri daya hula nasa na rufe kan na nemi guri na kwanta har yanzu kishin yarinyar na tsunkulin zuciyata.

Ina jin motsin shigowarsa dakin na rufe idona yayi dik abinda zaiyi ya gama yazo ya kwanta kusa dani yana ma’kale murya……”Big Aunty ki tashi na baki wani labari.”

Share shi nayi yasa hannuwansa ya janyo ni jikinsa fuskarsa yasa a tsakanin wuya na yana min magana kasa-kasa…….Ganin yana so ya rinjaye ni yasa nace.”Khalid don Allah ka barmu yau mu rintsa haba jama’a kai baka gajiya da abu d’aya ne.”

“Aa Ni ba zan ta’ba gajiya dake ba kwanciyar hankalin ki kawai ki bani abinci naci.”

Shuru nayi masa, yasa hannusa kan breast d’ina yana mutsikawa tsigar jikina gabadaya ta mike…..a kasalance nace.” Ba zaka rabu dani ba kenan”

Cigaba yayi da abinda yake takaici ya ishe ni ‘karfi nasa zan tureshi ya danne ni jikina ya hau ya kwanta gabad’aya ya sauke min nauyinsa…..Jajayen idanunsa ya tsira min na kauda fuskata daga kallonshi

Hannu yasa ya juyo da fuskar kasa-kasa yace.” Ya labarin tsofaffin mazajen ki ina fatan yanzu kin bambamce aya da tsakuwa a tsakanin mu.

Shuru nai ina kallonsa yayi murmushi tare da lasar lips d’inshi fuskarsa daf da tawa ya fara kokarin kama baki na.

Babu yanda na iya haka na hakura na kyaleshi ya dinga jagwagwala ni sai da ya tayar min da dukkanin sha’awata gabadaya na rikirkice sai nishi nake ina rungumarsa wasu zafafan kesses ya dinga sakar min ina mayar masa da Martani Jikina ya riga ya jiqe babu abinda nake bukata sai biyan bukatata yanda ya rike wuta nima haka na rike sosai na rikita shi da salo na cikin fitar hayyaci ya dinga k’ananun hawaye yana sambatun surutai.

Washe gari cikin walwala da farin ciki ya tashi don be takale ni da rigima ba sai dai ni kuma gabadaya na kasa nutsuwa kishi ne ke damun zuciyata yau kwanaki na ya kare zai tare a dakin Jamila wannan dalilin yasa na kasa sakewa dashi wani irin haushin sa nake ji.

Koda dare da ya shigo domin yayi min sallama da ‘kyar na kula shi, ya tsaya yana kallona da fadin.” Naga tun safe kike da damuwa ko zaki fad’a min abinda ke damunki.”

“Babu abinda ke damuna kaje kawai.” qin tafiya yayi ya koma ya zauna wai lallai sai na fada masa abinda yake damuna.

Ganin ya damu yasa na sasasauta fuska da fadin.” Na fada maka babu komai fa kada ka damu aji*zanci ne irin na dan Adam amma ni babu abinda ke damuna.”

Jikina ya matso yana kokarin rungume ni da sauri na matsa ina hararsa da fadin.” Menene haka.”? a kasalance yace.”Sallama za muyi.” Gurin na bari ya sake biyo ni yunkurin mi’kewa nayi ya mayar dani ya zaunar kan kujerar da karfi na zauna ina kallonsa da mamaki a tare dani.

Yatsansa ya d’ora saman le’buna na “Ki bani nasha wannan sweet din kafin na tafi.” Kaina ne ya daure kawai na rasa abun cewa sai kallo. Cinyata ya zauna ya karkato da fuskata bai jira komai ba ya had’a bakinsa sa nawa……….Sosai yake sucking din harshena da le’bena duk ya wani gigice nasa hannu na cikun rigarshi fatar gefan cikinshi na mintsina da karfin gaske.

Saki na yayi yana kallona duk yayi wujiga-wujiga idanuwa sun zama tamkar jan gauta……..”Ni zakiyi wa mugunta.” a kasalance yayi maganar.

Hannu nasa na tureshi da fadin.” D’aga ni don Allah duk kabi ka sagar min da gwiwa.” Tashi yayi daga jikina yana shafa sumar kanshi yace.” Wai menene a cikin bakin ki idan ina sha tamkar ina shan zuma.”

Cikin kasala da tsananin sha’awa nace.” Kan ka zaka tambaya.” Kanshi ya shafa ido a lumshe yace.” Eh wannan gaskiya ne ni zan tafi sai da safe.” Ba tare dana kalleshi ba nace.” Allah ya bamu alkairi.” Ameen yace ya kama hanyar fita…Kallo na bishi dashi ina mamakin halayyarsa.

*102*
A daran ranar da k’yar na iya rintsawa (bacci ) saboda tsabar kad’aici da asubah da wata irin kasala da mutuwar jiki na tashi, na dinga komai cikin rashin kwarin jiki…….. tsaf na kammala abin kari na shirya daining din da jikina na zauna zaman jiran shigowarsa…………Khalid kuwa na can tare da Yarinyar mutane sai wajigata yake Amina raguwa ce dan tun kafin tafiya tayi nisa take masa kuka da magiya akan ya kyaleta ai kamar kara tunzurashi take ya zage sosai a kanta yana biyan bukatarsa Ya samu gamsuwa amma ba kamar irin wacce yake samu gurin auntynshi ba.

Amina na share hawaye ta lalla’ba ta shiga toilet domin gyara jikinta shi kam yaji dadi sosai da ya samu budurcinta sai ya tuna lokacin daya keta budurcin auntynshi rintse idonsa yayi yana girgiza kanshi sam beso hakan ba yaso ace ta hanyar aure komai ya faru amma kaddara ta riga fata haka Allah ya shirya musu.

Yana gama kimtsa jikinshi ya fice daga dakin ba tare da ya bari ta fito daga bandakin ba hakan yayi mata masifar ciwo a hankali ta zauna gefan gado tana kukan bakin ciki yanda ya jigata ta ya bata wahala ta dauka ai zai tsaya ya rarrasheta amma da yake ba itace a ranshi ba har ya fice ya bar mata dakinta zuciyarta ta sake cika da kishin abokiyar zaman nata.

Khalid kuwa yana fita bai ko kalli Side din Auntyn nasa ba kai tsaye inda motocinsa suke ya nufa Yaron shi Chinedu ya mike da sauri yana mika gaisuwarsa motar ya bude masa ya shiga ya zauna shima da sauri ya shiga gurin zaman shi ya tashi motar kafin su fita daga gidan sai da ya sauke gilashin na motar suka gaisa da Maigadi Khalid bashi da girman kai da wulakanci yanda yake Mu’amula da jama’a abin zai baka sha’awa.

Sai yamma ya dawo gidan kai tsaye gurin Sa’ida ya nufa domin ya dubata…….Kallo daya nayi masa na dauke kaina a nutse ya karaso kusa dani ya tsaya tare da zuba hannuwansa a cikin aljihu.

Babu walwala a tare dani nace.” Barka da yamma.” ajiyar zuciya ya sauke a hankali yace.” Barka dai kinji shuru ban shigo na dubaki ba ko.”

Shuru nayi hankalina akan Tv ya cigaba da cewa.” Da wurwuri na fita kuma tunda na fita ban samu kaina ba ballantana na kira wayarki ina fatan kin wuni lafiya.”

Ajiyar zuciya na sauke ina d’an jin sassauci a cikin raina nace.” Lafiya lau na Wuni ina fatan ka leqa gurin Gwaggo.”

Yace.”Aa banje ba saboda uzirin daya sha kaina mybe sai gobe zan shiga mu gaisa.” Nace.” To Allah ya kaimu.”

Zama yayi kusa dani na dan kalleshi sai naga kwarmin idanunsa sun zurma. ” Ki bani abinci tun safe babu komai a cikina.”

Cike da mamaki nace.” Tun safe babu komai a cikin ka? amma kake yawo a haka.”

Hannuwansa yasa ya rufe fuskarsa da fad’in.”Ke dai ki bari kawai jiya na kwana banyi bacci ba yau kuma na yini da yunwa abubuwan sunyi min yawa.”

Maganar ta bani haushi sosai sai kawai na kauda kaina na rabu dashi. Ya kalleni da fad’in.” Ko dai ni zan shiga kicin din na dauk’o abincin.”?

“Kaje kicin din ko kuma ka tafi gurin matarka tunda a dakinta ka kwana.” ” Wace irin maganace wannan.”?

Shuru nayi masa gabad’aya haushinsa nake ji ko kunya yazo yana fadin ya kwana beyi bacci ba yaron ya gama raina min hankali.

Ganin yanda nayi watsi dashi a gurin yasa ya mi’ke ba tare da ya sake min magana ba ya kama hanya fita, ‘karamin tsaki naja tare da bin bayansa da harara.

Yau tsayin kwana ki uku kenan bai sake shigowa inda nake ba, damuwa da kadaici suka dabaibaye ni gabad’aya hankalina ya tashi na rasa abinda yake nufi dayin hakan, kullum ni kenan cikin leqen sa a duk sanda zai fita ina kallonsa ko kallon Gurina ba yayi zai shiga mota dravar sa yaja motar su tafi……..Duk yanda nake kokarin daurewa sai da na kasa zama nayi naci kuka na na k’oshi na dinga tunanin hanyar da zanbi gurin shawo kansa.

Ina lissafe Yau kwanansa bakwai a gurin Jamila ya gama mata kwanakinta zai dawo guri na tunda na tashi nake jin annushuwa da farin ciki abinci kala uku nayi masa nayi ado sosai irin wanda zai ja hankalinsa. sai dai me? Daf da magariba ya kira waya ta cike da zumudi da murna na daga wayar.

Ciki-ciki ya amsa gaisuwata yace.” Yau girki ya dawo hannunki ko.” ? Nace.”Eh.” Yace.” Kiyi hakuri yanzu haka bana gari naje Bauchi tare da abokanan sana’ata zanyi kwana uku sai na dawo.” Kafin nace wani abu ya kashe wayarsa.

Jiki a masifar sanyaye na zube a gado kawai naji hawaye masu zafi sun k’wace min. Na riga na gama cin buri nasa rai yau karshen matsala ta dashi zai k’are saboda na gama shirya duk yanda zanyi na sanya shi cikin farin ciki bayan haka kuma a matse nake don ni kadai nasan halin da na shiga tsayin kwanaki bakwai din da yayi a gurin Jamila……Ina jin wani irin d’aci a ma’kogwarona nasa hannu na dinga share hawayen dake zuba a fuskata.

Alhaji Nura cikin shiga ta alfarma yayi parking din motarshi a inda ya saba idan yaje gidan zance fitowa yayi daga motar tashi yana gyara babbar rigar dake jikinsa……Wayarsa ya dauko domin ya sanar mata da zuwansa, Ya kira ya kai sau nawa bata shiga sai ya hakura ya fara neman yaron da zai tura gidan. Kawu ne ya fito daga gidan sai ya ganshi a jingine a jikin motarsa cike da mamaki ya karasa inda yake. Alhaji Nura ya saki fuskarsa cikin mutunci da girmama juna suka gaisa da juna.

Kawu yayi shuru yana so yaji abinda yake tafe dashi. Alhaji Nura ya gyara tsayuwarsa a nutse yace.” Kwana biyu bana gari wallahi ban samu na shigo mun gaisa ba jiya na dawo naje india shine yau nace bari na shigo mu gaisa inaso naga Sa’ida domin mu tattauna abin da yake gaban mu.”

Kawu yace.”Ayya ashe baka garin shiyasa baka da labarin al’amuran da suka gabata.” Yace.”Kwarai kuwa Kawu inaso yanzu a lamunce min na bada sadakin Sa’ida ranar juma’a mai zuwa a daura aure.”

Kawu ya jima kanshi a kasa kafin yace.” Alhaji sai dai kayi hakuri da abinda Allah ya tsara domun dai a yanzu maganar da nake maka yau sati biyu kenan da daurin auran Sa’ida tare da Dan uwanta Khalid.”

Alhaji Nura gumi ne ya tsinke masa ya cire hularsa yana firfita da ita kamar mara hankali yace.” Ya za’ayi ayi min haka? Yarinyar nan fa ni take so tayi min alkawarin komawa gidana domin ta kula min da ‘ya’ya na mai zai sanya ka tilasta mata auran d’anka wannan ai rashin adalci ne.”

Kawu ya dinga kallonsa yana mamakin maganarsa……..Alhaji Nura ya cigaba da cewa .” Wannan yaron naka mara kunya kwata-kwata bai dace da kamilar mace irin Sa’ida ba saboda haka duk yanda zanyi sai nayi na ruguza auran da kuka daura.”

Kawu na ‘kokarin magana Muryarsa ta bayyana a gurin ya jima da zuwa gurin basu sani ba…….”Kai wane irin wawan mutum ne bagidaje mara hankali da nutsuwa.”
Gabadaya suka juya da sauri suna kallonsa.

Rai a masifar ‘bace yace.” Ka jima kana kira na da mara tarbiya shin kai d’in menene sunanka? Kana gadara da dukiya ko? to inaso na sanar maka da cewa a yanzu idan nayi Ra’ayi ba zaka koma gidan ka ba zan sa a daure min kai har karshen rayuwarka.”
Kawu ya daga masa hannu da fadin.”Ya isa haka kowa ya bawa zuciyarsa hakuri.” Khalid shuru yayi sai wani irin huci yake yana jin kamar ya shaqe wuyan Alhaji Nuran ya had’a masa jini da majina bai ta’ba ganin mutum mai mugun naci kamarsa ba.

Kawu ya kalleshi da fadin.” Alhaji idan rai ya ‘baci ba’a sauran yanke hukunci ya kamata kayi mana uziri sannan kuma ka dauki kaddara komai kaga ka samu a duniya dama rabonka ne idan kaga baka samu abu ba to dama baka da rabo saboda haka sai kayi hakuri ka barwa Allah al’amarinsa.

Gumin goshinsa ya goge rai a bace yasa hularsa ya bude motarsa da karfi yaja Kawu yayi saurin matsawa yana kallon ikon Allah sai da ya bar gurin ya juyo yana kallon yaron nasa yana tsaye bakin kishi ya cika masa rai idanuwansa sunyi jajawur.

Yace.” Yau shigowar dare kayi kenan.”? ajiyar zuciya ya sauke yace.”Eh kasa hakuri nayi sai da safe ina so naga Gwaggo ne.” Yace.” To babu laifi nima yanzu nan na fito daga gurin nata. Yana kokarin shiga kofar yace.”Bari a gurguje na shiga mu gaisa Allah yasa ba tayi bacci ba.” Kawu yace.” Bana tsammanin hakan.”

Gwaggo na gyangyad’i ya shiga ya sameta, kamshin turaransa taji da sauri ta bude idonta tana kiran sunansa.

Kusa da ita ya zauna yana gaisheta ta amsa cikin kulawa tace.”Kwana uku ina lissafe baka zo inda muke ba.”

Yace.”Nayi tafiya ne Kuyi hakuri yanzu dawowata kenan na kasa hakuri na shigo na duba ku.” Tace.”Jarumi za kayi tafiya amma babu labari ko baka bukatar adduarmu.”?

Yace.” Gwaggo kuyi hakuri nayi laifi tafiyarce babu tsammani ina fatan na sameku lafiya.” Tace.”Lafiya kalau alhamdulillhi Ya iyalin naka.”?

Yace.” Duk suna nan kalau.” Tace.” To masha Allah sai ka tashi ka tafi gurinsu su ganka kada ka shiga hakkinsu.”

Yace.” Tom ki bani abinci naci.” Girgiza kanta tayi tace.”Aa babu ruwana ba zan baka abinci ba mai girki taji haushina.

Yar dariya yayi yace.” Gwaggo bana sha’awar komai sai abincin ki kawai ki bani idan da akwai.”

Jim tayi tana nazari tace.” Bari na baka kadan idan kaje gida sai ka ‘kara wani.”

Yace.” To ki had’a min bari na shiga gurin Ummatu mu gaisa na fito.” Tace.” Tom shikkenan sai ki fito.

Da ‘Kyar Gwaggo ta kore shi ya tafi dan bayan ya gama cin abincin kwanciya yayi kusa da ita tana bashi labarai sai dariya yake kyalkyalawa ganin dare yayi beda niyyar tafiya gida yasa tace ita kwanciya za tayi ya tashi ya tafi gurin iyalinsa da kyar ya tashi ya tafi cike da ‘kaunarta a cikin ransa.

Sai da ya fara duba Jamila tukkuna ya nufi Gurin ta.

Duk da nasan yau zai dawo gida Ban yi tsammanin zai shigo inda nake ba wannan dalilin yasa ban zauna zaman jiransa ba na shige daki nayi kwanciyata.

Maganarsa kawai naji a kaina, da sauri na bude idona ina kallonsa, ganin fuskarsa a murtuke yasa gabana faduwa ni kam Allah yana jarrabata da masifaffun maza.

Zaune na mike a sanyaye nace.” Khalid ka dawo ashe.”? a dakile yace.” Na dawo ina fatan kuna lafiya.”? Nace.” Lafiya kalau Ya hanya.”? shuru yayi min kawai ya zuba min ido.” Nace.” Kana bukatar wanka na had’a maka ruwa.”?
“A’a idan ina bukata zan shiga na had’a da kaina yanzu inaso nayi magana dake ne.” Yanda yake magana a harzu’ke yasa na gane cewa lallai da tashin hankali ya shigo gidan.

*103*
A nutse nace.”To Allah yasa alkairi ne ina sauraranka.” Cikin sigar tuhuma yace.”Har yanzu akwai sauran alaqa a tsakanin ki da Alhaji Nura ko.”? Gabana yayi wani irin fad’uwa! Ido na tsira masa raina idan yayi dubu ya ‘baci nace.”Khalid wace irin magana ce wannan.”?

Hannu ya d’aga min “Kinga tambayarki nayi yana da kyau ki bani amsa ba ki tambaye ni ba.” Ajiyar zuciya na sauke tare da bawa zuciyata hakuri nace.”Tunda nayi aure alaqa ta yanke a tsakanimu.”
“To mai yasa yake bibiyarki har yanzu.”? Kallonsa nayi duk ya tsareni da ido Nace.” A’ina zan ganshi da har zai bini.”

Tsaki yaja cikin tsananin kishi yace.”Yau yaje can Mandawari ya samu Kawu yana cin mutuncinsa har da fad’in ba ayi masa adalci ba kin san Allah wannan mutumin yana cin darajar abu guda ne da ba don haka ba da tuni na dauki mataki mai tsauri a kansa sabida haka ki fad’a masa cewa komai maitar sa dole ya hakura dake idan kuma yaqi zai k’are rayuwarsa a prison.”

“Ka daina wannan maganar Khalid yanzu ni a ina zan sameshi har na fad’a masa sa’kon ka a kansa don Allah ka rage kishi ba abune mai kyau ba.”

” Wannan abun da nake ba kishi bane gyara ne na lura dake dashi baku da Ilimin addini ba kusan menene hakkin aure ba shiyasa kuke abinda kuka ga dama to ke d’in ma tsatstsauran mataki zan dauka a kanki mutukar baki daidaita sahun ki ba.”

“Khalid ni kake kira da suna jahila har kana fadin ban san hakkin aure ba har yaushe aka haife ka? yaushe kazo duniyar da zaka dinga yi wa mutune rashin kunya ko ka manta cewa a gabana aka haife k……….Kafin ta ‘kara maganar ya kifa mata lafiyayyan mari! yana wani irin huci yace.” Kada ki kuskura kice zaki min wannan haukan! ranki ne zai ‘baci wallahi ina ruwana da wani shekarun ki duk girman ki a k’arkashina kike dole kibi umarnina idan ba haka ba ki fuskanci bacin raina.”

Yana gama maganar ya bar gurin yana numfarfashi na bacin rai.

Hannu dafe da fuska na bishi da kallo har ya bude kofar toilet din ya shige.

Wasu hawaye masu tsananin zafi ne suka tsinke min wai yau yaron nan ni yake mari ikon Allah! wani abu mai nauyi ne yazo ya tsaya min a makogwaro shin wai menene mafita? ta yaya zan daidaita alaka ta dashi wai shin gabad’aya haka halin maza yake? babu shakka idan duk haka halinsu yake dole aure ya dinga saurin mutuwa babu uziri a cikin al’amuransu duk mazan data aura hakan suke da irin wannan halin.

Ina jin motsin fitowarsa nayi saurin Kwanciya ido na rintse ina nanata kalmar innalillahi wa’ina ilahi raji’un a cikin zuciyata…….Ina jinsa ya gama shirye-shiryen sa yazo ya kwanta gefe na amma ko da wasa baiyi kuskuran ta’ba wani sashe na jiki na ba……Cikin mintinan da basu wuce goma ba naji saukar numfashinsa bacci har ya daukeshi, ajiyar zuciya na sauke a hankali na lalla’ba na sauka daga gadon toilet na nufa domin daura alwala Nafila zanyi domin na kaiwa Allah kuka na.”

Alhaji Nura kuwa tsabar tension ya sanya sitiyarin mota ya k’wace daga hannunsa a take motar ta dinga walagigi a kan titi abinka da daran sanyi sahun mutane ya dauke sai jefi-jefi Cikin tashin hankali ya dinga kokarin kashe motar domin ta tsaya abun yaci tura sai kawai ya shiga kalmar shahada Mussaman daya hango wata katuwar akori kura cike da katako tayo kansa. hannu na karkarwa ya fara kokarin bude motar domun ya fita daga ciki sai kawai yaji motar ta hantsila dashi ‘kasa……”Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un.” A take motar tashi ta fara hayaki wuta na kokarin tashi, hayaniyar jama’a ya dinga ji sama-sama a kunnenshi ya dinga kiran sunan Allah yana kalmar shahada wutar ce ta tashi a daidai lokacin da jama’a ke kokarin taimakon sa ganin haka yasa kowa ya watse daga gurin wuta ta tashi a motarsa da motar katakon da suka had’u. da kyar ‘yan a gaji suka samu nasarar kashe wutar gurin ya turnuke da haya’ki Alhaji Nura k’urmus aka fito dashi duk wani mai imani idan ya ganshi sai ya zubar da hawaye Allah sarki duniya ashe dama Alhaji Nura daf yake da barin duniya babu wanda ya san gaibu sai Allah….Labarin mutuwarsa ya zagaye garin Kano saboda shi din sanannan mutum wanda duk mutumin da yake shiga kasuwar Kwari ya san da zaman shi Abokan kasuwancin sa suka shiga alhini da damuwa.

Gwaggo kuwa kuka ta dinga yi tana fad’in “Allah Sarki Alhaji Nura Allah ya jikan ka mutumin arziki babu kai babu shiga wutar jahannama Allah ya jikan ka ya kar’bi shahadar ka.” Rigima tasa akan lallai sai Kawu ya shirya ya kaita gidan mutuwar domin ayi jana’iza da ita.

Kawu da yake shima a cikin alhini yake bai mata gardama ba ta shirya ya d’auketa a motarsa domin zuwa gidan jana’izar DUNIYA KENAN ALLAH KASA MU CIKA DA KYAU DA IMANI.

Koda Khalid yazo gidan Ummatu ke sheda masa mutuwar jikinsa ne yayi sanyi damuwa da nadama suka baibayeshi ashe ma dik wannan hargitsin mutumin saura kad’an ya mutu kai gaskiya al’amarin ya girgiza shi mutuka, adduar samun rahamar Allah yayi masa yayi mata sallama domin tafiya harkokinsa.

To koda ya dawo da daddara kasa fad’a mata mutuwar yayi ya dai sassauta fuskarsa Sa’i da lokaci kuma yana satar kallonta da tunanin yanda zaiyi ya fad’a mata mutuwar mutumin.

Washe gari da safe yana shiryawa na shiga dakin cikin rashin kuzari nace.” Amma Zaka tsaya kayi break fast ko.”? Ya kalleta da fadin.” Ba zanci abu mai nauyi ba don bana so jikina ya mutu za muyi wasa da abokaina sai dai idan na dawo.

Nace.”Ai ko tea kasha ka gasa cikin ka ko.” Yace.” To shikkenan muje ki had’a min.” Gaba nayi ya biyo bayana, tea din na had’a masa ya dauka yana sha yana kallona ni kam gabad’aya jikina a mace yake na rasa abinda yake damuna.

“Kina da labarin mutuwar…..Kasa ‘karasawa yayi kawai ya zuba min ido.

Cikin fad’uwar gaba nace.” Mutuwa waye ya mutu.”?

Sunkuyar da kansa yayi yana motsa tea din gabansa yace.” Sai hakuri dukkanin mai rai mamaci ne Alhaji Nura ya rigamu gidan gaskiya kwana biyu da suka wuce.”

Wani irin kallo nake masa kafin wasu zafafan hawaye su wanke min fuska nace.” Yanzu Alhaji Nura ya mutu har anyi kwana biyu amma a rasa wanda zai fad’a min.”

Haushi ta bashi ganin tana kuka, sai kawai yaja bakinsa yayi shuru ya cigaba da kur’bar tea d’insa.

“Khalid me yasa kasan da mutuwar baka fad’a mun ba ashe shiyasa kwana biyu gabad’aya na rasa abinda ke damuna Allah Sarki Alhaji Nura ya mutu ya bar wannan duniyar mai cike da rud’ani.”

Ya kalleta da fad’in.” Wannan kukan dai da kike bashi da fa’ida addua zaki masa idan kuma zaki bishi lahirar dama hanya a bud’e take.”

Cikin hawaye tace.” Eh idan lokaci na yayi dole na tafi ko inaso ko bana so babu wanda zai zauna ya dawwama a duniya can ne gidan gaskiya sabida haka dik wanda ya dauki zafi da duniya to gwara ya sauke domin ba matabbata bace.”

‘Bata rai yayi yace.” Sa’ida maganar nan ta isa haka bana bukatar ta.” Miqewa nayi na bashi gurun, ina jin sanda yake jan dogon tsaki a kaina.

Bayan Kwana uku da faruwar al’amarin Hauwwa har gida tazo tayi min gaisuwa muka jima muna jajanta al’amarin yanda take bani labarin irin mutuwar da yayi yasa na dinga zubar da hawaye nace.” Hauwwa aini gabadaya Khalid bai fada min ba yace kawai ya mutu amma bece dani accident yayi ba.”

Tace.” Aikuwa yana da kyau kije gaisuwa domin a ranar da mukaje gaisuwa da jama’ar gidanmu Mahaifiyarsa da matarsa Murja sai tambayarki suke.”

Nace.”Allah Sarki Insha Allahu zanje nai musu gaisuwa Hauwwa amma bana tsammanin har ya mutu da aure a tsakaninsa da Murja kin san tunda asirinta ya tuno shikkenan suka rabu.”

Hauwwa tace.” Allah sarki amma ba kiga yanda ta shiga damuwa ba ni dai har muka fito daga gidan bata daina kuka ba.”

Nace.”Hauwwa ai dole aunty Murja tayi kuka Uban ‘ya’yanta ne fa kuma ta cutar dashi sosai ta yaudareshi ya dauki amana da yarda ya bata amma ta zalince shi take masa fasikanci a gida.”

Hauwwa tace.” To Allah ya shiryeta yasa mutuwar tasa ta zama silar shiryuwarta Allah kuma ya raya abin da ya bari.”

Hawaye na share da fad’in.” Ameeen ameeen Ya Allah.”

Mun jima tare da Hauwwa muna hira nan take bani labarin tsakaninta da Yaya Aminu sun fahimci juna sosai amma kuma tana jin tsoron auransa saboda kada ya kasa biya mata bukata.

Kwantar mata da hankali nayi nace.” Hauwwa insha Allahu ba zaki samu matsala ba domin kuwa ina ji a jikina cewar Yaya Aminu ya samu lafiya saboda haka ki aureshi da kyakykyawar manufa.”
Tace.”To shikkenan Sa’ida ki taya ni da addua akan al’amarin.” Nace.”Insha Allahu zan miki addua Hauwwa Allah ya baku zaman lafiya.”
Ta amsa da “Ameen ya Allah ‘kawata.”

Duk da nasan ba a gurina yake ba sai da na zauna zaman jiran shigowarsa domin sheda masa uziri na na zuwa gidan gaisuwar Alhaji Nura, to har wajen goma da Rabi na dare ina zaune a falo bai shigo ba mikewa nayi na nufi bakin window domin na duba naga ya dawo ko kuwa wani sa’in haka yake yi ko ya dawo baya shigowa yayi min sallama sai da safe idan zai fita, duka motocinsa suna nan alamu ya nuna ya jima da dawowa, girgiza kaina kawai nayi na saki labulan window din daki na nufa domin na kwanta na samu nutsuwa amma a zahirin gaskiya al’amarin yaron ya soma isa ta.

Washe gari
Da wuri na kammala komai na shirya tsaf na zauna zaman jiran shigowarsa………..Cikin ‘kananun kaya ya shigo ya shirya tsaf da shirin futa amma babu walwala a tare dashi.

Kauda ‘bacin raina nayi na gaishe ya amsa yana gyara wuyan rigarsa Yace.”Za muje asibiti da Jamila yanzu.” A nutse nace.”Me yake damunta.”?

‘Dan ya mutsa fuska yayi yace.”Zazza’bin dare take sai kasala da rashin kwarin jiki.” Nace.” Allah sarki Allah ya bata lafiya .” Ya amsa da ameen yana kokarin fita…….Sunansa na kira yaja ya tsaya yana kallona.

Nace.”Inaso naje gidan gaisuwar nan.”? Shuru yayi yana kokarin bude kofar dakin. Nace.” Kaga yau sadakar bakwai zan samu jama’a sosai sai nayi musu gaisuwa.”

Cikin takaici yace.”Ke yanzu idan akace dake kije sai kije.”?

Rai a ‘bace nace.” Wace irin magana ce wannan ko babu haihuwa a tsakanina da mutumin akwai ala’kar aure data had’amu kada kuma ka manta irin hidimar da yayi mana nida Gwaggo wannan mutumin bai cancanci wulakanci ba.”

A harzu’ke yace.” Ke komai qabli da ba’adin da zaki kawo min babu inda zakije mutu’kar ni ne zan baki umarni idan kikayi masa addua ma a gida ta isa.

Yana gama maganarsa yasa kai ya fice daga dakin….Rasa bakin magana nayi kawai na tsirawa guri guda ido ina mamakin al’amarin.

Jamila ashe ciki ta samu sai bayan sun je asibitin likita ya tabbatar musu dashi Khalid yayi farin ciki sosai sai dai kuma likita ya kafa sharad’ai domin ingantuwar cikin nasu mahaifar Jamila bata da k’wari tana saurin budewa likitan yace kada ta dinga daukar abu mai nauyi babu zurga-zurga sannan shima Khalid din kada ya takura mata da fitina. duk abinda za suyi su bari cikin yayi ‘kwari tukkuna.

Jamila rawar kai ya ‘karu sai langwa’bewa take miji na rarrashinta Baito kakarsu ‘kullo kaya tayi ta tare a gidan wai tazo tayi jinyar ta zuwan ta ne ma yasa nasan da samuwar cikin dan har sashena ta shigo tana yar min da habaici ni dai uffan ban ce mata ba ta gaji da surutan ta ta tashi ta tafi.

Tun da likita ya kafa masa wannan sharad’in ya takura min da fitina babu dare babu rana gajiya nayi na daina yarda yana wahalar dani da yake makiri ne sai wani shagwa’be wani sa’in har kuka yake min yayi ta rarrashina amma fa idan rashin mutuncinsa yazo sai ya sauke min sama da kwando goma hakuri kawai nake da zaman aure domin nasan ibadah ne.

Gwaggo tazo duba Jamila da ‘yan kayan dubiyarta…… guri na ta fara yada zango muka gaisa sosai na bata abinci taci ta koshi sai bayan tayi sallar azuhur ne ta kalle ni cikin alhini tace.”Ke kuma Sa’ida me yake damunki naga kinyi rama dubi kashin wuya ko dai kishi kika sa a ranki.”

Girgiza kaina kawai nayi nace.”Gwaggo wane irin kishi kuma Khalid ne kawai yake azabtar dani yaki bari mu zauna lafiya masifar yau daban ta gobe daban kullum babu sassauci.”

Tace.”Me yasa kin san halinsa ba zakiyi hakurin zama dashi ba ina nufin kiyi kokarin ganin kin kauda abinda zai kawo muku sa’bani a tsakaninku.”

Girgiza kaina nayi nace.” Gwaggo kenan ban san me zance miki ba amma ni nasan ta kowane ‘bangare bana zalintar yaron nan shine kawai ya kasa kwantar da hankalinsa.”

Tace.”To kuwa idan hakane zaizo ya sameni ni bana son rashin adalci na lura dama kamar yafi karkata gurin kishiyarki to mutukar yace ba zaiyi adalci a tsakaninku ba yana tare da fushin Ubangiji.”

Nace.”Yana dai da kyau ki zaunar dashi ki masa fad’a ni na gaji da wannan masifar wallahi.” Tace.”Kada ki damu tashi ki rakani na duba jikin nata.

Hijabi nasa muka fita tare………Kaca-kaca muka samu falon Baito da Ummatu da mahaifiyar Jamilan suna zaune sai hira suke sun ci abinci dik sun baja-baja dashi a kasan kafet Jamilan kuma na kwance akan doguwar kujera tana bacci.

Gwaggo ta samu guri ta zauna tana kallon Ummatu tace.”Ashe nan kika nufo kema.”? Cikin inda-inda tace.”Eh wallahi nazo duba jikin nata ne ” Tace.”Ai babu laifi.”

A nutse na gaisa dasu suka amsa babu yabo babu fallasa Gwaggo kuwa babu wacce ta gaisar a cikinsu ya mutsa fuskarta tayi tace.” Ku kuwa don Allah bakwa jin tsami da karni a falon nan wace irin rayuwa ce wannan kuzo gidan yara kuna ‘barna a maimakon gyara.”

Falon yayi tsit! cikin zuciyata nace.”Gwaggo ba’a ci miki bashi……..Ta cigaba da cewa.” Ai amfanin zuwanku shine kuyi mata gyare-gyare ku sata tayi wanka ku kwantar mata da hankali amma duba don Allah sai hayaniya kuke kunyi kaca-kaca da gurin Haba Baito a wannan zamanin da ake saurin daukar ciwo ai idan su basu da hankali ke kina dashi sai ki tsawatar musu.”

Baito ta ‘bata rai da fad’in”Gwaggo Matsalata dake kenan shiga sabgar da bata shafe ki ba ina ruwanki da abinda idonki ya gane miki.”

Tace.”Babu ruwa na amma ni bazan ga abunda bai dace ba nayi shuru dole sai na fadi gaskiya koda zaku tsire da tsinken tsire .” Nace.”Gwaggo dan Allah maganar ta isa haka.

Jamila ta mike zaune tana hamma! Gwaggo ta zuba mata ido tana kallo magana ce a bakinta amma dai tayi shuru…..Jamila kamar bata so ta gaisheta ni kuwa ai ko kallon inda nake bata yi ba.” Gwaggo tace.” Jamila ga kayan Lambu nan na kawo miki Allah ya kara sauki ya raba lafiya.”

Gabadaya suka amsa da ameeen ya Allah.” Ta mike tana gyara lullu’bin mayafin ta “To ni zan tafi.” mikewa nayi Baito da Ummatu suka ce “To shikkenan muma yanzu zamu tawo.”
Tace.”Oh!o kuna iya kwanciyar ku tunda zaman ku a gurin shine zai bata lafiya ciki dai ba akanta a kafara ba kuma ba za’a k’are a kanta ba.”

Baito tace.”Ramatu wannan habaicin ya isa haka ko don kinga nayi miki shuru ne ? ciki dai Allah ne ya bawa Jamila kuma babu mahalu’kin da ya isa yace ciki ba na Khalid bane.”
Gwaggo tana kokarin magana na rufe mata baki da sauri na rike hannunta na jata muka fita daga falon……..

*104*
Kamar ‘Yar jagora haka nake jan hannunta ta fizge da fadin.”Sakar min hannu ni ba makauniya ba sai jana kikeyi ina zaki kaini.” ? Kallonta nayi tana gyara mayafinta nace.”Gwaggo don Allah ki dinga hakuri da rayuwa wannan cacar bakin da kuke yi sam bai dace ba yanzu an riga an zama daya ni wallahi zuciya daya nake zaune da Jamila shiyasa kwata-kwata bana daukarta a matsayin kishiya sai ‘yar uwa.”

Ajiyar zuciya ta sauke tace.”To naji dadi da kika fad’i haka saboda haka sai ki cigaba da zama da ita da zuciya daya idan ma ita ta nufe ki da sharri zai koma kanta, sannan kina magana akan su Baito kin dai san halina ni ba zan ga ana ba daidai ba nayi shuru da bakina sai na fad’a musu gaskiya sai dai duk abinda zasuyi suyi.” Nace.”To gurin fadar gaskiyar ki san irin maganar da zaki dinga fad’a dan Allah.” Shuru tayi nace.”Muje nasa driver ya kai ki gida ko.”

Tace.”To dama zaman me zanyi tunda nayi abinda zanyi sai dai idan Jarumi ya dawo ki fada masa cewa ina nemansa domin da kyar idan zai je inda nake tunda ba kullum yake zuwa ba.”

Nace.”To shikkenan Insha Allahu zan fad’a masa.” Ina tsaye dravar yaja motar maigadi ya bude gate suka fita daga gidan, ajiyar zuciya na sauke tare da juya da niyyar komawa cikin gidan.

“Baito wai menene naga tunda na shigo kike shan kunu ko kin gaji da zaman jiyyar kina so ki tafi gida.”? Khalid ne yake wannan maganar a lokacin daya dawo gidan.

Cikin b’acin rai tace.” Khalid raina ne a ‘bace wallahi saboda bayan fitarka daga gida kakar ka Gwaggo da matarka suka zo har nan inda nake suka ci mana mutunci harda kiran zuriarmu da makwad’aita matalauta ‘kazamai kai babu irin cin mutuncin da ba suyi mana ba ‘Karara suka nuna bakin cikinsu akan cikin dake jikin Jamila Al’amarin ya bani mamaki sosai.”

Shuru yayi yana kallonta da nazarin maganarta yasan halin Gwaggo da fadin gaskiya da kuma rashin hakuri amma baya tsammanin za tayi irin wannan cin mutuncin kuma tunda ta samu labarin cikin Jamila take farin ciki da adduar sauka lafiya shiyasa yake nazarin maganar.

Baito tace.”Ai dama nasan ba yarda za kayi ba tunda kai kullum baka son laifin kakar ka ‘kiri-‘kiri ka nuna mana cewa tafi mu muhimmanci a rayuwarka.”

Yace.”Baito kiyi hakuri don Allah zanyi binkice akan maganarki idan na gano da sanya hannun Sa’ida a cikin al’amarin zan dauki mataki domin ni babu wata mace da zan aura ta raina min dangi.”

Baito tace.”Ai shikkenan tunda ka ‘karya ta maganata sai kaje kayi ta binkicen.” Shuru yayi mata ya mayar da hankalinsa kan Jamila dake xaune a gefansa tana faman ya mutsa fuska……”Ya jikin naki ina fatan dai lafiya.”? a shagwabe tace.”Lafiya lau amma fa babyn nan naka yana wahalar dani ko ba haka bane Baito.”?

Tace.”Kwarai kuwa hakane wannan cikin ai tsirfar sa yawa gare ta.” Yace.”To ko zakuje asibiti idan Allah ya kaimu.” Baito tace.”Aa ai ba sai anje asibiti ba laulayi ne kawai kuma duk mai yaron ciki tana irinshi mu dai babban fatan mu yarinya ta haihu lafiya.” Yace.”To shikkenan Allah ya kara lafiya ya kuma sauketa lafiya.” Gabadaya suka amsa da Ameeen.

Mi’kewa yayi da wayoyinsa a hannu yace.”Ni zan shiga na watsa ruwa na kwanta na huta sai da safe in Allah ya kaimu.” Baito tace.”To Allah ya tashe mu lafiya.” Jamila kuwa shuru tayi tana bin shi da kallo wani irin bakin kishi yana taso mata gaskiya ta kusa ta karya dokar likita dan ba zata iya jure rashin mijinta ba.

Jin motsin shigowarsa yasa nayi saurin kallon bakin kofar……….Ido muka had’a dashi a lokacin da ya shigo falon. a nutse nayi masa barka da zuwa ya amsa tare da nufar bedroom d’inshi.

Kamar kada nabi bayansa sai da na mike na shiga dakin na sameshi zaune a bakin gado yana kwance necktie din wuyanshi. kallona yayi nan naga yanda kwayoyin idanunsa suka sanja a nutse nace.” Da alama dai ba kajin dadi.” Shuru yayi baice min komai ba ya kwance agogon hannunsa ya ajiye kan bedside trouser din jikinsa ya cire ya kwanta daga shi sai gajeran wando. Zama nayi kusa dashi da fadin.” Ba za kayi wanka ba zaka kwanta ga abinci can yana jiran ka.”

“Babu wani abu da zan iya gabatarwa a halin yanzu.” A nutse nace.”Saboda me ko wani abu na damunka.” ?

Ido ya ‘kura min yana min wani irin kallo lokaci guda na fahimci abinda yake da akwai. ‘Bata raina nayi na fara kokarin barin gurin. da sauri ya janyo hannuna na afka kanshi, rungumeni yayi tsam-tsam a jikinsa yana shashshafa ni! “Kada kice zaki hana ni don Allah ki bari nayi koda sau d’aya ne wallahi da masifar sha’awa na yini da kyar na dinga gabatar da al’amura na ki taimaka min kinji Auntyna.”

Ajiyar zuciya na sauke nace.”Khalid ka iya dad’in baki idan kana neman biyan bukatarka ko me yasa wai baka ganin mutuncina sai sanda kake bukata ta.”

Yana kesses din fuskata yace.”Aa ni kinyi min mummunar fassara sam ba haka nake ba mutukar kinga ina miki fad’a akan wani dalili ne na daban amma ba wannan ba.”

Shuru kawai nayi masa sabida nasan duk tawayen da zanyi masa ba zanci riba ba tunda ya riga ya matseni nasan sai ya biya bukatarsa.

Sosai naji jiki a hannunsa kafin ya saurara min ina kallonsa yasa wandonsa ya nufi toilet domin tsarkake jikinsa………Har ya fito ban motsa ba ina kwance a gadon zazzafan zazzabi ya rufe ni.

Sai da ya kimtsa jikinsa yazo ya tsaya a kaina da fadin.” Har yanzu baki tashi ba ko dai sai na kara wani.” ? Ido a rufe nace.” Zazza’bi ne ya rufe ni wallahi.”

Yace.”Sannu ki daure ki tashi ki wanke najasar dake jikin ki ina falo ina jiran ki.” Hanyar fita ya kama Idona na bude ina kallonsa yana kokarin bude kofa nace.” Kazo ka taimaka min mana kaina yayi min nauyi sosai.”

Dawo wa yayi ya mikar dani tsaye ya kalleni da fadin.”Ko na d’auke ki ne.”? girgiza kaina nayi kawai nasa hannuna a kafadarsa ya rike ni muka nufi toilet din. sai da ya tabbatar ta fara wankan sannan ya fita daga bandakin.

Koda na fito daga toilet din kayan bacci kawai nasa nasha paracetamol na nemi guri na kwanta bacci mai nauyi ne ya dauke ni………….Can cikin bacci na dinga jin magana da sauri na bude idona yana tsaye a kaina magana yake akan na tashi na bashi abinci.

Takaici kamar ya kashe ni nace.”Don Allah yau d’aya kaje ka zuba abincinka da kanka wai kai ba kai wa mutane uziri ne.”?

A hasale yace.”Ni kike wa tsawa.”!? Na daga masa hannu da fadin.” Kaga yanzu dare ne bana bukatar hayaniya bayan haka kuma nace maka bani da lafiya me yasa ba zaka tausaya min ba.” Wani irin kallo ya watsa min kafin yaja tsaki mai karfi ya bar gurin. kallon mamaki nake masa har ya fita daga dakin.
Washe gari da safe da rashin karfin jiki na tashi amma dai hakan bai hana ni yin ayyuka na ba yana kwance yana bacci na kammala komai na zauna ina tashinsa.

Ido ya bude da fadin.”Malama ki kyaleni na huta bacci nakeji.” Daure zuciyata nayi nace.”Ba zaka fita ba kenan.”? banza yayi min yaja bargo ya rufe jikinsa.

Nace.”Jiya Gwaggo tazo ta bani sa’ko gurin ka.” Kallona yayi da lumassaun idanunsa, nace.”Gwaggo tace lallai kaje tana neman ka.” Idonsa ya rufe da fadin.”Naji sai na tashi a bacci zanje.” Ba tare da nace uffan ba na mike… ina kokarin fita kira ya shigo wayarsa. ” Zo ki miko min waya ta.” Yafad’a ba tare da ya bude idonsa ba, ko kallonsa banyi ba na bude kofa na futa daga dakin.

Ransa ya ‘baci sosai da abinda tayi masa ya mike cikin kasala da bacci ya dauki wayar yana dubawa sai yaga Jamila ce. Wayar yasa a kunnansa da sallama ciki-ciki a bakinsa.

“Yaya Khalid kazo baby naso yaji d’umin ka.” Jamila ce ke wannan maganar.

Cikin yanayi na me jin bacci yace.”Ki bashi hakuri kafin nazo yanzu bacci ne a idona amma daga na tashi zan shigo na gaisa dashi.

Fashewa tayi da kukan shagwaba da fad’in.”Ni dai don Allah kazo yanzu muke so mu ganka.” Ajiyar zuciya ya sauke yace.” To daina kuka gani nan zuwa.” Kashe wayar yayi ya lalubi singlet dinsa yasa…..Ina zaune a daining ina karyawa ganin ya kama hanyar fita yasa na bishi da kallo koda ya fita din kasa hakuri nayi sai da naje na daga labulan window ina lekansa nan naga ya nufi Side din Jamila, girgiza kaina kawai nayi na koma na zauna Wato na fad’a masa Gwaggo na nemansa yana masifa amma yanzu gashi matarsa ta kirashi ya tafi Allah ya kyauta.

Ita kuwa Jamila dama da wata manufa ta kirashi koda ya shiga gurin nata rikeshi tayi ta dinga tsokano masa da sha’awa dama me neman kuka ne nan take ya turmushe ta a gado ya shiga biyan bukatarsa ya manta da sharad’in Likitansu.

Sai waje sha d’aya ya shigo ko kallon inda nake zaune beyi ba ya bude dakinsa ya shiga ya kwanta ya cigaba da baccinsa.

Misalin karfe biyu da rabi na rana Uwale tazo gidan cikin girma da mutunci na tar’be ta muka gaisa sosai na bata abinci taci ta koshi nan take sheda min cewa tazo duba jikin Jamila ne da yake kwana biyu taje kauye ziyara sai jiya ta dawo shine data shiga gidan Gwaggo take fada mata shine tace yana da kyau tazo ta dubata tunda an zama d’aya.

Nace.”Kwarai kuwa hakan yana da kyau bari na dauko hijabi na raka ki gurin nata.

Lokacin dana shiga dakin yana zaune akan dadduma da alamar sallah yayi ba tare dana kalleshi ba nace.”Uwale ce tazo yanzu.” Kallona yayi fuska a hade yace.”Me tazo tayi .”?

Nace.”Duba jikin Jamila tazo wai jiya Gwaggo take fada mata shine tazo ta dubata.”

Tsaki yaja da fadin.” Munafurci ne dai ya kawo ta yanzu zan korata dan ni bana son gulma da had’a husuma a gida.”

Mikewa yayi zai fita na tare hanyar da fadin.”Wai kai don Allah me yake damunka? me yasa dik wanda zaiyi maka alkairi sai ka mayar masa da sharri ina laifin Uwale don tazo duba matarka.”

Ture ni yayi da fad’in.” Uwale ba mutuniyar arziki bace shiyasa bana son mu’amularta da Gwaggo yanzu ma na tabbata sharri ne ya kawo ta gidan ba alkairi ba.”

Nace.”To don Allah kayi hakuri kada ka wulakantata koda ta nufe ka da sharri zai koma kanta kayi hakuri ka kyaleta.”

Ba tare da ya sake magana ba ya bude kofar ya fita da sauri nabi bayansa da hijabi a jikina.

Uwale na ganinsa ta washe bakinta da fadin.”Au Ashe ma maigidan yana nan Khalidu Jarumin maza na Gwaggo mijin Sa’ida da Jamila.”

Duk wannan rawar jikin da take masa bai sa ya saki fuskarsa ba a dakile ya gaisheta ya kama hanyar fita Uwale jikinta yayi sanyi da wulakancin da yayi mata……….Nace.”Kiyi hakuri Uwale daga bacci ya tashi shiyasa babu walwala a tare dashi.” Ya’ke tayi tace.”Aifa naga alamun haka to yanzu wannan soyayyiyar gyad’ar dana kawo muku ya zakuyi da ita.

Nace.”Bari na d’an d’ibi kad’an sai ki bawa Jamila sauran nasan zata fi ni bukatarta saboda cikin jikinta.”

Tace.”To shikkenan kema Allah ya baki naki musha suna.” murmushi nayi na amsa a cikin zuciyata.

To a takaice dai Khalid bai je kiran da Gwaggo take masa ba sai bayan kwana hudu da zuwanta gidan……..Koda yaje gidan Gwaggo kin kallonsa tayi sai da ya rarrasheta sannan ta saurareshi Tace.”Khalid ka watsar dani kana nuna min ban isa da kai ba ko? yanzu tun yaushe nake nemanka ba kazo ba sai yau da kayi ra’ayi.

Yace.”Gwaggo don Allah kuyi hakuri kuyi min uziri Abubuwa da yawa suka sha kaina itama Ummatu rabona da zuwa inda take kwana hudu kenan.

Tace.”Ko ba kaje inda take ba ai kana waya da ita.” Murmushi yayi yace.”Eh hakane kema ai na baki daya daga cikin wayoyina kince bakya so.” Tace.” Yo ni me zanyi da wannan waya ai wahala zata bani gwara irin wacce ta lalace tafi sauki.”

Yace.”To insha Allahu kuwa yau zan siya miki in yaso duk sanda banzo ba sai na dinga kiran ki muna gaisawa.” Tace.”To hakan yayi daidai.

Shuru tayi na minti biyu kafin tace.” Khalid me yasa kullum baka bukatar zaman lafiya da iyalinka.”?

Cike da mamaki yake kallonta “Gwaggo bangane maganarki ba.” Tace.” Lokacin da naje duba Jamila hankalina ya tashi da naga Sa’ida cikin halin damuwa duk ta rame ta lalace haba Khalid ya zakayi min haka kuma.” Murya na rawa ta karasa maganar.

Jikinsa a sanyaye yace.”Gwaggo tace dake inayi mata wani abu ne.”?

Girgiza kanta tayi tace.”Aa ba tace ba amma dai tace kullum babu kwanciyar hankali a tsakaninku.” Shuru yayi yana dan tunani…..Tace.”don Allah idan da wani hali da kake mara kyau ka daina ka zauna lafiya da iyalinka Khalid ka tausayawa ‘yar uwarka mana ko baka ganin ramar da tayi.”

Yace.”Gwaggo ni yanzu ban san abinda zance miki ba nasan ni ina kokari a cikin gidana kuma duk wani abu da zan fito nayi magana a kai mai muhimmanci ne to amma tunda kince haka zan kara kiyayewa.

Tace.”To nagode sosai Khalid ina rokon Allah yayi riko da hannuwanka Allah ya baka ikon adalci a gidanka.” Ya amsa da ameeeen ya rabbi Gwaggo nagode sosai.

Fuskarsa kadai na kalla na gane akwai damuwa kama kaina nayi ban shiga sabgarsa ba, hakan da nayi sai ya sake tunzura masa zuciya yazo ya tsaya a kaina da fadin.” Me nake miki kika kai ‘karata gurin Gwaggo shin na hana ki ci ko na hana ki sha a gidana.”?

Girgiza kaina nayi a murtuke nace.”Babu rashin ci babu rashin sha a gidanka sai dai akwai rashin nutsuwa da kwanciyar hankali.” Ya kalleni da jajayen idonsa yace.” Ko zaki fada min abinda ya janyo miki rashin nutsuwa da kwanciyar hankalin.”?

“Wannan kuma kai za’a tambaya namiji shike kawo nutsuwa da zaman lafiya a gidansa idan yaso idan kuma beso ba zai iya kawo akasin haka.”

Tsaki yaja da karfi yace.”Tun sanda kika fahimci cewa Jamila nada juna biyu kike fushi da b’acin rai shin waye yake bada haihuwa idan ba Allah ba me yasa Zaki sanya kanki a cikin damuwa saboda kawai kishiyarki nada ciki ke baki dashi gashi kin janyo jamaa nayi min wani irin kallo.

Cike da takaici da bacin rai nace.” Khalid cikin matarka baya gabana ballanatana na damu dashi haihuwa da rashinta duk Allah ne yake yi saboda haka idan ma tunanin da kake kenan to ka daina domun ni nayi imani da Allah da manzonsa.”

Yace.”Idan kinyi Imani da Allah da Manzonsa kuma kin dauki Jamila a matsayin ‘Yar uwarki me yasa har yanzu baki saki jiki da ita ba? me yasa kullum kike cikin damuwa da ‘bacin rai.”

Girgiza kaina kawai nayi na mike da niyyar bar masa gurin…..Ya tare ni da gangar jikinsa kallonsa nayi da fadin.”Bani hanya na wuce.” Yace.”Wato kin mayar dani mahaukaci kenan.” dauke kaina nayi yasa hannu ya juyo da fuskata ina kallonsa……”Kada ki sake zuwa ki kai ‘kara ta gurin Tsohuwa bana bukatar ‘bacin ranta.” fuskata na fuzge da fadin.” Dallah malami matsa ka bani guri kullum kana ‘kara girma da shekaru amma ka’ki kayi hankali.”

Baki ya bud’e yana kallona na buge kirjinsa da ya tare ni dashi bedroom d’ina na bude na shiga na kwanta kan gado bakin cikin duniya ya isheni.
Tunda ranar ya dauke min wuta ya daina kula ni ko shigowa sashen yayi baya shiga sabgata zaiyi abinda ya zaiyi ya fita gabadaya ya tare a gurin Jamila ya ma daina kwana a gurina hakan yayi min dadi sosai dama takura min yake gashi ba cikakkiyar lafiya gare ni ba.

Sati guda da faruwar al’amarin Jamila ta tashi da ciwon mara mai tsananin gaske kafin ma suyi wani yunkuri jini ya yanke mata hankali a tashe suka nufi asibiti suna zuwa cikin ya fita sosai tasha wuya kuma ta zubar da jini mai yawa……..Baito ta dinga kuka saboda rashin tawakali sai suka d’orawa Uwale sharri suka ce ai gyad’ar data kawo ce tayi sanadiyar zubar da cikin wai had’a baki sukayi da Gwaggo tunda ‘kawarta ce……Shima khalid din da yake bashi da tsinkaye sai ya yarda da maganarsu ya dinga cika yana batsewa da fadin.” Sai yayi sharia da ita…….Gwaggo tare da Uwale suka je asibitin domin duba Jamilan Baito da sauran ‘ya’yanta suka dinga sakin habaici dan wata mara kunya ma a cikinsu har sai da ta zagi Uwale da fadin.” Duk sharrin da suka k’ulla cikin ya zube sai Allah ya tona musu asiri…..Uwale ta dinga share hawaye tana fadin.” Ni kuwa me Jamila za tayi min da zan bata guba a cikin gyada.” Gwaggo ranta a bace ta kalli Baito da fadin.” Wallahi ku dai ‘kananun mutane ne marasa tawakalli masu yarda da jita-jita kawai.” Baito tace.”Asiri dai ya tonu baku da bakin magana.”

Rai a ‘bace suka bar asibitin…..Bayan sun koma gida da daddare Khalid yaje gidan yana tashin hankali wai wallahi Sai ya daure Uwale tunda ta bawa matarsa gubar da tasa cikinsa ya zube .

Tashin hankali yasa Gwaggo ta fad’i hawan jininta ne ya tashi, hankali a tashe suka nufi asibiti ganin halin da Gwaggon nashi take ciki yasa jikinsa yayi mugun sanyi.

Ni kam in banda share hawaye babu abunda nake masifar yau daban ta gobe daban gashinan garin rashin hakurinsa matsala ta afku gabad’ayanmu hankalinmu bai kwanta ba sai da aka sallami gwaggo daga asibiti…….Kawu ya dinga yi masa fad’a da fadin.” Mutukar ‘bacin ransa ya kashe masa mahaifiyarsa sai ya hukuntashi. Khalid dai hakuri kawai yake bashi yana fadin.” Insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba.

****
Hajiya Aziza a gurin harkar lesbian ta hadu da wata mata mai suna Elizabeth suka kulla abota ashe ‘yar mafiya ce bata sani ba ta saki jikinta da ita sosai suke sha’aninsu matar na sakar mata kudi sosai Hajiya Aziza ta dinga cin duniya da tsinke tana jin dadin duniya……….Rana tsaka k’ungiyarsu ta mafiya ta ‘bukaci da Elizabeth ta bada mutum dodon tsafinsu na bukata ba tare da tunanin komai ba ta mika musu Hajiya Aziza a daran ranar dodon tsafin ya shanye mata jini tas Aka wayi gari da gawar ta, Elizabeth ta dinga kuka tana kiran Jesus ‘Yan uwanta arna suka taimaka mata gurin had’a gawar ba tare da sun sallace ta ba suka sa a akwati sukaje suka binne suna wa’ke-wa’ke…….
*Duniya kenan Allah kasa mu gama lafiya*

****
Aunty Murja bata sare da al’amarin duniya ba sai da ta samu labarin irin mutuwar da Aziza tayi ta dinga kuka tana nadamar rayuwa tunda tsohon mijinta ya mutu ta zama saliha ta kasance kullum cikin addua da nema afuwa gurin Ubangiji babban burinta ta daidaita da ‘ya’yanta domin ta gane sune farin cikinta yayin da su kuma yaran suke masifar nadama fitowa ta tsatsonta suna jin bakin ciki a nuna ta a matsayin mahaifiyarsu……
*105* Bayan sati uku Al’amura sun d’anyi sauki Ya rage wulakanci dalilin rashin lafiyar Gwaggo ya sanya kullum burinshi bai wuce mu samu zaman lafiya ba ni kuma a lokacin ne nake jin mugun haushinsa tunda na fahimci ina da ciki shikkenan na tsane shi duk sanda ya kusance ni sai munyi rigima na tsani kamshin turaransa gashi ya’ki ya daina amfani dashi duk da na fada masa cewar bana so amma kamar kara tunzura shi nake……B’angaran sa kuwa shi sam be san tana da ciki ba tunda bata fada masa ba kawai dai yaji gabad’aya ta sauya masa ni’imar ta tafi ta da yana masifar jin dad’inta duk sanda yake gurin Jamila ya dinga bacin rai kenan sai yayi ta neman ta da rigima idan ta biye masa sukayi fad’a sai ta kulle masa kofa wanda dama shi hakan yake so sai kawai ya tafi gurin auntyn nashi ya dameta da fitina Khalid sam baya gajiya da sex kullum kamar kara masa karfi da kuzari ake…………..Yau Yini nayi ina bacci sai bayan la’asar na tashi nai wanka da salolina doguwar riga mai hula nasa kai tsaye kicin na nufa domin samawa cikina abinci, daidai cikina nayi tunda bani ke da girki ba a kicin din na zauna naci na rage wanda zanci da daddare, falon na fito na zauna ina duba waya ta text messages dinshi na gani yana tambayata gida wai ya kasa aikata komai sai tunani na. ‘Karamin tsaki naja ina mamakinsa tunda mukayi aure bai ta’ba fad’a min kalmar so ba sai yau da alama akwai abinda yake bukata aikuwa yau da rigima kenan domin ba zan lamunci shiga hakkin wani ba……Kafin magariba ya dawo gidan a maimakon ya wuce gurin mai girki sai ganinsa nayi ya shigo ido jawur sai kace wani bugagge. babu fuska nayi masa sannu ya zauna kusa dani yana ya mutse fuskarsa, Jin zuciyata tana tashi yasa na mike da sauri na bar gurin. dakin ya biyo ni rai a bace yace.”Wai meya sa kike min hakane.” ? Ba tare dana kalleshi ba nace.”Bana son warin turaranka.” Babu sukuni yace.” Wannan ba hujja bace me yasa tunda nake amfani da turarena baki ta’ba gudu na ba sai yanzu.” Shuru nayi masa Ya matso jikina da fadin .” Tunda na fita nake tunaninki gabadaya na kasa aikata komai kinzo kin tsaya min a raina.” Kallonsa nayi da fad’in.” Ina fatan baka mance cewa ba girki na bane.” Yace.” Ina sane auntyna ke kadai nake bukata Wallahi manège kawai nake da Jamila bata gamsar da ni.” Nace.”Hakanan za kayi hakuri kaje gurinta.” hannuna ya rike murya na rawa yace.”Ba zata iya ba wallahi kece zaki iya ki taimaka min.” Nace.” To jeka tambayeta idan ta amince sai kazo.” Shuru yayi yana kallona nace.” Ko tsoronta kake.” Murmushin takaici yayi yace.” Ni nafi karfin naji tsoron macan dake karkashina kema ba karfi na kikafi ba kawai ina lallaba’ki ne.” Nace.”Okey to kaje kawai.” Mikewa yayi ya fita minti biyar da fitarsa naje na kulle kofar palon na shige daki nai kwanciyata………….Jamila tana zauna a falon ta ya shigo dauke kanta tayi tana kumbura fuska shima bai kula ta ba ya bude dakinsa ya shiga ya watsa ruwa ya shirya jikinsa ya fito massalaci ya nufa sai bayan isha’i ya dawo gidan. Gurin cin abinci ya nufa yaga babu komai akai falon ya sameta tana kallo yace.”Ke baki abinci bane.”? A kumbure tace.” Nayi daidai cikina na cinye.” Yace.”Saboda me.”? Cikin tsiwa tace.” Saboda bana bukatar kaci kaje gurin matar so ta baka.” Ransa a bace yace.”Ke zanci ubanki wallahi ni kike d’agawa murya.” Sai ta fashe da kuka tana nuna kirjinta take fadin.” Yaya Khalid ni kake zagi.”? Yace.” Ko zaki rama ne.”? Tana share hawaye tace.”Duk dai wanda ya zagi uban wani nasa ya zaga.” Wani bahagon mari ya kwad’a mata yana huci! yace.” Tuntuni na gaji da zama dake domin Baki da wani amfani a gurina saboda haka ki tashi ki fitar min a gida bana bukatarki tunda baki da mutunci.” Gabanta na faduwa tana kuka take bashi hakuri rufe idonsa yayi yaki sauraranta yace maza ta tashi ta fitar masa daga gida sai ya neme ta. Jamila na kuka wurjajan ta hada kayanta cikin akwati ta yafa mayafi ta nufi gidansu cikin tsananin tashin hankali…….Ajiyar zuciya ya sauke bayan fitar ta ya kulle sashen kai tsaye gurin auntyn nasa ya nufa.
Ya jima a tsaye a kofar falon yana bugu da dai yaga bata da niyyar bude masa kofar sai ya yanke shawarar kiran wayarta nan yaji wayar a kashe takaici kamar ya kashe shi ransa a masifar bace yaje ya lalobo spire key yazo yana kokarin bude kofar falon yafi awa guda kafin ya samu wanda ya bude kofar shiga yayi ya mayar da kofar ya rufe………Kai tsaye bedroom dinta ya nufa ya tura kofar ya shiga tana kwance tana bacci sadidan, gadon ya haye ya janyota jikinsa ya fara abinda yake muradi….Cikin wani irin yanayi na tureshi daga jikina zaune na mi’ke na kunna bedlamp dakin yayi haske, tsira masa ido nayi ina kallonsa zuciyata na wani irin tashi, jikinsa na kyarma yasa hannu zai janyo ni na janye ina watsa masa harara. a sarqe yace.” Kince na tambayi Jamila idan ta amince to na tambaye ta ta amince min da biyan bukatata.” Nace.” Ban yarda ba.” Zaune ya mike da fadin.”Kada fa ki sanya na gwada miki karfina ba zakiji dadi ba.” Mikewa nayi na shiga toilet nai uziri na na fito na kwanta kan Sofa na barshi zaune a gadon yana bina da kallo! Cikin kunar zuciya ya sauko daga gadon ya isa inda take. “Kina so na mutu ko? ki duba kiga yanda hallitata ta fito.” kallon inda yake nuna min nayi na d’auke kaina da fadin.” Bari na kira yarinyar a waya naji daga bakinta.” da sauri yace.”Baki isa ba.” Nace.” Ai dama nasan karya kake kana satar kwana kana kawo min saboda rashin tsoron Allah.” ” Kada ki sake k’aryata ni.” yafadi maganar a kufule. Nace.” To idan kana da gaskiya ka bari a kira ta a tambaye ta mana.” Tsugunawa yayi a gabana a sanyaye yace.” Ko kin kirata ba zata saurareki ba saboda tana cikin fushi.” Nace.”Khalid wallahi kaji tsoron Allah kana azabtar da iyalinka kana kuma dorawa kanka nauyin zunubi.” Ya jima yana kallona kafin yace.”Wace irin azaba nake muku? kuna so na kwanta a kasa ku takani kenan.”? Girgiza kaina kawai nayi Yace.”To mu bar wannan maganar muyi wacce zata taimaka mana.” Nace “Kasan Allah yau kome za kayi ba zaka samu abinda kake so ba bani ma da lafiya ta kaina nake.” A marairaice yace.”Don Allah ki bari nayi ko Allah zai sanya ki samu ciki wallahi haihuwa nake so.” Kallonsa nayi ya wani langwab’e kai sai lumshe idanuwansa yake. ” Kayi hakuri ka bari sai girki yazo hannu tukkuna.” Wani irin kallo yake min fuskarsa ta rikid’e da bacin rai yace.”Saboda kinga ina sonki kike wulakanta ni.” ? Kokarin bar masa gurin nake ya rike min hannu “Ba zan kara tunkarar ki da wata bukata ba.” cikin zuciyata nace.” Dama haka nake so.” Hannuna ya saki yaje ya kwanta kan bed komawa nayi kan Kujarar na kwanta ina sauke ajiyar zuciya sosai naji dadin yanda yayi zuciya dama haka nake so ya kyaleni na huta…….Washe gari da safe babu yabo babu fallasa muka gaisa cikin rashin kuzari ya zauna yayi breakfast, yana shiga wanka kira wayarsa dake samar mirror, Ina dubawa naga sunan Ummatu. ajiye wayar nayi yana fitowa na fad’a masa, daukar wayar yayi ya zauna kusa dani……………”Rai a b’ace naji maganarta “Khalid ni zaka tozarta ko? me Jamila tayi maka kace ta fice maka daga gida.”? Yace.” Ummatu ki kwantar da hankali yanzu zan shigo na sheda miki dukkanin abinda yake faruwa.” Tana kuka tace.”Aa ai zuwanka bashi da amfani tunda ban isa na baka umarni ka dauka ba kana so ka tozarta ni ko to shikkenan kaje duniya ce.” Kafin yace wani abu ta kashe wayarta. Shuru yayi da wayar a hannunsa nace.”Me tayi maka da zaka kore ta a gidanka.” ? Hannu ya daga min da fadin.” Ba abinda ya shafe ki bane.” Nace.”Ya shafe ni tunda ya shafe ka.” Tsaki yaja ya mike ya nufi wardrobe kayansa ya dauko yasa yana d’acin rai Nace.”Don Allah duk abinda tayi maka kayi hakuri ka dawo da ita dakinta ina amfanin hakan idan laifi tayi maka bata wannan sigar zaka hukuntata ba tunda kaga ‘yar uwarka ce.” Uffan bece min ba ya kwashi wayoyinsa da key na mota ya bude kofa ya fita ya barni da mamaki………..Baito har kofar Gwaggo ta shiga ta dinga zazzaga masifa Gwaggo tace.”Baito ni dik abinda yake faruwa bani da labari amma kuyi hakuri dukkaninmu mu jira zuwansa domin muji laifin da tayi masa. Baito tace.”Bayan daukar kwanan da yake yana kaiwa Jikarki duk hakan be isheshi ba sai da ya koreta to wallahi daku da malamin dake muku aiki sai munyi maganinku.” Gwaggo tace.”Baito kece kika yarda da shirka da surkulle ni Allah kadai na gazgata saboda haka dik abinda zakuyi kuje kuyi.” Baito na numfarfashi ta fita daga gurin…Ita kuwa Gwaggo hawaye kawai take sharewa tana jin bakin ciki da takaicin abinda yaron yayi………Kwata-kwata Ummatu kin sauraran uzirinsa tayi ta rufe shi da fad’a Baito tana taya ta Jamila tazo ta fada musu karya da Gaskiya sun yarda da maganarta sosai al’amarin yayi masa ciwo ya kuma kudiri aniyar sakin yarinyar tunda ta zame masa annoba….Koda ya shiga gurin Gwaggo ma rufe shi tayi da fada tace.”Wannan ai shashanci ne saboda kawai kun samu sa’bani da yarinya sai ka koreta wannan ba hukunci bane.” Yace.”Gwaggo yarinyar nan fa rashin kunya take min sam bata ganin girmana Sa’ida da take da shekaru sama da nawa tana bani girma tana mutuntani amma Jamila ban isa ta durk’usa min ba kullum cikin tsiwa da izgilanci har da zagi ni ba sakaran namiji bane wallahi matakin da zan dauka a kanta dukkaninku ba zai muku dadi ba.” Gwaggo jikinta yayi sanyi tace.”Kai amma yarinyar nan bata da mutunci ashe haka kake fama.” Yace.”Eh hakuri kawai nake da ita a gurin Sa’ida kawai nake samun sasaauci ” Tace.” To ni na zare hannuna a maganar duk hukuncin da zaka yanke kaje ka yanke hausawa suna cewa(Mai daki shi yasan inda yake masa yoyo.”)
Sati guda da faruwar al’amarin Jamila taji shuru babu wani labari tana zaune a gida bata san makomarta ba kullum idan sukayi waya da Ummatu babu wata cikakkiyar magana sai kawai ta shirya ita da kanwarta sukaje har gida suka ci mutuncin Ummatu tas. Al’amarin yayi masifar bata tsoro cikin damuwa ta kira wayar Baito ta sheda mata irin cin mutuncin da jamila tazo tayi mata budar bakin Baito sai tace.” Ai hakan da sukayi shine daidai tunda ke kin zama shashasha kin kasa tan’kawara d’anki sai abinda yake so zaiyi saboda haka ni banga laifin Jamila ba Ke da d’anki kun riga kun ‘bata mana Zumunci dan haka kada ki sake kira na a waya mutukar ba abin arziki zaki fada min ba.” Ummatu a ranar yini tayi cikin tsananin damuwa da tashin hankali, ashe da sauran rina a kaba dan a daran ranar Kawu ya sheda mata da maganar daurin auransa ranar Jumaa mai zuwa, ihu! ta dinga kurmawa kamar zautacciya ta nufi kofar Gwaggo tana kuka na fitar hankali….A lalace Gwaggo ta kalleta tace.” Yanzu ke Rabi wannan ba abun kunya bane a gurin ki saboda kawai za’ayi miki kishiya kike kuka sai kace wata k’aramar yarinya.” Tace.”Gwaggo me nayi miki kika tsaneni yanzu ace Mijina zai kara aure amma a munafurce ni ba za’a fada min ba.” Tace.”Ashe nice munaf*cka tunda ni nasa shi yayi auran.” Tace.” To Gwaggo me yasa zaki sashi yayi aure bayan kema baki ta’ba zama da kishiya ba sai shi.” Tace.” Allah ne bai nufi mijina da ya kawo min abokiyar zama ba saboda haka idan zakiyi misali ki daina had’ashi dani Ibrahim zaiyi aure babu mahalukin daya isa ya hana abinda Allah ya hukunta.” Ummatu tasa bakin hijabinta ta share hawaye ta bar kofar dakin cikin tsananin damuwa da tashin hankali……………..Tun daga ranar daya nemi ni naki bashi hadin kai bai sake ba tsakanina dashi ido ne idan magana ta kama muyi ya shige ya tafi harkokinsa………..Ana ya gobe daurin Auran Kawu Hauwwa tazo take sheda min cewa sun tsayar da ranar daurin auransu ita da Yaya Aminu sosai nayi farin ciki da jin hakan, da zata tafi ta dinga tsokana ta da uwar biyu nace.” Wai ke waye yace miki ciki ne dani.” Hararata tayi da fadin.” Kada ki rainawa kanki hankali mana gashinan duk kin sanja kammani kinyi haske da ki’ba goshinki sai kyalli yake.” Murmushi nayi nace “Wallahi Hauwwa kunya nake ji wai yau nice dauke da cikin yaron nan Har bana so na fita jama’a su gane gashi gobe Kawu zai daura aure ina jin nauyin zuwa gidan sabida surutun mutane.” Tana dariya tace.”To menene abin kunya Yaro da babban duk aiki d’aya suke dan Khalid yayi miki ciki ba’ abun kunya bane abun alfahari ne.” Nace.”Hakane.” Sallama mukayi da juna na koma cikin gidan da tunanin halin da Gwaggo zata shiga idan ta fahimci cikin da nake dashi……….Washe Da sassafe muka shirya ni dashi muka nufi gidan.Gwaggo taci kwalliya da atampa super tayi lalle a kafafu da hannaye idonta rambad’e da kwalli dauri kuwa har gaban goshi Uwale na kusa da ita suna hira…..Khalid daga bakin kofa ya tsaya suka gaisa ya nufi massalacin da za’a daura auran……..Tun kafin na zauna Uwale take rangwada bud’a tana kallona Gwaggo kuwa sai murmushi take tana gyara min gurin zama na zauna da kyar tace.”Sannu ashe haka kikayi nauyi babu labari.” Cike da mamaki nake kallonta tace.”Ga ciki nan har ya huda zani kai alhamdulillhi Allah nagode maka.” Nace.”Gwaggo waye yace miki ciki ne dani.” Tace.”Idona ne ya gane min munaf*cka dake da mijin naki.” ‘Yar dariya nayi nace.”Shima Khalid din be sani ba.” Tace.”Karya kike kina kareshi ne.” Nace.”To shikkenan idan ya shigo sai ki tambayeshi.” Tace.”Ai ba sai kin fada ba yanzu cikin watanshi nawa.”? Shuru nayi ina tunanin watannin cikin.Uwale tace.”Ai kin san cikin fari ba kowane yake iya gane sanda ya sameshi ba amma dai daka gani yayi kwari.” Tace.”Aikuwa dai cikin fari tunda ya huda zani ya fito to da alama daf yake da zuwa duniya.” Uwale tace.”To Allah dai ya raba lafiya.” Cikin zuciyata na amsa da ameen ameen….Nace.”Gwaggo a ina amaryar Kawu zata tare.”? Tace.”Can unguwar gadon kaya ne Khalid ya siya mata gida mai kyau shine uwarsa take bakin ciki yanzu maganar da nake miki ma tayi yaji tana gidansu sannan har gida Jamila tazo ta zageta taci mata mutunci tas.” Nace.”Kai amma banji dadin wannan labarin ba wallahi.” Uwale tace.”Ai duk wanda yace tukunyar wani ba zata tafasa ba to tasa ma ko d’umi ba za tayi ba.”……………..Khalid tun bayan kammaluwar daurin auran ya tafi harkokinsa bai dawo ba sai yamma likis sai da yaci abinci ya samu damar gabatar da sallar magariba………Gwaggo ta kalleshi bayan dawowarsa daga massalaci tace.”Sannu munafiki to abinda kuke ‘boyewa yau Allah ya nuna min.” Ya dinga kallonta yana mamakin maganarta. Ta kalleni da fadin.” Kince shima bai sani ba ko.”? Nace.”Eh mana Khalid ko kasan ina dauke da juna biyu.”? Kamar wani shashasha ya girgiza kansa.” Mafici ta kwada masa da fadin ” Ni zaku mayar shashasha ko.”? Hankalinsa ya shiga yana kallona babu wasa a tare dashi yace.”Yaushe kika samu cikin bani da labari.”? murmushi nayi da fadin.” Tsayin wata biyar kenan.” Ya dinga kallona yana so ya gazgata magana. Nace.”Kada kayi kokwanto domin kai ka kasance mara kula shiyasa baka fahimta ba amma lokatan da nake gudunka da kamshin turaranka yaci ace ka gane abinda yake da akwai.”
Inda nake ya dawo ya fara kokarin daga rigata. na rike hannunsa da fadin.” Me za kayi.”? Kai tsaye yace.” Gani zanyi.” Gwaggo tace” Bude masa ya gani ya tabbatar.” Kin bude masa nayi ya janyo ni jikinsa ko kunyar Gwaggo ya daga rigar cikina suka tsirawa ido ita dashi Gwaggo ta share hawayen farin ciki a fili tace.”Allah kasa ina da rabon ganin abinda ke cikin nan.” Shi kam hannu yasa ya dauke ‘yar ‘kwallar dake kokarin fitowa daga idonsa yasa hannu kan cikin yana shafawa a hankali a hankali yace.”Gwaggo kinga yaro na a cikin Aunty ko.”? Gwaggo tace.”Eh na gani Jarumi ikon Allah ai yafi gaban wasa ashe da kai zata fara haihuwa duk aure-auren da tayi kaddara ce rabon yana tare da kai.” Yace.”Gwaggo babu abinda zance da Ubangijina da yayi min wannan kyautar.” Tace.”Kwarai kuwa baka da bakin magana amma abinda za kayi ka kara kusanci dashi shine salatin ANNABI MUHAMMAD (SAW) Yace.”Allah ya karawa Annabi daraja da wasila filjannati.” Gabad’aya muka amsa da “Ameeen ya Allah.” Zaune na mike ina gyara rigata yana min wani irin kallo ya janyo ni jikinsa rungumeni yayi tsam-tsam a jikinsa yace.” Gwaggo ina rokon Allah ya dawwamar mana da zaman lafiya a zamantakewar auranmu sannan ina rokon Allah ya azurta mu da zuria masu albarka.” Tana murmushi ta amsa da “ameeen ya Allah Jarumi Amma meye makomar Jamila ne.”? Ajiyar zuciya ya sauke yace ” Gwaggo nasha fad’a muku cewa babu wata mace da zan bari ta wulakanta min iyayena tun ranar dana samu labarin irin cin mutuncin da yarinyar tayi wa Ummatu na datse igiyar aura na da ita taje tayi aure ni na gama zama da ita har abadah.” Gwaggo tace.”Subahanallahi amma gaskiya banji dadin wannan al’amarin ba Jarumi me yasa ka yanke irin wannan hukuncin kana so duniya ta zage mu ko.”? Yace “Gwaggo rabuwa ta da Jamila ita tafi alkairi saboda haka kiyi addua akan Allah yasa hakan shi yafi alkairi.” Tace.”To shikkenan Allah ya kyauta amma yana da kyau kaje kayi bikon mahaifiyarka a gidansu.” Yace.”Babu inda zanje mijinta shine zaije yayi bikon ta idan yana bukatar zama da ita saboda haka kada ki sake sanya ni cikin al’amarin tunda lokacin da sukayi auransu ban sani ba.” Yanda ya fadi maganar ya nuna mata cewa ransa a ‘bace yake. Tace.”Kayi hakuri ba laifin Ibrahim bane tunda shi dai bece mata ta tafi gida ba itace ta tafi.” Yace.”To idan yana ra’ayin cigaba da zama da ita sai yaje yayi bikon ta.” Tace.”Sosai kuwa ai dole ma yaje ya daukota ta dawo dakinta ta zauna kishiya kuma ba akanta aka fara ba.”………….Kwanciya nayi bacci na nema ya dauke ni yace na tashi mu tafi gida Gwaggo tace.” Ka barta ta kwana mana.” Girgiza kansa yayi yace.” Gwaggo mai rabani da matata sai mutuwa ba zan barta ba” Tace.”To ai shikkenan ba sai ka fada min bakar magana ba.” Ni dai dariya kawai nake musu tana fada yana fad’a haka muka fito har soro ta rako mu tana mana fatan alkairi……………Bacci nayi a motar sai da muka isa gidan ya tashe ni da kansa ya bude min mota na fito, ya rike hannuna muka nufi cikin gidan sai tarairayata yake har yaso ya bani tausayi. tare mukayi wanka na dinga Jin feelings na taso idona a lumshe nake kallonsa yana cud’a jikinsa nace.”Kazo kayi min idan ka gama. Yace.”Okey kada ki damu .” Yana gamawa ya daura towel yazo yana min duk sha’awar dake taso masa danneta yayi ya kauda kansa yayi mata wankan kamar yanda ta bukata, yayin da ita kuma nata b’angaran tayi masifar galabaita sai kallonsa take tana lumshe ido da lasar lips hannunta ya rike suka fito daga toilet din gefan bed ya zaunar da ita ya bude wardrobe kayan bacci ya dauko musu yasa nasa ya karaso gadon da nata, da kyar na iya kar’bar kayan nasa a jikina na kwanta ina kallonsa zaune a Sofa yana duba wayarsa a sarqe nace.”Kazo ka kwanta mana.” Yace.”Yanzu zanzo kada ki damu.” lumshe idona nayi ina jan ajiyar zuciya…..Jin shigowarsa cikin bargon yasa na sauke ajiyar zuciya dan motsawa nayi na Juyo ina kallonsa idonsa a rufe bakinsa yana motsi da alama adduar bacci yake…..Sunansa na kira ya bude ido yana kallona nace.”Babynka yana bukatar ku gaisa.” Murmushi yayi yace ” Yanzu zamu gaisa” Dad’i ne ya ratsa ni, dan matsowa yayi ya daga rigar jikina sumbatar cikin ya dinga yana surutai Na dinga murmushi ina kallonsa ya gyara min rigar yana kallona fuskarsa na fitar da annuri yace.”Mun gaisa yace yana gaishe dake.” Dariya nasa nace.”Aa ni ba irin wannan gaisuwar nake so kuyi ba.” Tsira min ido yayi yace” Wace iri kike so.”? Jikinsa na matsa nasa hannuna a kirjinsa da fadin.” Irin wacce kuka kwana biyu bakuyi ba.” Yace.” To ai ke kika hana mu shiyasa na kyale ki.” Da sauri nace.” To yanzu ina bukatar ku gaisa” a kasalance yace.”Kin amince kenan.”? Nace.” Eh na amince ku gaisa sosai da sosai.” Murmushin jin dadi yayi yasa hannu ya janyota jikinsa ya rungume ta tsam-tsam! a kirjinsa suka dinga sauke wani irin numfashi……..
*ALHAMDULILLAHI*
_Jama’a Nan na kawo ‘karshen wannan Littafin mai suna GA IRINTA NAN! Ina rokon Allah ya yafe min kuskurena ladan dake ciki kuma Allah ya had’amu dashi Ina mika godiya ga ‘Yan Vip group godiya ta mussaman a gare ku, dubban masoyana ina godiya ta mussaman nagode kwarai da adduarku Allah ya kara kauna ina alfahari daku💜🤝🏻 Sai mun sake saduwa daku a littafina mai zuwa. NAGODE_
*LITTAFAN MARUBUCIYAR*
*NANA KHADIJA*
*YARO DA KUDI*
*GIMBIYA BALARABA*
*BABBAN YARO*
*MASHAHURI*
*LADADI KWADAGA*
*SADAUKI OMAR*
*NIDA YAYA SADAM*
*TSANTSAR BUTULCI*
*’YAR BANGAR SIYASA*
*DA WATA A KASA*
*MADADI*
*RUWAN DARE*
*KWARYA TABI KWARYA*
*GA IRINTA NAN*
*Ga mai bukatar d’aya da cikin books din sai ya nemi wannan numbers domin karin bayani 08089965176_07084653262* *BINTA UMAR ABBALE*

GA IRINTA NAN!!!🙆🏼‍♀️ COMPLETE - (2024)
Top Articles
Latest Posts
Article information

Author: Horacio Brakus JD

Last Updated:

Views: 6029

Rating: 4 / 5 (71 voted)

Reviews: 94% of readers found this page helpful

Author information

Name: Horacio Brakus JD

Birthday: 1999-08-21

Address: Apt. 524 43384 Minnie Prairie, South Edda, MA 62804

Phone: +5931039998219

Job: Sales Strategist

Hobby: Sculling, Kitesurfing, Orienteering, Painting, Computer programming, Creative writing, Scuba diving

Introduction: My name is Horacio Brakus JD, I am a lively, splendid, jolly, vivacious, vast, cheerful, agreeable person who loves writing and wants to share my knowledge and understanding with you.